Showing 21001 words to 24000 words out of 85627 words
zata koma. Da gari ya waye haka Inna ta kama hanya dama tunda taje yakumbo tsahare bata ko kalli inda Inna takeba har ta kama hanyar komawa sumaila.
Koda Inna ta koma gida malam Hamza baya nan, kafin ya dawo harta sarrafa musu gero tayi musu burabusko yana dawowa yaci yayi hani'in data sanar masa cewar INdon tak'i dawowa sai yace. "Kyaleta Maryamu ni kaina na huta da fitinarta taje can karta dawo d'in."
Bayan sati biyu.
Tunani da damuwa da begen son ganin INdo suka addabi zuciyar Abubakar, duk iya yinsa na ganin ya kawar da hakan daga cikin zuciyarsa hakan ya gagara. Ya rasa meyagani a tattare da ita har yakejin irin abinda yakeji cikin ransa da gangar jikinsa, yasan duk lokacin da asirin zuciyarsa ya fito fili zaisha wulak'anci gurin Sadeeq dama sauran abokansa. Tashi yayi ya tafi Sumaila kauyen na sani direct babu wanda ya sanarwa.
Yana zuwa zuwa ya tarar su Sadeeq sun tashi daga makaranta yarama sai fitowa sukeyi, samun kanshi yayi dayin gaba zuwa unguwar su INdo ko Allah zaisa ya ganta, amma har Sadeeq ya dawo ya tarar dashi besamu yaga ko kyallin kallabinta ba hakan kuma ya hargitsa ilahirin tunaninsa na Ina zai ganta?
"M twinnie..! Ta6 lallai kaida kace min kaida garinnan saidai in wucewa zakayi shine yau na ganka at this time..?!"
K'ak'alo murmushi Abubakar yayi yana kallon hanya dan befidda ran zai hangota ba. Ganin yadda Sadeeq d'in ke kallansa ne yasa shi saurin cewa.
"Malam Sadeeq nasu INdo, wai kuwa har yanzu kana basu kyautar?!"
"Meza'a fasa twinnie? Itace dai tun ranar bata sake zuwa ba, dana tambayi babanta rannan danaje gidan yace wai ta gudu kauyen su sai randa aka koreni zata dawo kaga kuwa ba rana kenan.."
Daram..! K'irjin Abubakar ya buga besan lokacin da ya furta "what...?!"
*HAJJA CE*👈
[7/1, 5:02 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥
♥♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
_Shafin yau naki ne tawan *HALEEMATU G KHALEEL* (Aneesa didi), Allah yayi miki albarka ya k'ara nisan kwana Allah ya tayaki rik'on Namcy na khadijatu (shareefat) Allah ya azurtaki da miki Nagari ina sonki fisabilillah like H³_💋
Page *11*
Sadeeq ya bishi da kallon mamaki ganin yadda ya furta kalmar tamkar yace masa shine yabar garin ko Mama. Kallansa ya kumayi kafin ya juya yayi hanyar shiga gida yana cewa.
"Kai twinnie bafa Qibd'iyya nace maka ba naga har kana ihu."
Harya bud'e gidan ya shiga Abubakar betaso ba, hanyar gidan su INdo yabi da kallo ji yake tamkar zai ganta amma bako kurarta haka ya k'araci zamansa kafin ya tashi yabi Sadeeq cikin gidan. Lokacin daya shiga tararwa yayi Sadeeq harya shiga wanka hakan yasa shi zama tare da dafe goshinsa sabida tsananin saramai dayaji yana yi. Fitowa Sadeeq yayi zama yayi kusa dashi yana kallansa soyake ya gano wani abu a tattare da d'an uwannasa, Abubakar ya d'ago ya kalli Sadeeq ganin yana mai kallon tuhuma yasa shi wayan cewa ta hanyar cewa.
"Twinnie wai yaushe zakuyi hutu ne?!"
Sadeeq ya mik'e tare da janyo singlet zai sanya yace "kasan ba'a fiyeyin hutun maulud ba so kawai sai term ya k'are ni yanzu mafa na farajin dad'in makarantar sabida suna bani had'in kai yanzu shi yasa na dena neman transfer."
"Oh idan na fahimta kana nufin kace dama Humaira ce ke baka matsala duk fad'in makarantar ko?!"
Abubakar ya tambaya yana zaro ido, Sadeeq yafara shafa mai yana cewa, "eh toh idan nace maka a'a nayi kamar kuskure idan kuma nace maka eh toh shima banyi karya ba domin tun sanda ta dena zuwa nake ganin students d'in suna k'ara maida hankali, haka nima ban sake zagin wata ko wani ba, kai banma sake rik'e bulala ba kaga kuwa idanma nace itace matsalata banyi k'arya ba.."
Abubakar ya dafe kai jin Sadeeq yace INdo ce matsalarsa yaji haushin Sadeeq sosai saidai ya danne dan yanzu so yake INdon ta dawo gida bayajin zai iya hakura har ranar da tayanke hukuncin zata dawo yayi yace.
"Amma twinnie a ganina a matsayinka na malami kamata yayi ace kaine ka fara k'arfafawa yarinyar nan gwiwa wajan ganin tasamu wani kyakyawan abun dazai taimaka mata a rayuwarta kuma a matsayinta na mace."
"Kai twinnie kasan kuwa yarinyar nan? Ka manta abinda tace min da addu'ar datayi min, wai ko'a lahira ina kusa da fir'auna. Wallahi a yadda naji zuciya ta a lokacin ko naso in targad'ata Allah yayi malamai suka saka baki na kyaleta."
Ganin yadda Sadeeq yad'auki zafine yak'arawa Abubakar damuwa, babu ta yadda zai iya samun ganin INdo sai ta hanyarsa yau gashi ta kaishi bango yace bazai temaka mata ba. Cikin nuna halin damuwa Abubakar yace.
"Okey naji ni nayadda zan tallafa mata koda dawani abunne nasan wata rana al'umma zasu amfana da ita. Yanzu inason kasanya kaya kaxo muje gidan su muji inda ta tafi."
"Twinnie wai yaushe kadawo me sauk'in kaine? Kodai-kodai so kake ka kiwata ta tun yanzu kafara banruwa?!"
Mtwww Abubakar yaja tsaki dan shi kansa jinsa yake a wani bai-bai, yau ko kiran Qibd'iyya beyi ba sabida zumud'in son ganin INdo.
"Kai meye haka twinnie? Ni kamar ni zan tsaya jiran wannan kurkurar yarinyar, har yaushe ma zata waye tayi kamar yadda nakeson Qibd'iss? Kawai dai ina son mu sami ladane ta hanyar gina mata wata rayuwar sabuwa wannan shine kawai manufata..."
"Ohh toh ai akwai irinta da suke buk'atar hakan m twinnie bawai dole sai itaba, ni wallahi na tsani yarinyar nan garama data bar garin wawuya kawai sai idanuwa kamar na mayu.."
"Shhhhiii m twinnie duk meyayi zafi hakan? Kayi hakuri nitunda nayi niya zan temaka mata insha Allahu tunda kai kayi fushi..."
"Hakan dai yafi.."
Cewar Sadeeq. Sun dad'e suna hira har akayi la'asar zasu tafi masallaci Abubakar yake cewa "M twinnie idan mundawo ina son karakani muje gurin baban ta ko Maman ta dan Allah."
"Ohh wai daman baka manta da zancen ba?"
Sadeeq ya tambayesa yana dariya, Abubakar ya kalli katangar gidan ya tuno lokacin da ta watso mai hijjab da takallmi yayin da Sadeeq ya tuna sanda ta watso mai ruwan k'anzo suka wuce Abubakar na murmushi yayinda Sadeeq ke faman jan tsaki.
Suna dawowa Sadeeq ya d'auka ko mutumin nasa ya manta dan haka yak'i kallon koda gidan su yarinyar, suna zuwa zasu yi kwana Abubkhr yayi saurin dakatar dashi ta hanyar rik'e masa hannunsa yana cewa.
"Ya haka ne twinnie? Ina kuma zakaje?!"
"Oh wai dama baka manta ba?"
"Eh ai kasan ba'a manta yin alheri musamman idan mutum yayi niya."
Sadeeq yace "naji toh karka gayan magana,ke shiga kice ana sallama da malam Hamza."
Yayi maganar yana kallon Nafeesah dake zaune a k'ofar gida, ta kallesu ganin su iri d'aya sak bakinta bud'e haushi ya Kama Abubakar cikin takaicin kallon da take yi masa yasa shi cewa "Ke bazaki kibane kika saka mana na mujiya?!" Da sauri tayi firgit tana susa tace "Ai baya nan yana can wajan aikinsa a bakin hanya."
Kallon Abubakar Sadeeq yayi dan yaga yazai yi amma sai yaga ya wani ta6e baki irin sunyiwa kansun nan amma cikin zuciyarsa kwata-kwata ba haka bane suka juya suna tafiya Sadeeq yace.
"M twinnie muje na kaika inda zaka temaki masu neman temako domin bawai rayuwar INdo ce kad'ai take buk'atar hakan ba, indai kayi niyar temakawan to kazo muje wani gidan."
Mtwwwww Abubakar yaja tsaki ganin yadda Saseeq d'in ke takura masa da zancen wani gidan, shi duk gaba d'aya mafa yafi buk'atar yaga INdon ko zaiji wani 6arin na gangari jikinsa da ruhinsa sun samu sassauci amma Sadeeq ya kasa ganewa ya kuma had'e rai cikin basarwa yace, "okey bari next week zan dawo sai musan abinyi yanzu bari na koma sabida aikin yamma gareni." Yafad'a yasan duk bala'i nan da ranar asabar INdo ta dawo, shi dai Sadeeq be damuba dan dama be d'aukarwa wani aiki ko takura ba bare yasa kansa cikin damuwa, yana yin alheri a duk lokacin da yake da kud'i. Sallama suka yi a bakin k'ofa Abubakar ya tafi yayin da Sadeeq ya shiga cikin gida cike da kewar abokin haihuwar tasa.
Abubakar kuwa tsakanin sa da Qibd'iyya sai hange daga nesa, sam yanzu ya dena ganin kyawunta bare yaji kwarin guiwar zuwa wajanta. Ita kuma ta rigada ta kamu da kaunarsa domin ya riga yayi mata dashen zazzafar soyayyarsa gashi ta dena kula kowa sabida shi, yau kimanin sati uku kenan ta kasa ganokanshi ya rage nemanta ko kiranta a waya bare ya taka yaje gidansu tad'i sam ya dena har abun ya fara damunta.
Kwanaki na tafiya Abubkhr na kuma shiga cikin damuwa da tunani. Ana ya gobe zai koma sumaila kauyen na sani k'aninsa Khaleefa ya shigo d'akin nasu, kwance ya tarar dashi yayi rub da ciki ko shirin tafiya asibiti beyi ba khaleefan ya k'arasa ciki tare da cewa.
"Yaya Habu Abba na k'iranka yana d'aki."
Beko juyo ba ya d'aga mai hannu sannan khaleefa ya fita shi kuma ya mik'e dakyar ya sanya zilaika sannan ya fita yana wani 6acin rai. Kwankwasa k'ofar yayi Abba yace ya shiga, yana shiga ya gaidashi sannan yasamu guri ya zauna abban yace.
"Yauwa Abbakar dama zance Mariya ne, mahaifinta yayi min magana an tambayeta wanda ta tsayar tace kai shine nace toh ya bari nazo naji ta bakinka ya ake ciki."
Gabaki d'aya ya daburce besan lokacin da yace.
"Abba aure kenan fa..?"
Yafad'a cike da tashin hankali dashiga cikin d'imuwa, Abba ya kallesa tare da cewa.
"Eh Abbakar aure tunda ai kaine kaje gidan nasu."
"Amman Abba da an d'an k'aramin lokaci kafin ayi maganar auran nawa zuwa nan da wani d'an lokaci."
"Amman kai Abbakar kasan dai bazan zuba ido kaida d'an uwanka kuzauna har yanzu babu Aure ba? Kuma gashi kai har gidan su yarinyar sunsan da zamanka."
"Eh Abba ai bayi ne baza muyi ba, lokaci kawai nakeso ka k'aramin dan inason tabbatar da wani abu dan Allah..."
"Tom naji zan k'ara maka lokaci aman da sharad'in wanan maganar tamu ta karo karatunka zuwa k'asar Spain dan nariga na samu duk abinda ake buk'ata. Yanzu gobe nakeson kaje abuja zakayi wani signing na tabbatar da tafiyar taka, sai kuma na koma kan Saddiqu shima a sake mai wajan aiki."
A rud'e yace "Abba har yanzu dama kananan da burinka na k'aro karatun mu? Innalillahi."
Ya furta cikin sanyin murya, Abba yace "Eh Ina nan da wanan burin Abbakar Ina matukar kaunar naga kun cigaba a duniya, don Allah kucika min wanan burin nawa dan wata ran kune iyayen k'annanku, sannan nima naji dad'i a tattare daku."
Nan da nan jikin Abbakar yayi sanyi, babu yadda zai yi dole yacikawa Abban su burinsa ya mik'e da kyar yana had'a bango harya koma cikin d'aki.
Kwanciya yayi ruf da ciki ya fara tunanin taya zai iya samu yaga INdo har ya tallafi rayuwarta sannan ya bawa zuciyarta abinci dan yana son ganinta ra'ayul Ayn. Ina zaije yasake ganinta kafin ya tafi, yanzu ya yarda ba shida wani buri sai son ganishi tare da INdo...
*HAJJA CE*👈
[7/1, 5:03 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥
♥♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
_*HASKE WRITER'S ASSO..* wannan shafin na kune yau na bakushi kyauta. Allah ya k'ara had'e kanmu ya kuma k'ara fasaha mai amfani #ana tare all_🤝😍
Page *12*
Washe gari Abubakar ya tafi abuja danyin abinda Abba yasa shi. Tunda kuma ya dawo daga abuja kullum akwai inda zashi sam baya samun zama gashi yayi-yayi Sadeeq ya d'aukar masa amana da alk'awarin nemo INdo ya kula da ita amma Sadeeq yak'i shi adole idan zai tayashi toh saidai ya canza wata amma ba INdo ba, da haka sukayi bankwana baram-baram kowa najin haushin d'an uwansa.
INdo kuwa wayyo Allah tazo saye kauyanci da k'arin abubuwa duk sun dad'a k'aruwa ta zama tamkar 'yar garin duk inda kaje sai kaji labarinta kaf kauyan sun-santa dan akwai shiga jama'a. Da mutum d'aya ne basa shiri wato yakumbo tsahare, sam basa jituwa da juna ko a layin band'aki.
Ranar da lawisa ta haihu kuwa su INdo sune masu jigo, anyi ruwa anyi tsaki tazama tamkar itace me jegon dan ta kanainaye komai lawisa kuwa sai kawaici take bata magana. Ranar suna aka sanyawa yarinyar Raihanatu suna kiranta da Ladi kasan cewar ranar lahadi aka haifeta.
Watan INdo biyar a garin saye ta kuma irin wayewar nan ta karkarar fulani. Jin dad'inta kawai takeyi samari kuwa su tara ne kowa sonta yakeyi suna yi mata kyaututtuka sosai dan da haka take tattara kaya sawa tana kuma siyan kayan kwalliya abin sai wanda ya gani duk bak'in cikin yakumbo tsahare sai dai ta kawar dakai.
Ta manta dasu Inna tama manta dasuwaye malam Sadeeq sam yanzu rayuwarta takeyi babu takurawa...
*BAYAN SHEKARU UKU*
K'arfe hud'u da rabi da minti shida, Sadeeq Salman Haruna ne cikin mota 403 ash color yana bin bayan wata kyakyawar budurwa. Tafiya take cikin nutsuwa da iya bawa k'asar da take takawa hakk'inta, duk da cewar taga ana binbayanta hakan besanya ta waiga ko tayi alamum tsayawa ba har ta shiga kwanar gidansu.
Shima beyi mata magana ba yana ganin gidan data shiga yayi murmushi sannan ya juya kan motarsa yabar layin yana sak'awa da kwancewa ta yadda zai fara tunkarata da kalma mafi tsada da daraja a gurin wata d’iya mace.
Saida aka d'ibi kwanaki hud'u yana bibiyar rayuwar budurwar ba tare da tasani ba sannan. Ranar asabar da misalin k'arfe hud'u da rabi ya dira a k'ofar gidan, yaro yajira yazo yace yashiga ya k'ira masa Fatima Kabir ya'u. Ba jimawa sai ga yaron da wani matashin saurayi wanda zaiyi sa'an Sadeeq d'in sun fito tare, yana zuwa suka kalli juna cikin tsananin mamaki matashin yace.
"Kardai ace twin's d'in dana sani ne? Abbakar ne ko kuma Sadeeq?!"
Dariya Sadeeq yayi tare da bawa saurayin hannu suka tafa yana cewa "cinka da kanka Shamsu kabeer Ya'u dama kananan.?!"
"Hahaha ina nan mana, dallah ka tabbatar min waye a ckinku kasan kud'inne sai a hankali."
Sukayi dariya dukansu sannan yace.
"Sadeeq ne Shamsu ya rayuwa."
Shamsu yace "Alhamdulillahi, gaskiya na dad'e ban sake sanya ku cikin idona ba tun sanda mukayi candy a GSS kwankwaso, ya wai kaine kenan ka biyu sisi na gida."
Shafa kai Sadeeq yayi bayan ya zame hular zannar shi sannan yayi murmushi yana cewa.
"Wallahi kuwa ashe ma k'anwata ce. Anywaya nidai nagani kuma ina so ya za'ayi kenan?”
"Toh ya zanyi tunda kazo kawai zaka jamin raini, k'anwata ce Fateema kuma kayi sa'a this year tayi graduation but gaskiya munan gidan ba'ayi wa mace aure sai tana da ilimin NCE ko Diploma, gashi ita kofarawa batayi ba yakenan?!"
Murmushi Sadeeq yayi cikin jin dad'i domin hakan yayi dai-dai da lokacin dawowarsa daga k'wara state. Cikin rashin nuna damuwa yace.
"Shamsu babu damuwa ni dai burina gidan ku susan dani, kuma a bani dama mufara fahimtar juna tun yanzu."
"Karka damu tunda kana dani babban yaya, wai yanzu wane aiki kake yi..?!"
Sadeeq yayi murmushi tare da cewa "Toh kasan rayuwa babu yadda bata zuwar mawa d'an Adam, da ina teaching ne a wata secondary school amma yanzu ina nan BUK shekarata d'aya da dawowa nan ina lecturing, sai dai akwai wani business danakeyi acan k'wara state hope babu wanda ya rigani Fateema..?!"
Dariya Shamsu yayi tare da sake bawa Sadeeq hannu suka tafa yace.
"Karka damu abokina insha Allahu zaku dai-daita bari ma naje nafito maka da ita."
"Toh godiya nake dad'in aboki a gidan su budurwa🤪." suka kuma tafawa sannan Shamsu ya koma gida. Yana shiga falo ya kalli Fatima dake kwance tana karatun wani novel akan kujera, had'e rai yayi shi a dole babban yaya yace.
"Ke Fatima tashi ki shirya kije waje abokina yana jiranki."
Da mamaki ta d'ago tana kallasan yace "eh ko bazaki jeba ne?!"
Fatima tace "Haba Yaya Shamsu amma kasan dai baba yace karna kula kowa ko..." Ya sake had'e rai sannan yace, "ke! Toh waye baban yanzu a gabanki? Zaki tashi kosai na bugeki, sakarai kawai."
Tashi tayi tana zumburar baki ta kalli Umman su ganin harkar gabanta kawai takeyi yasa Fateema shiga d'aki tana gunguni. Hijabi ta zurma ta fito Shamsu ya kalleta tare da cewa.
"Ke koma ki shafa hosa da janbaki, kinsan ko waye yazo gurinki kuwa.?"
"Gaskiya ni Yaya..." Yayi saurin katseta ta hanyar daka mata tsawa yana cewa, "Baxaki je Kiyi abinda nasaki bane?!" Sake komawa tayi harda hawaye sannan ta shafa hoda tasa coffee d'in janbaki sannan ta kuma fitowa, Shamsu ya kalleta sannan yace "Good girl sauran kuma kije kiyi mai fitsara ko ki gayamai babu dad'i ranki saiya 6aci wallahi domin 6atamana suna zakiyi wuce."
Fita tayi tana kunkuni, a zaure tagan shi suka had'a ido Sadeeq ya sakar mata Murmushi tayi saurin kawar dakai tare da tsayawa ta jingina jikin bango. Jitayi yayi mata sallama ta amsa yayi dariya kad'an ta kuma d'agowa ta kallesa karaf suka had'a ido. Samun kanta tayi dayin murmushi sannan ta gaidasa ya amsa tare da gabatar mata da kansa tana jidai amma batace komai ba sai daya ce mata.
"Ina fatan zaki yarje min nashiga cikin rayuwarki har muyi aure, nayi miki alkawarin kare duk wani hakkinki da kare miki duk wani mutuncin ki burina kawai ki yarda dani."
Samun kanta tayi da cewa "Shikenan na gode tunda har Yaya nane ya baka damar da banta6a tsayawa da wani ba kamar haka."
"Toh godiya nake yiwa Yaya Shamsu, sai kuma yaushe zan kuma dawowa Zarah..?!"
Ya tambaya yana kasheta da salon shi tayi murmushi cikin sanyi, ita kanta batasan lokacin da take maida reply ba. Ya had'u iya had'uwa dan k'irjinta banda bugawa babu abinda yakeyi.
"Nima ban sani ba."
Ta bashi amsa yace "Toh sai wani satin insha Allahu a gaida Umma." Da sauri ta shiga gida yayi dariya yana zuwa mota sai ga Shamsu ya fito yace.
"Kai abokina irin wannan shaf-shaf d'infa wai har kagama siye tane?!"
Sadeeq yayi dariya tare da cewa, "ban fad'a ba nidai, kawai dai dama zuwa nayi na gabatar mata da kaina."
"Hakan