Showing 33001 words to 36000 words out of 85627 words
β₯
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*π
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*π‘
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.
*Duk da cewar kinfi k'arfin page amma duk da haka zan bak'ishi ba a matsayin komai ba sai dan kawai naga nayi hakan, I am proud of you My Xoxo (miss Xoxo) Allah ya baki abinda kike so Duniya da lahira.*β€π
Page *17*
"Wallahi kuwa itace, INdo malam dama zaki iya zama haka? Ikon Allah da...."
Cikiin sauri Abubakar yayi magana ranshi a bace ganin yana neman kwance mata zani a kasuwa yace,
"M twinnie ya isah haka ko ka manta matsayinta a gurina ne ah..? Kake neman cin zarafina."
Sadeeq ya k'arasa wajan Abubakar tare da dafa kafad'arsa ta hagu yace.
"Oh sorry M twinnie ba nufina kenan ba abinne ya d'aure min kai."
Jin-jina kai Abubakar yayi yana kallon yanayin INdo yaga ta cukume ta kasa boye fushinta sai faman cizon le6anta takeyi na k'asa tana murd'e k'asan mayafin jikinta ya kalleta yace.
"Humaira zo muje kiga wani abu."
Kamar jira takeyi yace taje ta mik'e suka fita lokacin Sadeeq na tsaye a parking space tsananin mamaki sun addabi zuciyarsa sai gasu, INdo na hangoshi ta k'arasa gurin Abubakar ya bi bayanta. Tsayawa tayi tana kallon Sadeeq cikin salon raini tace.
"Oh malam Sadeeq kayi mamaki ko? Toh aishi dama Allah ba yadda bayayi da bawansa nasan baka ta6a kawowa ranka cewar zaka ganni a makamancin haka ba sai gashi ta silar d'an uwanka."
"Hakane Aisha nayi mamaki kuma har yanzu ina kanyi, shin wace school kike yanzu.?β
Ya tambayeta ta yatsina fuska tare da gyara mayafi tana gyara zaman d'ankwalinta tana son cewa, ba zamu iya magana anan ba da turanci dan ta bashi mamaki amma ta kasa tana dai d'anjin alamu-alamun zata iya amma batason ko gwadawa ne dan karyayi mata wani kallon (We can not talk here) tayi mata wahala kawai ta maze tace.
"I dant talk." (I don't tell you)
Suka kalli juna Sadeeq da Abubakar fuskar Abbakar a had'e ganin haka yasa Sadeeq girgiza kai yana kallonta yace.
"Oh good Allah ya bada sa'a, Ina su Innar ku da malam..?!"
INdo tace "K'alau suke duk suna gaihe ku."
Tayi maganar tana matsawa kusa da Abubakar,murmushi ya sakar mata itama ta mayar mai sannan tace.
"Kazo ka maida mu gida Yaya Abbakar dare nayi."
INdo akwai dad'in murya saidai ta kasa dena sh da hi musamman idan tana magana cikin fushi.
"Toh kuje ku shirya sai mun fara zuwa gidan su budurwar Sadeeq daga can sai mu wuce."
Abubakar ya fad'a yana kallon fuskarta, wucewa tayi ta koma ciki shi kuma Abubakar ya gayawa su Mama cewar zaije ya maidasu. Nan fa kowa na gidan ya fara k'ok'arin fito da abinda zai yiwa INdo kyauta dashi baga k'annan ba baga su Mama ba, haka suka cika INdo da Nafeesah da tsaraba kala-kala.
Fita suka yi duk 'yan gidan suka rako su mota anayi musu fatan sauka lafiya. Sadeeq ne yake tuk'in yayin da Abubakar ke kusa dashi suka su INdo suna baya har suka k'arasa gidan su Fateema, waya yayi mata dama dawowarta kenan daga gidan suna ta raka Ummanta, fitowa tayi lokacin anata k'iran magrib INdo ta kalli Fateema itama Fateeman ta kalli INdo kowa ya fara sak'e-sak'en abubawa a cikin ransa.
"My Zarah ga girlfriend d'in M twinnie nan kusan juna bari muyi sallah tukunna."
Cewar Sadeeq Fateema ta kamo hannun INdo tana cewa,
"Okey My D sai kun dawo, shi yasa naga mutumin ankasa an tsare ashe-ashe."
Tayi maganar tana kallon Abubakar ya galla mata harara tare da cewa.
"Whatever dai please take care of her, if not.. Hmmm."
Dariya Fateema tayi INdo kuma ta bita da kallo, oh itakam taji abinda yace tunda gashi tana dariya ita kuwa please d'in kawai taji amma raguwar duk bata ganeba shi kuma Sadeeq ya zauna saman motar kafin yace.
"Ki kawo mana ruwan alwala karmu rasa jam'i."
Jan hannun INdo tayi suka shiga Nafeesa na biye dasu, a falo suka zauna Fateema na zuba ruwa a buta tanayiwa Umma bayani kasan cewar itama alwala take a gurin. Bayan takai musu ta dawo suka gaisa da INdo ta kawo musu juice da cin-cin a cikin wanda tayiwa Sadeeq d'inta domin ba k'aramin so itama Fateema takewa Sadeeq ba kowa yasani tana mugun sonshi.
Kad'an suka ci wai na 'yan birni karsuci da yawa duk da cewar yayi shegen dad'i amma haka suka hakura, suna Idarwa Sadeeq yayi mata waya cewar su fita zasu tafi.
A bakin mota suka tarar dasu banda ban-bancin kayan jikinsu da babu wadda zata gane waye nata, suka k'arasa Fateema ta kalli Abubakar marainin wayon nata tace.
"Toh gata na dawo da ita, kaga har 'yar k'ibama saida tayi a gode min."
Murmushi yayi tare da zagawa drive seat ya zauna yana cewa.
"Tayaya zan yadda bayan ni a yadda na baki haka na kuma kar6a, anyway thanks amma kad'an."
Tayi dariya su INdo suka shiga mota bayan sunyi Sallama da Fateeman, a bakin titi suka sauke Sadeeq ya kalli INdo itama tad'ago ta kallesa tana faman had'e rai dan karma yayi mata turanci sai taji yace.
"Aisha sai yaushe?!"
Ta sauke numfashi tare da cewa, "Sai wata rana kuma."
"Okey please send m regards to your parent."
Mtwwww taja tsaki mai k'arfi cikin kufala tace.
"Idan bazakai Hausa ba kayi gaba ai bada yaren annabi kayi min magana ba."
"Lallai Aisha ni kike gayawa maganar nan?"
Sai tayi mai da fulatanci itama shi kuma yayi shiru dan shima baji yake ba ta kallesa tace.
"Ko bakaji abinda nima nace ba? Toh duk sanda zaka ganni kayi min wani turanci nima henayi maka wanda na iya ai kowa Allah ya tsaga ya bahi."
Juyawa Sadeeq yayi yana taran napep yana mamakin INdo, wato yanzu ta koyi rainin hankali gashi yagano cewar tanada d'auke kai akan abinda beshafe taba amma idan ka shiga nata zata yimaka rashin kunya duk girmanka.
"Humairah dawo gaba."
Abubakar ya fad'a ba tare daya juyo ba, fitowa tayi ta koma kamar yadda ya umarce ta. Kallonta yayi ita kuma tana gyara rigarta yaja motar suka tafi. Tun suna hira dashi da Nafeesah hartayi bacci, sai da yayi nisa sosai sannan ya gyara murya yace.
"Humairah meyasa kikewa Sadeeq rashin kunya..?!"
Banza tayi Mai sai kunkuni takeyi ya kuma yin tambayar tayi mai banza sannan yace.
"Baki ga d'an uwana bane? Kuma bakiga ta dalilinsa nasanki ba meyasa kikai mai haka."
Tunda suka saba da juna bata ta6a jin haushinsa ba sai yau, Allah kuma ya k'imsa mata yin magana cikin taushi dan da wani ne k'ila su kwashi 'yar kallo tace.
"Duk babu wanda yafiku sanin wacece INdo daga iyayena heku, meyasa hida yasan bajin turanci nakeyi ba amma heya dinga yi min, wannan ai izgilanci ne. Kuma malamar mu a islamiya tace mana, komai na Duniya jarabawa ce haka tace mana lafiya da Allah ya baka jarabawaci rashin Lafiya ma haka,idan Kud'i Allah ya baka hima jarabawa ce hakama talauci, Ilimi idan Allah ya baka jarabawa ne idan bebaka ba hima jarabawa ce, aure jarabawa ne rashinsa ma haka, amma himeyasa yake min haka kuma yasan ban iya ba? himeyasa baka yi mihi magana ba heni...?!"
Shiru Abubakar yayi yana tuk'i, lallai wannan kad'ai yaci ace angodewa Allah tunda har INdo tasan shi. Murya a sanyaye yace mata.
"Haka ne kiyi hakuri."
Cigaba da tafiya sukayi har saida suka shiga garin Sumaila yayi parking akan kwanar dazata kaisu kauyen Sani ya kalleta ta kalleshi bayan ya kunna kwan cikin motar yace cikin wata irin murya.
"Humairah kina sonah..?zaki iya aure na...?!"
INdo tayi saurin rufe fuskarta da gyale tanajin wani farin ciki da annashiwa suna yawo aduk wani sashe na jikinta. Murmushi yayi shima yana jin tamkar an d'auke mai wani gungumeman abu aacikin k'irjinsa ya kuma tambayar ta INdo ta d'aga mai kai alamar Eh sannan ya furta kalmar Alhamdulillah.
"Thank you Humairah Ina sonki so me tsanani, Zan kula dake iya gwargwadon iyawata, zan kare duk wani hakkinki daya rataya a wuyana zan baki kulawa a cikin rayuwar auran mu sannan zanyi iyayina wajan ganin kin cigaba da samun Ilimi ta kowacce hanya indai alkairinki na thanks again I love you."
Tunda ta rufe Ido bata bud'e ba harya gama magana, ganin haka ne yasa shi rik'o hannunta ta fara k'ok'orin kwacewa murya a sark'e yace.
"Idan kina son na sakar miki hannu sai kin bud'e fuskarki."
Kad'a mai kai tayi sannan kuma tak'i bud'ewa, ganin dare nayi mai ne yasashi sakar mata hannun yana murmushi tare dajan motar suka shiga cikin kauyan har k'ofar gidan su lokacin malam Hamza na zaune zaman jiransu.
Da sauri Abubakar ya fito yaje gurin Malam Hamza yana bashi hakuri, shidai malam Hamzah tunda yaga yaransa sai yaji hankalinsa ya kwanta yace ai ba komai. Sim-sim INdo ta shige gida Abubakar ya tambayi malam Hamza inda zaije ya nemi auranta Malam Hamza yace.
"Ai malam Habu tunda ka tambayeni ai kagama tambayar duk wani wanda zai baka uwata, yanzu kawai kaje duk sanda ka kintsa saika kazo ayi."
Godiya Abubakar ya dingayi tamkar cewa akayi an bashi kijerar president. Kayayyakin su ya ciro musu su Sagiru suka kwashe suka shiga dasu cikin gidan shi kuma yaja mota ya tafi yana mai jin farin ciki da nishad'i.
Washe gari yayiwa abban su magana k'annan abban sukaje har kauyen Sani aka tambayowa Abubakar auran INdo malam Hamza ya tara abokansa suka shaida an bashi, a take a gurin k'anin abban su Abubakar ya bada kud'in nagani ina so dubu Hamsin sannan suka tafi suna mamakin gidan da Abubakar yazo neman aure sai dai sunsan ba yadda Allah baya tsara abinsa dan haka babu wanda yaja da al'amarin.
Labari ya zaga gari an kawo kud'in INdo dubu Hamsin masu bak'in ciki nayi masu murna nayi dama haka lamarin mutane yake. A cikin satin ya siyo mata waya sabuwa tecno sabida anyi mai transfer zuwa abuja sabida haka zasu kuma yin nisa.
INdo ta cigaba da zuwa makaranta duk da tana saka wasa a cikin lamari sai dai fa ta k'ara yin clean domin idan kaganta sai ka d'auka tana a matakin degree program ne nan kuwa ko secondary school bata kammala ba. Ta kuma rik'e alk'awari bata kula kowa duk kud'inka duk kyawunka duk ajinka duk meye d'inka bazata kulaka ba tace bazata yi *MUSAYAR ZUCIYA* da kowa ba Abubakar shine a cikin zuciyarta shi kuma take da burin aura...
*HAJJA CE*π
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *ββMUSAYAR ZUCIYA...ββ*
β₯β₯
β₯
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*π
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*π‘
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
*Gaskiya ban san me zan cewa masoya maso bibiyar labarin nan ba sai dai nace muku love you all.*
_Shafin naku ne My Shuwa Arab, Dota Fatima, Dota Marok'i, My Shama, My Olo, aunty Jidder_ππ
Page *18*
*Bayan wasu shekaru.*
Gaba d'aya an kammala yin komai ansa rana da Fateemah ta kammala school za'ayi dan haka ginin su kawai suke yi. Gidane me kyawun gaske kowanne yake ginawa kowa kuma da yadda yake son abunsa. Gidan Abubakar yafi tsaruwa nesa ba kusa ba yafi na Sadeeq sosai kasan cewar shi yana son ya samu wani acan inda yake business dinsa idan sunje da matarsa babu wani fargaba dama yanada gidanshi dan haka biyu ya raba sa6anin Abubakar dashi a abujan ma yana da k'atan gida a quarters d'in asibitin da yake aiki.
*****
Fateema na shekarar k'arshe domin sauran 'yan watanni ta kammala, yayin da a 6angaran INdo itama sai hamdala domin zata iya rubuta wasu kalmomin harma ta rubuta wasik'a da Hausa koda ajimi kuma iya yawancin surorin alkur'ani me girma an samu cigaba sosai.
Kyawunta ya fito ta waye ta goge kai in baka cika ishasshe bama bata kulaka bare harkuyi hudd'a tare. Zaune malam Hamza da Inna suka suna tattaunawa akan yadda zasu yi da kayan d'akin INdo gashi INdo tace harda gararta zata tafi batason abin gori.
"Toh malam ya zamu yi, iya abinda Allah ya bamu shi zamu yi mata ai suma sunsan damu dasu ba d'aya bane sun fimu ta ko'ina."
"Hakane Maryamu yanzu dai dole naje na siyar da gonata dake can saye guda d'aya, sannan na siyar da shanuna guda biyu sai ayi mata amfani da kud'in nasan dai bazamu yi mata irin yadda take so ba saidai ai munyi k'ok'ari kuma mani wallahi dandai Dacta Habu zata aura hiyasa zanyi mata duk abinda nasan Zan iya sabida yaron nan d'an k'irki ne, duk sanda na kalli katangar nan naganta da suminti sai naji dad'i."
"Hakane kam malam toh sai a siyar d'in Allah ya bada lada."
Malam Hamza yace "Amin."
Kwana hudu dayin zance ya d'auki abokinsa malam kallah suka tafi Saye bayan rabansa da zuwa kusan shekaru goma sha biyar kenan. Sun gaisa da kowa saidai tsakaninsa da yakumbo tsahare babu ko kallon banza, bayan an gayawa sarkin shanu aka yi cinikin shanun malam Hamza wanda shine ya baiwa yakumbo talatu su yace idan sun haihu ya barmata saidai duk lokacin da yake da bukata toh zai dawo ya karbi guda biyu. Dubu talatin-talatin aka siye su nan aka bawa malam Hamza kud'insa dubu sittin, aka koma kan gona wani mutum ya siya dubu cas'sa'in malam Hamza ya kar6o kudin suka dawo gida da dubu d'ari da Hamsin cas.
Had'awa akayi da kud'in nagani inaso d'inta aka had'a suka zama d'ari biyu cif malam Hamza yace aje ayi cinikin gado madubi da wardrobe, nan aka nuna musu kud'ad'an ko wanne babu ma na k'asa da dubu d'ari a cikin irin wanda INdo ta nuna tana so.
Na dubu d'ari da hamsin suka za6ar mata wata yayar Inna ce da take aure a dawakin tofa sukaje suka tayo. Sai kud'in gudun mawar da aka dinga kawo musu dan su kauye basai ranar biki suke bada gudunmawa ba. Haka dame d'ari d'aribiyu dubu biyu gashinan dai aka dinga vawa inna da malam Hamza suka had'e ya basu dubu hamsin da biyar da naira ashirin. Suka had'e da ragowar hamsin dinnan aka had'a d'ari na kujeru gaskiya INdo taci Kud'i wai...!
Sai kuma masu kawo kayan amfani na kitchen me kofi , me tasa, me plate, gashi nan dai suma aka had'a Inna tasa aka siyar da gonarta itama sai aka sissiya abubuwan da babu a kitchen d'in.
****
Gidan su Fateema kuwa ko shirin basu farayi ba sabida su ba wani case karatunta kawai takeyi hankali kwance.
'Bangaren mazan kuwa, kayan lefe ake had'awa komai iri d'aya Mama tace azuba colors ne kawai suke ban-bantawa da kuma size domin INdo tafi Fateemah jiki ita kuma Fateemah tafi INdo haske da tsawo.
Akwatuna bakwai-bakwai akayi musu kowacce shak'are da kaya domin mazajen ba k'aramin k'ok'ari suka yi ba sun kashe Kud'i over.
Ranar da su Fateema sukayi graduation a ranar aka kai kaya murna biyu ta had'ar mata.
'Bangaran INdo ma ankai kayan tana gidan Rukayya kwance tana waya da Abubakar, cikin salon mak'e muryar data koyo wajan su Zainab da Hadiza tace mai.
"My key wai me kakeyi ne yanzu?!"
"Ina office a zaune tare da frame d'inki inata kallonki."
"Yeeee naji dad'i nima ka tambaye ni.."
"Habibty mekike yi yanzu..?"
Ya fad'a kamar yana cikin maye, dariya INdo tayi me sauti sannan tace.
"Ni tunaninka nakeyi dan Allah yauhe zaka dawo.?!"
Dariya yayi tare da cewa, "Sai ending d'in month d'innan, ya mekika tanadar min?!"
Tace "kana nufin ending k'arhen Month watan nan ko?!
"Eh haka nake nufi madam."
"Toh kenan kana nufin ankusa biki."
Yace "Eh amma ai Sadeeq yana nan ba kuma zai koma ba sai an gama biki kokina buk'atar wani abun nasa ya aiko miki dashi?!"
INdo ta kuma gyara kwanciya domin yarinyar ta iya kar6ar sakwan love tace.
"Eh akwai abinda nakeso."
"Toh madam menene shi..?!"
Tace cikin jan numfashi "Kai nake son gani."
Abubakar saida tsigar jikinsa ya tashi yarrrr ya d'ora k'afarsa kan table tare da jin gina da jikin kujerar dayake kai, hannu yasa a k'irjinsa yana d'an bubbugawa tsawon wani lokaci sannan yace mata.
"Sorry Habibty da ace da yadda zanyi danayi na taho, saidai na riga na k'ar6i aikin wani abokina inason idan na taho ya kar6i nawa sabida idan munyi aure bazan dawo da wuri ba sai na gama shan amarci na."
INdo ta guntse baki jin abinda ya fad'a sannan taji yace.
"Ko kina son da an d'aura aure na dawo."
Da sauri tace "A'a bana son ka koma."
"Toh ki tanadar min kanki a duk ranar da aka kawoki gidana."
Kit..yaji ta yanke wayar ya sauke yana kallon screen d'in yana murmushi bata san wannan zantuttukan baya manta ranar daya fara gaya mata irin maganganun tace mai ita ba 'yar iska bace. Ranar yaci dariya kamar cikin sa zaiyi ciwo, bebi kiran ba yaci gaba da aikinsa yana ta murmushi INdo na bashi laugh yasan idan sukayi aure zai dinga shan dariya.
INdo kuwa bata koma gida ba sai da tayi magariba sannan ta koma gida, wayyo Allah dataga irin akwatinan zamanin da Abubakar ya kawo mata bata san lokacin data fad'a jikin Inna ta rushe da kuka ba. Inna sai faman lallashi takeyi Sagiru da shehu suna kallon kayan kowa sai nuna abinda yake sukeyi da kyar tayi shiru aka cigaba da kallon kaya Inna ta nuna mata dubu hamsin tace,
"Gashi 'yarnan sunce kud'in d'inki ne."
K'ar6a INdo tayi tana godiya, tana gama kallon kayan suka rufe ta fita waje. Unguwar su kezy taje ta samesu zaune sai zuk'ar sugari sukeyi ta toshe hanci tana musu magana.
"Kai kezy aji tsoran Allah dai za'a mutu."
Tayi maganar tana sake toshe hanci, jazuli yace.
"Kefa 'yar rainin hankalice dan kinzama babbar yarinya shine zaki dinga yi mana kallon equal.."
"Kai masifaffe ni gurinku nazo, kunsan ankawo kayan aurena, toh sonake kuzo gida kuyi gadi Allah ma yace tashi intemake ka, idan ma kune 6arayin nidai kuzo gobe he'in baku dubu goma."
"Kai hajiya INdo kin zama hajjaju fa Allah."
Kezy ya fad'a tace "Eh koma dai meye nidai kuyi min."
"Karki damu zamuci uwar hegen dazaiyi gigin zuwa."
"Toh nagode."
Tafad'a ta wuce ta shiga gidan su Sahura, ta dad'e