Showing 36001 words to 39000 words out of 85627 words
kafin ta koma gida. Haka akayi suka yi gadin gidan Allah kuma ya temakesu babu wanda yaje. Washe gari ta basu 10k suka tafi, ta ciro atamfa d'aya ta bawa Nafeesa tayi ta murna sannan ta ciro tirmi biyar ta bawa Inna tace tasa da biki. Inna tace a'a itama INdo ta dage tace tabar mata. Cikin shaddojinta kuma ta za6o wata ash tace abawa babanta, gaskiya INdo batada kyashi wajan bawa iyaye abunta amma fur taki bawa Sagiru yayi mitar yayi magiyar tace bazata bayar ba yana da kud'i. Aikuwa yaji haushi duk abinda tasashi bayayi mata shima.
***
Kowanne 6angare shiri akeyi ta kowanne side, 6angaran Fateema anje an fara jere haka itama INdo an fara, saidai tsarin gidan yasa bazasu iya cewa sai sun saka mata komai ba domin basu da halin yin hakan. Iya d'akinta kawai suka sawa kaya sai parlon farko dining area kuwa kokalansa basuyi ba gashi gida yayi masifar yin kyau domin yafi na Sadeeq had'uwa.
Ana sauran sati d'aya biki Abubakar ya dawo kano, gidan su harya fara cika da bak'in nesa sai tsiya suke mai da masu nuna cewar ya auro 'yar talakawa ga gida har gida amma babu kaya. Sharesu yayi yana yin wanka Sadeeq yazo suka fita. Gidan Sadeeq suka fara zuwa sai sambarka domin kayane nagani na fad'a aka zubawa Fateema, royal ne furniture d'in sannan babu inda va'a k'awata ba sannan suka wuce gidan Abubakar babu abinda yaji aransa na 6acin rai suna shiga cikin bedroom d'in INdo ya fad'a kan gado katifar ta lotsa da alama sakance kuma ba vita form bace ya ware hannuwa yana cewa Sadeeq.
"M twinnie remain 6days na kwana anan nida Humairah tah."
Sadeeq yayi murmushi tare da girgiza kai gaba d'aya INdo ta rikita mai d'an uwa, shi har yau ya kasa manta INdon da ta baya can domin duk sanda zai tuno ta a k'azamarta yake haskilota har tausayin Abubakar yake idan yaka yana wani abun dominta.
Cikin kwanaki uku Abubakar yasa aka sake zuba mai wasu k'awatattun furniture's a inda ba'a zuba ba aka sanya labulaye da site na dining area ba tare daya sanar da kowa ba sai Sadeeq domin cikin dare akaje akasa komai harda plasma TV. Koda dangin INdo suka dawo gidan ba k'aramin mamaki suka yiba.
Ana gobe kamu/yini da d'aurin aure....
*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *âš—âš—MUSAYAR ZUCIYA...âš—âš—*
♥♥
♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
Page *19*
Suna cikin d'akin su kowanne yana k'ok'arin k'arasa had'a ragowar kayanshi a cikin trolley domin da daddre idan zasu tafi gidajen su kowa ya tafi da abinsa, Abubakar sai murmushi yake yi Sadeeq na kallonsa amma be tambayesa ba domin yasan dole ya gaya mai tunda abin da alama na farin cikin sune.
Jin yayi shiru yasa Sadeeq yin gyaran murya Abubakar ya sake yin dariya ya ganosa shima sarai hakan yasa shi k'in gaya masa saya wanashi tukunna, Sadeeq ya sake d'aukar towel yana yarfewa amma still Abubakar yayi shiru ganin haka yasa Sadeeq yin magana da cewa.
"Kai twinnie kasani a gaba sai faman smiling face kakeyi, kagaya min muyi tare kak'i."
"Oh sorry ai bansan kana son jiba, kawai tunani nakeyi naga tunda aka haifemu har muka girma bamu ta6a raba d'aki ba indai muna cikin garin nan, amma sai gashi m twinnie kana cikin garin kano Ina ciki amma mata sunsa zamu rabu muje mu kwana kusa dasu."
Shima Sadeeq murmushin yayi yana k'ok'arin zuge zip d'in trolley d'in, shi kansa haskilo hakan yake yana hangosa da Zarahn shi abar kaunarsa. Duk jinsu sukeyi tamkar wasu sababbi a cikin duniyar suna jin wani nishad'i Abubakar yana hango yadda zasu kwashe a daran yau shida INdo ya kuma yin wani murmushin har yana fitar da sauti Sadeeq ya kuma kallonsa tare da mik'ewa yana cewa.
"Amma dai ba abinda ka gaya min kad'ai kesaka wannan farin cikin ba dan abin naka yayi over..?!"
"Ina tunanin yadda zamuyi rayuwa ne da Humairah, ina ganin kamar bazan iya barinta anan ba kafin a gama gyara min gidan danake acan, twinnie advice me please."
Mamaki Sadeeq yake ganin wai INdo Abubakar yake yiwa wannan sambatun tun kafinma suyi rayuwar aure ya kuma fahimtarta. Jan trolley d'insa yayi yakaita saitin k'ofa sannan ya dawo yana k'ok'arin cire singlet d'in jiginsa zai shiga wanka dan sai anfara d'aura nasa auran sannan zasu wuce ayi nashi yace.
"Toh mezai hana idan kagama 2weeeks d'innaka kutafi tare sai ta zauna a gidan haka tana ciki ana gyarawa ai tasaba da rayuwa a irin wannan yanayi bazata damu ba."
Wani banzan kallo Abubakar yayi mai kamar yasan hakan zata faru yak'i kallonsa saima saurin shigewa toilet dayayi yana murmushi ciki-ciki. Kwafa Abubakar yayi tare da zuge tashi trolley d'in sannan ya kira INdo a waya ringing biyu ta d'auka yaji muryarta a dashe tana gaidashi yayi dariya yana cewa.
"Kai babyna tun yanzu.?!"
Tayi dariya murya a dashe tace "Tun jiya da yamma."
Yace "Nikam banajinki amma tunda naji kad'an bari na kyaleki inyi wanka kafin gobe kizo kiyi min.."
Kit.. Yaji ta kashe wayar dama yasan za'arina yayi dariya tare da ajiye wayar ya gama kimtsa komai nashi shima Sadeeq yana fitowa ya shiga kafin ya fito har abokansu sunfara zuwa. K'arfe 11:00am suka fito cikin shiga iri d'aya hatta aikin babbar rigar da agogonan su takalminsu da huluna duk iri d'aya ne sai faman k'amshi suke zubawa lokacin gidan yacika da mutane, waje suka koma inda maza suke suna gaggaisawa kafin a d'unguma a tafi gidan su Fateema bakunan su kaf yak'i rufuwa kai daka gansu kasan suna cikin farin ciki.
Shad'aya da rabi dai-dai dubban mutane suka shaida auran Sadeeq Salman Harun da Fateema Idris yahaya. Sadeeq murna kamar zuciyarsa zata fito sai gaisawa suke da mutane wanda yawance basu gane waye angon yanzun sabida kowa akayiwa murna saiya amsa. Bayan sun shiga gidan su Amaryar sun gaisa da iyaye amarya ta fito cikin makeup tayi masifar yin kyau cikin farin les riga dazani tazo ita kanta kasa gane waye nata tayi saida aka ce za'ayi musu su biyu sannan aka musu su uku itace a tsakiya, ana gamawa suka fita.
Bayan an koma gida mutane sunci abinci sukuma suka kumayin wanka suka sa wasu fararan kayan wanda suma babbar rigace kalar surfanine ba irin wanda suka cire ba nan ma sunyi masifar yin kyau Abubakar yayi ma INdo text message cewar gashi nan zasu taho.
Motoci ne reras sunfi ashirin aka tafi Sumaila kauyen Sani unguwa kuwa unguwar su INdo akayi parking motocin, ana gayawa su INdo jikinta ya fara rawa hankalinta ya tashi tsoro ya fara shigarta suna zaune a gidan Rukayya ta kule cikin uwar d'akinta tayi shiru domin su Uwani su Rukayya duk suna bata labarin aure Abubakar nata kiran wayarta tana gani tak'i d'auka shi kuma befasa kiranta ba. Sai da su baffajo na saye suka shigo zauran gidan sukace a fito musu da ita sannan ta fita jikinta ya kuma yin sanyi. Hannayenta suka kama sanye take cikin shadda maroon color sai hijjab datasa fuskarta tashi kwalliya kaida kagani kasan amarya ce su Baffajo suka wuce da ita wajan masu d'aurin auran Abubakar na zaune aka zaunar da ita a kusa dashi ga uban maza waliyin amarya ya tambaye ta.
"Aisha kina son Abubakar wanda za'a d'aura muku aure yanzu..?!"
Kan INdo a k'asa jikinta sai uban rawa yakeyi Abubakar hankalinsa yayi mugun tashi ganin tayi shiru, ana k'ok'arin sake tambayarta ta d'aga Kai alamar Eh sai a sannan ya sauke wata uwar ajiyar Zuciya yana dafe k'irji shima wakilinsa ya tambayesa.
"Abubakar kana son INdo zaka aureta da yardarka ba takurama akayi ba ko..?!"
Yace "Eh uncle." Sannan akayi kabbara aka fara addu'ar d'aurin aure a gurin aka damk'awa INdo kud'in sadakinta naira dubu tamanin lakadan kowa ya shaida sannan su Baffajo suka shiga da ita cikin gida, fuskarta kunshe da murmushi ganin yadda Abubakar d'inta ya tsure taji ta k'ara sonsa cikin zuciyarta.
Shigowa ango yayi da abokansa cikin gidan aka fara hotuna wasu sun tsaya sun shiga cikin matan yayin da wasu abokan da girman kai yayi musu kwaliya suka ja baya cewar mutanen basuyi musu ba wata ma mata tukin tuwo sukeyi suka saki dan ayi hutonan dasu, hatta Sadeeq buya ya dingayi a bayan Abubakar.
Shikuwa babu ruwansa duk Matar data matso zai matsa suyi tare za'ayi musu shida INdo yayi k'ok'arin cafko hannunta ta cikin babbar rigarsa, da sauri ta kallesa cikin sa'a akayi musu hotuna sai hakan ya bada style zata yi magana yayi saurin sakin mata yana dariya Sadeeq yazo akayi musu su uku sannan suka tafi sam an hanashi amaryar su ke6e har suka kammala komai aka bar motocin da zasu tafi da amarya sukuma su Sadeeq suka wuce.
Duk zaman dasu Abubakar sukayi a garin an hanasu ganin amarya sunyi magiyar sunyi duk iya yinsu amma mutanan bikin nan suka hana. Sai bayan la'asar an shirya amarya za'a tafi sannan Abubakar suka tafi yabar abokansa da zasu d'akko su duk da yasha wulak'anci wai yaja zasu d'akko 'yan kauye a motarsu.
INdo na lullu6e su Inna nayi mata fad'a idanta har’wayau hawayen sunk'i zuwa sai Innace keyi dan tama kasa tsayawa sosai tayi mata fad'a sai faman cewa takeyi. "Tabi mijinta tayi zaman aure." Sune kawai kalaman Inna, haka ma malam Hamza shima abinda yace mata kenan sai kuma nuni dayayi mata da yadda Inna takeyi mai biyayya. 'Yan uwa duk sunyi mata fad'a ana k'ok'arin fita da ita saiga malamarsu ta islamiya malam Hansa'u tazo yi mata Allah yasanya alkhairi ta jata d'aki suka zauna ta Fara mata nasiha.
"Toh Aisha yau dai gashi Allah ya kawo ranar da kika koma k'ark'ashin wani ba iyayanki ba, yanzu ya koma shine uwar shine kuma uba shine danginki. Aisha kiyi biyayya yin biyayya ga mijinki shine zaki samu aljanna, karki manta da karatun da ake koya muku duk abinda mijinki yace kiyi toh kiyi indai besa6awa addininki ba, ke ko cewa yayi Aisha ga wuta fad'a karkiji d'ar kifad'a din kawai, Aisha kibi aure karki yiwa mijinki rashin kunya ko gaddama ko kiyi musu dashi yin hakan Allah zaiyi fushi dake fushin Allah kuwa babban had'arine akan kowanne halitta.
Allah ya bada zaman lafiya Aisha ya kad'e muku fitina a cikin auranku ya baku zuri'a masu albarka tashi muje akaiki gidanki mai tarin ni'ima da albarka.."
Sai a lokacin INdo ta fara kuka tsoro ya kuma shigarta har aka shigar da ita jibgegiyar motar abokin Abubakar dayazo daga Abuja.
Su uku suka shiga sai driver da friend d'inshi a kusa dashi, ana gama cika motocin suka d'auki hanya shikenan INdo tabar kauyen Sani saidai tazo da ziyara Allah ya d'agata. Gudu suka dingayi kafin wasu awanni sun k'arasa k'ofar gidan su ango lokacin duhu yafara yi.
Bayan an kaita su Mama sunyi farin cikin shigowarta zuri'arsu sunyi mata nasiha aka sake d'inguma aka kai INdo gidan Abubakar masoyinta farin cikinta abin alfaharinta, fuskarta a lullu6e aka shigar da ita cikin d'akinta.
Ita kuwa Fateema saida akayi sallar isha'i sannan aka kaita gidansu Sadeeq itama su Mama sukayi farin cikin shigowarta cikin su sannan aka wuce da ita gidan Sadeeq farin cikinta abin kaunarta, ta riga ta tsara musu yadda zasu gudanar da rayuwar auransu abinku da 'yar boko wayayya.
Masu kawo INdon kauye sai da suka kwana Abubakar yace abarsu sabida dare yayi kuma duk masu motocin sun tafi wai bazasu koma wannan kauyan ba yadai sha iskancin abokai wanda hakan besa yaji kaunar INdo ta ragu koda da kwayar zarra ba. Sadeeq suka raka gidansa aka yi musu nasiha shida amaryar sannan Abubakar suna k'ok'arin fita yace ma Fateema dake lullu6e cikin mayafi.
"Ke..! Sauran kibawa twinnie d'ina wahala ko kiyi mai rowa."
Tana jinsa ta k'i cewa komai har suka fita Abubakar ya kalli Sadeeq tare da cewa.
"Kai twinnie wallahi kabi yarinyar mutane a hankali, nasanka sarai a mafarki ma kana wuce k'a'ida bare kuma yau gaka ga mace mallakinka. Idan ka kirani da safe ba zuwa zanyi ba ah toh..."
Hannu Sadeeq ya bashi suka tafa suna dariya kafin su rungumi juna Sadeeq yace.
"M twinnie har gobefa kai saurayi ne sorry to you wallahi but zaka iya sato Aishan ku koma wani d'akin fa."
"Nop karka damu zan hakura harsu tafi ai daga yau ne gobe zan samo musu mota ta maidasu."
Kamar karsu rabu haka sukeji amma babu yadda zasu yi yana fita ya rufe gidan ya koma ciki. A hankali ya zauna kusa da ita tare da yaye mayafin kanta cikin kunnanta yasanya bakinsa yace.
"Amarya muje kiyi alwala muyi sallah."
A kunyace ta mik'e ya kama hannunta ya kaita har bedroom d'insa cikin toilet sannan ya fito ya shimfid'a musu sallaya ya ajiye mata sabon hijjab, tana fitowa shima ya shiga yayi alwalan sannan yazo yajasu sallah suka yi raka'a biya ya dafa kanta yayi mata addu'a sannan ya kalleta yace.
"Nasan akwai yinwa a cikin nan tashi muje na baki kici bana son kwana dayinwa."
Ya fad'a yana shafa mata ciki, Fateema cike dajin kunya ta mike yayi saurin rik'ota tare da janta jikinsa suka nufi parlor. Kajine gasassu sunsha kayan had'i da lemuka da fresh milk suka zauna yafara bata, a yangance suka gama ci sannan ya wanke hannunsa ya jata suka shiga d'akinsa.
Kayan bacci yasa ya d'akko wata shegiyar rigar mata ta bacci ya mik'a mata yace tasa, ta d'aga rigar nan ta ganta 'yar firit Fateema aka dinga raba idanuwa ta kasa tashi tasa yayi murmushi tare da cewa.
"Bari nazo na temaka miki."
Ya mik'e daka bakin gadon tana ganin haka tayi wuf ta shige toilet yayi murmushi yana lasar leb6ansa. Fitowa tayi bayan tasawo sai kuma ta nad'e jikinta da mayafi kamar tasa lafaya ta kwanta a kunyace, shi kuma yayi musu light of (kafin naji kici-kicin su k'ila k'ok'arin kwance mata yake yi nidai Hajja nayi kwana dan d'akin badai duhu ba yau su Sadeeq za'a angon ce na fita zuwa gurin Abubakar.).....
*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *âš—âš—MUSAYAR ZUCIYA...âš—âš—*
♥♥
♥
A true life story
Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*
*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu
Page *20*
Around 1:45am Abubakar ya shiga cikin gidan nasa bayan ya gama kulle ko'ina yana son lek'awa yaga yasuke amma yana tsoran yadda zai shiga ya gansu dan yasan matan kauye basu fiye kwanciya da riguna ba dan haka ya koma yashiga d'akinsa ya kulle.
Wayar INdo ya dinga k'ira amma ba'a d'aga ba ya ajiye tare da shiga wanka. Sukuwa su INdo bayan an kawota tafita suka zagaya gidan farin cikinta ya kasa 6oyuwa ganin irin gidan da take ciki gida irinna cikin films had'add'e wanda ko cikin mafarkinta bata ta6a zaton zata ta6a koda jikin gidan ba, tun shad'ayan dare suka barbaje bayan sinci sunyi hani'an ga iskar fanka na kad'a su ai babu wanda ya kuma motsawa munshari kawai kakeji yana fita hahhhussss ta kowace kusurwa.
Tun sallar asuba yafita, su kuma suna tashi suka hau shirin tafiya, saida yaje gida yasa Mama ta bada abinci aka kaimusu sukaci wajan k'arfe goma na safe ya kawo musu buses biyu ya biya masu motar sannan suka tafi sunata yiwa INdo Allah sanya alheri. Saida yaga sun tafi sannan ya shiga gidan, a tsaye ya tarar da INdo tana wajan dining bakinta a bud'e sai shafar kujerun takeyi ya tsaya yana kallonta ba tare da tasan yana tsaye ba.
Yana kallonta ta d'an d'osana d'uwawunta akan kujerar sai kuma tayi saurin mik'ewa tana dariya tana karkad'e gurin, ya shigo a hankali cikin rashin sa'a ta hangosa ta cikin glass d'in drawer flat's na dining dake wajan. Da sauri tayi hanyar shiga d'aki zata gudu yayi saurin cafko ta yana dariya yasanya ta a jikinsa.
Fisgar jikinta takeyi zata gudu amma ya hana hakan faruwa, kanshi ya zura a wuyanta ya fara shin-shina wuyanta yana sanya siririn hancinsa cikin kunnanta iskah na shiga ciki, INdo taji wani irin abu hankalinta ya fara tashi kwakwalwarta ta fara aika mata da wasu bakwannin al'amra.
Jin hannunsa a kan k'irjinta ne yasata kwallara mai wata uwar k'ara, Abubakar yak'i sakinta saima jikin bangon k'ofar da zata kaita bedroom d'inta ya jinginar da ita gaba d'aya ta tsure ya kamo fuskarta da duka hannunsa biyu, bakinsa yakai saitin nata zaiyi kissing d'inshi INdo ta kwalalo mai ido tana bin harshensa da kallo tamkar idonta zai fad'o sai girgiza kai take alamar bata so.
Ganin kamar abinda yake shirin yi mata ne bata so yasa shi sonyi mata dan ta gane cewar ba wani abun aibu bane. Gate yajiyo ana bugawa nan INdo ta fara sauke numfashi dan tasan dole yanzu yaje ya bud'e, ba zato bare tsammani kawai taji ya zura mata tongue d'insa tayi-tayi ta datsa bakin amma ta kasa ya fara tsotsa tare da zame d'ankwalin kanta yana shafar gashinta. Nan da nan jikin INdo ya fara kyarma tamkar shocking yajata yayi k'ok'arin tattarota zuwa jikinsa still mouth nasa na cikin nata idanunta a tamke ta dunkule hannayanta jira kawai takeyi taji zubar fitsari.
Sake bugun gate d'in ake da k'arfi amma yak'i kulawa hankalin INdo ya kuma tashi, sai da yayi mata ya tabbar da sakon salonsa na farko ya shigeta sannan ya cikata aikuwa ta zandama d'aki da gudu hartana bugewa da bango yayi dariya yana kallonta harta shige sannan ya gyara wuyan rigarsa ya fita yana bud'ewa yaga sisters d'in Mamansu ne da yaransu ya fara sosa k'eya aunty Shafa'atu ta kallesa dakyau sannan tace.
"Doctor ko baku tashi bane ba tun d'azu sai faman bugu mukeyi..?!"
"Ah mun tashi mana aunty yanzu ma na koma ciki da