Showing 45001 words to 48000 words out of 126031 words
Chapter 16 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt
daya a kan hutunsu, don haka ta tadda note mai yawa a wurin Alex da abubuwa masu yawa da suka soma tsere mata. Sai dai tana tunawa da Abulkhair da alkawarin da ta yi masa ba ta kara kebewa da Alex ba. A cikin aji suke magana gaban kowa, Khaleesat da Yesmin su da ma nasu hutun na sati hudu ne. Islamiyya kawai suke zuwa.
6/28/21, 7:33 AM - Buhainat: HAULATU 66
%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%%
A haka satin ya kare musu, tana lissafe da kwanakin. Ranar juma’a wadda ta kama ranar zuwan Abulkhair kasa zaune ta yi ta kasa tsaye. Kwalliya ta yi ta har sau uku tana canzawa. Ba ta da lecture ranar, don haka ta makale a kicin da sunan taya Easther aiki. Nan kuwa masoyinta ta ke son yi wa girkin da zai yi farin ciki da shi. Waina (massa) ta soya masa wadda ta jika shinkafar tun daren jiya, ta markada da safe. Sai miyar ganye wadda ta ji tsokar naman talo-talo (Turkey). Ta dade da sanin Abulkhair na son chips wato soyayyan dankalin Turawa, ta zauna ta fere ta yi masa kyakkyawar suya. Mummy na office, Basma na school, Khaleesat da Yesmin suna Tahfiz dinsu. Gidan daga ita sai Easther, ta yi light make up kamar yadda ta saba, sannan ta zabo wani lallausan swiss lacelemon green mai stones da aka yi wa dinkin gown ta sanya.
Ita da Easther suna shirya abincin a diningaka danna kararrawar kofar gidan. Cewa Easther ta yi ta je ta bude, ita kuma da gaggawa ta gudu upstairs dakinsu. Ba ta san me ya sa ba, kunyarsa ta ke ji yau, kunya sosai, it has been long…har wata uku da rabi without them seeing each other (ba tareda sun ga juna ba)Ba ta san da fuskar da za ta kalle shi ba, ko wace tarba za ta yi masa. Fuskarta ta sanya cikin tafukanta ta zauna a bakin luntsumemen gadonsu.
“Yaa Allah! Grant me the courageâ€. Shi ne abin da ta furta a hankali.
Ya tambayi Easther da ta shigo masa da jakarsa, “Duk ina mutanen gidan?â€
Ta ce da shi babu kowa sai Aalimah. Cikin mamaki ya ce, “Sun dawo? Yaushe? Tana ina?â€
Bai kuma tsaya ta ba shi amsar ko guda daya ba, ya shiga hada steps biyu-uku, yana hawa sama.
Sai da ya murdo kofar dakin nasu ya shigo ya yi daidai da dago kanta da ta yi ta dubi saitin kofar. Kirjinta na harbawa.
Yana nan yadda yake, handsome Abulkhair. Well dressed in a Nordstromshirt and jeans trouser, masu kalar baki da fari, mai yawan gargasa a jiki, da sumar kai irin na buzayen usul. Ko bakar jakar da yake goye da ita a bayansa bai sauke ba. Sai dai kuma ya yi rama sosai. Kallo daya za ka yi masa ka san cewa ya rame din, duk da physique chest din yana nan ba abin da ya girgiza shi.
Idanunsa suka sauka cikin nata, sun dade suna kallon juna kowannensu yana sakin murmushi kafin ya saki jakar da ke bayansa kasa, ya bude mata hannayensa. Girgiza masa kai ta shiga yi alamar a’ah, ba ta san sanda ya iso gabanta ba har inda ta ke zaune ya zube gwiwoyinsa ya zauna a gabanta, ya zuba mata ido ba ya ko kiftawa. Daga bisani lumshe idanu kowannensu ya yi cikin jin wata irin nutsuwa na sauka a zuciya da gangar jikinsa.
“Kallon ya yi yawa. Babu aure a tsakaninkuâ€. Tunanin da ya shiga kan Aalimah kenan, ta mike tsaye da sauri. Shi ma mikewar ya yi ya harde hannayensa a kirjinsa yana kallonta a tsanake, ta kara kyau ta cicciko sosai, wanda ke nuna ita kam cikin kwanciyar hankalinta ta ke. Duk wahalar nan da ya yi tsayin sati hudu bai ji ko da muryarta ba, ita ba haka ba ne a tare da ita ba.
Murmushi Aalimah ta yi, “Monsieur…â€
“... Don’t dare call me Monsieur againâ€.Yakatseta. “Na ga abubuwa sabanin yadda na zace su, ni kadai na yi kewarki. Ni kadai na damu da ke…!â€
Ya karasa maganar in subdued wato cikin muryar da ke nuna how dissappointed he was. Tare da juya mata baya.
Takowa ta yi a hankali har ta zo dab da shi, sannan ta tsaya. Cikin sanyin murya ta ce,
“Ba haka ba ne. tunda muka je ban…â€
“...Ba ki sake tunawa da ni ba, balle halin da rashin ji daga gare ki zai sanya ni. Quite four weeksâ€. Ya fada yana daga yatsun hannunsa guda hudu, akwai fushi sosai cikin muryarsa.
“Daddy bai ba mu layi ba…â€. Ta fada cikin son kare zarginsa na cewa ba ta damu da shi ba.
“In ba ku da layi ba za ki iya siya ba? Ko ba za ki iya roaming naki layin ki yi amfani da shi ba a ko’ina? In duk hakan ba mai yiwuwa ba ce, ba za ki iya aron wayar wani ki kira ni ba?†Wannan karon da fada sosai yake magana.
Abin da Aalimah ta ki jini kenan, tuni idonta ya cicciko da kwallah.
Hakan ya sa Abulkhair sassauta fushinsa, ya juyo yana kallonta. Fahimtar hakan ya ba ta damar iya yin magana cikin kwantaccen sauti.
“Na ji Basma na fada wa Malam Razee cewa jarrabawa ka ke yi, kuma ka yarda da ni ko su Mamanmu ban kira ba har muka je muka dawo. The house is always full and very busy… Mun kuma yi tafiye-tafiye na garuruwa masu nisa cikin sahara inda babu network har mutum sai ya manta ma yana da waya, amma ba don na manta da kai ba, ko ba ka zuciyata. Ina dawowa na yi niyyar kiranka na tuna ba weekend ba ne kada in ha’inci Daddy. Ina tabbatar maka tunaninka na tafiya ne tare da bugun zuciyata. Babu inda zan shiga, ko wani yanayi da zan shiga da zai sa in manta ka ko na kasa tunaka…â€
Ba karamin sanyi kalamanta suka yi masa a zuciya ba. Ya manta duk wani bacin rai da ya samu kansa a ciki.
“Then give me a hug… don in tabbatar ba dadin baki kika yimin don in yarda da ke baâ€. Ya fada yana cin magani.
Dariya ta yi, ta ce, “Not nowâ€.
Kwafa ya yi ya fice daga dakin jin shigowar motar Mummy, yana ce da ita,
“Jira ba ya kisa. Da yana kisa da ban kawo yau ba!â€.
******
Kamar yadda Mummy ta yi alkawari washegari ta shirya musu tafiya picnic zuwa ‘Miami’.
Ko a kwanaki uku da suka karar tare a Miami Resort, Mummy ba ta fahimci komai tsakanin Abulkhair da Aalimah ba. Suna zaune a gabanta suna chatting da juna da wayoyinsu bata san me suke yi ba. Sannan daki daya ta kama musu dukkansu ita da yaran, Abulkhair na dakinsa shi kadai, sai sun fito bakin beach suke haduwa. Watakila kuma don ba ta da kurillah ne da ta gano yadda suke magana da juna cikin halittar idanunsu. Da ta hango matsananciyar soyayyar da ke kwance cikin idanun kowannensu.Sun shakata yadda suke so. A jirgin Alaska Airlines suka je Miami daga Boston a cikinsa suka dawo.
Da suka sauka a filin jirgin saman Boston Logan, Mummy ta fiddo waya ta kira Joseph. Shi ya zo ya kwashe su zuwa gida.
Tun daga harabar gidan suka ga alamun an canza wa motar Daddy matsugunni. Motar da shi kadai yake hawanta, wato Chevrolet volt. Har suna hada baki yaran da Mamansu wajen tambayar Joseph, “
Daddy ya dawo ne?â€
A nan yake gaya musu ai tun washegarin tafiyarsu suka dawo shi da second madam dinsa.
Mummy ba ta wani fahimce shi ba. Cike ta ke da dokin ganin mijin nata abin kaunarta. Amma su sun gane me Joseph ke nufi da second madam, ban da Abulkhair. Jikinsu gabadaya ya yi sanyi, don haka ba su wani fita da sauri ba, Mummy ta riga su isa kofar shiga gidan da kanta ta danna kararrawa kafin su karaso.
Wata kyakkyawar ba’abziniya kamar balarabiya, ita ta bude kofar. Idanunta cikin na Zulaiha. Ba ta fice age mate (sa’ar) Abulkhair, wato ba za ta wuce shekarunsa ba. Mai yawan fara’a da hasken idanu da na hakora. Kallon-kallo suka shiga yi, sai dai kowacce nau’in kallon da ta ke yi wa ‘yar uwarta daban yake da na ‘yar uwarta. Zulaiha kallon ya tashi daga na mamaki ya koma na tsoro, da tunanin aljana ce ta shigo mata gida, don wannan ba ta yi kama da turawa ba. Yayin da Gumsu Moiram, ke kare wa uwargidan Ishaq kallo da son tantance rukunin matan da ta ke ciki don ta san da fuskar da za ta rayu da ita.
Daddy ne ya iso kofar ya katse kallon kudan matan nasa biyu. Shi ma kansa a darare yake, amma ya karfafi kansa ko don ya zama cikakken miji a gidansa ya ce, “Sun dawo ne? Gumsu shige ciki su shigo, ina zuwaâ€.
Ta wuce ta koma ciki.
Mummy Zulaiha ta kalli Daddy cikin ido, yawu ya kafe a cikin bakinta. Kin shiga ta yi kamar yadda yaran ma suka ja tunga a bayanta. Ta ce, “First, tell me who is she?â€
Da sassauci a kan fuskarsa ya ce, “A bakin kofa, a gaban yara ki ke so mu yi magana irin wannan? Ki shigo ciki tukunnaâ€.
“Magana irin wacce?†Ta tambaya cikin danne ko ma wane irin tunani ke son shiga zuciyarta a lokacin. Hannunta kawai ya kamo ya janyo ta cikin falon su Aalimah suka biyo bayansu.
Bai cika hannun Mummy ba (upstair) ya haye da ita don su kauce ma idanun yaransu. Yayin da amarya Gumsu ta wuce dakin da Daddy ya ba ta tun zuwansu, dakin Mu’az na da, kafin ya sama mata matsugunni.
Duk wani bayani irin na nuna concern, wanke kai da kawo dalilai Ishaq Raazee ya yi ga Mummy Zulaiha don ta karbi kaddarar aurensa kamar yadda ya karbe ta, ta yarda bai yi da niyya ba, bai yi don ya tozartata ba, bai yi don ya daina sonta ba. Zulaiha ta ki fahimtar ko guda daya. Wani dan karamin hauka ne ya same ta a wannan lokacin. Ta gaya masa ta bar gidansa kenan, har abada ba zai burge ta ba sai ya auro matan Niger Republic bakidaya sannan za ta amince danginsa ba sa sonta. Ga gidansa nan, ga ‘ya’yansa nan, ya manta ya taba saninta a rayuwarsa.
Su dai su Aalimah suna zaune jigum-jigum kowacce da jakar matafiyanta a gabanta a falon kasa, tun bayan da suka shigo Abulkhair bai zauna gidan ba, ya shiga cikin gari ne tun bayan ya gaisa da amarya Gumsu da bai wan wace ce ba. Ya dai fahimci Daddy ya zo da ita ne daga Niger, sai ganin saukowar Mummy suka yi a sukwane tana hada steps biyu-uku, ta ja jakarta da suka dawo da ita ta yi waje, sai ga Daddy ya biyo bayanta da sauri shi ma. Yesmin ta bi ta da gudu, ya ce Khaleesat kada ta barta ta fita. Ta je ta riko ta tana kuka tana kiran Mummy. Wayarsa ya fiddo ya kira Abulkhair ya ce, “Kana ina?â€
Abulkhair ya amsa da cewa, ya dan fita ne amma ga shi nan ma ya shigo kwanar gidan.
Ya ce, “Ka kula da Mamanka, ga ta nan za ta dau mota ta fita. Kada ka barta ta yi tuki. Take care of herâ€.
Abulkhair ya amsa, “Don’t worry Daddyâ€.
A take kuma ya shiga hasashen abin da yake faruwa da matar da ya gani daga Nijar.
“This cannot be possibleâ€. Ya fada a fili.
Karawa motar gudu ya yi ya karaso gida, daidai Mummy na sanya jakarta a but din motarta tana rufewa. Ko daidaita parking bai yi ba ya kashe motar ya fito har da gudu ya hada ya bude mazaunin direba ya shige ya rufe. Kofar kusa da shi ta bude ta zauna tana fadin.
“Please go out, tafiya zan yiâ€.
“Ina so in raka ki ne Mummyâ€.
“Wannan karon tafiyar ba ta dawowa ba ce, please go to your Dadâ€. Sai a lokacin ne ta samu hawaye suka zubo mata.
Abulkhair ya ji wani iri a zuciyarsa, tissue din motar ya zara ya shiga tsane mata hawayen fuskarta.
“Mummy kun wuce wannan level din ke da Daddy, don Allah ki koma ku sulhunta kanku albarkacinmuâ€.
Girgiza kai ta shiga yi tare da fadin, “Ni da Babanku har abada! Kishiya ya yi min a shekarun girmana da furfurarsa da komai. Me zan yi da danginku? Tsakanina da su sai Allah ya isa!â€
“Hasashena ya tabbata gaskiya kenan?†Abulkhairi ya fadi a zuciyarsa, “Na fahimta Mummy. Amma yanzu komai zan gaya miki ba za ki fahimce ni ba. Kina bukatar nutsuwa. Yanzu ina zan kai ki?â€
Da sauri ta ce, “Las Vegasâ€.
Murmushi ya yi. A ransa yana fadin, “Wurin sanyin idaniyarta, mai share mata hawaye, mai fada mata ta ji kamar iyayenta. Kai ka ce shi ne uban ita ce ‘yarsaâ€.
A fili kuma ya ce, “Mummy, ni ma ki so ni yadda ki ke sonsa!â€.
Duk halin da Mummy Zulaiha ke ciki sai da maganar Abulkhair ta sa ta murmushi. Anya za ta so wani Da cikin ‘ya’yanta irin son da ta ke yi wa MU’AZZAM?
******
Bayan fitarta da kamo Yesmin da Khaleesat ta yi, Daddy dakin da Gumsu ta ke ya shiga. Kiranta ya yi suka fito tare. ‘Ya’yan na nan zaune yadda suke tun shigowarsu. Cikin yanayi na zugum-zugum sai Yesmin da ke ta kukan an hana ta bin Mummy.
Zama ya yi a kujerar da ke fuskantarsu, Gumsu za ta zauna kusa da Aalimah ya ce, ta dawo kusa da shi ta zauna. A nutse ta bi umarninsa cikin tsananin ladabi. Ya dube su bakidaya, ya ce, “Ga Antinku Moiram na taho da ita. Ina ganin hakan zai fi min sauki a kan na baro ta a can na dinga zarya. Inyaso duk karshen shekara sai mu je hutu. Basma, Aalimah da Khaleesat dukkanku na san masu hankali ne, kuma masu adalci a tsakanin iyayenku. Ban auro Gumsu-Moiram don bana son mahaifiyarku ba, sai don cika sunnar manzo sallallahu alaihi wasallam, da biyayya ga iyayena. Moiram uwarku ce, kuma gaba ta ke da ku, don haka na hore ku da da’a da biyayya a gare ta. Ku bi ta yadda za ku bi mahaifiyarku. Ke kuma Moiram ga amanar ‘ya’yana nan ki zauna da su yadda za ki zauna da wadanda ki ka haifa. Wanda ya yi miki ba daidai ba, ki sanar da ni, balle kuma dai na shaide su dukkansu masu kaunar Daddy ne ba za su taba kin abin da ya kawo ya ce nashi ne ba. Haka ne ko ba haka ne ba?†Ya maida maganar cikin sigar tambaya, ta wani bangaren lallashi.
Basma ce ta fara amsawa da, “Haka ne Daddy. Aunty Gumsu muna miki barka da zuwa cikin family dinmu. Insha Allahu za ki same mu yadda Daddy ya shaide muâ€.
Khaleesat ta dan ja fasali kafin ta ce, “Welcome Aunty Moiramâ€.
Kallo daya za ka yi mata ka san cewa tafiyar mahaifiyarta ta taba ranta. Gab ta ke da fashewa da kuka tana dai daurewa ne.
Aalimah Daddy yake kallo, yana so ita ma ta yi magana. Da farko ba ta yi niyyar cewa komai ba don a ganinta wannan abu ne da ya shafe su su kadai, ita ai ba ‘yar gidan ba ce. Amma ganin kowa ita yake kallo da saurare, sai ta ce,
“Sannu da zuwa Aunty Gumsu. I’m Aalimahâ€.
Daga nan kowacce ta fadi sunanta. Yesmin ma ta share hawaye jin kowa na fadin suna, ta ce, “Aunty I’m Yesmin, Mummy’s loveâ€.
Sosai ta ba wa kowa dariya. Gumsu ta matso ta janyo ta jikinta ta dora ta a cinyarta, cikin faransanci ta ce, “Ni kuma sunana Aunty Gumsu. Yesmin’s Auntâ€.
Yesmin ta girgiza kai cikin rashin yarda, “I’ve my Aunty, her name is Aunty Aalimahâ€. Ta fada tana nuna mata Aalimah.
Daddy ya ce, “Sun zama su biyu Yesmin, Aunty Aalimah da Aunty Gumsuâ€.
Cikin hikima Gumsu ke jansu da hira cike da kulawa da nuna kauna. Ba ta iya Hausa ba sai faransanci, abzinanci da turanci, don haka da turancin kadai suke magana da ita. Suna jin faransancin amma sama-sama amma. Tun suna dan jan jiki har suka ware musamman da ta ce kowacce ta je ta canza kaya ta zo ta daura apron su shiga kitchen tare. Abin da kowacce ta ke so shi za ta dafa mata, daga yau sun daina cin abincin mai aiki sai nata, tsakaninsu da mai aiki yanzu share-share da wanke-wanke ne kadai. She has a degree in Pastry-Art (tana da digiri kan girke-girke) kuma a gidansu za ta bude ofis dinta (tana nufin a kicin dinsu). Duk kinsu da shiga kicin kasa musa mata suka yi.
Aalimah ta ji dadin hakan sosai, don ita duk yadda za ta yi da su ba sa yarda. A ganinta da a gida Nigeria suke, duk sun isa aure. In aka aurar da su me za su tabuka a gidan miji?
******
Washegari suka koma makaranta dukkansu, Aunty Moiram kawai ake bari a gida, sai ko Easther in ta zo aiki, da ta gama ta ke tafiya. Abulkhair tunda ya kai Mummy gidan Mu’azzam bai dawo ba. A kwanaki uku da suka biyo baya sabo ne mai tsanani ya shiga tsakaninsu da Auntynsu Gumsu, wadda ke kula da komai nasu tsakani da Allah. Shi kansa Daddy yanzu da wuri yake dawowa gida don ya san in ya dawo zai tadda mai jiransa, abinci lafiyayye sai wanda ya zaba. Tun Gumsu na jin kunyar hawa upstairs turakan Daddy sabida idanun su Basma, har ta gaji ta zubar, inda ta fahimci yaran daban suke da irin wadanda ta sani a Nijar, wadannan masu budadden ido ne, kowa rayuwar ‘yanci yake yi babu takura. Sannan ginin benen ya fi na kasan girma da fadi sosai, a can dakin Mummy Zulaiha yake, na Daddyn da na su Basma. Inda aka batan karami ne, Mu’az ne ya zauna a dakin farkon dawowarsu gidan, kafin ya tafi jami’a a Las Vegas. Daddy ya ce zai kama mata apartment na haya a nan kusa da su, amma ta ce in dai hakan ba zai zama matsala ga