Showing 120001 words to 123000 words out of 126031 words

Chapter 41 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt

da suka kawo mata ya janyo gabansa, ya fiddo kwalin boost (locozade) karami ya bude ya saka straw a ciki ya mika mata tunda Inna tace madara zata sanyata amai. Saida ta harare shi sannan ta yunkura ta tashi zaune. Har yanzu murmushin bai bar fatar bakin shi ba yace “karbi ki sha wannan Maman Aboulkhair. It will boost your energy ki daina wannan kwanciyar kamar ruwaâ€.
Ta mika hannu ta karba jikinta har rawa yake yi sabida yunwa, duk abinda ake dafawa a gidan babu wanda zuciyar ta ke sha’awa. Wadannan masu ruwa-ruwan su take so. Nan da nan ta shanye ta bashi kwalin, zai bude wani ta nuna fresh milk din tace shi take so. Ya bude ya zuba mata. Ta kafa kai kamar Allah ya aikota ta shanye gorar madarar nan bakidayanta. Tayi wata irin ajiyar zuciya mai nauyi. Kafin ta sunkuya ta fashe da wani kakkarfan kuka.
Tace ita tun kafin su zo Niger rabon ta da period dinta. Amma ta saba tana tsallaken wata shi yasa bata damu ba. Idan ciki ne ita ina zata tsoma rayuwar ta?
Aboulkhair yayi mata wani irin kallo, yace “shi uban Dan yace baya so? Koko bashi da yadda zai yi da shi in an haife shi?†Tace “ni bazan haifi Da bana gidan ubansa ba†yace “to da kyau, kisa a ranki kin haife Dan nan lafiya kin gama, ko kwarzane kika yi mishi muma mun san hanyar kotu. Taimaka min da fitsarin ki Yesmin ta kawo min yanzuâ€. Wata uwar harara ta zabga masa ga idanun kaca-kaca da hawaye tace “bani badawa din†mikewa yayi daga zaman da yayi a gabanta yana wani makalallen murmushi. Allah-Allah yake ya bar wajen ya kira Mu’az don yi masa wannan kyakkyawan albishir, yace.
“Rike abunki. Shi ciki ai dan duma ne da sannu zai bayyana kansa. Bansan me zai zama tukuicina na wannan albishir din ba. Oh me!â€.
Inna Kasisi ta dade da barin dakin tun sanda Aalimah ta soma kukan nan nata mai ban haushi. Yesmin dai na jinsu bata tofa ba amma zuciyarta ta cika fal da farin ciki. Tana addu’ar Allah yasa albarkacin wannan cikin Aalimah ta hakura ta komawa Mu’azzam.
Yace “zan dawo na kawo miki magungunan da zasu taimaka aman ya tsaya dana karin lafiya, saura ki ki sha, wallahi zaki ga abinda baki soâ€.
A wannan rana Aalimah yadda taga rana haka taga dare. Ta rasa inda zata tsoma ranta. Wannan ciki shi ake kira unwanted pregnancy. Tun tafiyar Mu’azzam da ‘ya’yansa bata ware lokaci tayi tunaninsu ba sai yau, kullum makomar rayuwarta kawai take tunani.
Ta tuno ranar da aka yiwa Mu’azzam albishir din tana da ciki, riritawar da ya dinga yi mata lokacin rainon cikin ta, bautar da ya dinga yi mata don ta haife masa ‘ya’yansa lafiya, yadda ya hanata girki daga samun cikin ta zuwa haihuwarta. Duka rabin rainon ‘ya’yansa shi yayi abinsa. Duk abunda ya mallaka nata ne da ‘ya’yanta. Kulawar Mu’azzam a gareta unexpressable ce. A cikin maza samun mijin da ke muhimmanta matarsa da daga girman darajarta kamar sa, abu ne mai matukar wuya.
Yau gata zata yi rainon ciki a dakin kakarta, ba wanda ya damu da ta ci ko bata ci ba sabida son zuciyar ta. Yo son zuciya mana! Laifin me Mu’azzam yayi mata data yanke wa rayuwar su wannan tsatstsauran hukuncin? Wanda ta tabbata cutuwa ne ga dukkannin su. Ba don Allah ya jefo su Aboulkhair ba, da haka zata kwana da yunwa. Ba abinda ya damu su Inna Kasisi, dan gara-gara Inna Bintou tana sassauta mata.
Aboulkhair din da ta ke fadin bazata iya kalla alhalin tana auren Mu’azzam ba, shi gashi yana rayuwa da wata macen a kan idanunta. Har da albarkar zuri’a a tsakani.
Me Mu’azzam yayi mata a rayuwarsu banda alkhairi? Abinda ya faru dasu Ubangiji ne ya rubuta shi bata isa ta kankare faruwarsa ba. Yanzu gashi sakamakon rashin tawakkalinta ta janyowa kanta kiyayya a zukatan mafi yawan ‘uwan ta. Ta janyowa kan ta rainon ciki a dakin kakarta, ta yi missing duk wannan gatan na Mu’azzam! Ta tabbata Mu’az yayi mummunan fushi da ita, tunda har ya kai tsayin wannan lokacin bai taba nemanta ba, bai taba hada ta da ‘ya’yanta sun gaisa ba, anya bata yi kuskure ba? The deadly mistake din da ba zata iya gyarawa ba?
Gashi da Ubangiji ya tashi nuna mata bata isa ta kashe auren da kwanansa bai kare ba, ya kaddareta da boyayyen ciki, wanda ke tabbatar da har yanzu tana cikin zummar mijin ta har sai ta haihu. Ko yaya yake rayuwa da yaran shi kadai? Koda yake ko tana nan abubuwa da yawa shi yake musu, a wannan fannin bata jin sa, sai ko ta bangaren lafiyarsa.
Anan din ma tana da tabbacin he is doing well, in dai da Dr. Nebrass a raye, to kowacce irin matsala zata zo masa da sauki. Yawan ibadarsa kuma zai zamo kariya a gare shi.
Abu daya take da yaqini dashi akan Mu’azzam, duk fushinnan da yake yi da ita, bazai shafi abinda ke cikin ta ba. Zai so shi tamkar sauran ‘yan uwansa.
Zata yi masa rainon abunsa, ko albarkacin sa ya dubi nadamar ta ya yafe mata kuncin data jefa shi a ciki, koda bazai yi mata alfarmar komawa dakinta gaban ‘ya’yanta ba.
A washegari kowa dake gidan ya ji batun cikin Aalimah. Anas murna ta koma ciki, domin kuwa a baya yana kirge da watannin cikar iddarta. Yanzu kuwa ya fara fidda rai duk da ance faduwar gaba asarar namiji.


A daren ranar da suka baro Aalimah, Aboulkhair ya kulle kansa a daki ya kira Mu’azzam. Yana cike da wani irin doki da farin ciki.


A can Las Vegas, adaidai lokacin Mu’azzam na yiwa yaransa shirin kwanciya barci zasu kwanta, sabida gobe litinin don haka da wuri suke kwanciya.
Ya amsa wayar Aboulkhair da hannu guda, daya hannun yana shafa kan Basma, wadda ke dan rikici irin na mai jin barci.


“Mu’az.... kunnenka nawa? Menene goron albishir dina? Aalimah dai ciki gare ta, kuma a yadda na kintata yayi watanni ukuâ€.


Gaba-gadi ya fadi sakonsa, ba tare da jan rai ba .


Wani irin shiru Mu’azzam yayi, tamkar ruwa ya cinye shi.
“Mu’az.... Mu’az kana kan layi?â€
Aboulkhair ya tambaya jin shirun nasa yayi yawa.
“I’m on the call†ya fada a matukar gajarce.
“Ba zaka yi hakuri ba ku daidaita haka ko sabida shi? I didn’t expect it to be that longer, ban zaci fushin naku zai kai har zuwa wannan lokacin baâ€
Murmushi yayi, yace “Aalimah ba zata taba sona ba Aboulkhair, I’m sure she is not happy with it. A da ne ban damu data so ni ko ta ki ni ba, abinda nafi baiwa muhimmanci shine kasancewar mu tare.
A yanzu kuwa na san how it feels to be loved by the one you love. Ciki kuma nayi farin ciki da shi Allah ya raba su lafiya in karbi Da na. Ka barta tayi rayuwarta yadda ta zabe ta. Yanzu haka aure zan yi niâ€.
Aboulkhair ya kaskantar da murya yace “na roke ka kada kayi wannan kuskuren, ka bata lokaci. Auren huce haushi kake so kayi, kuma bazai haifar mana da alheri baâ€.
Murmushi Mu’azzam yayi, har ransa ya san Aboulkhair gaskiya ya fada, auren da ya amsawa Inna zai yi na huce takaicin Aalimah ne, amma ba zai iya rayuwa da wata diya mace bayan Aalimah ba, amma wani bangare na zuciyarsa yana insisting da ya yi auren don ya huce haushin tozarcin da Aalimah tayi masa. Ta rasa inda zata ce ya sake ta sai a gaban Alkali. In ta bukata cikin sirri ita da shi ai shi me iya sadaukar da komai ne don farin cikinta da kwanciyar hankalin ta.
Har suka yi sallama bai ce da Aboulkhair ya fasa ko bai fasa ba.


Cikin kwana bakwai Aalimah ta samu karfin jikinta, sabida kulawar data ke samu daga Aboulkhair da Yesmin. Ya hadata da magunguna masu kyau wadanda suka taimaka wajen rage mata yawan aman data ke fama da shi, ga kayan dadi iri-iri kullum yana baiwa Yesmin ta kawo mata leda-leda, tuni ta barwa su Inna abincinsu sai kayan kara jini dana kara kuzari da yake aikowa. Mummy Zulaiha kuma kullum sai tayi mata waya ta tambayeta abinda take son ci, tun tana jin nauyi har ta daina. Don haka kwanon abincin ta na musamman ya koma gidan Daddy wanda Mummy da kanta ke shiga kitchen ta girka mata, kullum Yesmin da Nurat ke kawo mata.
Saida ta warware sosai ta maida jikin ta Malam yayi mata iznin tafiya Kanon kamar yadda ta bukata.
A daren ranar ta hada kayanta tsab tana cike da doki. Washegari Aboulkhair ya saya mata tikiti ta tafi Nigeria. A Abuja tayi transit kafin ta taso ta sanya layin ta na Nigeria ta kira Yaya Aboubacar ta gaya masa lokacin da zata sauka. Kafin aje Kano ta jigata sosai. Amma tarbar data samu a gidan su tasa ta mance da duk gajiyar data kwaso.
Ta samu gidan nasu da albarkar baki na musamman, Dr. Suraj Kashim wan Mama da matarsa Ilham da biyu daga cikin yaransu Mustapha da Maryam sun zo ganin gida daga kasar Canada. Maryam zata yi sa’ar Sultana itace ta biyu a ‘ya’yan aunty Ilham. Mustapha zaiyi sa’an autarsu Suhaima. Don haka tuni ta ware a cikin ‘yan uwanta data dade bata gani ba anata harkar arziki, tana ta taka-tsan-tsan kada wani cikin su ya fahimci cikin nan da bata so a sani. Sai fama take da zumbulelen hijab tun zuwanta har aunty Ilham na tsokanar ta ko Mu’azzam ne yasa ta yawo da hijabi, anan Mama take gayawa Ilham ai babu auren, ta gaya mata duk abinda ya faru.
7/13/21, 5:59 PM - Buhainat: Aunty Ilham ta taimaka mata ta sanya lallausar leshin data kawo mata, ta zaunar ta gefen gadon ta tana yi mata sassanyan make-up. Sai gyaran muryar Uncle suka ji a bakin kofa yana fadin “Ilham ina ‘yar taki ne? Ta zo suje ko tausa ta yiwa mijinta ya rage gajiyar zirga-zirgar nan da ya shaâ€. Ilham tayi dariya Aalimah ta sadda kai kamar tace kasar ta tsage ta shige. Yace “maza fito ki same shi a mota driver zai kai ku masaukin shi. Daga yau har kwana uku na sallame ku, in zaku wuce U.S kuzo muyi sallamaâ€.
Aalimah kamar tayi kuka bayan wucewar Daddy, bata ankara ba kuwa ta ji hawaye sun sauko mata data ji cewa da gaske zata bar Ilham da iyalin ta bada jimawa ba. Aunty na cewa ta yi hakuri ta bi umarnin babanta, ta bar Mu’azzam ya fanshe watannin da ya yi ba tare da ita ba cikin kwanaki ukun nan. Ta armasa masa su su shiga cikin kundin tarihin rayuwar su. Sakamakon haka Allah zai iya bata Aljannah. Ga bin iyaye ga bin mijiâ€. Dariya tayi don ta san aunty Ilham wayo take mata.
Ita ta tsitstsintar mata duk abinda tasan zata yi amfani dashi ta jefa mata a jaka. Ta dauko mata jakar suka fito tare. Mu’azzam da Uncle na bakin motar Uncle suna magana direban yana daga cikin motar. Fitowarsu yasa suka yi sallama, aunty ta bude mata kofa shi kuma Dr. Suraj ya bude masa, suka shiga suka rufe musu tare da daga musu hannu.
Har suka iso hotel din da Mu’azzam ya sauka basu yi magana a junansu ba, shi Mu’azzam waya yake da Aboulkhair yana gaya masa gashi a Canada ya zo biko, Aboulkhair yace “Canada kuma?†Murmushi yayi yace “can ta yi kaura, tunda zaman gidan Malam Raazee ya gagara, kasan mace in ta wuce zaman gida tace kuma sai ta zauna to akwai matsala, don bazata taba jin dadin sa ba, musamman a cikin dattijai†Aalimah ta harare shi ta gefen ido. Aboulkhair yace “gidan Dr. Suraj ta koma kenan?†yace “eh, in dama ta ki ba sai a koma hagu ba?†Murmushi Aboulkhair yayi yace “kuma Inna Kasisin tana can tana cigiyar ta, ta dade da saukowa, auren data ke nema maka ma da bakinta tace ta fasa, ba za’a samu macen da zata zauna da Mu’azzam tsakani da Allah cikin kowanne hali irin Aalimah ba.
Tana fadi da bakin ta “Aalimah ce ta zauna dashi a halin rashin lafiya, don lafiya ta samu bazata amince wata ta more ta ba Aalimahr baâ€. Duk zancennan da suke yi akan kunnen Aalimah sabida a hands free Mu’azzam ya sanya wayar.
Ta tsurawa Mu’azzam ido jin abinda Aboulkhair ke fada. Mu’azzam ya samu lafiya as in how? Dama lalurarsa mai warkewa ce? A take kuma kwakwalwarta ta tafi tunano mata wani zance makamancin wannan da suka taba yi da Daddynta farkon aurenta da Mu’azzam. Cewa Mu’azzam zai iya warkewa bayan samun accurate treatment na akalla shekaru goma. Kuma ya dade da cika wannan ka’idar. Yadda yake romancing dinta dazu passionately kuma cikin nutsuwa ba yadda ya saba ba. Idanunta suka cigaba da budewa akan Mu’azzam yana ta hira da Dan uwansa yana ta murmushi kamar ya manta da ita cikin motar. Irin murmushin da ba kasafai yake yi ba sai yana cikin matsanancin farin ciki. Sassalkan sajensa ya kwanta lufff akan fuskarsa ya kara masa ilhama da cikar zati. Fararen hakoransa a waje, kamar wanda aka yi wa bushara da Aljannah.
Lumshe Idanunta tayi, a lokacin data ji sanyin hannun Mu’azzam a cikin nata. Ta kuma ji motar ta daina motsi wato sun iso masaukin nasu. Direban ya daukar mata jakarta da Ilham tasa mata daga bayan mota, ya rakasu da ita har kofar dakinsu ta cikin lifter. Sannan ya sake biyo lifter ya dawo kasa ya dauki motar don kaiwa ubangidansa.


Tun daga shigarsu dakin da Mu’azzam ya sanya mukullin shi ya bude, abubuwa basu kara daidaituwa ga Aalimah ba, duniyar ta bata kara zama cikin seti ba, haka shima Mu’azzam. Duk yadda ta zaci kewar data ke jin ta yi ta Mu’azzam mai dumbin yawa ce, ashe na fatar baki kawai ta sani. Ba da sanin ta ba kowacce gaba ta jikinta tayi kewar tasa ba zuciyarta kadai ba. Da farko akwai dari-darin abin da ‘yar fargaba a tare da ita. Kafin wani dan lokaci kuma ta tsinci kanta da mika wuya bakidayan ta. Sakamakon ganewa data yi cewa Mu’azzam din da ba shine yanzu ba. Gabadaya Mu’azzam din data sani a baya ya canza mata, things are going very soft and gentle from him. Ta yarda bayan lafiya da nutsuwa harda kwas (course) a soyayya ya samu wanda a baya bashi da kamarsa.
A can baya ta haqqaqe abinda ya sani shine ya biya bukatar sa anyhow; disregarding her own emotions. Kuma akai-akai kamar cin abinci. A hakan kuma take son abinta, take kula da dukkannin bukatun sa, domin tana gamsuwa ta kowannne bangare. Amma yanzu it goes along with her own pleasure and contentment. Tare da kula da rashin jigatar da ita a matsayin ta na mai tsohon ciki. Hawaye ta soma yi na farin ciki da godiya ga Allah. Ta yarda Mu’az ya samu lafiya. Komai ya koma dai-dai yadda ya kamata ya koma. It tastes good.... It tastes romantic. Wata rayuwa ce da bata taba mafarkin samu a Mu’azzam ba.
Daga nan kuma sai barci, barcin da suka dade basu yi mai nutsuwar sa ba a kafatanin rayuwarsu. Ba su suka farka ba sai karfe biyar na asubahi, tare suka yi jam’in sallar asubah. Sun dade suna addu’a batare da kowanne ya san abinda dan uwansa yake roka akan dan uwansa ba. Aalimah rokon Allah take ya dorar da lafiyar Mu’azzam, bata taba samun nutsuwa a rayuwar aure irin ta yau ba. Tana rokon Allah ya dorar da wannan rayuwar ya dawwamar dasu cikin alherinsa.
Ga Mu’azzam, rokon Allah yake ya sauki Aalimah lafiya, ya raya musu ‘ya’yansu rayuwa ta addinin muslunci. Abubuwan da bai taba ji akan Aalimah ba, su suke kara overwhelming dinsa yanzu. Ashe wannan sune feelings.....sune emotions. ..... sune affection… sune so da kauna wadanda a baya bai san su ba? Idan kuwa har sune dan uwansa Aboulkhair yayi kokari, kokarin da a yau ya jinjina masa, yayi masa sadaukarwar da shi ba zai iya ba! Don abu na karshe da bazai iya ba a yanzu shine rabuwa da Aalimah!!!
Suna kwance kalmashe cikin jikin juna, lullube cikin lallausar duvet, sanyin Ontario na yau kamar har yafi na kullum ratsa kashi da bargo. Mu’azzam yace “umh Aalimah, gaya min yaya bayan rabo? Na same ki cikin yanayi na kwanciyar hankali da jin dadin rayuwar da ta same ki, sabanin ni da darare suka yi ta wucewa da yawansu idona biyu har ketowar alfijir. Bana komai sai zubawa ‘ya’yanki ido suna nasu baccin ina kallon fuskar ki cikin fuskokin su. Me yasa ki kayi tunanin cewa rabuwar mu ita ce mafi alkhairi?â€
Aalimah ta kwantar da kai bisa kirjin Mu’azzam tana mai jin komai na rayuwa yanzu yayi mata daidai, daidai da yadda take kwana tana addu’ar Allah ya mayar mata da shi, daga lokacin data yanke musu hukuncin da ta ke ganin shine abinda ya dace dasu bakidaya, tace.
“Ya Mu’az nima bansan dalilin da yasa na yanke hukuncin dana yanke ba, abinda na sani a lokacin shine I’m desperate, hopeless. Amma daga ranar da hakan ta faru ni kuma ban kara rayuwar farin ciki da jin dadi ba, ji nake kamar na yanke bangaren daya kunshi dukkan farin cikin na yar. It was regrettable, though, ko kai ne a matsayi na a lokacin abinda zaka yi kenan. Dawowar Monsieur Aboulkhair abin farin ciki ce a garemu amma hakika ta ruda ni sosai. Wani al’amari sai Ubangiji.
Zawarcin bashi da dadi ko kadan, bana son tunawa, kowa bai min ta dadi ba sai Daddy da Mummy, su kadai suka karbi uzrina, kai dan gata ne Ya Mu’az ban ga wanda ake so a zuri’ar mu kamar ka baâ€.
Dariya Mu’azzam ya saki yayi cuddling dinta sosai, dan kankanin bakin ta yayi kissing kafin yace.
“Kina jin dadin yimin wannan gorin Aalimah; ba wanda ake so a gidan RAZEE kama na, na yarda basu yi miki ta dadi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login