Showing 15001 words to 18000 words out of 85627 words
dan ya amsa. Dubawa yayi sai yaga ansa my twinnie yayi murmushi sannan ya d'anyi baya da ajin sabida hayaniyar da suke yi ya d'aga tare da karawa a kunnansa.
"Twinnie me ya how far..?!"
Sadeeq ya fad'a yana d'an sosa k'eyarsa da k'asan biro, daga can 6angaran Abubakar yace.
"Surprise..!"
Sadeeq najin haka yayi murmushi tare da cewa.
"Kana gate ko..?!"
Abubakar yayi dariya yace "yah kana ina yanzu.?”Sadeeq ya kalli ajin sannan yace "twinnie me kashigo ciki ina aji uku jss 3c nima yanzu zan k'arasa shiga ciki."
"Okay..."
Suka kashe wayar Sadeeq ya shiga hannunsa d'auke da ledar viva yana shiga 'yan aji suka tashi ana gaida shi da k'arfin tsiya dan yanzu ba k'aramin so suke mishi ba, ya ajiye akan teburin sa ba tare daya kallesu ba yace su zauna nan ma suka ce "thank you Sir..." Shima da k'arfin su kamar kuma had'in baki.
Waje ya lek'a ya gani ko ya k'araso yana hangosa ya d'aga mai hannu suka yiwa juna murmushi tundaga nesa har Abubakar ya k'araso suka yi musabuha sannan suka shiga cikin ajin, nan ma yaran suka sake tashi suka gaida d'ayan daya shigo amma kotakan su bebiba ya tsaya suna magana sai Sadeeq d'inne yayi musu alamar su zauna da hannu tunda shi ba yadda zaiyi d'alibansa ne dole ya kulasu.
"Twinnie ga abin zama ka zauna."
Avubakar ya kalli kujerar sannan ya juya yana kallon 'yan ajin sai ya gansu fes-fes dasu hakan ya bashi mamaki ya kuma rasa wadda zai kira ta goge mai kujerar dan bazai zauna a haka ba. Shi duk a tunaninsa ba wad'anda ya sani bane ya kalli Sadeeq yana shafa sajen fuskarsa yace.
"Twinnie congrats an sake ma class."
Sadeeq yayi murmushi tare da juyawa ya kalli 'yan ajin sannan ya kalli Abubakar yace, "twinnie sune dai wad'anda ka sani kawai canjin yanayi aka samu."
"Woww good of you."
"Thanks twinnie."
Abubakar ya kalli 'yan matan ajin kawai ya nunu Maryam Ali ya yafitota, jikinta na rawa ta mik'e ta k'arasa inda yake tace.
"Malam gani."
Mtwww “wai ban hanaku ce min malam vane? Ko kunga nayi kama da teacher?"
"Allah baka hakuri."
Maryam ta fad'a bakinta na rawa, yayi banza da ita sannan yace "daga yau kar wanda ya kuma ce min malam ko sir suna na doctor Abubakar Salman Harun, karna kuma zuwa ajin nan wata tace min malam ko wani sir ku kirani da doctor Abbakar or doctor ASH."
Ajin yayi tsit babu meyin motsi yaja tsaki tare da kallonta yace "Oya tashi ki goge min kujerar da zan zauna."
Da sauri Maryam ta zaro ido jin abinda yace sabida ta tuno sanda yasa INdo ta goge mai da hijjab d'inta, ya zata yi gashi ba'a duba taba yau ta shiga uku zai ja mata.
"Ko baza kiyi vane.?!"
Ya tambayeta ganin bataje tayi abinda ya sanyata ba, hawaye suka zobu mata shi kuma Sadeeq yak'i yin magana jiki a sanyaye tana kuka taje tasa hijabinta ta goge mai tasss sannan ta koma gurin zamanta sai kuka takeyi shi kuma yaje ya zauna tare da d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana d'an kad'asu. Sadeeq ya kalli Abubakar yace.
"Bari sai na fara yi musu inspection."
Abubakar ya kallesa yace "na ina kuma..?!" Sadeeq ya d'auki rular yana cewa "na jikinsu har kyauta nake basu that's why kazo ka gansu neat." Abubakar ya ta6e baki sannan Sadeeq ya tafi farawa wanda har lokacin bemasan INdo na ajin ba, Abubakar yace "okey twinnie duk wani wanda beyi maka wani abunba ka turosa nan gurin." Ya fad'a yana d'aukar wayarsa dan kiran Qibd'iyya yace mata ya sauka lafiya kuma yaji sassanyar muryarta mai sanyi.
'Yan aji najin abinda ya fad'a kowa ya fara duba abinda beyi ba dai-dai lokacin da Sadeeq ya k'arasa gurin bencin da yake farawa kuma INdo ce a farko dan haka kafin ta gama duba abinda bata yiba har ya k'arasa.
"Ohh my God..! Wacece wannan kamar Aisha?"
INdo ta dashare baki kamar gonar auduga yayin da 'yan aji suka bita da kallo shi kuma malam Sadeeq ya saki wani tattausan murmushi ganinta yau tsab-tsab da ita sai dai makeup d'in da tayi ne duk ya cuceta dan duk ta cika fuskar da d'ige-d'igen baki da janbaki sai dai yaji dad'i dayaga tayi wanki yace.
"Toh muga bakin." Ta bud'e mai hak'oran nata ya gani ya d'aga kai sun d'an fi na baya ya kuma cewa "muga kanki." Nan ma ta bud'e da saurinta ya kalla gashin nan yayi d'as da kitso ya kuma kad'a kai domin tayi k'ok'ari sosai lallai hakan yana nuna masa cewar ba k'aramin son a bata kyauta takeyi ba yayi murmushi yana wani sak'e-sak'e cikin ransa kafin yace.
"Toh kinyi komai Aisha muga farcanki."
Sai a lokacin ta tuna sam bata yanke ba sai ta 6ata rai idanunta yayi rau-rau zata yi kuka dan tasan rashin yanke farcen ba k'aramin asara zai janyo mata ba Sadeeq ya kuma cewa "muga farcan ki Aisha."
A hankali ta mik'a mai hakan yasa shi saurin kallanta domin beso ta fad'i tausayinta ya kamashi ba yadda zaiyi dole yace.
"Aisha baki yanke farce ba, tashi kije wajan doctor Abbakar..."
Tana hawaye tace “Amma malam hikadai nefa banyi ba kuma wabillahillaxi mancewa nayi dan Allah kayi hakuri kabani atamfar.."
"Tashi ki fito Aisha."
Tashi tayi tana kuka domin ba k'aramin haushi takeji ba ta k'arasa wajan Abubakar wanda waya take kare a kunnansa shi kuma Sadeeq ya cigaba dayi idan yaga wanda beyi wani abunba sai ya turasa wajan Abubakar, shi kuma ganin yara sun taru a gabansa yasa shi cewa Qibd'iyya.
"M love bari na barki zan..." Ya kasa k'arasawa sabida ido hud'u da sukayi da INdo zuciyarsa tayi wani rass gashi idanta yayi jah sabida kuka sai kawai yaji zuciyar sa nayi mai wani irin zillo ya kashe wayar bema sani ba sannan ya mik'a hannunsa ya janyo na INdo ita kuma ta fara dak'irewa a tunaninta dukanta zaiyi ta fara ihu tana bashi hakuri shi kuma ya damk'e hannun nata sabida yadda yaji shi cikin wani irin mood akanta....
Love u m Fan's👍
*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:53 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥
♥♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
_Shafin yau naki ne tawan daughter'n My Nana Hafsatu Xoxo da Nana Hafsatu Rano wato *BILLY S FARI* wannan mata Allah yayi miki abinda kikeso duniya da lahira, ya azurtaki da 'ya'ya na gari masu albarka. Hajja ce tana sonki kamar yadda take son H², Allah yabar k'auna da soyayya.😍_
Page *7*
Da gudu suke bin ta suna cewa ta basu bokitan su na talla amma tamkar iska gudu kawai take har se da ta shige cikin gida sannan ta dire bokitan ta zauna tana maida numfashin wahala. Inna ta kalleta tana jimamin hali irin na 'yarta ta ganin babu ranar da zata fito ta fad'i INdo bata yi wani abun na zagi ba, wannan dalilin ne yasa tayi niyar zuwa gidan me salati ko zata samu wani temakon da za'ayi mata akan fitinar ta amma baban su ya hana yace shi 'yarsa lafiyar ta sumul.
Kad'a kai kawai Inna tayi ta cigaba da mark'ad'an ta akan irin dutsen nan, INdo na gefe su kuma su Idi sai faman kumbura suke ta bud'i bokitan Ubale me d'auke da awara ta d'ibi guda biyu sannan ta tura mai bokitin nasa, ta janyo na idi shima ta d'ibi wainar rogo ta mik'a mai sauran tana cemusu.
"Naci lada kuma wabillahillazi kuka sake ganina kuka fad'i wata kalmar sai na jamuku asara kuce ba suna na A’isha ba." Suka d'auki bukitan su sukayi waje kowanne da irin kalar wulak'ancin da zai mata a zuciyarsa, Nafeesa k'anwarta ta shigo gidan tana ganinta tayi saurin 6oye kwanon awarar dan karta d'aukar mata.
"INdo rowar jaraba." Cewar Nafeesa tare da k'arasawa wajan INdon ta zauna harda su tankwasa k'afafuwa ta mik'a mata hannu alamar ta sammata.
Mtww "idan ni marowa ciya ce dalla malama kekuma mecece? Ungoni ki matsa ki bani guri." Ta juya tana kallon Inna tace "Inna ga awara idan zaki ci."
Inna ta k'araso gurin tana cewa "Ni wallahi 'yar nan bana son wannan fitinar taki, inda Allah ya temaka ma kun koma makaranta zaku shiga ajin gaba ni banaci na k'oshi da abin fitina." INdo ta fara sosa kai tana kanne ido d'aya sabida jin zafin yajin bakinta tace "Inna wallahi bazan koma makarantar nan ba wata zaku sakemin, wai d'azu harni malam Sadeeq zai cewa tinkiya! Wallahi toh bazan koma ba yaje yacinye makaranta."
"Yanzu kin dena zuwa 'yar nan? Toh wacce kike son a mayar dake ke ba tsayayyan saurayi ba bare ayi miki aure yau na shigesu ni Maryama."
"Inna wallahi bazan koma tsefawa ba na fasa zama likitar dama temako zan dinga yi toh yanzu kuma nafasa suje sunemi wata." Inna ta kad'a kai babu abinda zata iya cewa akai koda baban su ya shigo ma bata gaya maiba bare su d'auki wani mataki haka suka barta kullum bata nan unguwar bata waccen har aka d'iba sati biyu ko hanyar makarantar bata bibare asakaran zata shiga, tsab Sadeeq ya manta da ita domin ya toshe duk wata hanya daya san suna had'uwa.
**
A 6angaran Abubakar kuwa yana matuk'ar son Mareeya har hakan ya fito fili ragowar nurses suka fuskanta, wasu suka hakura dashi yayinda wasu kuma suka d'auki tsana da takura suka d'orasa akan ita Mareeyan suna ganin itace tayi wani kulla-kullan har ya karkata wajanta ya barsu. Sosai suka shaku Abubakar har ya had'a su da Sadeeq awaya suna gaisawa hakan ya sake narkar da sonta a cikin zuciyar Abubakar d'in.
**
Wata ranar juma'a ne Sadeeq dayaje makaranta dama duk juma'a yakewa 'yan ajinsa duban tsabta, yana duba farcensu, hak'oransu, mata ya duba kitso maza kuma aski da kuma uniform duk wanda yafi kowa tsafta zai bashi kyauta. Ashe INdo ta samu labari yau yana cikin dudduba su sai gata ta shigo askwane cikin ajin malam Sadeeq ya kalleta cikin tsananin mamaki kamar aljana uniform d'in nata sharkaf da ruwa a haka tasa su gashi tayi wata mahaukaciyar kwalliya kamar wata ifirituwa ta fara tafiya zuwa bencin su Uwani halilu suka matsa mata har ta kusa kai duwawunta k'asa yayi saurin dakatar da ita ta hanyar yi mata wata razananniyar tsawa ya had'a da cewa.
"Ke meya kawoki wannan ajin? Wacece ke haka? Daga wane sahun aka zakuloki..?!"
INdo ta kalli kan teburinsa taga kayan kyaututtukan da zai bayar sai ta dashare mai jawur d'in hak'oranta domin tunda ta siyi brush da makilin d'in nan bata ta6a yi ba zuwa tayi ta zubesu a gida toh dama ba'a sababa ta k'arasa zama tukunna tace masa.
"Haba malam Sadeeq nicefa INdo malam Hamza."
"Will you shut up...Nonsence, zoki fitar min daga aji wawuya waya kawoki jss 3? Keda har yanzu kina jss 1 shine yau zaki wani shigo min zoki fita kafin na lahira ya fikijin dad'i." Yayi maganar yana nuna mata k'ofar data shigo ransa a matuk'ar had'e, sai ta fara kallon 'yan ajin d'aya bayan d'aya tare da mutsittsike idanuwa taga dai still sune dai 'yan ajin nasu na da amma ya za'ayi yace wai nan ba ajinta bane dan shi munafukine, tokuwa babu inda zata dan nan gwamnati ta tsaga mata dan haka tayi kicin-kicin da fuska wai taga ko zai kuma cewa tafita.
"Ke Aisha ba magana nake yi miki ba?"
Ya fad'a yana k'arasowa bencin da take, INdo tayi saurin mik'ewa tana kallonsa tace "Yo toh malam duk fa k'awayena ne kuma 'yan ajinmu ne ya zakace na fita ina zanje ni."
Yace "Tallah, koba ita kika fiso ba? And bakin ce bazaki sake suwa tsefawa fa yau kuma wane munafuncin ne ya shigo dake da wasu jik'akk'un kayanki kila ma fitsarin kwance kika yi, oya zoki out kina 6ata mana lokaci."
Duk cikin maganarsa babu wacce take k'ona mata rai irin yace tazo ta fita, kuma kallon kayan kyautar tayi kawai sai ta rushe da kuka tana fad'in "Kai malam.. Kai malam, sai da kaga nazo na kusa cinye kyautar nan shine zaka ce natafi ba ajina bane. Toh malam wane ajin zan koma kuma?."
Tsananin mamaki ya cika Sadeeq ganin tana kuka, tunda yake be ta6a ganin hawayenta ba sai yanzu haka kurum kuma sai yaji duk ya tsani kansa domin yasan ita d'in mahaukaciya ce ya kamata ya dinga bata kulawa ta wani 6angaran ko Allah zaisa ta gyara wani abun hakan yasa shi juyawa yanaci gaba da duba 'yan ajin har ya zabo mutum shidan da zai bawa kyautar . Yana zuwa kan INdo tundaga kan uniform ya fara rankwashin ta domin haka yake yiwa duk wanda yake da gyara, INdo tayi saurin dafe gurin tana furta.
"Kai...kakai...kakai..! Malam da zafifa." Yace "ha..bakin muga teeth naki." INdo da taji yace ha bakin yasa ta bud'e mai tamkar zata cinyeshi yayi saurin matsawa sabida wani hamami dayake tasowa daga ciki yana toshe hanci yace.
"Such a stupid hak'oranki zaki nuna min bawai cewa nayi ki hangame min ba."
Hannu tasa ta toshe bakin tunawa da tayi lokacin da sukace bakinta yayi yalo ya kalleta yace.
"Bazaki bud'e ba saina mareki..?!"
Ta d'aga maikai bakinta a toshe da hannunta tace "Malam gara ka marenin da na bud'e ma ballahillazi." Mtwww yaja tsaki dan yasan babu abinda za'a za6a a gurinta, ya kuma matsawa ta baje hancinta tana shak'ar k'amshin turaren jikinsa yace "muga farcenki." Tana jin haka tayi saurin zame hannunta daga baki ta cukwaikuye hannuwan acikin hijjabi tana zaro mai ido ya kuma kuluwa yace "muga kanki..?!"
A hankali ta bud'e shi ya kalla tare da ta6e baki ya bar gurin, akwai kitso saidai ya tsofa sosai dan ko tsagar ba'a gani gashi gashin nata jah ne kamar gashin akuya sai dai da ka ganshi kasan zaiyi laushi domin irin me yalai-yalai d'in nan ne, ta kalli Uwani halilu tana sosa hanci tace.
"Uwani kin ta6a cin gasar kuwa?!" Uwani ta harareta tare da k'in bata amsa ganin haka yasa tayi mata kallon sama da k'asa tana fad'in "ji banza kina jima ina tambayarki." Malam Sadeeq ya d'akko wani yadi na maza ya mik'awa D'ahiru Miko ya durkusa har k'asa ya kar6a sannan yayi godiya malam Sadeeq yace.
"Ku tafawa D'ahiru miko ya samu wannan kyautar ne saka makon d'inkin uniform d'insa sabo ne, yayi aski sannan baya barin farce zak'o-zak'o gashi yana k'amshi babu wari a jikinsa hak'oransa ma sun fara haske.." Aka fara tafawa raf-raf-raf INdo sai k'arayi take da k'arfi har aka gama yi sau biyar yadda ya koya musu INdo bata denayi ba sai da yace "ke inji..!, ya isa haka baki ji yadda suka had'u suka yi nasu ba ne a tare?" Sai a lokacin ta dena amma fa bakin nan a wangale tamkar ita aka bawa yadin.
Mace kuma Murja Ashiru ce ta samu ya bata fallen atamfa biyu itama aka tafa mata still INdo sai da ta zarce har wani dak'irewa tayi sai da Atika bawa ta bige mata hannun sannan ta denayi yace musu "Yau Atika bawa tafi ko wace mace tayi kitso harda kunshi, kayan makarantar ta harda guga babu farce ta yanke itama tayi brush." Aka sake tafawa sam INdo bata iya ba da kowa zai denayi amma ita sai ta k'ara. har ya kammala bama ragowar suka koma suka zauna yayi musu nasiha akan tsabta sannan ya kwashi littattafansa zai fita INdo tayi saurin cewa.
"Malam...!" Ya tsaya cak ba tare daya juya ba tace, "nima wata juma'ar zanyi duka amma ni hadda (shadda) nakeso ruwan bula kaji ko...?!"
Juyawa yayi ya kalleta sannan yace "Toh kiyo amma bake zaki gaya min abinda kike so ba sai abinda nayi niyar bayarwa kinjiko..?!" Tayi shiru bata amsa mai ba yayi tafiyarsa ta zauna tana cewa "kajishi fa, salan kawai a baka abinda bakaso mtww." Babu wanda ya kulata ta mik'e ta koma wajan Atika ta k'arbi atamfar tana gani ji take inama ta tace har ta hango irin d'inkin da zatayi dan taga wani style a jikin Rukayya amarya. Duk wanda aka bawa kyauta sai da taje ta ansa ta gani har ta fara Allah-Allah wata juma'ar tazo itama taci za6e....
*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:53 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥
♥♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.
Page *9*
Still hannunsa na rik'e da nata ya rik'e sai kallon fuskarta yake dan ba k'aramin kyau kwalliyarta tata tayi mai ba, INdo kuma sai k'ok'arin ture mai hannunsa take tana hawaye murya k'asa-k'asa kamar munafiki yake mata magana yace.
“What's your name make up artist..?!”
INdo tayi shiru sai tasa ka hijjab d'inta ta sharo hawayen fuskarta duk bak'in kwallin da tayi kwalliya ya wanke hijjabin daga gaba Abubakar ya kalleta sosai shi har lokacin begano taba domin be ta6a ganinta tsab-tsab kamar yau ba ya kuma cewa.
"Baby ya sunanki ne.?!"
Sai a lokacin INdo ta fahimta ya kalleta ya kuma cewa,
"kinga kin goge kwalliyan naki da kuka ki dena kinji ko? Ya sunanki??"
Ta share majina da bayan hannunta wanda be rik'e ba ai yana gani yayi saurin sakar mata d'ayan hannun ita kuma ta matsa baya tare da cewa cikin kuka.
"INdo malam Hamza." Abubakar ya d'an zaro ido waje kad'an kafin yace.
"Zonan gurin." Ya nuna mata inda yake son ta tsaya da k'afarsa, a hankali taje gurin ta tsaya sai dai idanunta nakan tebur din da malam Sadeeq ya ajiye kayan kyautar da zai bada. Tsaye tayi mai k'ik'am sam hankalinta baya kansa shi kuma ya kalleta yana murmushi yace.
"Woww sunan Mama na gareki, toh amma ba zaki tsugunna ba kika min k'erere..?!" Da sauri ta tsuguna still fuskarta na wajan kayan, ganin bashi take kallo ba yasa shi maida kujerar sa saitin da idanta yake gurin tayi saurin kallansa ya tsuke fuska yace. "Menene baki yi ba aka fito dake?!" Ta cukwai-kuye hannunta tun kafin ta bashi ansa dan tasan mugune a hankali tana turo baki daya sha bakin kwalli a le6an tace.
"Wallahi nayi komai, kawai farce na manta ban cire ba shine malam Sadeeq yace na fito kuma wallahi