Showing 42001 words to 45000 words out of 85627 words

Chapter 15 - MUSAYAR ZUCIYA COMPLETE BOOK by Hajja Ce.txt

Hajja Ce   

14 Sep 2025

51

sukaci abincin daya dafa musu suna gamawa sadeeq na yin knocking .

Sai data fara sanyo hijjab sannan Abubakar yaje ya bud'e masa kasan cewar ya hanata zama a haka idan wasu suka zo.

"Aishatu Hamza..."

Cewar Sadeeq cike da zolaya tayi murmushi tare da cewa.

"Malam Sadeeq ya gida..?!"

"Kalau."

Yabata amsa Abubakar yace.

"Twinnie gidana a hannunka please ka kular min da babyna."

"Au wai kana nufin sai an kula da ita? Ta6 Aisha ai ta iya haura katanga bakada case da ita ka kwantar da hankalin ka."

INdo ta turo baki haushinsa ya cika ta Abubakar ya janyo ta tare da cewa.

"Kabari twinnie ai dane kuma kaima ai kayi kana yaro."

Ya kalli INdo tare da cewa "Sorry sweetie karki kulasa Zan dawo na d'aukeki."

Suna dariya dukansu suka fita Abubakar ya shiga mota shida Sadeeq zai saukesa gidan Mama idan yaje, INdo ta zagaya 6angaran Abubakar idonta yayi ruwa murya na rawa tace.

"Allah ya kiyaye hanya."

"Amin." Ya fad'a yana zuro hannu sukayi musabuha yaja motar suka bar gidan, tana share hawaye ta rufe gate d'in tare da shiga cikin gidan. Suna hanyar zuwa gidan Mama Abubakar ya dinga ba Sadeeq hakkin lurar mai da gida musamman ma INdo abin ya dinga bawa Sadeeq mamaki wai yau INdo ce take da matsayi a zuciyar d'an uwansa, koda yake yafishi sanin INdo tun a kauyan Sani.

Bayan sunyi sallama da mutanan gidan ya kama hanya ya tafi bayan ya bugawa INdo waya yace mata ya tafi tayi mai fatan sauka lafiya.

****
K'arfe 11:36am tana zaune a falo tana kallo bama taje gidan Maman ba ganin an kawo wuta, shigowa yayi kai tsaye gidan tana ganinsa ta mik'e da gudu raje ta rungume shi kamar yadda ya sabar mata. Jin jikinsa yana rawa ne yasan ya INdo d'agowa tana kallon kafin k'irjinta ya fara bugawa sam bata gane bashi bane ta sha'afa da kayan dayasa tace.

"My key menene? Inzo mutafi?!"

Wani kallo dataga yayi mata ne yasa hankalinta dawowa jikinsa ta zaro ido tana kallon fuskarsa tace.

"Malam Sadeeq kayi hakuri na d'auka Yaya Abubakar ne."

Da kyar Sadeeq ya samu ya bud'e baki yace.

"Aisha jeki d'akko hijjabinki zamu gidan Mama."

INdo ta kallesa cikin sauke numfashi tana warware d'ankwalinta tayi mayafi dashi tana cewa.

"Ah ai inajin sai anjima zani idan ma banjeba ai yace su Haleema zasu zo."

"Ki d'akko hijjab nace miki kenake jiya bawai surutu ba."

Juyawa tayi tana kunkuni ta d'akko ta fito shi kuma ya juya ya fita. Saida ta fito sanye cikin atamfa blue da zanen ganye fari ta sanya blue d'in mayafi suka fita ya rufe gate d'in suka shiga mota. Kasa tukawa yayi jikinsa sai rawa yake yi INdo ta bishi da kallo cikin mamaki k'arshe ya fito daga motar yace.

"Fito muje."

A k'afa suka taka har bakin titi ya tarar musu napep suka shiga aka kaisu gidan Mama lokacin har mutane an fara taruwa a k'ofar gida Sadeeq ya cewa INdo.

"Shiga ciki gurinsu."

Yana dad'a ya juya yabarta ita kuma ta nufi ciki tana bin mutanan da kallo. Tana shiga parking space taji abbansu yana waya yana cewa.

"Eh wallahi Abubakar d’inne....










*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu


*MUSAYAR ZUCIYA:- Hak'ik'a banyi zato ko tsammanin makaranta labarin nan sunkai yawan haka ba sai da akazo page 21, a hak'ik'anin gaskiya naji matuk'ar tsoro na razana da ganin millions of people's da suk'e matuk'ar son Dr Abubakar da Aishatul humaira a ranar da waya nata tarwatsewa toh da tuni an wuce babin wayata, everywhere MUSAYAR ZUCIYA Hajja karki kashe Dr becan-canci haka ba, idan kikai hakan kin sakamu cikin tashin hankali INdo kuma baki kyauta mata ba. Karku manta Allah babu ruwansa da lokacin da zaka farajin dad'in rayuwa ya d'aukeka, anytime kowane irin yanayi kake ciki idan lokacinka yayi dole ka barshi katafi ba tare da kashiryawa hakan ba. A yanzu haka nasan wad'anda suka tanadi likaffani na mutuwarsu sabida suna ganin sun tsufa rayuwa ta k'are musu amma har yanzu basu mutuba sai 'ya'yansu da jikok'insu wad'anda ba'a saka musu ran mutuwa sune suke mutuwa. Dan Allah badan niba kuyi hakuri ku d'auka a cewar kuma akanku hakan zata iya faruwa sannan kuma kowacce zata yiwa Abubakar addu'ar Allah ya sadashi da rahamarsa. Labarin gaske ne domin da Ummi Aisha itace zata yishi so bansan Stylish Bch ta bata labarin ba sai jiya. Kuyi hakuri harda masu cewa sundena karantawa sabida sunsan karshe dai Sadeeq zata aura suzo suna kishi da fateema🤭toh duk kuyi hakuri kuma sannan ku yafewa 'yar uwarku, da ace tun farko bansa muku true life ba wallahi akwai yadda zanyi na sauya salon amma yanzu kona sauya toh araina zan dingajin abun tunda nasan ba haka yake ba, duk wanda na 6atawa tundaga kan fara novel din har zuwa wannan pagen kuyi hakuri ku yafewa Hajja ce👈 'yar Adam ce kamar ku sannan kuma meyin kuskure a duk inda ta samu kanta, wallahi dana dinga ganin comments d'inku dakyar nayi bacci zuciyata na rawa Ina ganin ban kyauta muku ba ciki rayuwarku. Nasan da yawanku zaku dena karantawa toh Ina fatan duk wanda ya tsaya iya nan ya d'auki wani darasi a ciki amma Zan samu na k'arasa shi a WATTPAD dan nima na samu nutsuwar Zuciya. Nagode gaduk wanda suka karanta farkon labarin Allah ya sadamu da rahamarsa a cikin kabarinmu Amin Love you all m fan's❤🤝❤*

Page *22*


Hark'asa INdo ta tsugunna tana gaida shi idanta akan fuskarsa tace,

"Abba ina wuni?"

Ya zura wayar cikin aljihunsa yana kallonta ya amsa.

"Lafiya lau Aisha tashi kishiga daga ciki."

"Toh adawo lafiya."

Tafad'a tana mik'ewa ta nufi cikin gidan, tana shiga sallama tayi tana k'iran Haleema kamar yadda takeyi idan suka zo gurin da zasu had'u. Haleema dake zaune a falo tajiyo INdo na nemanta da sauri ta mik'e ta shige d'akin su dan bata son su had'u a cikin wannan yanayin. Mata tagani a zaune a falo wasu sunzo wasu kuma na shigowa Mama a gefe gurin kujera ta takure Umma kuma a bakin k'ofa INdo ta dinga binsu da kallo kafin ta k'arasa kusa da Fateeman Sadeeq ta zauna itama ta takure tana gaida su, suka amsa mata a sanyaye. Juyawa tayi tana lek'an fuskar Fateema wadda take faman hawaye a dai-dai fuskar tata tace.

"Kai amaryar malam menene kike kuka? Ko malam Sadeeq ne,dan nasan shi sarai tun a makarantar mu meh yayi miki..?!"

Zame jikinta tayi daga na INdo ta juya tana kallon Mama sai taga itama ta d'auke kai Fateema ta rasa yadda zatayi gashi INdon ta takura mata akan sanjin abinda takewa kuka,mutane dake shigowa ne ya k'ara sanya INdo cikin wasi-wasi kuma da sun shigo zasu samu guri su zauna a cigaba da zaman shiru sai kuma kallonta da ake yi. Mama ce tayi k'arfin halin yin magana tana kallon su fateema tace.

"Fateema jata kushiga cikin d'aki mana."

Hakan akayi kuwa suka shiga ciki nan INdo taga Haleema a mak'ure jikin gado sai shashekar kuka takeyi, cikin sauri ta k'arasa wajanta dayake Allah ya had'a jininsu da ita ta janyo ta da sauri cike da damuwa da nuna kulawa tace.

"Haleema Hali dubu kyakyawa, me kikema kuka kema?!"

Rungumeta Haleema tayi yayin da INdo tayi shiru tana rik'e da ita, ita INdo ba komai yake sanyata saurin kuka ba har sai abin yakai mak'ura sannan batada tsoro musamman a fagen magana kafin Haleema tayi magana Mama tashigo d'akin Fateema na zaune fuskarta cikin hijjab Mama ta rik'o INdo ita kuma jinta ajikin Mama yasa tayi murmushi sai taji tamkar Abubukar d'inne ya rik'ota.

A bak'in gado ta zaunar da ita can suka jiyo muryar Wata tsohowa mak'ociyar su ta shigo tana fad'in.

"Allahu akubar Garbati ankai sa'i, d'azu-d'azun nan yana fitowa daga gidannan ya lek'a zaurena muka gaisa yace min zai tafi birnin taraiya, Allah sarki kungani ya bani yaci inci goro Allah yajik'anka Garba.."

Ta k'arasa maganar tana nuna musu naira d'ari biyar d'in daya bata, a cikin d'aki INdo ta kalli Mama tana zaro ido tace.

"Mama waye Garba a gidannan da ya mutu?!"

Cikin dakiya Mama ta k'arasa wajan wardrobe tana cewa.

"Anan gidan yake Aisha zakiji ko waye."

Farin hijjab ta zaro tare da mik'awa INdo shi tana cewa.

"Ciro mayafin Aisha a ajiye shi."

Kamar yadda Mama tace haka tayi tasanya hijjab d'in Mama zumbulele sannan Mama tace ta zauna karta fito. Suna zaune zugum sai ta d'akko wayarta number'n sa ta k'ira cikin sa'a aka d'auka cikin zumud'inta tace mai.

"Salama alaikum my key kaje ko kakusa zuwa..?!"

Taji ance "Sorry hajiya me wayar yanzu haka Allah yayi mai rasuwa."

Da mamaki tace "Rasuwa kuma? Toma waikai waye ma tukunna?!

Kashewa akayi INdo ta zaro ido tana kallon wayar tare da furta.

"Rainin hankali toh ko fad'uwa wayar tayi wani ya sace shine zaice min haka. Aniyarka ta bika mugu 6arawo."

Ta fad'a su kuma Haleema dasu Fateema da wasu da suka shigo d'akin suka bita da kallo. Hawwa ce ta shigo tana kuka sosai saida tazo falo ta kuma 6arkewa da wani kukan tana shashek'a tace.

"Allah sarki Yaya Habu yanzu ya gama min waya Mama kinga kiran da yayi min yace gobe insa aje a d'akko min Humairansa... Tazo muyi hira da daddare a maida ita baya son ta zauna it...."

Ta kasa k'arasawa sai kuka, INdo ce ta fito fululum cikin hijjab jin muryarta ta k'arasa kusa da Hawwa ai Hawwa na ganinta ta janyota jikinta kukan ya tsananta amma bakin be fasa magana ba.

"Aunty Humairah kinyi rashi Allah yajik'an Yaya Habu yaso kuyi long life a tare sai gashi Allah ya d'aukesa ya barki...."

Muryar Mama ce ta katsewa Hawwa kukan da takeyi cikin fad'a tace.

"Amma dai ban ta6a sanin bakida hankali ba sai yau Hawwa, wannane wane irin hauka ne daga shigowarki sai kace ba gidan musulmai kika shigo ba. Toh kin gaya mata kinji dad'i tun zuwanta kowa ya kasa gaya mata saike wawuya kawai..."

Da sauri Hawwa ta kalli INdo sai taga ta kura mata ido fuskarta a murtuk'e tun daga nan kuma sai bakin mutane ya fara bud'ewa aka fara zance mutuwar kunnuwan INdo suka dinga jiyo mata ai yana tafiya har ya wuce Kaduna Allah yayi masa rasuwa.

Sosai hankalin Hawwa ya tashi ganin yadda INdo ta kafeta da ido hakan ya bata tsoro tayi saurin matsawa baya INdo ta bita cikin tashin hankali Hawwa tace.

"Aunty Humairah Lafiya? Please wannan kallon fa..?!"

A hankali INdo tasa hannu ta rungume Hawwa cikin rawar murya tace.

"Yaya Hawwa kema sokike Yaya Abubakar ya mutu? Yanzu na buga mai waya wani ya d'auka yace min me wayar ya mutu ashe kema sokike ya mutu? 'Dazu ni narakasu mota suka shiga shida malam Sadeeq amma meyasa kike son yayanki ya mutu? Kinga yana sona dayawa d'azu fa har cemin yayi yana son duk wani mesona kuma zai sani a makarantar abuja..."

"Kiyi hak'uri aunty Humairah nima inason Yaya Habu amma Allah yafimu sonshi shi yasa yayi hatsari..."

Hawwa ta fad'a tana kuma sakin kuka, da sauri INdo ta hankad'a Hawwa baya iya k'arfinta jikake gam..! ta bugu da kujera cikin kukan bak'in cikin maganarta yasa INdo cewa.

"Daga yin bikin mu shine zaki mana addu'ar ya mutu sabida bakya sonmu, toh insha Allahu sai Isyaku ya riga dacta mijina mutuwa fatanki ya biki, ance miki Garba ne ya mutu shine zaki zo kice Yaya Abubakar ne dan bak'in ciki..."

Umma ce tayi saurin toshewa INdo baki cikin rufewar ido ta fara tureta domin ta baya ta rik'ota ta kuma toshe mata. Cikin kwantar da murya Umma kishiyar Maman su Sadeeq take mata magana a hankali.

"Kinga Aisha kiyi shiru kinga mutane sun fara cika gidan yi hak'uri taho muje ki zauna kinji 'yar albarka."

Tana nishi Umma taja ta still bata dena yiwa Hawwa kallon banza ba duk kuwa da cewar ta girmeta nesa ba kusa ba amma cewar Abubakar d'inta ya mutu shine ya d'arsa wata k'azamar kiyayya a zuciyar INdo.

Fateema ce ta fito idanunta jawur ta kama hannunta suka koma cikin d'akin Mama, suna zama amma sai mita INdo takeyi Mama ta shigo ta kalleta tare da cewa.

"Aisha kidinga hakuri kinji ko?"

INdo tace "Toh Mama ki gaya mata bana son wasan mutuwa."

"Toh zan gaya mata tashi muje ki wanke fuskarki da sabulu."

Babu musu ta mik'e suka shiga bathroom saida ta gama wankewa sannan Mama ta kamo hannunta suka wuce, d'akin Abba suka shiga yana zaune yayi shiru yana bud'e likkafani gefe turare ne a kusa dashi suka shiga bayan Mama tayi sallama. Sake gaisawa suka yi da INdo sannan Abba ya kalleta tsawon lokaci ya kasa cewa komai, can dai ya nisa yace.

"Aisha ke musulmace ko?!"

'Dan murmushi tayi alamar kunya tana sunkuyar dakai tace,

"Eh Abba."

"Alhamdulillahi ina son sanar dake Abubakar dai Allah ne ya bani shi, nina raineshi tundaga zanin goyo har girmansa da temakwon Allah, bayan ya girma ya mallaki hankalinsa shida d'an uwansa suka d'auke min duk wani nauyi nasu dana k'annansu, kafin ya aureki ya nemi auran wata yarinya Allah ya k'adarta beyi ba sai dake, toh Allahn daya baki Abubakar Aisha ya k'ar6i abinsa domin yanzu haka suna hanya za'a kawo gawarsa ina son ki daur...."

Bek'arasa ba yaji ta fashe da kuka, kusa dashi ta rarrafo tare da rik'o Hannunsa tana jijigawa tana fad'in.

"Abba... Abba wallahi ba dacta bane, ba shine ya mutu ba shi yatafi abuja k'ila dai malam Sadeeq ne, dan Allah Abba karku ce haka wallahi yace zai dawo ya tafi dani can garan..."

Mama Abba ya kalla alamar tazo ta zanye ta, tana zuwa INdo ta juya kanta tare da rik'o hannunta itama tana cigaba da magana tana basu rabarin abinda yace zai yi mata nan gaba sai kawai itama Maman ta fashe da kuka Abba ya fara mata fad'a amma ina ta kasa yin shiru bare ta bawa INdon.

"Kutashi kuje yanzu suna hanya zasu kawo shi, karku sake kubarta tafita ko'ina kinajina...?"

Mama ta kad'a kai tare dajan hannun INdo suka shiga gidan sai ihu take mutane na kallonta cikin tsananin tausayawa.

Tana shiga ciki ta zu6e ak'asa jikinta sai rawa yakeyi aka rufa a kanta kowa sai nemar mata d'auki yake ta zame jikinta daga na wata mata tana kallon Matan tace.

"Sani zantafi."

Umma ta rik'ota itada Fateema ta fara tirje musu dama INdo yaya lafiyar kura, dacta ne yasanta ya kuma san yadda zai biyo mata gashi babushi dan haka abin nata ya kuma yawa.

Kullesu akayi a d'aki babu me fitowa suna jiyo kukanta har aka dawo daga d'akko gawar Abubakar, d'akinsu aka kaishi Sadeeq tamkar wani zararre fuskarsa fal hawaye idanunsa sunyi luhu-luhu tamkar kurji ya fito ya shiga cikin gida yana neman Mama. Da kyar ya iya tambayarta zani ta mik'e ta bud'e d'akin, suka shiga.

Gaidashi mutanan d'akin suke suna mai gaisuwa, yana furta "Alhamdulillah." INdo tayi zumbar ta mik'e daga ruk'on da Zulaihat tayi mata, lokacin Mama ta mik'a mai zannin ya k'a6a kawai yaji INdo ta mak'aleshi katak'am tamkar ba rik'on mace ba tana kuka tana cewa.

"Dacta ka dawoko? Nasan dama bazaka barni ba dan Allah da manzansa kace min Malam Sadeeq ne ya mutu ba kaiba, wallahi kaga zanyi kwalliyar da kace irinta d'azu, mu koma gidanmu nan kana da mak'iya ciki harda Abba duk fatan mutuwa suke ma..."

"Aisha sakar ni please."

Sadeeq ya fad'a yana 6an6areta daga jikinsa amma tamkar mutum biyu ne suka rik'esa, ya rasa dalilin dayasa takeja masa mugayan alkaba'i tun suna makaranta nan fa su Mama suka k'arasa suna nuna mata bashi bane amma tak'i sakinsa cewa take.

"Duk inda zahi zan bihi wata k'ila akwai masu bibiyarsa basa sonshi toni ina sonsa."

Janta yayi ganin ta mak'ale suka k'arasa bakin gado ya zaune tare da nunawa Fateema alamar tazo ta zauna kusa dashi. Tana zuwa INdo ta kare shi alamar karta ta6ashi Fateema ta toshe baki kuka na shirin kwace mata, haskilowa kawai takeyi tasan da shi ya rasu k'ila da tuni itace a cikin wannan yanayin da INdo take ciki.

Kabeer ne ya shigo ya kar6i zanin domin sam INdo tak'i sakin Sadeeq, Mama kuwa so take ta 6an6areta domin tasan hankan ba dacewa bane kuma INdo tashiga cikin takaba hakan yasa ta fara sanya ta cikin dokokin da musulinci ya tanadarwa ga duk macen da mijinta ya rasu...








*HAJJA CE*👈


[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu


*MUSAYAR ZUCIYA:- Hak'ik'a banyi zato ko tsammanin makaranta labarin nan sunkai yawan haka ba sai da akazo page 21, a hak'ik'anin gaskiya naji matuk'ar tsoro na razana da ganin millions of people's da suk'e matuk'ar son Dr Abubakar da Aishatul humaira a ranar da waya nata tarwatsewa toh da tuni an wuce babin wayata, everywhere MUSAYAR ZUCIYA Hajja karki kashe Dr becan-canci haka ba, idan kikai hakan kin sakamu cikin tashin hankali INdo kuma baki kyauta mata ba. Karku manta Allah babu ruwansa da lokacin da zaka farajin dad'in rayuwa ya d'aukeka, anytime kowane irin yanayi kake ciki idan lokacinka yayi dole ka barshi katafi ba tare da kashiryawa hakan ba. A yanzu haka nasan wad'anda suka tanadi likaffani na mutuwarsu sabida suna ganin sun tsufa rayuwa ta k'are musu amma har yanzu basu mutuba sai 'ya'yansu da jikok'insu wad'anda ba'a saka musu ran mutuwa sune suke mutuwa. Dan Allah badan niba kuyi hakuri ku d'auka a cewar kuma akanku hakan zata iya faruwa sannan kuma kowacce zata yiwa Abubakar addu'ar Allah ya sadashi da rahamarsa. Labarin gaske ne domin da Ummi Aisha itace zata yishi so bansan Stylish Bch ta bata labarin ba sai jiya. Kuyi hakuri harda masu cewa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login