Showing 87001 words to 90000 words out of 126031 words

Chapter 30 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt

ki da ‘yar uwarki damuwa ki dinga cin abinci kin ji?
Allah ba ya dora wa rai abin da Ya san ba za ta iya dauka baâ€.
Ta kai kofin kunun bakinta. Aalimah ba ta da zabi ban da kurbar kunun. Tamkar koyaushe dandanon abinci ya fi dacin madaci daci a bakinta. Amma saboda wannan taron dangin da suka yi mata, Dr. Rayhanah na yi, Mama na yi, dole ta shanye kofin kunun nan tsaf. Nurse da Doctor na kara lallashi, Mama ma na yi da tattausan lafazi, yayin da Basma ke zaune daidai kafafun Aalimah tana shayar da jaririyarta, Hussainar na goye bayan Mama.


Halin da suke ciki kenan tun bayan rasuwar Aboulkhair da tafiyar Daddy 1 da Daddy 2 da Aboubacar kasar Amurka. Ba su da kowa da suke gani su ji dadi sai junansu. Wata irin kewa ke rarake zukatansu da ciwo mai tsanani. As a husband, ya kasance miji abin kwatance, kasaitacce a zuciyar matarsa wanda babu wanda zai iya tona zuciyarta ya ga halin da ta ke ciki, sai ita kanta. As a brother, shi dan uwa ne like a diamond a wajen kannensa, babu mai iya tona zuciyar Basma don hango zurfi da fadin wannan rashin da ta yi sai ita kanta. Amma sosai ta fi Aalimah juriya, domin ba a fada da ita a kan cin abinci ko don jariranta su samu nasu abincin da Allah ya halitta a jikinta. Sosai ta ke cin abinci, sai in abin ya ciyo ta ne ta ke dangwarawa Mama su ta kulle kanta a toilet ta yi ta kuka.
Yau likita ta ba su sallama, ba don zukata sun warke daga zogin da suke ba a’ah, sai don dukkaninsu suna da lafiya ta gangar jiki. Suka tattara suka koma gida, mama na ci gaba da gasa wa Aalimah da Basma jikinsu da tawul. Sun samu wayar Mummy da Aunty Gumsu inda suka yi musu sallama suka ce za su koma su ma don jinyar su Daddy, saboda Hamoud zai koma bakin aikinsa. Lokacin da suka bai wa Khaleesat wayar don ta yi sallama da su, domin tare da mijinta za ta wuce daga can ba su tsinana komai ba su duka ukun a handsfree sai kuka.
Mama ce ta kwace wayar. Tun daga ranar ba su kara ji daga su Mummy ba, suka ci gaba da jego karkashin kulawar Mama.
Ranar da Basma ta yada wanka aka yi arba’in din Aboulkhair a Yamai, sakon Malam Raazee ya isko su cewa, dukkansu su yi shiri su koma Niamey, zuwa har su Aboubacar su dawo gida. Mama ta soma yi musu shirin tafiya, an yi sa’a su Sabrina suna cikin hutun makaranta.
Basma ce ta saya musu tikiti, daga na Abuja har na Niamey. A washegarin ranar suka daga bakidayansu bayan Mama ta sallami masu aikinta Tabawa da Sabira da cewa inta dawo za ta neme su su dawo bakin aiki. Bilyaminu ya yi musu fatan alkhairi bayan Aalimah ta biya shi kudin aikinsa na gadi, har na wata uku masu zuwa a gaba.


A dakin inna Bintou suka sauka, Mama na dakin Inna Kasisi. Tunda suka zo Basma ba ta san kukan jariranta ba, kullum suna goye a bayan Bintou da Kasisi, idan Malam ya dawo zai ce a kai masa su su taya shi hira. Inna Bintou ba ta barinsu su zauna zugum-zugum din da suke zama, yanzu za ta dauke musu hankali da hira ko da ba za ta samu su tofa albarkacin bakinsu ba sukan yi murmushi. Ta ce Basma ce mai sa wa a yi kuka, don haka ta koma dakin ‘yammata ta bar mata Aalimah mai maida komai ga mahaliccinta.
Abin da ba ta sani ba har gara Basma na yin kuka ta ji dadi a zuciyarta, ita al’amarin da ta ke ji a tata zuciyar yanzu bayan dawowarsu Yamai ya fi karfin ta zubda hawaye. Baza ta gaji da cewa mutuwar Aboulkhair ta shammace ta ba; muguwar shammata. A daidai lokacin da take ganin babu diya macen data kaita sa’ar samun farin cikin dake cikin rayuwar aure. Rokon Allah ta ke yi ya dau ranta ta bi Aboulkhair a ko’ina yake, kuma cikin kowanne hali, a ganinta hakan shi ne kawai kwanciyar hankalinta da samun farin cikinta.
Ba ta son tuno komai na rayuwar da suka shimfida tare. Idan ta kai hannu ta shafa cikinta ta ji shi ma babu, zuciyarta neman fitowa ta ke daga allon kirjinta. Hakika an jarabci rayuwarta da mafi tsananin jarrabawa, tana rokon Allah cikin sujjadar kowacce sallar farillarta, ya kawo sanadin da za ta cinye wannan jarrabawa idan mai cinyuwa ce. Domin ta shafa a ko’ina ba ta ga ranar da za ta haye ta ba. Idan dawowar farin ciki cikin rayuwarta shi ne tsallake wannan siradin, tana da tabbacin har abada ba za ta tsallake shi ba. Ba mutane irin Aboulkhair ke shigowa cikin rayuwar dan Adam su fita da sauki ba. Ba mutane irinsa ke ajiye memories irin wadanda da za’a iya daina tunawa cikin rayuwar auratayya ba.
****

A LAS VEGAS
Watanni hudu kenan da faruwar wannan al’amari ga iyalan Raazee. Cikin wadannan watanni al’amura da yawa sun faru, majinyatan suna ta samun sauki cikin yardar Ubangiji. Dorin Daddy 1 da Daddy 2 na kafafu da hannaye duka ya yi kyau, an kuma kunce. Daddy 1 na tafiya da taimakon croches karafa guda biyu, yayin da Daddy 2 ana jiran raunin kafarsa ya karasa warkewa a makala masa plastic leg, wadda Mu’azzam ya saya masa. Aboubacar ya warware bakidaya sai dan sauran abin da ba’a rasa ba, don haka aka soma yi masa shirin tahowa gida don komawa cikin iyalinsa.
Duk tsawon zaman jinyar nan da Aboubacar ya yi ba su yi waya ba shi da Basma, asibitin ba sa barin majinyatansu rike waya don samun cikakkiyar nutsuwarsu. Haka Hamoud da ya wuce Japan shi da Khaleesat bai hada su sun gaisa ba ko sau daya. Mummy da Gumsu da ke yawan zuwa ganinsu, sai dai su fada masa lafiyar Basma data jikokinsu twins Don haka a yau da likitoci suka tabbatar masa da samun lafiyarsa suka kuma ba shi sallama, cike ya ke da dokin ganin iyalinsa.


Ba yadda Mummy Zulaiha ba ta yi da Aboubacar ba a kan ya kara sati daya ko ya kara murmurewa ya kara samun karfin jikinsa, amma Aboubacar ya ki. Yace Basma ta karasa jinyarsa. A daddafe ya kara kwana uku a gidan Mu’azzam bayan sallamarsa daga asibiti. Mummy ta saya masa tikiti mai zuwa Niamey kai tsaye daga Las Vegas babu transit.


Mummy Zulaiha a wannan dan lokacin ta yarda kishiya ‘yar uwa ce (idan ka yi katari da mai kyakykyawar zuciya kuma ta kirki). Gumsu ta zama kamar kanwarta ta jini, tare suke gudanar da dukkan al’amuransu na yau da kullum a gidan Mu’azzam, kama daga girki yau wannan ta yi, gobe wannan ta karba, jinyar mijinsu da dan uwansa da taimakekeniya a tsakaninsu. Gumsu-Moiram, ba ta da matsala ko kadan, ke dai barta da wauta, ban dariya da barkwancinta wadanda ke sayo mata soyayyar jama’a, inda duk ta zauna sai an san da ita a wurin saboda ban dariyarta. Mummy ta samu kanta da jin kunyar kanta in ta tuno haukan data rika yiwa mijinta da ‘ya’yanta akan auren Gumsu. Ita kam in haka kishiya take, to tana alfahari da tata, da zuciya daya take son ‘ya’yan ta. Sai ka rantse da Allah kwanciyar mijinsu jinya ba ta dame ta ba, harkan gabanta kawai ta ke, shi ma kansa Daddyn gaya masa ta ke a gaban kowa.
“Gara ma ka mike daga jinyar nan haka Daddy, Allah ya gani na yi hakuri. Gumsu ba ta da wani mijin bayan kai, ya ya ka ke so ta yi da ranta?â€
Ko a gaban likitoci Gumsu kan fadi wannan magana idan ta bushi iska, sai dai Daddyn da Mummy su ji mata kunyar ita babu ruwanta.
Bayan tahowar Aboubacar, ya zama daga Daddy 1 sai Daddy 2 a gadon asibiti. Ba dakinsu daya ba, kowa da dakinsa daban, amma suna yawan haduwa, in an fito da su shan iska a garden din asibitin ko an fito da su motsa jiki a gym. A nan ne su kan yi hirarrakinsu da suka shafe su ko ‘ya’yansu, da kuma iyayensu da ke gida Niger.
A yau ma kamar kullum, an fito da su ‘garden’ domin shan iska. Daddy 1 ( Ishaq) ya dubi kaninsa Daddy 2 (Mansur) ya ce,
“Ina lissafe da watanni, Aalimah ta dade da gama takaba, me ka shiryawa rayuwar ta a bangarenka?â€
Daddy 2 yayi saurin girgiza kai, a sanyaye ya ce,
“Me kuwa na shirya mata ban da abin da Ubangijinta ya shirya mata?
Muna namu Allah na nashi, kuma nashin shi ne gaskiya, dukkanmu lalube muke yi a cikin duhu.
A da ne nake wannan wautar (future planning) ga ‘ya’yana, amma yanzu kullum cikin istigfari nake a bisa hakan. Duk abinda Allah ya shiryawa rayuwarsu dai-dai neâ€.
Daddy 2 ya yi murmushi, shi shaida ne a kan cewa Mansour ya fi shi shiga tashin hankali da rashin Aboulkhair, ya dade yana sambatu har a cikin baccinsa. Ko lokacin da ake masa gyaran karaya akwai Aboulkhairi cikin sambatunsa irin na radadin ciwo. Wani tunani ne mai nauyi ke yawo a zuciyarsa daga jiya zuwa yau, wanda ya ke tsoron furtawa gare shi, ko ko ya ce, ba shi da ikon furta shi ga kowa ko ta ina aka je aka dawo. Don haka ya ja bakinsa ya yi shiru, yana sauraron bugun da zuciyarsa ke yi, wanda ke tafe da sake da jaddada masa muhimmancin maganar da ba ya son yi din da kowa banda zuciyarsa a kowanne bugu guda daya na zuciyarsa, tunanin ya hana shi sakat, shi kuma yana bi yana danne shi da fin karfin zuciya da karfafa imani.


A yau ne aka sallame su bakidaya daga asibitin Southern Hills, direban Mu’azzam ne ya kwaso su dukkansu zuwa gidan Mu’azzam, Mummy ta ce ya lissafa mata albashinsu daga ranar da Mu’azzam ya shiga asibiti zuwa yau ta biya su. Budan bakin Harrison sai cewa ya yi, albashin shekara Mu’azzam yake kullawa a lokaci guda ya basu, kuma ko ba don haka ba shi mai hidimtawa iyayensa ne ko babu ko sisi sabida kyautayinsa, jin kansa da kyautatawarsa gare shi. Harrison ya kare zancensa da cewa;


“I wish him a quick recoveryâ€.


Ya fita ya bar falon. Fuskarsa dauke da alhinin rashin sanin halin da Ubangidan nasa ke ciki. Wanda yake jin kamar ya dauka ya mayar a kansa.


Falon ya saura Daddy 1, Daddy 2 da matansa guda biyu, Yesmin da Nurat sun fita da Harrison zai kai su saloon, Daddy 2 ya ce,
“To alhamdulillahi, ni ma lokacin komawata gida ya yi, wannan gari naku sai ku, sanyin cikinsa mai takurawa da matsantawa ne. Yaya Ishaq, Zulaiha, Gumsu-Moiram na gode da dawainiyar ku, Allah ya rubuta a mizanin Hassanaat na zumunci, ya sa ya zame mana silar shiga aljanna baki daya, Ya jikan Aboulkhair, halinsa na gari ya bi shi. I have missed a darling son but I’m sure Ubangiji Rahmanur-rahimu ya fi ni son shi….â€.
Bai rufe baki ba ya lura sun soma yin sana’ar tasu (sharbe) Zulaiha da Gumsu, babu yadda za’a yi a ambato Aboulkhair a waje ko a yi masa addu’a suna wajen ba su zubda hawaye ba. Don haka ya yi maza ya sauya zancen sa da tambayar Daddy 1 yaushe Mu’azzam zai fito daga asibiti?
Zai so ya ganshi kafin ya koma. Akwai zantuka masu muhimmanci da yake son yi da shi. A take Daddy 1 ya karbi wayar Mummy. Dr. Nebrass ya kira, suka yi magana ya maida wayarsa aljihu.
Ya dubi kanin nasa ya ce, sai sabon wata za su kyale Mu’azzam ya shiga harkokinsa, they are very cautious a kan aikinsu ba kamar kasashenmu na Africa ba, sai sun tabbatar ba shi da damuwar da za ta dami kwakwalwarsa, kuma zai iya aikinsa normally, sannan zai iya daukan al’amuran rayuwa a zahirin yadda suke ba tare da sun shafi matsalarsa ba, amma shi zai iya ganinsa idan Mu’azzam din ya amince.
Ko da Nebrass ya gaya wa Mu’azzam Kawunsa na son yin sallama da shi zai koma Nigeria, bai ki ba. Hasalima sosai yake son ganinsa shima, ko yana kin jama’a ban da kawu Mansour da Aboulkhair shi kansa bai san dalili ba. Watakila don sun fi kowa iya tafiyar da shi ne da odd behaviours dinsa (baudaddun halayensa). Tare suka shiga dakin Mu’azzam da yammacin ranar, inda suka same shi yana sallah, Dr. Nebrass ya fita, Daddy 1 ya zauna zaman jiransa ya idar yana jan tazbahar hannunsa.
Bayan ya yi sallama ya dade yana addu’a, ko ba’a tambaya ba Daddy 1 ya san me Mu’azzam yake roka. A yanzu ya sani ba shi da wata bukata mafi muhimmanci wadda ta wuce ta samun rahmar Aboulkhair a wajen Allah. A sanda yake raye, ba su da bukata mai muhimmanci sai junansu. Aalimah ta taba gaya masa sabida Mu’azzam Aboulkhair ya dage ya tsaya tsayin daka ya karanci neuropsychiatry.
Al’amarin da ya dade yana burge shi hadi da kayatar da shi a zuci. Ya dade bai ga ‘yan uwan da ke son juna fisabilillah irin Mu’azzam da Aboulkhairi ba ko a labaran hikaya. Ta kuma gaya masa irin takaddamar da suka sha da Mu’azzam kan su zauna gida daya amma ya ki amincewa. Ba ya karantar zuciya, amma ya san Mu’azzam na nan yana regretting. In ya ce regretting yana nufin nadama mai sa zuciya ciwo da hanata jin dadin rayuwa ko ta yaya. Allah kenan.
7/4/21, 9:48 PM - Buhainat: HABUBAKAR ADO










#######################################################


Cikin satin suka biyo jirgi da komai nasu suka baro kasar Amurka. Bari na din-din-din. Ishak Raazee na mai jin wata irin kewa wadda sabo ke haddasawa na mamayar zuciyarsa. Mummy na mai jin kamar ita daya ta rage a fadin duniya sabida kewar mijinta da ‘ya’yanta. Saidai ko kadan bata yi nadamar hukuncin da ta zartas ba. Yesmin na kuka kamar ranta zai fita a kan rabuwar iyayenta, suka taho shi da Moiram da diyarta Nurat, ya baro mata Yesmin ne don rage mata bacin rai.
Haka Mummy ta yi kokarin shanye damuwarta wannan karon ba tare da ta raba ta tare da Mu’azzam ba, ganin cewa bai jima da barin gadon asibiti ba. Kuma in ba za ta manta ba Aboulkhair ya hane ta dora wa Mu’azzam damuwa, ko dai ta shanye kayar ta ita kadai, ko ta raba ta tare da shi (Aboulkhair) din, amma sharing dinta da Mu’azzam babbar illa ce ga kyakkyawan treatment din da yake samu.
Ko da ta koma office a washegari da niyyar bada hakuri a maida ita bakin aikinta wani ta tarar a mazauninta (JP MORGAN CHASE) ba su daukar wasa da aiki, ko da kuwa da excuse. Balle ita nata babu excuse din ma. Rana daya aka nemeta a kasar aka rasa. Tsabar rudanin rayuwar data samu kanta ya mantar da ita cewa ita din ma’aikaciya ce, ma’aikaciyar ma ta babban bankin Amurka irin JP Morgan. Haka ta dawo kafafu a sage, ta soma neman wani aikin ta yanar gizo, amma har watanni uku suka shafe bata dace ba. Sakamakon matsin lambar da musulmin kasar ke fuskanta a lokacin daga sabuwar gwamnatin Amurka karkashin mulkin sabon shugaban kasa Donald Trump. Da yawa sai komawa suke kasashen su na asali. Ba don Yesmin da ke zuwa makaranta ba Las Vegas za ta tattara ta koma bakidaya, in Mu’azzam ba zai rike ta ba ita da autarta, ya san yadda zai yi da su. Shine kadai dolenta a yanzu.


******

FLASHBACK
An sallami Mu’azzam ranar wata lahadi, sati guda kacal ya kara a gida, sannan ya koma aikinsa. Ya hada wayoyinsa, ya kira duk wanda ya dace ya gaisar. Ciki har da Mummy, ta gaya masa tana Boston amma ba ta gaya masa cewa Daddy ya sake ta a kansa ba. Sosai ta koyi hadiye damuwa, in ta tuna da Aboulkhair.
Ta san da yana raye ransa zai yi matukar baci, za ta kiyaye abin da ba ya so a bayan ransa. Ta kasance mai bata masa rai da hakan a sanda yake raye. Zata kasance mai kiyayewa a sanda babu shi. Ta ce masa Daddy yana Niamey, kuma ta turo masa kudi cikin account dinsa kafin ya samu albashi ya soma shigo masa ta san zai bukace su sosai.
Sosai ya yi godiya, yana mai jinjina soyayyar uwa ga abin da ta haifa, ta Mummy is special. Ita dai ‘ya’yan ta kawai. Su samu jin dadi shine burin ta. Kada su nemi wani abu su rasa a rayuwar su. Bazata taba canzawa daga hakan ba.
Ya kira Daddy suka yi hira sosai, inda ya gaya masa ya koma Yamai, ya samu aiki a can da hukumar hulda da kasashen wajen su, yanzu kuma ya samu wani makeken fili kusa da gida ya saya ya fara gini. Gini yake so ya yi one in town wanda dukkansu zasu sake a cikin sa.
Ya cigaba da gaya masa amon muryarsa dauke da kauna irin ta uba ga dansa, irin tsarin duplex din da yake so a yi masa. Yace sai yafi gidansu na Boston kyau nesa ba kusa ba, zai masa part din sa guda wanda zasu ke sauka in sun zo shi da iyalinsa. Sosai ya baiwa Mu’azzam dariya. Ya canza position din rikon wayar daga dama zuwa hagu ya cigaba da sauraron almarar Daddy. Koko ya ce mafarkin Daddy. Ba tare da Daddyn ya kula da karbar da yake yiwa zancen nasa ba ya cigaba da labarta masa cewa har dakin yaran su za’ayi a cikin bangaren nasu, a zuba duk wani nau’I na kayan wasan yara. Mu’azzam tausayin mahaifin nasa yayi matukar kama shi, su

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login