Showing 87001 words to 90000 words out of 184891 words
Chapter 30 - DAURIN BOYE Complete Document by Safiya Abdullahi Huguma.txt
Daga wannan tunaninta ya gangaro kan mahaifiyarta,tunanin da rana bata fitowa ta fadi ba tare data yishi ba sau babu adadi,a hankali take nazarin labarin da gwaggo asabe ta bata,tana tuna duk wata kalma guda daya ta cikin labarin bata bari ta subuece mata ba,umminta tayi nisa,nisan da ba'ajin kira,abun ya ratsata shekarun da aka dauka ba wasa bane,wa zata kama?,wa zai taimaketa,wa zai taimaka mata ta dawo da umminta hayyacinta?,a qalla a yanzu ta samu sauqin wasu abubuwan ta wasu fannin,tunda har gashi dangin ummin da dangin mahaifinta suka iya tarayya waje guda lokacin bikinta,abinda iya zamanta bata taba gani ba,kusan yanzu babbar matsalarta shine yadda zata farkar da ummin nata,yadda zata samu soyayyar uwa kamar kowanne d'a
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil,wa ufawwidu amri ilallah,innallaha basirun bil ibaad" ta shiga maimaitawa sau babu adadi kan Allah ya kawo mata dauki,a haka bacci yazo yayi awon gaba da ita.
Bata tashi farkawa ba sai dai dai lokacin sallar azahar,duka sai take jin wani iri babu dadi jikinta saboda bata saba zaman dabe ba haka ba a gida,toilet ta laluba a nan parlourn ta daura alwala ta tada sallah.
Daga can wajen anni kuwa duka hankalinta na wajen aysha har sanda aka kammala abincin rana,da kanta tasa aka shirya komai tacewa mai aikinta ta dauka ta kai mata,karba amal tayi ta wuce da shi don tana son sake tabbatarwa da kanta haka ayshan take?
Tana shirin fita daga kitchen din haidar ya shigo,baya ta danja kadan ya samu ya shigo din saboda tasan halinshi sarai,haka nan yaqi jininsu batasan dalili ba,saidai dalilin kusa yayi shige dana khalipha ne,a sanda dukkan abinda ke faruwar ya farun haidar nada dan sauran wayo,yana tuna wasu abubuwa daga ciki,yana da zuciya sosai shi yasa shima ya kasa mantawa,dalili kenan ma da sukaqi zaman gidan gaba daya da aka tashi hidimar bikin,suka koma gidan wani abokinsu shi da mus'ab dake bayan layinsu.
A ladabce kaman yadda suka saba ya gaida anni
"Ina mus'ab ne?,ai an gana bikin sai ku dawo gida hakanan ko?"
"Yau in sha Allahu....munyi missing dinki anni..." Murmushi kawai tayi tana dubanshi sanda yake duba abinda aka dafa,donshi ba daga nan ba wajen son abinci musamman mai dadi,kusan halayensa suna mata kamanceceniya dana khalipha.
Sanda ta shiga tana zaune saman abun sallah data samu kan hannun kujera,da murmushi kan fuskar ayshan ta amsa mata sallamar,amal din ta qaraso ciki idonta na kan ayshan wadda,ranta yacu gaba da suya irin na kishi gami da fargaba,lallai adazune ma bata kalleta sosai ba qila saboda kada wani ya gano kallon qurillar da take mata
"Ya bakici komai ba?" Amal din ta fada tana bubbuda abincin,murmushi ta sakeyi
"Naci mana"bata sake cewa komai ba don bata jin zata iya sake cewa din ta aje mata wancan kwandon ta dauki dayan ta fice,sai ayshan ta bita da kallo saboda ta fuskanci kaman ta dan sauya,gabanta ya fadi taji babu dadi a ranta,wataqila taji rashin dadi ne saboda bata ci wani abu ba a dazun,ita kuma taci iyakar cikinta kenan,bazata so ta soma bata musu ba daga kwana daya tak cikin gidan,saboda haka ta sauko ta zuba abincin cikin plate,ita kanta tasan ba zata iya cinyewa ba amma haka ta dinga cusawa har sai data ji tana son yiwa kanta illa sannan ta rufe.
Ba dadi haka cikinta yayi mata,hakan ya saka ta tashi ta soma dan kade kade a falon da goge ko zai zazzage,abinka da wadda ta saba sai kawai ta zarce da shara,ta gyara falon sosai duk da ba'a hargitse yake ba,amma komai nason gyara take ya sake kyau da qyalli,sanda ta gama uku ta gota,sai ta sake alwala ta kuma zama tana jiran sallar la'asar,ita irin wannan zaman sam bata saba da shi ba,shi yasa take jinta kamar cikin kurkuku.
_Ya Allah ka rabamu da sharrin mutum da aljan_
*_ZAFAFA BIYAR NA KUDI NE,IDAN KIN GANI DON GIRMAN ALLAH KARKI SHARING,LITATTAFAN SUNE KAMAR HAKA_*
*DAURIN BOYE*
_SAFIYYA HUGUMA_
*WUTSIYAR RAQUMI*
_BILLYN ABDUL_
*BURI DAYA*
_MAMUHGHEE_
*SAUYIN QADDARA*
_HAFSAT RANO_
*KAIMIN HALACCI*
_MISS XOXO_
*GA WANDA KEDA BUQATAR SAYENSU SAI YA TUNTUBI WANNAN NUMBER*
08030811300
*KO KUMA*
07067124863
*DB*
31
Ana gama sallar la'asar mai aikin anni tayi knocking qofar,bata tambayi waye ba don tasan koma waye dan cikin gidan ne
"Anty....anni tace in duba mata lafiyarki" murmushi tayi tana jin dadi har cikin ranta,ganin ta sake samun dadin masoya a fadin duniya
"Lafiya lau...ko zaki yimin jagora na koma ciki?"
"Babu damuwa" itama ta amsa sauqin kan aysha na burgeta,takalmanta kawai ta zira ta maida qofar ta rufe kamar yadda ta sameta tabi bayan mai aikin suka jera
"Anty meye sunanki ne na gaskiya"
"Aisha sunana....zanfi jin dadi idan kika kirani da shi" bako ta kama sannan tace
"Wane mutum...uwar masu gida ce fa,ni na soma sunan anni kenan ai" murmushi aysha tayi har cikin ranta taji dadi,haka suka ci gaba da takawa raliya na sakowa ayshan hira jifa jifa.
A falo suka tadda annin,da fara'a take kallon aysha
"Raliya karkicemin tasota kikai"
"A'ah wallahi hajiya...ita tace min zata taho"
"Auho....shikenan to,tafi ki qarasa aikinki" wucewa kitchen tayi yayin da aysha ta zauna qasan carfet kusa da annin,annin ta lura kamar dabi'arta kenan,batayi mamaki ba duba da yanayin halayyarta da rayuwar data taso,zataso ta saki jikinta da ita,ta dinga jinta kamar mahaifiyarta
"Aishatu ya zaki zauna a qasa?,na gaya miki nan fa kamar gidanku ne" murmushi tayi kanta a qasa ta girgiza shi
"Nan ma yayi na gode"
"Kinqo sakin jikinki dani har yanzu 'yata,bana son ki dinga kunyata,so nake ki saki jikinki kamar khalipha kike a wajena"
"Na gode" ta furta a hankali tana mamakin sauqin kai da son jama'a irin na annij,duk da dukiyar da suke da ita amma sam bata ganinta.
A hankali anni ke jan aysha da hira duk don ta saki jikinta,saidai maganarta bata wuce eh ko a'ah,a haka amal ta cimmasu,zaman nasu sai ya dan taba ranta,da dane ita annin zata nema,amma gashi tun ba'a je ko ina ba kwana daya kacal annin ta soma sauya sheqa,hakan ya sanya tayi shuru bata fiya sakawa hirar tasu baki ba da yawa,duk da anni na sakota,saita dauki remote kawai ta canza tasha,saidai rabin hankalinta na kan hirar tasu.
Biyar da rabi na yammaci ya dawo gidan,da sallama ya shigo parlour din dukkansu suka amsa masa,idonshi ya sauka akanta,yadda take zaune a darare ya kalla sannan ya maida dubanshi ga anni,itama shi take kalla tare da yi masa sannu,ya samu daya daga kujerun ya zauna yana zare takalmin qafarsa yana dan cije lips saboda yadda yaji yatsunsa sun riqe,dora qafarshi yayi saman daya cinyar tasa yana lanqwasa yatsun nashi,a sace aysha ke kallonsa,abinda ta karanta cikin qanqanin lokaci kamar shine jigon gidan,bata taba ganin mahaifinsa ba hakanan bata taba tambayarsa ba game da mahaifinsa,sai taji kamar bata kyauta ba,yasan komai game da rayuwarta,ya damu da komai nata amma itabtaba taba karar tambayarsa komai nasa ba,duk da cewa ta sani a sannan data tambayeshin ba lallai ta samu gaskiyar abinda take son ji ba,tunda ta sigar daya zo mata daban,haduwar tasu tazo ta wani bahagon yanayi,bayan daurin boyen daya qulla yazo da shi a haka da fuskar daba tasa ba,har yau tana mamakin me yasa ya aikata hakan kuma tana son taji dalili,a sacen ya dubeta shima yana jin rashin kyautawarsa na wuni guda ya kamata ko sau daya ya kira yaji yata wuni a baqon guri,sai suka hada idanu,dukansu kowa ya janye idonsa daga dan uwansa,yaci gaba da matsa yatsunsa sannan yave
"Ya kika wuni ya baqunta" anni ce ta amsa
"Takwarata kam akwai baqunta,har yanzu ta kasa sakin jiki muyi hira" sake satar kallonta yayi,iya zamanshi da ita yasan cewa ba kasafai taje iya buda baki tayi hira ba,murmushi kawai ya yiwa annin a matsayin amsa,ido suka hada da amal,ya dan jefa mata harara ya kauda kai,tasan me yske nufi yswi jinin tayita kallon nan nashi,sai ta basar kamar bata gani ba
"Ya khalipha wannan ai aikin amarya ne ko" amal ta fada taba son kota yaya khliphan ya kulata,Allahvyasa anni na amsa waya bata ji me ta ada ba,tsuke fuskarshi yayi kadan,ya fuskanci sassaucin da taga yana matan ta dauka wani sauqi ne,take ta shiga taitayinta,sai ya miqe yana cewa anni
"Zan shiga na watsa ruwa"
"Ba laifi...saika fito,abinci fa?"
"A kawomin anni na gaji bazan iya fitowa ba inajin sai sallar magariba"
"Allah ya nuna mana" ya amsa da amin ya dauki socks dinshi ya fice a parlour din.
Amal ce ta miqe da hanzari ta shige kitchen ta hado dukkan kayan abincin ta fito da shi,dubanta anni tayi,ko zata qyalesu akan komai banda wannan,daga daren jiya zuwa wunin yau taga matar autwn khalipha tattare da aysha,ta gano haske da albarka mai tarin yawa tatare da ita,saboda fadar ma'aiki annabi muhammad S A W da yace"ita kunya dukkaninta alkhairi ce"duk inda kaga kunya to akwai alkhairi biye da ita(qalubale gareku 'yammatan wannan zamanin da suka watsar da al'adar kunya da akasan diya mace da ita,da kin nuna dabi'ar kunya take sai a fassara hakan da cewa rashin wayewa ce take damunki,to ki sani ita kunya ado ce a wajen diya mace,kai ba yammata ba har wasu matan auren yanzu ba ruwansu da kunya,duk mace macace,hakan ita take maida kanta gold ko kuma juji idan taso,ita ke saiwa kanta mutunci ko akasinsa,Allah yasa mu gyara ko ma samu dacewa amin),to amma kome zatayin tasan sai tayishi cikin hikima,dole ta shiga tarayyar khaliphan da aysha ba tare da sun gane ba,dole tati wani abu akai
"Ai daga yau Allah ya hutassheku amal,tunda tsohon tuxurun yayan naku yayi aure,baiwa aysha ta miqa masa kawai" har cikin ranta bata ji dadi ba,amma ba yadda ta iya haka ta miqa mata,tasa hannu ta amsa.
Cike da fargaba ta tura qofar gami da sallama,tsit falon yaje alamun ba owa ciki,saitayi tsai tana tunanin inda zata aje kayan kada tayi ba dai dai ba,qarar bude daya daga cikin qofofin falon yaja hankalinta,khalipha ne ke fitowa daga dakin,boxer ne a jikinsa da singlet da alama baiyi zaton samun mutum a falon ba,don ruwa ya fito dauka,da hanzari ya koma ya dan tura qofar sannan yace ta aje saman tebur,ta jira fitowarshi,jikinta na dan bari tayi yadda yace
din,muqulli ya sanyawa qofar ya cire kayanshi ya shiga wanka.
Kusan awa guda kafin ya sake fitowa cikin shigar qananan kaya,ba qaramin kyau sukayi masa ba,sai qamshin turare mai sanyi ke tashi daga jikinsa,turaren yakai mata ko ina saidai ta kasa daga ido ta dubeshi,har ya zauna qasan carfet kaman yadda ya sameta,tayi zaton abincin zai fara tambaya sai taji yace
"An kawo miki kayanki....ki duba idan akwai abinda babu saikiyi magana...babu baqunta ba nauyin baki....kinga anni ta soma damuwa da rashin sakewarki,bana son kuma ta zargeni,kiyi qoqari ki zama normal"
"Toh..na gode" ta fada tana wasa da yatsunta,kallonta yake yana karantarta,ya lura halayyarta kenan,sai ya dinga kwatanta yaya take iya zama da asma'u,mai surutu rawar kai wulaqanci da isgili
"And..." Sai kuma ya danyi shuru sannan ya dora
"Bakisan komai a kaina ba,baki taba kuma tambaya ba,duk da may be baki da interest ne akai,amma ya zama dole for now kisan wasu abubuwan,ni ne d'a na fari wajen anni,ina da qanne guda uku,maza biyu mace daya...saidai macen Allah yayi mata rasuwa" ya qarashe maganar da wani irin tune wanda ke nuna akwai abinda ya soki zuciyarsa
"Allah yayi mata rahama" ta furta itama tana tuna nata mahifin
"Amin ya Allah....mu hudu ne a gidan saidai bamu hudun muke zaune ba,akwai cousins dina yaran yayye da qannen mahaifina 'yammata dake yawan zuwa,yawancinsu suna da manufarsu ta zuwa,daga yanzu kuma zuwa kowanne lokaci zaki iya ganin wata ko wadansu sunzo,main point din shine,bana so ki sake da kowa don banson raini,banson kiyi hira da kowa ki gaya mata matsalarki ko wani abu daya shafeki ko ya shafi rayuwarki,and bana so ki dinga nuna rashin sabo ko baqunta tsakanina dake,let pretend like husband and wife that r loving each other....ina fatan kin fahimta?"kai ta gyada mishi gefe daya na zuciyarta tana tunanin wanne DAURIN BOYE ne shi kuma tsakaninsa da danginsa
"Idan lokaci yayi xaki san komai" ya furta kaman yasan me take qissimawa ranta,tunanin ta katse ta gabatar masa da abincin,ta zuba masa komai ya fara ci yana sauya tashar t.vn dake ci zuwa wata wadda kusan duka labaran kasuwanci suke.
Baiyi nisa da soma ci ba ya dubeta ta gefan ido,baisan ko taci abincin ba ko bata ci ba,saidai baisan ta yaya zai tambayeta ba,baiso taga kaman ya takurata,amma sai yakejin idan bai tambayetan ba kamar bai sauke nauyin daya daukowa kanshi ba
"Kinci naki ne?" Kai ta gyada masa bayan ta dan dubeshi kadan tana jin dadi cikin ranta,yau wani ya damu da cin abincinta,taci ko bata ci ba,kalmar da bata taba jinta daga bakin wani nata ba,shuru yayi bai sake magana ba,baici da wani yawa ba taga ya ture,ya tsiyayi wani ruwa mai dumi wanda batasan na meye ba don bai kama da ruwan shayi ba yasha,bedroom ya koma ya sake dauro alwala,ya fito yana goge hannayensa da suke da lemar ruwa da handkherchief
"Zan fita sallah...ki jirani idan na dawo zamu fita dinner,haka al'adar gidan take" kai ta gyada masa ya saka kai ya fice.
A inda tayi sallar magariba taci gaba da zama,duk jikinta bata jin dadinsa saboda ta riga ta saba da wanka sau biyu,gashi tun kayan jiya ne a jikinta bata cire ba bare ta sake wani wankan,kayan nata da yace an dauko bata gansu ba da ko kayan saita sauya,sai da aka idar da sallar isha'i taji shigowarsa yana waya,ta lura yana da yawan mu'amala da waya,sai daya gama sannan ya dubeta kadan ya kau da kai
"Wadan nan kayan basu isheki ba hakanan,ina tunanin tun na jiya ne ko?" Ya fada cikin basarwa yana ci gaba da latsa wayarshi,kunya taji ta dan kamata,yanzun haka sai ya tsammaci ita din qazama ce,sai ta rasa abun cewa
"Ina tunanin ba haka amare suke ba washegarin randa aka kaisu,let me ask" ya fada yana lalubar wata lambar a wayarsa,bugu uku ta shiga suka gaisa sannan ta jiyoshi yana tambaya daga can bangaren aka bashi amsa
"Thanks" yace yana kashe wayar
"Ce mishi akayi ban sani ba da zai tambaya" ta fada a ranta.
Bai ce da ita komai ba ya sake kiran wani layin,magana yayi da batafi ta second ba ya kashe,yana tsaye yana ci gaba da latsa wayarshi akayi knocking,ya zura wayar a aljihu ya nufi qofa ya bude.
Qaramin akwati ne ya shigo da shi baby pink da adon golden me azabar kyau da daukar ido,gabanta ya aje yana gyara hannun rigarshi yace
"Ki shirya sai mu fita,kina iya using bedroom toilet dina" jim tayi kaman ba zata ce komai ba,nauyi take ji tana raya kada dai ace kallon qazama yake mata koko meye?,amma maganarshi akan hanya take bai kamata taci gaba da zama haka ba,ita kanta tasan akwai matsala tunda baquwa take wajen al'ummar gidan karsu zaci haka dabi'arta take.
A nutse ta miqe ta dauki akwatin wanda ya danfi kit girma da kadan ta nufi qofar bedroom din daya nuna mata,cike da baqunta kamar zata tadda wani abu ta tura qofar ta shiga,babban bedroom mai kyau tsari da daukar hankali,kallon farko taji ya bugeta,babu tarkace babu kaye kaye aciki,furnitures din cikin ba wasu masu girma bane medium amma kyansu dole ka kalla ka sake kalla,gadon fes qal a mulmule kaman na amarya,a sanyaye ta aje akwatin saman mirrow don kada ta bata mishi gado,ta bude shi,wani lace ne mai azabar kyau a ciki butter colour,wanda aka yiwa dinkin riga fitted da zani simple,akwai dankunne da sarqa a ciki da abun hannu,zai wani.plate din takalmi dake maqale da mayafi dukka kalar da zasu shiga da lace din,sai body cream da powder da sauran tarkacen kayan makeup duka na kamfani guda,shafa lace din ta sake yi karo na kusan uku,ko baka san kudin kaya ba kaganshi kasan cewa ba qarami bane,jikinta yayi sanyi tana jin shakku cikin zuciyarta,anya ko bata zura kai da yawa ba kuwa?,zama tayi sosai tana ci gaba da kallon kaya,bata iya tuna wata rana guda data saka kaya kamar haka masu kyau da tsada,a qalla ta kusa kashe minti goma kafin ta iya tashi ta debi kayan ta shige toilet din da su,don ba zata iya fitowa ba ta shirya cikin dakin.
A toilet dinma sai da wasu abubuwan suka bata mata lokaci da batasan ya zatayi operating nasu ba,daga bisani ta gama wankan ta tsane jikinta ta saka wadancan,har shafa man duka a bayi tayi ta gyara gshinta,sai data gama ta dawo gaban madubi ta shafa powder ta dan goga jambaki kadan daya qarawa lips dinta colour pink dinsu ya sake fita,ninke wadancan data cire tayi ta maida cikin akwatin,tana shirin rufewa taji knocking,wuri wuri tayi da idanu tana duban mayafin da aka hada mata cikin kayan,sam bashi da wani kauri,jin ana turo qofar ya sanyata ala dole taja mayafin ta yane kanta.
Dubanta yayi sanda ya shigo na tsahon minti daya,kanta na qasa tana rufe akwatin,dagowa tayi suka hada ido saiya basar,yana tuna sanda anty ruqayya ta dauko lace din ta dinga kodashi da fadin zaiyi ma mutum kyau,a sannan shidai kawai yana biye da ita ne,saboda indai ba anni ba bansan ya zai sayawa mata kaya ba,gashi dai maison ado ne da kwalliya amma baisan ya zai saya ba,kodan bashi da 'yar uwa mace,wani abu ya taba zuciyarshi a lokacin daya tuna da hajar,har hakan yasa yanayin fuskarsa ya dan sauya,duk sanda zai tuna da ita da yadda ta tafi ta barsu komai walwalar da yake ciki sai yanayinsa ya sauya
"Mu tafi" ya fada yana fita daga dakin,gaba daya jin dakin yake kaman ba nashi ba,saboda tsahon rayuwarshi ba macen data taba shiga masa daki idan ka dauke anni,takalman ta duqa ta zira a