Showing 45001 words to 48000 words out of 85627 words

Chapter 16 - MUSAYAR ZUCIYA COMPLETE BOOK by Hajja Ce.txt

Hajja Ce   

14 Sep 2025

45

sundena karantawa sabida sunsan karshe dai Sadeeq zata aura suzo suna kishi da fateema🤭toh duk kuyi hakuri kuma sannan ku yafewa 'yar uwarku, da ace tun farko bansa muku true life ba wallahi akwai yadda zanyi na sauya salon amma yanzu kona sauya toh araina zan dingajin abun tunda nasan ba haka yake ba, duk wanda na 6atawa tundaga kan fara novel din har zuwa wannan pagen kuyi hakuri ku yafewa Hajja ce👈 'yar Adam ce kamar ku sannan kuma meyin kuskure a duk inda ta samu kanta, wallahi dana dinga ganin comments d'inku dakyar nayi bacci zuciyata na rawa Ina ganin ban kyauta muku ba ciki rayuwarku. Nasan da yawanku zaku dena karantawa toh Ina fatan duk wanda ya tsaya iya nan ya d'auki wani darasi a ciki amma Zan samu na k'arasa shi a WATTPAD dan nima na samu nutsuwar Zuciya. Nagode gaduk wanda suka karanta farkon labarin Allah ya sadamu da rahamarsa a cikin kabarinmu Amin Love you all m fan's❤🤝❤*

Page *22*


Hark'asa INdo ta tsugunna tana gaida shi idanta akan fuskarsa tace,

"Abba ina wuni?"

Ya zura wayar cikin aljihunsa yana kallonta ya amsa.

"Lafiya lau Aisha tashi kishiga daga ciki."

"Toh adawo lafiya."

Tafad'a tana mik'ewa ta nufi cikin gidan, tana shiga sallama tayi tana k'iran Haleema kamar yadda takeyi idan suka zo gurin da zasu had'u. Haleema dake zaune a falo tajiyo INdo na nemanta da sauri ta mik'e ta shige d'akin su dan bata son su had'u a cikin wannan yanayin. Mata tagani a zaune a falo wasu sunzo wasu kuma na shigowa Mama a gefe gurin kujera ta takure Umma kuma a bakin k'ofa INdo ta dinga binsu da kallo kafin ta k'arasa kusa da Fateeman Sadeeq ta zauna itama ta takure tana gaida su, suka amsa mata a sanyaye. Juyawa tayi tana lek'an fuskar Fateema wadda take faman hawaye a dai-dai fuskar tata tace.

"Kai amaryar malam menene kike kuka? Ko malam Sadeeq ne,dan nasan shi sarai tun a makarantar mu meh yayi miki..?!"

Zame jikinta tayi daga na INdo ta juya tana kallon Mama sai taga itama ta d'auke kai Fateema ta rasa yadda zatayi gashi INdon ta takura mata akan sanjin abinda takewa kuka,mutane dake shigowa ne ya k'ara sanya INdo cikin wasi-wasi kuma da sun shigo zasu samu guri su zauna a cigaba da zaman shiru sai kuma kallonta da ake yi. Mama ce tayi k'arfin halin yin magana tana kallon su fateema tace.

"Fateema jata kushiga cikin d'aki mana."

Hakan akayi kuwa suka shiga ciki nan INdo taga Haleema a mak'ure jikin gado sai shashekar kuka takeyi, cikin sauri ta k'arasa wajanta dayake Allah ya had'a jininsu da ita ta janyo ta da sauri cike da damuwa da nuna kulawa tace.

"Haleema Hali dubu kyakyawa, me kikema kuka kema?!"

Rungumeta Haleema tayi yayin da INdo tayi shiru tana rik'e da ita, ita INdo ba komai yake sanyata saurin kuka ba har sai abin yakai mak'ura sannan batada tsoro musamman a fagen magana kafin Haleema tayi magana Mama tashigo d'akin Fateema na zaune fuskarta cikin hijjab Mama ta rik'o INdo ita kuma jinta ajikin Mama yasa tayi murmushi sai taji tamkar Abubukar d'inne ya rik'ota.

A bak'in gado ta zaunar da ita can suka jiyo muryar Wata tsohowa mak'ociyar su ta shigo tana fad'in.

"Allahu akubar Garbati ankai sa'i, d'azu-d'azun nan yana fitowa daga gidannan ya lek'a zaurena muka gaisa yace min zai tafi birnin taraiya, Allah sarki kungani ya bani yaci inci goro Allah yajik'anka Garba.."

Ta k'arasa maganar tana nuna musu naira d'ari biyar d'in daya bata, a cikin d'aki INdo ta kalli Mama tana zaro ido tace.

"Mama waye Garba a gidannan da ya mutu?!"

Cikin dakiya Mama ta k'arasa wajan wardrobe tana cewa.

"Anan gidan yake Aisha zakiji ko waye."

Farin hijjab ta zaro tare da mik'awa INdo shi tana cewa.

"Ciro mayafin Aisha a ajiye shi."

Kamar yadda Mama tace haka tayi tasanya hijjab d'in Mama zumbulele sannan Mama tace ta zauna karta fito. Suna zaune zugum sai ta d'akko wayarta number'n sa ta k'ira cikin sa'a aka d'auka cikin zumud'inta tace mai.

"Salama alaikum my key kaje ko kakusa zuwa..?!"

Taji ance "Sorry hajiya me wayar yanzu haka Allah yayi mai rasuwa."

Da mamaki tace "Rasuwa kuma? Toma waikai waye ma tukunna?!

Kashewa akayi INdo ta zaro ido tana kallon wayar tare da furta.

"Rainin hankali toh ko fad'uwa wayar tayi wani ya sace shine zaice min haka. Aniyarka ta bika mugu 6arawo."

Ta fad'a su kuma Haleema dasu Fateema da wasu da suka shigo d'akin suka bita da kallo. Hawwa ce ta shigo tana kuka sosai saida tazo falo ta kuma 6arkewa da wani kukan tana shashek'a tace.

"Allah sarki Yaya Habu yanzu ya gama min waya Mama kinga kiran da yayi min yace gobe insa aje a d'akko min Humairansa... Tazo muyi hira da daddare a maida ita baya son ta zauna it...."

Ta kasa k'arasawa sai kuka, INdo ce ta fito fululum cikin hijjab jin muryarta ta k'arasa kusa da Hawwa ai Hawwa na ganinta ta janyota jikinta kukan ya tsananta amma bakin be fasa magana ba.

"Aunty Humairah kinyi rashi Allah yajik'an Yaya Habu yaso kuyi long life a tare sai gashi Allah ya d'aukesa ya barki...."

Muryar Mama ce ta katsewa Hawwa kukan da takeyi cikin fad'a tace.

"Amma dai ban ta6a sanin bakida hankali ba sai yau Hawwa, wannane wane irin hauka ne daga shigowarki sai kace ba gidan musulmai kika shigo ba. Toh kin gaya mata kinji dad'i tun zuwanta kowa ya kasa gaya mata saike wawuya kawai..."

Da sauri Hawwa ta kalli INdo sai taga ta kura mata ido fuskarta a murtuk'e tun daga nan kuma sai bakin mutane ya fara bud'ewa aka fara zance mutuwar kunnuwan INdo suka dinga jiyo mata ai yana tafiya har ya wuce Kaduna Allah yayi masa rasuwa.

Sosai hankalin Hawwa ya tashi ganin yadda INdo ta kafeta da ido hakan ya bata tsoro tayi saurin matsawa baya INdo ta bita cikin tashin hankali Hawwa tace.

"Aunty Humairah Lafiya? Please wannan kallon fa..?!"

A hankali INdo tasa hannu ta rungume Hawwa cikin rawar murya tace.

"Yaya Hawwa kema sokike Yaya Abubakar ya mutu? Yanzu na buga mai waya wani ya d'auka yace min me wayar ya mutu ashe kema sokike ya mutu? 'Dazu ni narakasu mota suka shiga shida malam Sadeeq amma meyasa kike son yayanki ya mutu? Kinga yana sona dayawa d'azu fa har cemin yayi yana son duk wani mesona kuma zai sani a makarantar abuja..."

"Kiyi hak'uri aunty Humairah nima inason Yaya Habu amma Allah yafimu sonshi shi yasa yayi hatsari..."

Hawwa ta fad'a tana kuma sakin kuka, da sauri INdo ta hankad'a Hawwa baya iya k'arfinta jikake gam..! ta bugu da kujera cikin kukan bak'in cikin maganarta yasa INdo cewa.

"Daga yin bikin mu shine zaki mana addu'ar ya mutu sabida bakya sonmu, toh insha Allahu sai Isyaku ya riga dacta mijina mutuwa fatanki ya biki, ance miki Garba ne ya mutu shine zaki zo kice Yaya Abubakar ne dan bak'in ciki..."

Umma ce tayi saurin toshewa INdo baki cikin rufewar ido ta fara tureta domin ta baya ta rik'ota ta kuma toshe mata. Cikin kwantar da murya Umma kishiyar Maman su Sadeeq take mata magana a hankali.

"Kinga Aisha kiyi shiru kinga mutane sun fara cika gidan yi hak'uri taho muje ki zauna kinji 'yar albarka."

Tana nishi Umma taja ta still bata dena yiwa Hawwa kallon banza ba duk kuwa da cewar ta girmeta nesa ba kusa ba amma cewar Abubakar d'inta ya mutu shine ya d'arsa wata k'azamar kiyayya a zuciyar INdo.

Fateema ce ta fito idanunta jawur ta kama hannunta suka koma cikin d'akin Mama, suna zama amma sai mita INdo takeyi Mama ta shigo ta kalleta tare da cewa.

"Aisha kidinga hakuri kinji ko?"

INdo tace "Toh Mama ki gaya mata bana son wasan mutuwa."

"Toh zan gaya mata tashi muje ki wanke fuskarki da sabulu."

Babu musu ta mik'e suka shiga bathroom saida ta gama wankewa sannan Mama ta kamo hannunta suka wuce, d'akin Abba suka shiga yana zaune yayi shiru yana bud'e likkafani gefe turare ne a kusa dashi suka shiga bayan Mama tayi sallama. Sake gaisawa suka yi da INdo sannan Abba ya kalleta tsawon lokaci ya kasa cewa komai, can dai ya nisa yace.

"Aisha ke musulmace ko?!"

'Dan murmushi tayi alamar kunya tana sunkuyar dakai tace,

"Eh Abba."

"Alhamdulillahi ina son sanar dake Abubakar dai Allah ne ya bani shi, nina raineshi tundaga zanin goyo har girmansa da temakwon Allah, bayan ya girma ya mallaki hankalinsa shida d'an uwansa suka d'auke min duk wani nauyi nasu dana k'annansu, kafin ya aureki ya nemi auran wata yarinya Allah ya k'adarta beyi ba sai dake, toh Allahn daya baki Abubakar Aisha ya k'ar6i abinsa domin yanzu haka suna hanya za'a kawo gawarsa ina son ki daur...."

Bek'arasa ba yaji ta fashe da kuka, kusa dashi ta rarrafo tare da rik'o Hannunsa tana jijigawa tana fad'in.

"Abba... Abba wallahi ba dacta bane, ba shine ya mutu ba shi yatafi abuja k'ila dai malam Sadeeq ne, dan Allah Abba karku ce haka wallahi yace zai dawo ya tafi dani can garan..."

Mama Abba ya kalla alamar tazo ta zanye ta, tana zuwa INdo ta juya kanta tare da rik'o hannunta itama tana cigaba da magana tana basu rabarin abinda yace zai yi mata nan gaba sai kawai itama Maman ta fashe da kuka Abba ya fara mata fad'a amma ina ta kasa yin shiru bare ta bawa INdon.

"Kutashi kuje yanzu suna hanya zasu kawo shi, karku sake kubarta tafita ko'ina kinajina...?"

Mama ta kad'a kai tare dajan hannun INdo suka shiga gidan sai ihu take mutane na kallonta cikin tsananin tausayawa.

Tana shiga ciki ta zu6e ak'asa jikinta sai rawa yakeyi aka rufa a kanta kowa sai nemar mata d'auki yake ta zame jikinta daga na wata mata tana kallon Matan tace.

"Sani zantafi."

Umma ta rik'ota itada Fateema ta fara tirje musu dama INdo yaya lafiyar kura, dacta ne yasanta ya kuma san yadda zai biyo mata gashi babushi dan haka abin nata ya kuma yawa.

Kullesu akayi a d'aki babu me fitowa suna jiyo kukanta har aka dawo daga d'akko gawar Abubakar, d'akinsu aka kaishi Sadeeq tamkar wani zararre fuskarsa fal hawaye idanunsa sunyi luhu-luhu tamkar kurji ya fito ya shiga cikin gida yana neman Mama. Da kyar ya iya tambayarta zani ta mik'e ta bud'e d'akin, suka shiga.

Gaidashi mutanan d'akin suke suna mai gaisuwa, yana furta "Alhamdulillah." INdo tayi zumbar ta mik'e daga ruk'on da Zulaihat tayi mata, lokacin Mama ta mik'a mai zannin ya k'a6a kawai yaji INdo ta mak'aleshi katak'am tamkar ba rik'on mace ba tana kuka tana cewa.

"Dacta ka dawoko? Nasan dama bazaka barni ba dan Allah da manzansa kace min Malam Sadeeq ne ya mutu ba kaiba, wallahi kaga zanyi kwalliyar da kace irinta d'azu, mu koma gidanmu nan kana da mak'iya ciki harda Abba duk fatan mutuwa suke ma..."

"Aisha sakar ni please."

Sadeeq ya fad'a yana 6an6areta daga jikinsa amma tamkar mutum biyu ne suka rik'esa, ya rasa dalilin dayasa takeja masa mugayan alkaba'i tun suna makaranta nan fa su Mama suka k'arasa suna nuna mata bashi bane amma tak'i sakinsa cewa take.

"Duk inda zahi zan bihi wata k'ila akwai masu bibiyarsa basa sonshi toni ina sonsa."

Janta yayi ganin ta mak'ale suka k'arasa bakin gado ya zaune tare da nunawa Fateema alamar tazo ta zauna kusa dashi. Tana zuwa INdo ta kare shi alamar karta ta6ashi Fateema ta toshe baki kuka na shirin kwace mata, haskilowa kawai takeyi tasan da shi ya rasu k'ila da tuni itace a cikin wannan yanayin da INdo take ciki.

Kabeer ne ya shigo ya kar6i zanin domin sam INdo tak'i sakin Sadeeq, Mama kuwa so take ta 6an6areta domin tasan hankan ba dacewa bane kuma INdo tashiga cikin takaba hakan yasa ta fara sanya ta cikin dokokin da musulinci ya tanadarwa ga duk macen da mijinta ya rasu...








*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu


Page *24*

Koda sukaje kauyan Sani bak'aramin mamaki Fateema tayi ba da ganin gidan su INdo da kuma kauyan da suke, lallai Allah ya d'aukakata daya aura mata Abubakar har kuma tashiga wannan uban gidan wanda yafi nata komai da komai. Basu jima ba Sadeeq yace zasu koma ya bada dubu ashirin Inna da malam Hamza suka dinga yi mai godiya amma INdo fateema kawai tayiwa sallama ta koma gida 'yan garin suka cigaba da zuwar musu gaisuwa.

Rayuwa gaba d'aya ta sauyawa INdo komai yayi zafi tunda ta dawo kauyan Sani komai nata ya canza, tana takaba a gidan su kamar yadda malam Hamza ya buk'ata sai dai itace inzata bayan gida sai abata sanda da wuk'a wai ta tafi da ita ko idan zatayi bacci toh ruwanta a buta da wuka wai mijinta yana biye da ita duk da cewar ba'a gidansa takeba. Sannan ta dinga tafiya a hankali karya tad'iyeta. wayace haka ake zaman takaba?wannan ba musulinci ya koyar dashi ba kawai mutanene suka maidashi al'ada har hakan ya fara zama kamar ibada. Satin INdo biyu a gida lokacin sati uku kenan da rasuwar Abubakar su Mama sukaje garin domin ita sam hankalinta ya kasa kwanciya, a zaure suka tarar dasu INdo suna tsinkar zogale harta fara komawa kalarta ta dah gashi dai jikinta da kaya masu kyau amma babu tsafta tunda ta dawo sau biyu tayi wanka wai ai duk cikin takaba ne. su Hawwah suka dinga kallonta cikin tsananin mamaki ita kuwa ta kasa 6oye farin cikinta da ganinsu.

Bayan sun gaggaisa ne Mama ta kasa yin shiru ta kalli INdo dake tsakiyarsu Haleema tace.

"Aisha ya naganki haka?duk kinyi wani iri anya kina wanka da kula da lafiyar jikin ki?!"

Cikin rashin damuwa tare INdo tace.

"Ai Mama nida nake takaba ai ance ba'a wanka sai dai a sati sau d'aya shi yasa ma banayi..."

"Subahanallahi inji waye ya gaya miki haka?"

INdo tace "Su Inna ne."

Inna nacan tana k'ok'arin had'a dambu ta samu tabasu suci Mama tace.

"Zonan Aisha na shiga uku ba haka ake yi ba a musulunci, ba haka qur'ani ya gaya mana ba."

Tashi INdo tayi zuwa kusa da Mama ta zauna Mama na kallonta cikin tsananin tausayawa ta janyo ta jikinta tace.

"Mecece Takaba Aisha?!"

INdo tayi shiru sai faman wulk'ita idanuwa takeyi Mama tace.

"Aisha Takaba dai itace Zaman da mace zatayi bayan rasuwar megidanta na wad'ansu kwanaki sanannu a cikin gidanta batare da tayi ado da kwalliya ba, ba kuma data kuma yin wani auren ba, ko sanya dukkan abinda zai ja hankalin wani a jikinta ba na tufafi ko kayan k'arau. Aanan Takaba ta sha babban da Iddar saki, shi yasa naso a barki a can domin d'an zaman da kikayi a gidan mu na gano cewar kinada gyara a cikin rayuwarki. Banda iyayanki sun kafe kancewar gara kitafi babu me zuwa ya zauna dake a cikin gidanki sannan kowa yasan mijinki ya rasu gashi idan kikaga Sadeeq wani tashin hankalin ne da bazan bari ba wallahi yanzu gashi kinzo nan sun k'ara dilmiyar dake cikin wani duhun kan.

Wallahi mahaifinki gaddama garesa Aisha ba yadda ba'ayi dashi ya barki ba yace dasun dawo bakwai za'a tafi dake sabida baya son abinda kikewa Sadeeq. Shin kinsan Gwargwadon kwanakin Takaba a musulunci Aisha?"

INdo ta girgiza kai alamar a'a Mama ta d'ago ta daga jikinta tace.

"Alokacin da mutun ya rasu, to zai bar iyalin shi ne a d'ayan hali guda biyu, kodai ta zama tanada Juna biyu ko kuma bata da shi. Idan bata da juna biyu to Takabarta itace tayi Wata hud'u da kwanaki goma Kamar yadda Allah yace cikin Suratul-Bak'ara _Kumma dukkanin mazan dake rasuwa daga cikin ku subar matayan su, to matan zasu zauna wata hud'u da kwana goma aya ta d'ari biyu da talatin da hud'u 234..._

To amma idan ya rasu ya barta da juna biyu a wannan lokacin k'arshen Takabarta shine ta sauk'e abinda take dauk'e da shi koda kuwa ranar da ya rasu ne ma'ana ta haihu ko tayi 6arin cikin. Misali ya rasu 10:00am na safe ita kuma ta haihu 10:05 na safiyar, shi k'enan ta kammala takabarta, idan wani ya gani yace yana so aka d'aura aure 2:30 na ranar aure ya d'auru _(ana k'ar6ar gaisuwa ana d'aurin aure)_ Dalili kuwa shi ne. fad'in Allah (s.w. a) a cikin Suratut-Talak aya ta 4 _Kuma dukkanin mata masu juna biyu to lokacinsu shine su sauk'e abinda suke d'auk'e dashi_ da kuma Hadisin Subai'a Al-aslamiyyah, Ita ta kasance tana auran Sa'ad Dan Khaulah, shi kuma ya fito ne daga gidan Amir d'an Lu'ayy, yana daga cikin wad'an da suka halarci yak'in Badar, sai ya rasu yabarta a halin bankwana tana da juna biyu, bata ko jima ba bayan rasuwar shi saita haihu, a lokacin data kamma biki sai tai kwalliya, sai Abu-Sanabil Dan Ba'akk yazo wurinta, shi kuma ya fitone daga gidan Abduddar, sai yace da ita Lafiya naga kin cancara ado haka, ko kina son ki aure ne? Na rantse da Allah lokacin auranki bai yi ba, harsai kin yi wata hud'u da kwana goma. Sai Subai'a tace Yayinda ya fad'a min haka maraice na yi sai na tattara kayana naje wurin Ma'aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, na tambaye shi hakan, sai ya ban amsa da cewa ai na kamala Takabata tun lokacin dana haihu, ya ban dama da inyi aure a duk lokacin da naga dama. Yanzu ke Aisha kina da ciki?!"

INdo ta kalli Yayya Hawwah kafin ta maida idonta kan Mama tace "Wallahi ban sani ba nima." Mama ta sake kallonta sannan tace.

"Kinyi al'ada sanda kika dawo?!"

INdo ta sunkuyar da kai sannan tace,

"Ai yanzu ma haka inayi yau kwanana biyu kenan."

"Hazbunallahu wani'imal wak'il, yanzu duk da kina wannan jinin Aisha bakya wanka?!"

INdo tayi shiru jin yadda Mama tayi magana da alama abin mamaki ya bata da haushi ita kuma ya zatayi tunda ance mata haka akeyi. Inna ce ta shigo tana tayi musu sanna tare da kawo musu ruwa a kwanan shin ruwan malam

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login