Showing 78001 words to 81000 words out of 126031 words

Chapter 27 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt

sun kasa hada ido da shi. Lokacin da sukayi transit a Abuja ya kara tabbatarwa ba tare suke da Aboulkhair da su Daddy ba.
A cikin jirgin da zai kai su Niamey hakurin sa da dauriyar sa ya gaza. Kallon su kawai yake yi cikin tsanaki. Malam ne a kusa da shi, yayin da Oncle Oussama yana daga kujerar bayan su. Dukkannin su tazbaha kawai suke ja, babu mai kallon shi, wani irin kallo yake yi musu idanuwansa na wani irin bubbudewa suna kankancewa duka a lokaci guda.
Duk yadda ya so su bude baki da kansu su bashi bayanin wani abu akasin abinda suka fada da farko amma sun ki cewa komai. Sai ya cigaba da zuba musu idon kamar yadda suke so. Amma bangare mafi rinjaye na zuciyarsa na tabbatar masa da cewa labarin da ke bakunan su ba mai dadin ji bane. Watakila dai su Aboulkhair sun bata. Ko kusa ransa mai yawan soyayya ga iyaye da tilon dan uwan nasa duk nisan zangon tunani da kintace da iyakar tsinkayen sa bai kawo masa mutuwar ko daya a cikinsu ba.
Yawan faduwar gaban da yake ta samu akai-akai na kara tabbatar masa da zargin sa na cewa su Daddy sun bata akan hanyarsu ta zuwa jamhuriyyar Nijar. Mu’azzam bai san cewa da gawar dan uwansa Aboulkhair suke tafe ba, sai da suka sanya kafa cikin family house din su na Raazii a unguwar plateaux. Shi dai Malam burinsa su isa Niamey da Mu’azzam lafiya. Ko ba komai uwarsa tana can, in ciwonsa ya tashi a bakon wuri inda babu kowa nasa ba su da yadda za su yi da shi, kuma Alhamdulillahi sun zo lafiya.


Gidan ya kacame da hidimar biki kamar jiya, saboda yau ne cocktail, dangi sun taru kamar su fasa gidan. Na birni dana kauye, Inna Kasisi na ta rabon abinci, Mummy Zulaiha ta tsame kanta tana daki da tazbaha a hannunta. Haka kawai ta ji duk bikin ya ishe ta tunda har yau babu labarin danta da mijinta.
Gumsu na yi wa amarya Khaleesat kwalliya suka ji maza na shigowa, Oncle Mainasara na fadin, “A kawo tabarmi. Ku matsa ku bada hanya. Sun dawo da gawar Aboulkhair, an ce shi kadai ne ya cika a cikin suâ€.
Mummy tana daga cikin daki ne amma tsaf kunnuwanta suna waje, komai da ake yi akan kunnen ta ne. Silalewa ta yi a zaunen data ke a sume yayin da Gumsu ta fito da gudu zaninta na kuncewa. Khaleesat ma haka.
A tsakar dakin Malam aka shimfide gawar Aboulkhair. Duka ‘ya’yan gidan maza sun shigo da makwabta da sauran al’ummar Annabi da suka samu labari a waje.
Malam ya ce a kira mahaifiyarsa ta zo su yi sallama, kafin a yi masa sallah. Sabida munin gawar ko wanka ba za a iya yi mata ba, sai ruwa aka yayyafa mata. Inna Kasisi ruwa take ta shafa wa Mummy, amma ko da ta farfado aka kai ta gaban gawar ta bude kyallen ta ga yadda Allah ya mayar da Aboulkhairinta da sauri ta rufe don fuskar duka ta zube. Baka iya shaida komai nasa. Sake silalewa ta yi ta suma a wurin. Gumsu ce da su Inna Bintou masu karfin gwiwar yi masa addu’a tare da sauran ‘yan uwa maza da mata. Amma Kasisi ma ta kasa duk irin taurin ranta kuwa. Kuka kawai take yi tana kiran sunan Aboulkhair. Khaleesat ma suma take ta yi kamar Mummy tana farfadowa. Yasmin na kururuwa ana hanata.
‘Ya’yan Malam gaba daya suna tsaye a kan gawar cikin dimuwa, kowanne rike da Alkur’ani mai tsarki suna karanta masa. Sabida yawansu nan da nan suka hattama sauka. Malam ya yi wa gawar Aboulkhair duk wani gata da addinin musulunci ya tanadar wa mamaci, suka hadu shi da ‘ya’yansa maza da jikoki da abokan arziki suka sallace shi, suka mika shi zuwa gidansa na gaskiya.
Mummy a karshe sai asibiti aka nufa da ita, don idan ta farfado ta tuno wai Aboulkhair ne babu, sai ta sake sumewa. Har aka yi addu’ar uku Mummy ba ta daina suma tana farfadowa ba. Likita ya tabbatar ta samu hawan jini farat daya. Khaleesat da Yesmin suna cikin wani yanayi wanda sai wanda ya taba rasa shakiki ne zai iya bayyana shi. Shakikin ma irin Monsieur Aboulkhair dinsu.
****


Ina Mu’azzam???


Mu’azzam ya bai wa kowa matukar mamaki, don kuwa abin da aka zata ba shi aka tarar daga gare shi ba. Shi ya sanya dan uwansa a kabarinsa, babu ko digon hawaye a fuskarsa, da hannunsa ya debi kasa sau uku da hannu bibbiyu ya rufe shi. Abin da Oncle Oussama ya lura da shi kawai shi ne; daga ranar bai kara sanya komai a bakinsa ba! Har maganinsa kuwa. Bai zubda hawaye ba, bai sake cewa kala ba. Wannan ya daga hankalin Malam wanda ke kwana daki daya da shi don kula da duk wani motsinsa yana kuma yi masa addu’o’i. Ba ya bari ya matsa ko nan da can. Ko bandaki ya shiga sai ya bishi ya tsaya a kofa.
Ranar da aka yi sadakar uku, ya ce da malam zai koma America zai nemi asibitin da ya dace ya kai su Daddy, ya kuma nema wa Dr. Mansour da Aboubacar medical visa suma a ci gaba da kula da su a can.
Babu wanda ya hana shi, don sun san cewa, hakan shi ne daidai, musamman da yake ya daina shan maganinsa, suna tsoron abin da hakan zai haifar, gara ya koma inda za a kula da shi shima.
******


Bayan tafiyar Mu’azzam ci gaba aka yi da karbar gaisuwa a gidan na Malam Raazee. Mummy na shan drip a asibiti har ta soma karbar reality.
Khaleesat ta kasance cikin tashin hankalin da ya fi na kowa a gidan, don a cewarta sanadin aurenta ne Monsieur Aboulkhair ya rasa kyakkyawar rayuwarsa. Tana mai kaico da wannan aure! Gumsu na kwabarta a koyaushe da cewa; mutum ba ya tsallake ajalinsa! Fadin halin da wannan family suke ciki ya yi kadan biro ya rubuta shi.
Mu’azzam ya kira malam Raazee ya sanar da shi ya yi processing visa din Daddyn Aalimah da Aboubacar, za su taso sati mai zuwa dukkansu, kuma ya hada da Hamoud don ya taya shi kula da su a can.
Malam ya ce,
“In ce ko kana shan naka maganin takwara?â€
Mu’azzam ya yi shiru.
Malam ya kwantar da murya, ya ce, “Takwara tafiyar wani tashin wani ce, rashin Aboulkhair ba yana nufin karewar taka rayuwar ba ne, tunda har yanzu kana numfashi. Na gane abin da ka ke yi, kana so ne kai ma ka illata kanka; ta hanyar kin shan magani. Takwara, mutuwar dan uwa na sani da ciwo, ciwo ba dan kadan ba, dan uwan ma irin Aboulkhairi mai tarin alkhairi, wanda samun kamarsa sai an tona.
To amma a matsayinmu na musulmi, dole ne mu yarda da kaddara komai dacinta. Mu kuma yarda cewa kulli nafsin za’ikatul maut. Ka yi hakuri Mu’azzam ka ji? Don Allah ka kula da lafiyarka…..â€.


Sai a wannan lokacin ne Mu’azzam ya fara wani irin kuka… Ya yi kuka ya yi kuka kamar ransa zai fita, Kakan nasa bai hana shi ba, hasali ma shi ma taya shi ya shiga yi suka yi ta yi a waya. A karshe Malam Raazee ya ce,
“Ba zan bari ka dauki kowa cikin majinyatan nan ba sai ka sha magani, ka kai kanka ga likitocinka sun kula da kai, in ba haka ba su zauna a nan kusa da ni, duk zan iya jinyar su. Gobe da ma zan kwaso su duka daga Kanon bakidayansuâ€.


Bai bari Mu’azzam ya ba shi amsa ba ya kashe wayar sa.
******


KANO, NIGERIA
Aalimah ba ta san wainar da ake toyawa ba sai a daren ranar dasu Mu’azzam suka wuce Niamey. Oncle Eidrissa ne ya kira ta a waya, ya ce suna tare da su Daddy an gansu. Cike da farin ciki ta ce,
“Ouncle Oussama ya gaya mini, har na gayawa su mama, sune a Aminu Kano da muka je dazu ko? Yaya jikin nasu? Oncle ina fata basu ji ciwo sosai ba?â€
Ya ce, “Eh, muna can, amma sun ji rauni sosai wallahiâ€.
Ya kara da cewa. Ta kawo musu dardumar sallah da ruwan sha.
Ta ce, “Oncle abinci fa?â€
Sai dai kuma ta karaya, da amsar da ya bata, da yadda take jin yana magana babu karsashi ko kankani a amon muryar sa, karfinta kuma ya kare dama da dawainiyar jinyar data ke sha a kwanaki ukun nan, she’s very exhausted, idanuwan ta har zafi suke yi na rashin barci, amma don karfin hali ba ta fasa kula da majinyatan ta ba. Ko dama can ita mai karfin zuciya ce akan komai. Duk da zuciyarta cike take taf, da kewa da tunanin mijinta. Taraddadin halin da yake ciki ya hana ta mallakar kanta. Tana jin salama ne in ta tuna an gansu kuma suna cikin gari daya itada Aboulkhair sannan suna samun kulawa daga likitoci yadda ya kamata kamar yadda su malam suka gaya mata, ta dan yi hakuri za’a barta ta gansu ba da jimawa ba.
Hawaye ya zubo wa Eidrissa, tausayin yarinyar yake ji sosai har cikin ransa. Takabar dake gabanta yake hango mata, da yadda zata haifi da ya rayu bai san Ubansa ba, ya ce,
“Bar maganar abincin nan Aalimah, wa zai iya cin shi? Ba ni Aseeyah idan tana kusa, kuma zata iya karba wayaâ€.
A lokacin mama ta soma warwarewa sosai, ta mika mata wayar, mama ta karba tayi masa sallama, ya ce,
“Aseeyah!â€
Ta ce, “Na’am Kawunsuâ€.
Ya ce, “Mu musulmi ne ko?â€
Ta ce, “Kwarai da gaskeâ€.
Ya ce, “Wadanda suka yarda Allah ke rayawa kuma shi ke kashewa?â€
A kwance ta ke a gado, amma jin inda zancen sa ya nufa sai ta mike zaune, Aalimah ta sanya mata pillow a bayanta ta ta jingina, sake manna wayar tayi a kunnenta. Ga Aalimah ta kafe ta da idanu kamar mai son a fadi komai akan kunnen ta, don haka ta mike daga gadon ta nufi bakin taga don kaucewa wadannan kaifafan idanu na Aalimah.
“Tafi kai tsaye Kawunsuâ€.
Ya rufe ido ya gaya mata komai. Ya ce, “Na rasa yadda zan yi in gaya wa Aalimah ta rasa mijinta, na ganta da ciki, wanda da alama bai gama girma baâ€.
Mama ta shiga salati, hawaye na zuba mata tarara! Ta ma manta Aalimahr na dakin. Jikinta ya hau tsuma da karkarwa.
Aalimah da Basmah da ke dakin duk suka yo kanta. Basma ta dauki wayar da ta yasar a kasa ta bi kira na karshe, Oncle Eidrissa ta gani, don haka ta bi bayan kiran.
“Oncle Basma ceâ€.
“Ku yi hakuri Basma kun ji, da kaddarar da Ubangiji ya dora mana. Kulli nafsin za’ikatul maut, Aboulkhairi bai yi gaggawa ba, mu ma duk lokaci muke jira!â€.
Basma ta shaki wani azababben numfashi, tana mai kokarin fizgo sauti daga makogaronta.
“Oncle Daddy? Hubby? Suna ina?â€
Ya share hawaye, muryar yarinyar kadai za ka ji ka fahimci ta gama mika wuya da jin ko ma me za ta ji. Tana da dauriya sosai kamar ko fiye da Aalimah.
Ya ce, “Basma ki dayanta Allah, ki yarda da kaddara sai ki samu cikar imani. Dan uwanki Aboulkhair Allah ya yi masa rasuwa. Har sun wuce da gawar Niamey don a suturta ta. Ga iyayenku da mijinki a nan tare da mu a gadon asibiti, sun jikkata. Mummunar jikkata. Mu gode wa Allah a cikin kowanne haliâ€.
Basma sai juyawa ta yi ta ga Aalimah a kasa, tana shure-shure, ta manta tsabar rudewa a handsfree ta sanya wayar. Allah ya taimaka a cikin asibiti suke, nan da nan ta danna kararrawar kiran likitoci, likitoci biyu da nurses biyu suka shigo suka dauke ta suka aza bisa gado suka soma kokarin ceto numfashinta da ceton abin da ke cikinta. Sakamakon jini da ya tsinke mata duka a lokaci guda.
7/2/21, 8:24 AM - Buhainat: KWATARKWASHI
A daidai wannan lokacin rashin lafiyar Mu’azzam ya fado masa a rai. Da sauri ya juya kafin ya karaso inda suke ya dubi babban dan sa Oussama da ke gefensa na dama a tsaye.
“Oussama yaya za mu yi da Mu’azzam? Ba’a gaya masa tashin hankali, idan ciwonsa ya tashi anan ya ya za mu yi da shi? Gashi babu Aboulkhairi tare da shi, babu shaidar komai na rashin lafiyarsa ko asibitinsa tare da muâ€.
Duk dauriyar Uncle Oussama da taurin ransa yau kallo daya zaka yi masa ka ga ya baka tausayi, murya a raunane ya ce.
“Yanzu ya za’a yi Malam? Dole ya je shima, za mu dauki Hamoud ne mu barshi? Tun jiya cikin damuwa yake, yana gaya min ya kasa samun nutsuwa saboda rashin samun wayar kanin nasa, da rashin isowarsu tun lokacin da ya kamata a ce sun iso dinâ€.
Suka yi zugum-zugum a tsaye, idanuwansu sun kada.


Daidai lokacin da Hamoud da Mu’az din suka isko su. Har kasa suka tsugunna cikin ladabi suna gaya musu an samu jirgi mai zuwa Abuja, wanda zai tashi nan da awanni biyu. Kuma duk Mu’azzam ya saya musu tikitin bakidayansu, ya ce shi ma zai je, bai yarda ya zauna a Niger bai san halin da suke ciki ba.
Babu yadda suka iya, suka yi shahadar kuda dukkansu suka taho Abuja, inda daganan suka hawo jirgi mai zuwa Kano. Mata ba su san wainar da ake toyawa ba. ‘Yammata na can suna shirya wa angwaye roti, manya na girke-girke, an boye amarya Khaleesat a daki. Gumsu da Zulaiha kadai ke cikin damuwar da ba ta hana su shiga mutane ba, saboda yadda kowa ya zo gidan su yake nema, don yi musu Allah ya sanya alkhairi.


*****
Da jirgi ya sauke su a Kanon-Dabo taxi biyu suka yi shata zuwa gidan Dr. Mansour, duk da Mu’azzam ya ce su bari ya yi waya gidan kakanninsa na wajen uwa a zo a dauke su, amma cikinsu ba wanda yake jin zai iya minti goma cikin filin jirgin bai san halin da wadannan rabin jikin nasa ke ciki ba. Shi ma Mu’azzam dalilin da ya sa ya fi su kwanciyar hankali shi ne, bai san komai game da wayar da Aalimah ta bugo ba. Hamoud ma bai sani ba, manyan kadai suka yi maganar a tsakaninsu. Edrissa cewa ya yi da Mu’azzam sun biyo baya ne don su bincika abin da ya hana su tasowa tunda an kasa samun wayoyin kowa a cikinsu, har na Aseeya.
Tun kafin su karasa gidan Uncle Oussama ya fiddo waya ya kira Aalimah. Ta ce ga ta nan zuwa za ta dauke su zuwa asibitin da suke.
A kofar gidan suka sassauka, sai dai sun kasa shiga duk da Bilyaminu ya ce su shigo din. Har Aalimah ta iso wajen a motar Aboubacar duk ta yi wani wujiga-wujiga ta fita hayyacinta kwana daya rak! Dabara ta zo wa Uncle Oussama yadda za su hana Mu’azzam zuwa police station, sai sun fara zuwa sun tabbatar da abinda ya faru, ya ce shi da Hamoud su shiga gidan su jira su, tunda motar ba za ta kwashesu su duka ba. Mu’azzam ya soma shiga rudu, ko daga ganin yanayin Aalimah, bai taba ganinta cikin wannan yanayin ba, yarinya ce ‘yar kwalisa ta kin karawa mai tarin nutsuwa a iya sanin da yayi mata.
Damuwarsa ta soma bayyana karara akan fuskar sa, sannan ya za’a ce ita mace mai ciki ta tuka mota su tafi wani wuri su samari masu jini a jika a ce su koma gida su zauna? Amma bai furta tunaninsa ba, don a fuskokinsu basu bashi damar yayi musu tambaya ba, don haka ya zuba musu ido ya ga iya gudun ruwan su, sai Aalimahr ya daga idonsa dake a rine ya jefa wa tambaya.
“Ina Aboulkhair? Ina Daddy da Baba Mansour?â€
Aalimah ta juyar da kai cikin wani yanayi mara fassaruwa, ba tareda ta dube shi ba kanta na kallon kasa tace.
“Ni ma ban sani ba!â€
Sai hawaye suka zubo batare da ta ankare ba. Wadanda suka kara dugunzuma zuciyar Mu’azzam.
“To yanzu ina za ki kai su?â€
Wannan karon kamar cikin fusata ya tambaye ta. Don ya kasa gane dalilin wannan kumbiya-kumbiya da ake masa.
Da sauri Uncle Ossama ya ce, “Mu’azzam, in na isa in fada ka bi, to ku je ciki ku jira mu kai da Hamoud, za ta raka mu mu yi bincike a kansu ne a ofishin ‘yan sandaâ€.


“I will drive youâ€.


Mu’azzam ya fada cikin soma jin wani abu mai kama da mugun tsoro da matsananciyar fargaba na shigar sa. Wace irin magana ce wannan, ba a san inda suke ba? Bata suka yi ko sace su aka yi? Sai ka ce wasu kananan yara?
“Ita ta san garin, kai kuwa baka san ko’ina ba, shi ya sa za ta tuka muâ€. In ji Malam, yana mai dafa kafadunsa wannan karon cikin sautin lallashi, ganin cewa jan ido da nuna karfin iko bazai yi tasiri ba gare shi a wannan lokacin.
Bai ce komai ba ganin cewa sun fishi hujja, ya dan ja da baya ya bi su da ido suna shiga motar daya bayan daya. Da Hamoud ya sanya hannunsa cikin nasa ya sarke, ya ja shi a hankali zuwa ciki, sai bai yi masa musu ba.


Kai tsaye ofishin ‘yan sanda na Bompai Aalimah ta nufa kamar yadda ‘yan sandan suka gaya mata. Da tambaya da komai har suka samu ofishin da ya kamata su nema.
Da ta dan soma bayani, tun kafin ta gama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login