Showing 84001 words to 87000 words out of 126031 words

Chapter 29 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt

dawo, ku taho da Khaleesat da Yesmin tunda mijinta yana nan tare da mu. Ki nemo (credit cards) dina a suitcase dina ku zo da su Las Vegasâ€.
Muryar Mummy Zulaiha gaba daya ta dushe sabida yawan kuka, wanda ya zama babban abin yinta tun ranar da aka ce da ita babu Aboulkhair, tun ranar da ta bude kyallen da aka rufe shi ko fatar fuskar sa ba ta yi saura ba, ta zagwanye kamar konewa ta wuta a sakamakon munin hadarin mota, al’amarin da ya jefa ta a wani hali na kaka-ni-kayi, har yau kuma ba ta fita daga cikinsa ba, da tashin hankalin da faruwar hakan ya jefa ta a ciki.


“Daddy Aalimah fa?â€


Mummy ta tambaye shi, wasu sababbin hawaye na tsinke mata. Jin cewa zasu koma rayuwa a Boston, babu Aboulkhairi babu mai dakinsa Aalimah.
Shi ma hawayen yake yi, ya ce, “Zulaiha babu magana a kanta yanzu sai ta haihu. Ki barta kusa da mahaifiyarta zata fi sakewa. Kuna tare ne?â€
Mummy ta rushe da kuka wurjanjan.
“Daddy cikin ma babu shi, ya tafi tare da Babansa. Na rasa laifin da mu kai wa Ubangiji Daddy, ya yi mana wannan talalar a lokaci daya…â€.
“A’uzubillah! Kul Zulaihatu! Maza ki yi istigfari ga wannan sabon. Shi Ya ba mu, ba tareda mun san zai bamun ba, kuma Ya ga damar karbe abinsa a lokacin da ya ga dama sabida ya fi mu bukatarsa. Maza ki yi tuba ga sabonki Zulaiha, ki gode maSa da kyautar rayayyun ‘ya’ya har guda hudu da ya bar maki. Ki roka musu rayuwa mai tsayi da albarka tareda ke.
Hakika rashinsa ba karamin rashi ba ne gare mu baki daya, amma tunda Mu’azzam ya jure ke ma za ki iya jurewa. Ki yi hakuri Zulaiha kin ji, ki yi hakuri, ki yi hakuri ki fauwalawa Ubangijiâ€.
Mummy na ci gaba da kuka da hawaye da majina, ta ce,
“Na yi hakuri Daddy, na yi hakuri. Ya ya jikinku?â€
“Muna kara samun sauki kullum cikin rahamar Allah, har an sayo kafar da za a sanya wa Mansour. Ki gaya wa Aalimah ya ce yana gaishe ta, amma ba yanzu zan hada su su yi waya ba, ina so duka su kara samun sauki a zukatansu tukunnaâ€.
Mummy ta ce,
“Daddy ko kudin tikiti babu a hannuna, namu duk sun yi expire, dole in shiga cikin tsohuwar ajiya ta. Allah sarki Mu’azzam, yau shares (hannun jari) din da ya saya min da kudina zasu yi mana ranaâ€.
Ya ce, “Amfanin neman naki kenan ai, ki rufa min asiri a sanda na gaza, ni ma yanzu aljihuna zan shiga mun cinye na Mu’azzam tas! Rayuwa kenanâ€.
7/4/21, 10:50 AM - Buhainat: KWATARKWASHI














Duk abin da Ishaq Raazee da dansa Mu’azzam suka mallaka cikin asusunsu na bankunan kasar America ya kusa karewa a wannan doguwar kwanciya jinyar ba da sanin kowa ba daga shi sai matarsa. Bayan su Mummy sun koma Hamoud ya hadu da amaryarsa Khaleesat don shi da direban Mu’azzam suka je debo su daga filin jirgi, sai dai kowanensu zuciya ba dadi. A motar babu wanda ya yiwa dan uwansa magana.
Kai baka ce masoyannan bane masu neman cinye juna sabida soyayya gabanin faruwar wannan al’amari. Saidai ko yaya Khaleesat ta motsa sai ta hango idanun Hamoud akanta ta mudubin motar tana mai mamakin rama da jemewar da yayi cikin ranta. Ta ji zuciyar ta ta tabu. Amma kallon su take shi da aurensa dake kanta matsayin silar rugurgujewar farin cikin iyayenta da ‘yan uwanta.
Dukkansu a tankareren gidan Mu’azzam suka sauka bayan Mummy ta je Boston ta debo katinansu na banki kamar yadda Daddy yayi mata umarni.
Mummy na tausayin wadanda ke kwance a asibiti, amma hakika tana tausaya wa Hamoud da Khaleesat. Wadanda suka dauki alhakin faruwar komai suka dora a kan ‘AURENSU’. Dalili kenan da ya sa suka bi suka tsani auren bakidaya. Har basa son ganin juna. Ga su dai a gida daya, amma Mummy sai ta takura wa Khaleesat ta ke gaida mijinta Hamoud da safe. A cewarta ita bata son ganinsa. Wajen aikinsa nata bukatarsa amma ya kasa tafiya ya bar Kawunninsa a gadon asibiti. A satin da su Mummy suka zo aka ci gaba da ba su treatment domin kafin su zo an yi suspending medical treatment dinsu saboda karewar kudin da ke cikin duka account din Mu’azzam dake hannun Dr. Nebrass.


A kokarin Mummy na rage musu kashe kudi, ta dakatar da sayo wa Hamoud abinci a restaurant da yaron Mu’azzam ke yi sau uku a rana, maimakon hakan sai ta yo cefane mai dimbin yawa ta ke dafa musu bakidayansu, su dama majinyatan asibitinsu ne ke ba su. Wanda ya dace da lafiyar kowannensu.


Mummy na zaune ita da Hamoud a falo aka kira shi a waya. Tana gani ya share kiran, akayi-akayi ya ki dagawa, shi kuma bai kashe ba.
Ta cira kai daga abinda take yi tace, “Mahmoud ba kiranka ake ba ne?â€
Ya ce, “To ya zan yi Mummy? Su na gaya min ne hutun da aka deba min na aure ya kare in koma bakin aiki, ni kuma Mummy ba zan iya ba, har yanzu cikinsu babu wanda ya fara taka kafafunsa a kan kasaâ€.
Idanunsa suka kada suka yi jajir, ya ce,
“Mummy duk aurenmu ne ya jawo ko?â€. Ya fara kuka.
Mummy ta tashi ta koma kusa da shi, ta manta da surukuta tasa hannu ta dafa bayansa tana rarrashinsa, sai ga Khaleesat ta fito daga kitchen da faranti shake da abinci a hannunta. Tana ganinsa yana kuka wani abu kamar kibiya ya soki zuciyarta, ta saki farantin a kasa, ita ma ta yi kan Mummy tana kuka.
“Mummy da na san abin da zai faru ke nan, da ban ce ina son auren ba!â€.
Hamoud ya dago daga jikin Mummy jin abinda ta fada, yai mata wani irin kallo da saida Mummy ta rasa inda zata sa kanta don kunya, yace.
“Yanzu ne kika san hakan???â€
Tace “ko dama can ni ban shirya aure ba, takura min ka yi†yace “nikuma fa da aka takurawa in taimaka in aure ki da wuri ake son yi miki aure ana tsoron kada ki rasa miji?†Sosai Khaleesat ta kulu da jin gorin da yayi mata tace “Ni ce zan rasa mijin? Ai wallahi ka dai fada ne kawai amma nice nayi maka alfarmaâ€.
Mummy Zulaiha ta rasa yadda za ta yi da su Khaleesat, suna manne jikinta sai gori suke jefawa juna, amma kallo daya zaka yi musu ka fahimci fatar bakin su ce kadai ke magana amma cikin kwayar idanunsu kauna ce da soyayya zallah. Cece-kucen su da kukan Khalisat shi ya jawo Gumsu da ke kitchen.
Ta fito ta tsaya daga bakin kofar shigowa falon da ludayin miya a hannunta, hannunta daya ta sa ta kama kugunta, daya hannun ta nuna su da ludayin miyar hannunta, ta ce.


“Mummy, me nake gani haka? Wannan wace irin tabara ce? Kukan soyayya ne wannan ko mene ne???â€


Mummy ta ce, “Taya ni gani dai Gumsun Babansu. Sun bi sun daga min hankali. To wallahi ba zai yiwu ba, ba za ku kara min hawan jini da tashin hankali kan wanda nake fama da shi ba.
Ka yi muku booking ku tafi, in ji da majinyatan da ke gadon asibitiâ€.
Khaleesat da Hamoud suka hau hararar juna, tareda janyewa daga jikin Mummy a lokaci guda, kowanne kamar ya rufe dan uwansa da duka haka yake ji. Gumsu ta yi dariya tace,
“Karshen munafurci yau ina ganinsa a gidan nan. Don Allah ku soke juna da mashi sannan zan yarda kun daina son junaâ€.
Babu wanda ya kula ta a cikin su.
Hamoud ya tashi ya bar wajen, ita ma Khaleesat haka, amma yana shiga daki ya zauna a bakin gadonsa sai ya samu kansa da sakin murmushi, wani irin lallausar murmushi wanda rabon sa da yin irinsa har ya manta. Zai iya cewa tun faruwar al’amarinnan ga ahalinsa rabon da murmushi ya ziyarci fatar bakin sa. Kalaman Khaleesat da yanayin innocent fuskarta a sanda take fadar su yake tunawa daya bayan daya suna ta sanya shi murmushi. At last she’s mine. Ya fada a hankali, ya mallake ta ta zama tasa da dadi ba dadi. Sai kawai ya hau duba travel routine na kasar Japan kamar wanda ake yiwa umarni. Koda yake umarnin ne Mummy ta yi masa amma mai kama da taimako a gare shi. Ita kuma Khaleesat tana shiga daki kayanta ta soma hadawa. Tana yi tana waiwayen kofa kada Mummy ko Gumsu su shigo su ga abinda ta ke yi.


Alhamdulillah a washegari Daddy 1 da Daddy 2 suka soma taka kafafunsu akan kasa. Da taimakon likitoci da malaman jinya, Aboubacar yana iya zama da kansa, ya samu lahani ne mai matukar hatsari, karfe ne da gilashi suka shige cikin cikinsa, kusan aikin da aka yi masa ya fi na su Daddy cin kudi, su sun taka kasa, shi kuma ya zauna da taimakon (pillow).
Suka yi hira da Hamoud sosai a wannan ranar inda ya gaya masa jibi zai koma bakin aikinsa, amma kafin nan yana matuqar son a barshi ya ga Mu’azzam. Aboubacar ya ce “idan Nebrass ya zo ka roke shi na ga alama yana da kirki. A hannunsu Mu’azzam yake a private clinic dinsaâ€.
Da shawarar Aboubacar Hamoud ya yi aiki. Washegari da Dr. Nebrass ya zo har kasa ya durkusa yana rokonshi ya bar shi ya ga Mu’azzam, shi yana yi Aboubacar na yi har da hawayen su, ya rasa yadda zai yi da su, shi da ma Daddy Ishaq bai sa aka ba. Ba su san Mu’azzam ba ne, yanzu haka ya dade da samun sauki, ba ya son ganin kowa ne. He prefers to be alone a irin wannan yanayin. Nebrass ya ce su yi masa alfarma ya fara neman izinin Mu’az din tukunna, kada su mayar masa da aiki baya.


Aboubacar ya ce,
“Ka gaya masa karfe da gilashi sun huda min hanta, ya bar ni in ganshi kafin in cikaâ€.
Hamoud kuma ya ce,
“Ka gaya masa gobe zan koma Japan, kuma sai na yi shekaru uku ban zo gida ba, zan tafi tare da kanwarsa, muna neman albarkarsaâ€.
Dr. Mansour ya ce, “Kada ka gaya masa na rasa kafa, amma ka ce masa I want to shed my tears before him, sannan ne zan daina jin rashin Aboulkhair da na yi. Sai na ganshi zuciyata za ta rage ciwo!â€


Dr. Nebrass ya ce, sakonnin sun masa yawa, ba zai iya rikewa ba, kowa ya rubuta nasa a takarda. Duk haka suka rubuta jiki na rawa suka ba shi. Ya dubi Daddy 1 (Ishaq) yana murmushi ya ce,
“Kai ba ka da sako?â€
Murmushi ya yi mai fadi (broad smile) ya ce a gajarce,


“Babu!â€.


Wanan kauna ta zahiri da badini da dan uwansa da ‘ya’yan ‘yan uwansa suka gwada wa Mu’azzam a kan idonsa, ta wadatar da shi da zuciyarsa, ya fahimci Mu’azzam din mutum ne abin so, mai matukar kima da daraja a gare su!!!.
****


Lokacin da Dr. Nebrass ya kai wa Engnr. Mu’azzam Ishaq Raazee sakon ‘yan uwansa da Baffansa, yana zaune gefen gadonsa na asibiti yana shan hot coffee. Coffee ne mai zafi da kauri wanda yayi daidai da yanayin da ake ciki na tsananin sanyi a birnin LasVegas a yammacin ranar wata Asabar. Yana sanye da thick coat ruwan toka a sama da karamar riga short-sleeved daga ciki da dogon bakin wando (Armani code). Suma ta taru a kansa sosai tasu ta buzayen usli duk da kasancewarsa ba ma’abocin tara ta ba. Amman zaman asibiti yasa yanzu ta taru sosai ta mummurde ta zama wani irin curl.
Takardun ya bi daya bayan daya cikin nutsuwa yana karantawa, Dr. Nebrass na tsaye a kansa yana son ganin reaction dinsa. A matsayinsa na likitansa komai na Mu’azzam din sai ya rubuta musamman ci gaba irin wannan ga lafiyarsa. Ana so Mu’az din ya dinga socializing da mutane na jikin sa musamman masoyansa irin haka, zasu taimaka kwarai wajen restoring farin-cikin da ya rasa.


Gani ya yi Mu’azzam ya yi dan murmushi abin da tun zuwansa gadon asibitin bai yi ba. Ya daga kai yana kallon likitan, murya a sanyaye cakude da damuwa ya ce,
“Haka Aboubacar ya ji ciwo???â€


Nebrass ya ce,


“Duk ya fi su jin mummunan rauniâ€.


Har zai gaya masa Dr. Mansour babu kafa, ya tuna ya ce kada ya gaya masa. Cikin lallashi da siyasa ya ce,
“In zuciyarka ba ta amince wa ganinsu ba zan ba su hakuri. Amma hakika sun damu sosai da son ganinka, musamman mai rauni a cikin, har hawaye yake min. Shikuma dayan dana ji sun kira, Hamoud, daga yanayin sa zai iya bada komai da ya mallaka don ya samu ganin ka ko sau daya ne kafin ya wuceâ€.
Mu’azzam ya runtse idonsa, da sauri kuma ya bude su akan likitan ya ce,


“Let them in, please…â€.


Dr. Nebrass ya bude kofar, Hamoud ya turo Aboubacar a hankali kan kujerar marasa lafiya na musamman, wadda ke hade da na’urori a jikinta, Mummy ta turo Mansour Raazee kan kujerar guragu, Mu’azzam sai ya saki kofin coffee da ke hannunsa ya zube a kasa, kofin ya fashe, ya sanya fuska a tsakanin cinyoyinsa ya sanya kuka mai tsuma rai.
“Wace irin kaddara ce ta fado wa rayuwarmu haka?â€


Gumsu ce ta karshen shigowa, ta turo Daddy Ishaq a tashi kujerar, bai rasa kafa ko hannu ba, amma raunikan jikinsa da suka sha plasta Allah ya yi yawa da su. Har gaban Mu’azzam Mummy ta kai Daddy Mansour.
Matsawa yayi kusa da Mu’azzam din sosai ya runguma shi a jikinsa, ya kai hannu bayansa yana shafawa a hankali, yana mai magana cikin taushin lafazi, yana tunasar da shi ya godewa Allah cikin kowanne hali. Ni’imominsa gare mu sun fi jarrabawarSa yawa.
“Mu’azzam ka ce Alhamdulillah! Ka yi wa dan uwanka addu’ar samun rahma da gafarar Ubangijiâ€.


Wato duk inda Gumsu ta ke, sai an san tana wuri, yanzu ma cewa ta yi cikin kulawa,
“Doctor me Mu’azzam ke son ci in dafa masa gobe?â€
A hankali Mu’azzam ya cira kai yana son ganin wace ce wannan ana ta rai da lafiya tana ta abinci?
Ganin kallon haushin da yake mata ta ce, “Kalle ni da kyau, ni ce Gumsun Daddynku. Mu’azzam komai ya yi zafi maganinsa Allah, ka daina kuka ka kama hailala. Na fi ka jin rashin dan uwanka, ni abokiyarsa ce, abokiyar shawararsa. Amma na san soyayyata da shi shi ne in ta yi masa addu’a ba zubda masa hawaye ba, ka ji Mu’azzam?â€
Cikin ransa yake tambaya, ita kuma wannan wace ce a cikin dangi??


Dr. Nebrass surutun Gumsu ya fara hawa masa kai. To balle kuma Mu’azzam ya sani, don haka ya ce su koma su bar Mu’azzam ya huta, tunda sun ganshi.
Da ma motar asibitin da suke ce ta kawo su da taimakon Nebrass, aka maida kowa inda yake.
Mu’azzam ya jingina da taga yana kallonsu, ana sanya majinyatan a mota with care, iyayensa masu tarin koshin lafiya da kuzari. Wato rayuwa gaba dayanta ba ta da tabbas! Kuma dan adam har ya mutu ba’a gama mai halitta ba; yau Baba Mansur ne ya zama gurgu. Wasu zafafan hawaye suka kwararo masa. Fata yake ya bude ido ya ga cewa duka wannan mafarki yake yi, fata yake ya juya bayansa ya ga shigowar Aboulkhair rike da magungunan da zai sha wunin yau maimakon Nebrass. Fata yake ya juya ya ga shigowarsa da jarida ya zo masa da labari. Fata yake ya juya ya ji ya ce ya sauko kasa su ci abinci Aalimarsa ta dafa musu! Fata yake ya juya ya ji shi yana hawowa upstairs din gidan sa da takun nan nashi gudu-gudu, sauri-sauri irin na zaratan matasa masu cike da koshin lafiya da kuzari.
Hakika dan adan bai hada sani da Ubangiji ba; Da ya san rayuwarsa a Las Vegas gajeriya ce da ya bar shi sun zauna tare a gidansa kamar yadda Aboulkhair din ke matukar so. Da ya san rayuwarsa gajeriya ce a Las Vegas da ko kusa bai bari sun zauna a muhalli daban-daban ba. Da ya jure wa kowacce irin hayaniya ta Aboulkhair ya zauna tare da shi har karshen rayuwarsa.....!


Inama ana maida hannun agogo baya!!!
Ina ma… Ina ma… Da na sani… Duka abubuwa ne wadanda dan Adam ba shi da maganinsu! Wadanda ba sa wanke zuciya a lokacin da suka riga suka yi wa zuciyar kawanya… Azabtar da zuciya suke don sun san cewa sun riga sun yi mata illa ta ko’ina. Kalmomi ne da ya tabbatar ba za su daina yi wa kunnuwansa azaba da amsa-kuwwa ba, daga yau har zuwa karshen rayuwarsa.
7/4/21, 10:50 AM - Buhainat: ADAMA DAUDA






“Daure ki sha, ko kurba uku ne kin ji?â€
Juyar da kai ta yi cikin son fashewa da kuka. Mama ta sake komawa barin da ta juyar da kan cike da damuwa da kofin mug na tangaran a hannunta mai cike da kunun kanwa.
“Kin san jikinki jikin jego ne Aalimah, ki dinga shan kunun nan ko da ba za ki ci komai ba bayan shi. A ce magana daya kullum sai an yi ta nanata ta kamar cin kwan makauniya?â€
Fuska ta sanya cikin tafukanta biyu ta fara wani irin kuka. Wanda ke tasowa tun daga karkashin zuciyar ta. Sautin sa na mai bayyana halin kunci da ragaita da zuciyarta ke ciki.
“Ni Mama ki rabu da ni, don Allah ki kyaleniâ€. Ta furta cikin wata murya mai ban tausayi.
Daidai lokacin da likitar da ke kula da ita ta bude kofa ta shigo da Nurse biye da ita. Cikin sakin fuska ta isa gaban gadon da Aalimahn ta ke, inda sabo sun saba da wannan kukan na Aalimah tun kwantar da ita a asibitin. Gata bata jin lallashi. Tausayi dattijuwar take bata sabida yadda ta damu da ‘yar tata. Ta karbi kofin daga hannun Mama, ta cire hannun Aalimah daga fuskarta, wanda tuni ya jike sharab da hawaye.
“Mrs. Aboulkhair ba sai na sake maimaitawa ba, jikinki yana bukatar sinadarin abinci mai gina jiki, kada ki manta ‘Da’ aka cire a jikinki ba karamin ciki ba. Ki rage wa Maman

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login