Showing 39001 words to 42000 words out of 85627 words

Chapter 14 - MUSAYAR ZUCIYA COMPLETE BOOK by Hajja Ce.txt

Hajja Ce   

14 Sep 2025

44

'yan uwan Humairan suka tafi."

"Oho toh." Suka fad'a tare da shiga ciki suna kiran sunan INdo.

Shiru tanajin su tak'i fitowa sabida gani takeyi kamar idan ta fito zasu gane, yana zaune a gurinsu yaga tak'i fitowa yasan dalili hakan yasa shi ce musu yana zuwa. Kwance ya ganta kan gado ta yaye bedsheet d'in ta cukwikuye jikinta gabaki d'aya ta kudindine ya tura d'akin yana murmushi da mamaki ya hau kan gadon.

Qarah curewa tayi Abubakar ya janyota gaba d'ayanta ya fara warware bedsheet d'in amma sai sake nad'ewa take cikin kasalalliyar murya domin wannan kokawar da sukayi wani shauk'i ne ya dinga saukar mai yace mata a hankali.

"Please Humairah tashi kizo muje sisters d'in Mama ne suka zo, bana son naji sun fara yin k'orafi dake kinji...?!"

Tana cikin zanin gadon tace mai.

"Toh amma kafita sai na fito.."

"Toh nafita kixo yanzo sai ki kawo musu lemo da ruwa."

Yana fad'a ya fita daga d'akin sai dai yana la6e, tashi tayi ta sakko a hankali ta k'arasa gurin madubi tana shafa bakinta ta kuma bud'esa ta kallesa a cikin madubin a fili tace.

"Kai likita da k'azanta kake wallahi irin na film yayi min, amma fa kamar da dad'i hi har wani lumshe ido yake yi."

Dariya ce ta kusa tona mai asiri hakan yasa shi juyawa ya fita falon yana yi gashi ya kasa denawa mutanen dake falon suka bishi da kallo suma suna murmushin kowa da abinda yake kisamawa wanda yasa shi dariyan.

"Abin na masoya ne me ta gaya maka haka kake 6a66aka dariya."

Shafa k'eya yayi yana shirin yin magana sai ga INdo ta fitoh hannunta a saman bakinta sai faman rarraba idanuwa takeyi aunty Siyama tace.

"Aunty amarya taho nan ki zauna."

A d'ard'ar taje ta zauna kafin ta fara gaidasu k'ananun kuma suka gaida ita, had'a ido suka yi da Abubakar yayi mata alamar ta kawo ruwa cikin sa'a ta mik'e taje inda taga an ajiye lemukan da ruwan ta d'ako ta kawo da yawa sannan ta koma zata zauna Abubakar yace.

"Hunairah baki d'akko musu kofina ba."

"Au dan Allah kuyi hakuri kunji bari na d'akko."

Ta fad'a tare da shiga tsalelen kitchen d'inta, kalle kalle ta farayi domin gabaki d'aya ta hargitse ta shagala da kallon dukiyar da aka kashe har ta manta da cewar aikota akayi. Itace ta6a nan shafa can shinshina nan haka ta dinga yi, shirun dayaji ne yasa shi mik'ewa yabiyo bayanta.

Tsaye ya tarar da ita tana ta6a electric oven taga hotan kaza a jiki ya bita da kallo, sam baya ganin aibunta domin yasan dole tayi haka tunda ba ko ina akeda irin abubuwan ba dan ko gidansu Abubakar d'in babu wasu abubuwan da ya zubawa INdo. K'arasawa yayi ta kallesa tare da juya Mai baya yayi dariya yace.

"Ohh su Humayrah daga zuwa d'akko cups sai mukaji shiru."

"Lah wallahi mantawa nayi bari na kaimusu, amma wanne zan d'auka..?!"

Ta fad'a ba tare da tajuyo ba, ya k'arasa tare da janyota jikinsa yace,

"Kibar shi sun ma farasha da jarkar."

"Toh sakarni na fita gurin su."

"Nak'i d'in da wayace kik'i komawa..?!"

Jin ya fara shafar jikinta ne yasa ta faraturesa ya juyo da ita ta kawar dakai sai ji tayi bakinsa a saman k'irjinta INdo ta zabura ya saketa ta ruga falo nan ma suka bisu da kallo ita dai INdo harta zauna jikinta be dena rawa ba a haka har suka gama zamansu sukayi musu fatan zama lafiya sannan suka fita suna tafiya wasu suka zo ranar ma dai haka suka wuni da baki.

Misalin k'arfe goma na dare Abubakar ya shigo gidan, tsit ba kowa sai k'arar inji ya rufe ko'ina sannan ya shiga falon, zaune ya ganta tana kallo ta kurawa TV d'in ido sai dariya takeyi da alama film d'in yayi mata kyau.

Duk sallamar da yakeyi bataji ba sai daya shigo har tsakiyar falon ya kare mata TV d'in sannan taganshi tana dariya tace.

"Kai dacta dan Allah ka matsa kana kare min."

Hannu ya bud'e mata alamar tazo suyi hugging amman tak'i sai ya kashe kallon gabaki d'aya tare da k'arasawa dining ya ajiye ledojin hannunsa. Tashi tayi tana turo baki ganin ya kashe mata gashi bata iya kunnawa ba dama su Hawwa ne suka kunna dasuka zo ya juyo ya kalleta tare da cewa.

"Kin manta ko, da bakinki kika cemin malama ta baku labarin matar da bata bin umarnin miji da abinda akayi mata ko? Shine yanzu nace kizo kiyi min oyo-yo kikaki ba ruwana dake."

INdo ta tuna tayi saurin zuwa gurinsa ta tsaya, ganin haka yasa shi kuma ware mata hannunsa a hankali ta shige bayan ta rintsa idanuwanta ya rungumeta shima. A saitin kunnanta ya tambayeta.

"Kinyi sallah..?"

Kad'a kai kurum tayi sannan nan yace.

"Zo muje muyi wata mu yi addu'a alkairin dake cikin auran mu Allah ya tabbatar dashi."

Tunawa INdo tayi da labarin dasu Uwani suka bata cewar indai taji miji yace ayi sallah akuma ci nama toh ranar aikwai aiki musamman ranar da aka kaika. Janta yayi suka nufi bedroom d'insa dama bata ta6a shiga ba, taga wani shegen gado me shegen kyau bakin ta yak'i rufuwa yace.

"Zokije kiyi alwala."

Tace "Dacta tsaya na gama ganin gadonka wallahi yayi kyau Allah sanya alheri."

"Amin Humaira amma ai shima nakine, duk abinda kika gani na gidan nan nakine ko mutuwa nayi baza a raba gadona dasu ba."

Cikin tsananin murna INdo tace tana kallonsa.

"Dacta da gaske kake nawane.?!"

Kai ya d'aga mata ta fara murna tana godiya sannan ta shiga bayin tayi alwala, tana fitowa shima yayi lokacin ta dawo daga d'akko hijjab, kar6a yayi ya bata sabo tasa sannan yajasu sukayi 2raka'at sannan ya dafa kanta yayi mata addu'a suka shafa. Hannunta ya kama suka koma falo ya kunna musu kallo suna dining suna kallo ya dinga feeding d'inta sai da taci ta koshi ta kora da madara sannan tace ta koshi.

12:49am suka shiga d'akinsa INdo sai hamma takeyi najin bacci, saida ya had'a mata ruwa tayi wanka sannan shima ya shiga ya fito sanye da boxer tayi saurin kawar dakai tana zaro ido gashi ya kulle d'akin itama daga ita sai towel ya kwashe mata kayan ta nema ta rasa.

Turare ya shafa kawai sai na mouth sannan ya nufi gurinta dasu, zama yayi a kusa da ita tayi saurin matsawa shima ya matsa tare da rik'ota da sauri tace.

"Na higa uku ni INdo dan Allah dacta kayi hakuri."

"Shhhh." Yayi mata tare da matsa mata turaren ya ce ta bud'e bakin ya fesa mata da sauri ta tufar da yawu a k'asan bedside carpet yace.

"Humaira ya haka.?!"

INdo kamar tayi kuka tace "yo toh ai ba dad'i."

Dariya yayi tare da girgiza kai sannan ya tashi ya mayar tare da d'akko handkerchief ya goge gurin. Light off yayi musu sannan ya kuma kunna bedside lamp bulb d'in green light ya haske d'akin yayi kyau INdo ta kalli d'akin ta kuma sakin murmushi ita dai yau tana ganin ikon Allah a gidannan. A hankali ya sargafota ta fara zillo towel ya fara kwancewa tace.

"Wai kai bazan sa kaya bane.?"

Cikin sanyin murya Abubakar yace "Eh a haka zaki kwana ko kina son nace bana so amma kuma kisa...?"

Ya tambaya yana shafa gashinta, wani kakkawar yawu ta had'iya tana kad'a kai, ya janyota kan gadon towel d'in ya yaye daga k'asa INdo ta saki k'ara jikinta na rawa. A hankali ya kuma janta jikinsa sannan ya zare mata towel d'in gabaki d'aya ai INdo sai kuka tana cewa.

"Yaya Abbakar karka kalleni in kanawa iyayenka, ni wallahi ka dena ta6ani banasan iskanci..."

Sam bazai iya yi mata abinda take so ba, shi amatsayinsa na likita yasan idan ya barta besamu nutsuwa ba zai shiga tashin hankali ya kuma San akwai illah hakan. A hankali cikin wayewa da iya *TATTALIN MACE* Abubakar ya dinga hillatar da ita yana kuma nuna mata illar hanashin da takeyi a haka ya samu INdo ta yadda dashi ta bashi kanta duk da tasha kuka hardasu majina.

Yana daga kwancen yace,

"Ohh so sorry my wife, please zoki rama kema."

Tana kukan ta k'asa-k'asa tace.

"Meh...?!"

Ai Abubakar besan lokacin daya kyalkyale da dariya ba haushi ya sake zuwar ma INdo ta juya ta fara dukansa yana karewa da hannu...










*HAJJA CE*πŸ‘ˆ
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *βš—βš—MUSAYAR ZUCIYA...βš—βš—*
β™₯β™₯
β™₯
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*πŸ‘ˆ

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*πŸ’‘
(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu


Page *21*

Ganin yak'i denayi mata dariya yasa ta lalubo towel d'inta ta d'aura ta kwanta tare da janyo bargo ta rufa sabida wani sanyi dataji yana shiga cikin jikinta. A hankali ya matsa kusa da ita tare da zura hannunsa ya rungumeta tana jinsa ta kasa yin koda kwakwaran motsi sabida jikinta duk ya lafe a haka bacci ya d'auketa shi kuwa kasa yi yayi se tashi mayayi yaje yayi wanka sannan yayi sallah ya d'auki sallayar ya maida ita inda zai dinga kallon fuskarta. Yana jan carbi yana shafar gashinta tare da shafar fashin goshinta wanda yake d'ansiriri.

Har aka kira asuba INdo bata koyi juyi ba bare asaran zata tashi ya mik'e daga kan sallayar yashiga bathroom ya tarar mata ruwa sannan ya fito, a hankali cikin nutsuwa ya fara tashinta amma babu alamar zata motsa sai ya yaye mata bargon ya fara k'ok'arin kwance mata towel tayi saurin tashi tana rarumarsa tana furta "6arawo..!" ta d'auka 6arawo ne sabida a tunaninta wannan uban gidan baza'a rasa 6arayin dazasu shigo yi musu sata ba. A mamakin ce Abubakar ya kalleta ganin yadda ta cakumeshi tayi saurin sakinsa tare da saurin komawa ta kudindine a bargo yace mata.

"Humairah a mimakwan yin auziya sai ki furta 6arawo? Toh ina 6arawon tashi ki gaya min ko mafarki kikayi..?!"

Tana cikin bargon tace "Allah mafarki nayi kayi hakuri."

"Toh tashi kiyi wankan tsarki sai kiyi sallah."

"Wane iri kuma dacta?!"

Ta tambaya da mamaki yace "na janaba ko bakisan anayi ba?"

Sai yanzu ta gane kenan a makaranta da aketayi musu bayanin wanka haila, wankan janaba da wankan bik'i shi yanzu wanda zata yi shine na janaba ikon Allah dan ita a karatu idan ba practical ba toh theories dakyar suke shigarta.

"Kin iya ko..?!"

Ya tambayeta tayi shiru ya kwanta a bayanta tare da janyota ya matseta, ihu ta farayi sannan tace.

"Toh sani nayi ne, ka gaya min mana."

Yace "Okey kin iya wankan tsarki na haila?" 'Daga kai tayi yace "tashi ki nunin in gani ko dai-dai kikeyi?"

Dakyar ta tashi zaune tana gwada mai ya gyagyara mata sannan yace taje tayi amma ta canzaxani.Ta shiga bathroom d'in da sauri wai dan yana kallonta, tana fitowa sukayi sallah sannan yace tazo su yi karatu, tundaga Nasi ya fara mata har akazo inda ta iya sannan yace toh zai dinga koya mata kullum da asuba indai yana gari.

Gadon ya sake janta ita INdo bata sabayin baccin safe ba hakan yasa tace mai ita kallo zataje tayi ya hanata dole taje suka kwanta, romance d'inta kawai yayi mai tsayawa a wuya dan tana k'ar6ar sakon yadda ya kamata kafin kace mene tuni INdo tayi baci shima ya samu yayi har kusan 9:16am sannan ya farka yana zare jikinsa itama ta farka a kunyace dan ko kallonsa bata iya yi.

"Muje kitchen yau dakan mu zamuyi breakfast."

Kama hannunta yayi suka fita suna zuwa kitchen ya sargafe hannu a k'irji yana jiran yaga ta ina zata fara, itama tsayawar tayi tana kuma bin kayayyakin kitchen d'in da ido.

"Jiya na shigo da slender bari na had'a sai ki soya kwai da tea."

Tace "Toh akan slimba d'in Zan d'ora."

"No Humairah slender itace abinda za'a zuba kalanzir toh ba shi za'a zuba ba gas za'a saka ajona na wannan sai da kin kunna zai kawo wuta idan ya k'are kuma zakiga yak'i kawowa."

Jinjina kai tayi tamkar ta fahimta, shi kuma dayake yasan dawa yake tare sai ya kamo hannunta suka nufi bayan kitchen d'in, a kan idonta yasa dan watarana idan ba kowa ya zama na ta iya. Komawa cikin kitchen d'in sukayi sannan ya kunna cooker d'in sai ga wuta INdo ta dinga murmushi kusan duk shi yayi koma tana kallonsa suna yi yana nuna mata amfanin komai na kitchen d'in komai saida ya nuna mata sannan suka kwashi breakfast d'in suka kai dining.

Yauma kamar jiya daddare shi yayi feeding d'inta taci sannan shina yaci suka koma wajan TV lokacin injinsu ya mutu suka kalli juna yace.

"Muje d'aki ki gani."

Yana rungume da ita yace suka shiga ya d'akko laptop d'insa ya kunna mata kallon yaga alamar tana masifar son yin kallo tana zaune a tsakiyar gado ya d'ora kansa a cinyarta tayi dariya tana kallonta. Hannunta ya kamo ya d'ora akansa tare da cewa.

"Sweetie bazaki dinga shafani ba, please inason ki koyi soyayya fa ni Ina son love."

Sosa mai ta fara yi ya dank'e hannun tare da cewa,

"Bafa haka akeyi ba, haka...!"

Ya fad'a yana rik'e da hannunta yana shasshafa kansa, haka Abubakar ya dinga tarairayar INdo yana nuna mata abubuwan da zata dinga mai cikin ko wane irin abu ko yanayi sai da ya nuna mata irin abinda zata yi mai tun tanajin nauyi da kunya harta fara sakin jiki tana yi mai ba tare da ya nema ko ya nuna buk'atar hakan ba.

Cikin sati d'aya INdo ta kuma wayewa da wasu abubuwan tayi kyau abinta ranar da ta cika kwana takwas ya d'auketa sukaje gida su Mama suka dinga shi musu albarka INdo bajin kai k'annansa duk babu wanda bata wasa dashi sun dad'e Kafin su tafi gidan Sadeeq sai INdo tayi mamaki ganin gidanta yafi kyau sai akayi sa'a bata kwafsa tayi maganar ba.

Sosai suka sha hira shima Sadeeq ya sakar mata fuska Fateema taja ta suka kule d'aki, nan ma sun dad'e kafin Abubakar yace tazo suka tafi.

Washe gari ya d'auketa suka jajje gidan abokansa na nan sannan ya kaita har Munjibur park wayyo farin ciki a gurin INdo ba'a musallatawa duk abinda taga anhau sai tahau shi kuma ya biya duk bata san sai ya biya ba sha'aninta kawai takeyi suka yi hotuna wasu tare wasu kuma ita kad'ai. Sun dad'e kafin suka koma gida INdo cike da murna ya kalleta shima cikin shauk'inta da soyayyarta sannan yace.

"Zo kimin tausa tunda yauma kin gajiyar dani."

Zuwa tayi tana shan ice cream tana mai sannan shima ta bashi yasha wani shauk'i yana fisgarta bata san lokacin da ta kwanta a bayansa ba a hankali ta furta mai.

"I love you mijina."

"Oh my God what did you say? Allah yasa ba mafarki nakeyi ba sweetie d'an jijjiga ni."

Cikin dariya INdo da bugeshi a baya ya juyo tare da janyo ta aikuma ice cream d'in ya zube a saman k'irjinshi yace.

"Aikuwa sai kin lashe shi kuma ki gama ki wanke ni ah bazan yadda ba."

"Ah my key nifa bani ce silaba kai kaiwa jikinka haka."

Ta fad'a tana masa cukali tana d'iban na k'irjin nasa tana sha yanzu duk ta waye bata kyama ganin shima vaya nuna mata akan komai na jikinta.

"Nifa inajin zafin na cukalin nan ki ajiyeshi."

"Toh baki zansa?!"

Ta tambaya kai tsaye shima kai tsaye yace mata "Eh shi nake so."

Harshe tasa ta fara lasa har sai data sud'e tass sannan shima ya faki idonta ya d'akko ragowar na rubar ya 6arar mata a k'irji yace.

"Ashhh sorry bari na ramamiki kema."

Dariya suka saki tare cikin dariyar tace.

"Kaifa kana sane."

Ya rik'ota yasa baki tass shima ya lashe mata daga nan kuma al'amra suka canza. Ana gobe zai koma abuja suna kwance duk sun mak'ala juna suna sauk'e ajiyar Zuciya kad'an-kad'an Abubakar yana shafar kanta yace.

"Humairah banson tafiya na barki anya bazan tafi dake ba?!"

Shiru INdo tayi babu amsa ya kuma janta jikinsa yana d'an shafarta tana biye mai ya kuma cewa.

"Kinyi shiru Humaira ko dama kin k'agara na tafi.?"

Tace "A'a bansan abinda zance ba nima shi yasa nayi shiru fa."

"Okey kema kina son ki bini ko?"

Tace "Eh mana."

Hannunta ya rik'o ya d'ora a k'irjinsa tare da cewa.

"Ina sonki Humaih ina kaunarki ban ta6ajin Ina kaunar mutum ba kamar yadda nake sonki, please kema ki soni koda bekai yadda nake miki ba kinji..?!"

"Toh ai Ina sanka nima."

Ta fad'a cikin sanyin jiki suka rungumi juna da haka sukayi bacci, washe gari tunda asuba suka yi wanka INdo tayi kwalliya irinta kauye tasa zani daban riga ma haka da d'ankwali. Abubakar na shigowa d'akin daga shi sai boxer da singlet ya kalleta yana murmushi yaga kwalliyar tayi mata kyau ya k'arasa ciki yana cewa.

"Woww sweetie gaskiya sai na biya wannan wanka I like it."

"Toh nawa zaka biya domin da tsada...?"

Ta tambayesa tana jan hancinsa, bakin gado ya zauna yana rik'e da kugunta yace.

"Bari kigani."

Kissing d'in bakinta yayi duk ya kwashe janbakin datasa ya matseta a jikinsa yace.

"Allah ya miki albarka matata kafin in dawo Zan samar miki makaranta damun koma saiki shiga."

"Kanason nayi karatu da yawa, nikuma kaga ban iya turanci ba."

Ta fad'a tana shafar sajansa ya sanya kansa tsakiyar kirjinta yana goga fuskarsa a jiki yace.

"Zaki iya kema sweetie ai da koyo akasan gwani, abaya ma dandai baki tsaya kin koya bane amma yanzu kisa aranki cewar kema zaki iya turanci kinji ko..?!"

"Allah yasa toh.."

Ta fad'a yace "Amin sai kuma abani bye-bye dan bazan tafi haka ba"

Rufe fuska tayi ta zauna kan cinyarsa wannan karan itace ta fara sanya mai mouth nata cikin nashi ya k'ara tabbatar da lallai tana d'aukar naganar tana kuma jinta tare da aikata ta a aikace. Sai da ya samu nutsuwa sannan sukayi wanka kamar karsu rabu duk da yace mata kwana biyar zaiyi yaxo yayi weekend amma gani yake tamkar rasa ta zaiyi, itama haka ta dinga cewa ya barta su tafi abuja tare dama bata ta6a zuwa ba amma ya dinga kwantar mata da hankali yace kila ma jibi ya dawo idan yaje ya rage wasu abubuwa.

'Dakinsa saka koma ya shirya duk ta nanik'e mai ya kalleta yace.

"Idan na tafi kiyi tafiyarki gidan Mama ko gidan M twinnie ki zauna kuyi hira zuwa yamma sai ki dawo dan nace dasu Haleema suzo su zauna a nan harna dawo kinji.?!"

"Toh.."

Tabashi amsa ta fesa mai turare

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login