Showing 54001 words to 57000 words out of 85627 words
hannu batare da tayi mai magana ba kawai yaji ta bud'e k'ofar ta fita tana cewa.
"Bari na siyawa Inna barkono da gyad'a ko kwano d'aya-d'aya ne."
Kafin ya harzuka yayi magana ta k'arasa wajan, Sadeeq ya kifa kansa a steering shi kam ya shiga uku wannan wace irin yarinya ce tana ganinsu a tsakiyar titi amma ta 6alle murfin motar ta fita. Idan ta dawo sai ya mareta gobe bazata sake yi mai makamancin haka ba.
K'arasowa tayi wani yaro na biye da ita a baya da kaya ta bud'e gidan baya ya zuba sannan ta bashi naira hamsin ta shiga motar ta zauna tare da kallonsa tana gyara mayafi tace.
"Malam muje na dawo, wallahi kuma da arha shi yasa na siyo mata kwano biyu-biy....."
Bata k'arasa ba taga ya d'ago hannu tayi saurin sunkuyar da kai tare da boyeshi tana sauke a jiyar zuciya cike da tsoro da mamaki. Fad'a ya fara yi mata kamar ya samu student d'inshi har ya gama bata d'ago ba ya figi motar taji sun fara tafiya sannan ta d'ago tana kallonsa.
Kasa yin magana tayi ganin yadda yayi kicin-kicin da fuskarsa dan haka ta share Sa har sukaje k'ofar gidansu. Mutane kuwa aka fara murnar ga INdo ga INdo, wad'an da suka sanshi kuma suka dinga gaidashi yana amsawa da kyar tamkar 6eyi rayuwar garin ba. Kayanta ta kwasa tare da shiga cikin gidan su bata sake fitowa ba, shiru-shiru taji babu wanda ya lek'o shi kuma jira yake su gaida koda Inna koda Malam Hamza amma babu kowa daya fito daga gidan haushi da takaici suka sa shi ya tafi ba tare daya aika ankira wani ba.
A cikin gidan kuwa INdo cewa tayi musu ai ya tafi hakan yasa Inna bataje sun gaisa ba su kuma murnar zuwan INdon yasa basu fita ba bare su ganshi harya tafi.
Har Sadeeq yaje gida be denajin haushin abinda INdo tayi mai ba, lokacin da yaje gidan a cike yake da 'yan uwan Fateema hakan yasa shi juyawa yayi hanyar gidan su ba tare da ya shiga ba dan yasan akwai wad'anda zasu yi mai kallon banza.
Mama na ganinsa hankalinta ya kwanta tace.
"Yauwa Sadeeq har ka dawo?!"
"Eh suna gaida ku."
Ya fad'a yana k'ok'arin zama a kujera, Mama tayi murmushi cikin jin dad'i sannan ta shiga d'aki ta kawo mai abinci, beyi musu ba yaci dan yasan Fateema ba iya yi zatayi ba sabida ciwon marar daya barta tana yi. Yana gama ci ya fita yaje can gidan marigayi ya gano sannan ya wuce gurin abokinsa har sai da aka kira magariba sannan ya koma gidan.
****
Bayan sati biyu Abba ya gaji da sanya mai ido da safe ya kirasa, yana zuwa sai daya shiga suka gaisa da Umma da Mama sannan ya shiga gurin abban. Gaisawa suka yi Abba ya kallesa tare da ajiye magazine d'in hannunsa yace.
"Sadeeq yaushe zaka koma kwaran ne?"
"Abba nan da kwana uku insha Allahu zamu koma."
"Kai dawa?"
Sadeeq yace, "Abba da Fateema mana."
"A'ah Sadeeq ya kamata ka farayi musu adalci tun yanzu, ina son tunda zuwan nan na k'arshe da Fateema kukayi toh wannan karan sai ku tafi da Aisha bana son ta cigaba da zama da auranka acan gidan su ina fatan ka fahimce ni.?!"
Wani irin 6acin raine ya ziyarci ran Sadeeq kansa a k'asa yana danna yatsansa cikin zuciyarsa kuwa abubuwane kala-kala a cikinta. Jin yayi shiru ne yasa Abba kuma yi mai magana Sadeeq yace.
"Abba ai tafiya ta da Aisha garin nan bazai yiwu ba sabida kaga su ba Hausa sukeji ba itama kuma ba yarensu takeji ba dama tanajin turanci ne da sauk'i amma gaskiya tafiya da ita matsala zai jazamin wallahi, nasanta tun kafin Abubakar yasan ta."
"Toh yanzu me kake nufi?!"
"Abba kawai zan samu gida na ajiyeta anan idan yaso sai ta zauna a ciki har mu dawo."
Abba ya kallesa sosai kafin yace.
"Kana nufin ta dinga zama anan har lokacin da zaka dinga dawowa yayi."
Sadeeq yace. "Eh Abba idan ba hakan ba wallahi bansan yadda zanyi da Aisha ba idan mukaje can, gashi ta raina ni sam bata ganin girmana tun sanda na koyar dasu a makaranta."
"Shikenan kafin ka tafi kaje ka d'akkota sai ta tare anan gidan Najib tunda naga ya kammalasa kuma 'yan haya zai zuba gashi dai-dai itane gidan."
Sadeeq yayi shiru tunani yake yana kuma jin takaici, kawai yana zaman-zamansa an d'akko mai wani aikin, yanzu duk shekara sai ya bada kud'in gidan hayar da INdo zata zauna dubu d'ari da talatin. Mtwww yaja tsaki ba tare da yasan ya fito fili ba sai da yaji Abba yace.
"Sorry ko na shiga hak'inka ne??"
Da sauri Sadeeq ya hau kad'a kai alamar a'a sannan yace.
"Toh Abba kuma ni zanje na d'akkota? Na d'auka kawo ta zasu yi.?!"
"Eh toh kuma hakan dai yafi, amma ina son ka k'ara d'aga tafiyar ka har ta tare sannan sai kutafi."
Dakyar ya iya amsawa Abba sannan ya tafi. Yau ya kuma yin Nadamar zuwa tsefawa secondary school domin zuwansa ne yasa Abubakar ya ganta harya aure ta gashi ya mutu shi anbarsa da alak'ak'ai.
Yana komawa gida ya bawa Fateema labari tace Allah ya sanya alkairi, kallonta kawai yayi ya shige d'aki.
***
Cikin kwanaki biyu tal Abba yasa Sadeeq aka kwaso kayan INdo na gidan Abubakar harda wanda duk shine ya siya aka kaisu gidan da INdon zata zauna a matsayin ta na Matar sadeeq. Su Haleema Rukayya da Amina yasa sukaje suka kwaso kayan sawarta suka kai can gidan akajera mata sai dai babu dining area gashi INdo tana matuk'ar sansa dan idan tana kai ji take tamkar tana kusa da sharukhan.
Sadeeq da Umma da Hawwa suka tafi d'akko INdo, hirarsu ce duk ta sashi mance wadda zasu je su d'akko har suka k'arasa k'ofar gidansu INdo wanda yake cike da mutane wai ashe su biki suke yi wannan abun ya k'onawa Sadeeq rai sai kace wani sabon aure mtww.
Sun dad'e a ciki kafin a fito da ita su Uwani sai mata murna akeyi ta baro gidan dad'i zata koma gidan dad'i INdo taja tsaki ita kad'ai tasan gidan da zata shiga dan tasan sam basanta yake ba ta kuma riga ta shirya ma zama dashi a kowane irin yanayi indai vazai hanata abinci da fita yawo ba.
A kusa da Umma ta zauna yayin da Hawwah ta zauna gefensa anata yi musu fatan sauka lafiya bayan Malam Hamza yazo sun gaisa dashi Sadeeq din ya kuma bashi amanar 'yarsa sukaja mota suka tafi.
Tunda suka kama hanyar komawa yaja bakinsa ya tsuke jin INdo ta zage sai subirbid'a hira take tamkar ba amarya aka d'akko ba, yaja tsaki ganin sam babu jan aji a tattare da ita. Suna zuwa a k'ofar gidanta suka sauke ta su Umma suka shigar da ita ganin amarya yasa mak'otanta suka shiga suma dan su ganta.
Har kusan k'arfe shad'aya na dare Sadeeq be shigo gidan ba, gidan yayi matuk'ar yin kyau domin yasha tile's bangon da k'asan ta ko'ina sai dai bekai girma da tsaruwar na marigayi Abubakar ba amma hakan be damu INdo ba domin na iyayanta sam be kama k'afar su ba. Kallon agogo Hawwah tayi tare dajan tsaki tace.
"Wallahi Yaya Sadeeq d'an wulak'anci ne, yasan fa muna jiransa amma bazai zo ba ga mijina can sai waya yake yomin."
"Kinga yayya Hawwah kiyi tafiyarki mu zamu jirashi."
Haleema ta fad'a tana gyara kwanciya akan kujera hannunta rik'e da waya wanda hakan yake nuni da cewar chatting takeyi.
"Ba haka mukayi da Abba ba, cewa yayi karna bar gidan nan sai na tabbatar mai da shigowar Yaya Sadeeq."
"Toh saiki zauna gyara wani auran ke kuma ki 6allo naki ba."
Waya ta zaro zata k'ira Abba sukajiyo sallamarsa a k'asan makoshinsa. Tashi kowanne yayi yana sanya mayafinsa ya zauna a kan kujera.
"Toh Yaya Allah ya bada zaman lafiya."
Yayi shiru yana canza channel Hawwah tace.
"Yaya ina muku addu'a kayi shiru."
"Ke malama ku wuce kutafi gida bana son sa ido."
"Amin yayya Hawwah mun gode a gaida gida da abban siyama sai munzo."
Suka jiyo muryar INdo tana fitowa daga bedroom, hatta shi kansa saida ya kalleta ta gyatsina mai hanci tabi bayansu danyi musu rakiya.
"Amarya kamar karmu barki wallahi."
"Allah sarki Aminatu idan Allah ya kaimu basai ku dawo ba."
"Zamu zo amma da yamma kinga gobe monday akwai makaranta."
Cewar Haleema INdo tace.
"Toh koma dai yaushe ne sai kunzo a gaida Mama."
"Zataji."
Suka fad'a tare da juyawa su shiga mota da driver na jiransu itama ta juya ta shiga ba tare da ta kulle gidan ba. Zama tayi a falon tana wak'ar Nas ya shareta yana kallonsa itama bata kulasa ba domin ba so takeyi ba daman.
"Ke jeki kwanta dare yayi."
Yayi maganar yana gyara kwanciya akan kujera. Itama ta gyara zama tare da d'aukar remote tana murmushi tace.
"Wallahi malam Sadeeq banajin bacci."
Had'e rai yayi domin yana son yin waya da Fateema ya rage mata dare yayi mata alk'awari gashi wannan yarinyar zata samai ido.
"Ke bakya jin magana ko? Kin tashi kosai ranki ya 6aci.?!"
Tashi tayi cike dajin haushi ta shiga bedroom, kan gadon Abubakar datake so shi aka sanya mata a d'aki d'ayan kuma dayake matsayin nata aka sashi a d'ayan d'akin da ake nufin na sadeeq ne. Tana kwance kwai ya fad'o mata ta zura hannu k'ark'ashin filo wayam babu sweet d'insa da yake ajiyewa ta kalli agogo da yanzu suna tare kawai ta mik'e ta koma falon tana k'ik'ifta ido.
"Idan Zan iya zama ni d'aya a d'akin Allah ya tsinen..!"
Sadeeq dake manne da waya a kunnensa yaji da fad'a. A hankali yace.
"Babyna wait zan sake kiranki."
Kashewa yayi tare da juyawa ya kalleta sai kuma ya juya ganinta sanye cikin riga da wando pink and white na bacci sun kuma zauna a jikinta d'as duk da basu kamata ba yace.
"Toh kina son nazo mu kwanta tare ne."
"Malam Sadeeq ko bakazo badai toh kabarni anan."
"No baki isaba ko kuma ki kwanta anan d'in ni saina shiga ciki."
Zama tayi kan kujerar tare da cewa,.
"Tunda waya kakeyi toh ka k'arasa anan idan ka gama sai ka tafi nasan sannan nayi bacci bazanji tsoro ba."
Mtwww yaja tsaki ta kwanta suna kallo duk sunyi jigum har wajan 1:45am duk ya gaji ita kuma sai a lokacin tad'an fara lumshe ido ya zaro wayarsa ya lalibi Fateema amma abin mamaki switch off ya cillar da wayar gefensa yasan haushi taji be kiraba yanzu kila tana can tayi mai fassara kala-kala. A takaice duk anan falo suka kwana, haka har yayi kwanaki biyu a gidanta washe gari Sadeeq da Fateema suka wuce kwara state cike da farin cikin su ita kuma INdo aka turo mata Aminatu ta taya ta zama..
_M fan's kuyi hakuri gobe zakujini shiru zanyi 'yar tafiya insha Allahu dana dawo zamu d'ora I need ur prayers please._
*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥
♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
*Godiya mai yawa tare da d'inbin farin cikina zuwa ga fan's, na gode da addu'o'inku garemu munje Lafiya mun dawo lafi na gode sosai da sosai.😍 HAJARAH (MUM ILHAM) godiya mai tarin yawa a gareki domin kin nuna mana soyayya nida 'yar uwata STYLISH BCH da kuma 'yata IHSAN, Allah ya saka da alkairi ya bar kauna da soyayya Allah ya raya Ilham👏UMMUL MEENAL, BILLY S FARI & OLO addu'atw gareku bazata fad'u ba sai dai ince Allah ya baku abinda kuke nema duniya da lahira domin kuna nuna min sayayya ta hak'ik'a HAJJA CE na sonku fiye da yadda kuke nunan kauna.💋😍💋*
Page *28*
Tunda suka tafi koda wasa Sadeeq be ta6a gigin k'iran INdo a waya ba, bashi dama phone number d'inta bare yace zai nemeta. A 6angaranta itama bata ko tunaninsa tana gidanta hankalinta kwance babu abinda yake damunta. Ranar da su Sadeeq suka cika sati d'aya da tafiya a ranar INdo ta fara fita, kullum tana gidan mak'ota bata nan layin bata can sam bata zama cikin kwanaki takwas mutanan unguwar sun santa maza da mata yara da manya. Yayin da a 6angaran Sadeeq yana son ya kirata tunda yasan tana da hakki akan sa amma baya kaunar ya kirata tayi mai rashin kunya ko ta gaya mai maganar da zai kasa bacci dan ya lura akwaita da shuka magana ba kuma ta barinta indai harka gaya mai toh zata baka amsa hakan yasa ya shareta.
Misalin k'arfe hud'u ta fito daga wanka tana shafa mai tajiyo me tallah a k'ofar gida, cikin sauri ta janyo doguwar riga a cikin wardrobe ta zura tare da d'aukar mayafi ta fita. A k'ofar gate d'in ta tsaya dan sake tabbatarwa da kunnuwanta abinda me tallar yake cewa still taji yana cewa.
"A sai kajin gidan gona matasa..!"
INdo tayi saurin fita tare da kwala mai k'ira ya dawo baya kasan cewar harya wuce gidan nata. Tsayawa tayi suka fara ciniki zata siya har yace zai siyar mata a yadda cinikin ya tsaya, guda bakwai ta siya ta shiga gida ta d'akko mai kud'in ta bashi ya tafi ita kuma ta shiga da 'yan kajinta sai kuka sukeyi iya-iya-iya tana ta murna taje ta zuba su jikin bathroom d'in tsakar gida dama ba'a shigar sa.
A hankali ta ci gaba da kiwonsu tana bayarwa ana siyo mata abincin su hankalinta a kwance su Haleema idan suka zo suyi ta mata dariya ita kuma tace da tayi kud'i saudiya zata tafi idan ta dawo a dinga k'iranta Hajiya INdo kasan cewar sunan ya bazu cikin gidajen mak'ota k'annan su Sadeeq ne kawai ke kiranta da aunty Humairah kamar yadda marigayi ke fad'a mata.
Rayuwar INdo ta cigaba da canzawa sana'o'i take yi kala-kala kajinta ma sunata girma har ta samu sun fara kwai tana tarawa taci takai gidan su Sadeeq sai da Mama tace ta fara siyarwa sannan ta fara.
Da daddare tana kallon arewa 24 Sumayya tana gabatar da shirin tauraruwa taji yadda wata mata da ake hira da ita yadda rayuwarta ta faro tun daga tushe har yanzu da takai wannan matsayin nan da nan INdo tayi sha'awar yin karatu itama tana son ta iya turanci sai dai tayaya zata iya? Sam kwakwalwarta bata gane turanci ba kuma ta iya rubutawa sannan ba ta iya maida hankali wajan koya tayaya zata iya zama tauraruwa kamar yadda taga ana haskilo mata masu aji ana kuma alfahari dasu, tasa a ranta zata fara koyan turanci kamar yadda marigayi yaso tayi kafin mai rabawa ta rabasu.
Sannu a hankali tana jin takaicin Sadeeq nak'in nemanta tun ranar da Aminatu ta guntsa mata cewar ai dan batajin turanci ne yasa Yaya Sadeeq cewa baxai tafi da ita can ba hakan yasa abin ya kuma ba ta haushi tsanarsa ta kuma hauhawa a cikin zuciyarta dama ya saba yi musu wulak'anci tun a tsefawa.
M.M Haruna English academic taji anata tallar makarantar a gidan redion express, ta fara tunanin yadda zata yi ta samu shiga cikin ta.
Tanason zuwa tana tsoron kar da taje ta tarrar da garzazzu wad'anda basa Hausa sai turancin, wai shin ma meyasa aka maida turanci tamkar saukar alkur'ani da komai za'a ce in zaka yi sai ka iyasa? Ga larabci yaran annabi amma ba a dagewa da zuwa islamiyoyi ba'a basu muhimmanci kamar yadda ake baya yaran jajayan farar fatar nan. idan aka kyaro baka iya bama sai ka zama wani hulugu ka zama abin raini da wulak'anci a wajan al'umma.
Zata yi turanci itama za kuma taje ta koya badan wulak'ancin Sadeeq kad'ai ba sai dan wata rana itama ak'irata ayi hira da ita a kuma tambayeta tauraronta tace Abubakar ne,haka zakila kuma a Dama da ita ita duniya wannan burinta ne ba kuma zata canza shi ba koda Sadeeq zai saketa.
"Hello mubassheer, kana Ina yanzu.?!"
"Ina majalisa ya akayi ta samu ne..?!"
"Kai d'an rainin wayo ne, kazo dan Allah zamuyi sirri."
"Toh aunty Humaira gani nan zuwa amma fa zaki ban jarkar kunun aya guda biyu."
"Dallah idan baxaka zo ba sai na kira khaleefa wallahi."
"Sorry Matar broth ina zuwa."
Kashewa yayi yana dariya sannan ya d'auki abokinsa guda d'aya suka tafi gidan a mashin. A falo suka zauna ta kawo musu kunun ayar da zobo da jallop d'in taliya suka ci sukayi dam sannan mubashsheer ya kalli INdo yana cewa.
"Toh meye sirrin Matar broth, tunda kin bamu munci..!"
Sai da ta hararesa sannan tace mai.
"Dallah kaga ni ba surutu na tambaye ka ba, jujun labo store zaka dan Allah ka siyo min farm (form) d'in shiga makarantar M.M Haruna Englihi menene ma d'ayan na gaban ma oho na manta."
"Ah Matar broth wai kina nufin shiga zaki yi..?!"
INdo tace "Eh ya ranka? Zakaje kayi min duk abinda za'ayi na fara zuwa kokuwa wulak'anci zaka yi min Kai ma..?!"
"Ah Matar broth na isa, kawo kud'in toh sai muje muji ya za'ayi, amma tukunna kin sanar da broth Sadeeq d'in zaki fara ne dan karya zo yayi min masifa."
"Kai zaka siyo min ko kuwa na sake wani?!"
"Ah na isa kawo kud'in muje muji ya za'ayi."
"Toh nawa zan baka..?!"
"Haba ki kawo ten thousand muje mu fara manage dasu."
"Kana nufin nawa kenan?!"
"Kai Matar broth dubu goma zaki kawo naga kina min wani kallo."
"Ta6 goma fa kace? Wallahi ku tafi na fasa ai ba dole."
Ta fad'a tana shiga cikin d'aki Mubasheer ya dinga yi mata magiyar ta fara bada ten thousand d'in tace ta yafe bazata ba sai da yace.
"Toh kawo five thousand, dubu biyar wallahi Matar broth kin fiye san Kud'i da yawa, duk sati dubu biyar broth yake badawa a kawo miki ga kud'in zobo ga kunun aya ga gullisuwa da kwan kaji dan Allah mekikeyi da kud'i bayan duk akwai abinci a gidan..?!"
Dubu biyar d'in ta bashi ya kar6a ya k'irga sannan suka tashi zasu tafi INdo tace.
"Dan Allah k'anin miji a rage sa ido, duk lissafin ka yana kaina toh da ba kud'in zaka ci naman dakaci a cikin abinci ne? Ko zaka ci harda vegetables d'in ne d'an rainin wayo."
"Magana ta wuce bari