Showing 81001 words to 84000 words out of 126031 words
Chapter 28 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt
aka yi musu jagora zuwa ofishin kwamishina. Kamar dama jiran su ake yi. Malam yace da Aalimah ta koma mota ta zauna ta jira su. Kuma bata yi musun bin umarninsa ba.
Mikewa kwamishinan ya yi ya ba su hannu dukkansu cikin mutuntawa. Ganinsu manyan mutane farare tas-tas dasu kamar larabawa, ga tsohon ya sha rawanin da ya sanar da shi malamin buzu ne. Sannan suka samu kujerun dake fuskantarsa suka zazzuna. Daga inda suke suna iya karanto sunan kwamishinan dake like jikin wani dan karfe ruwan gold akan teburinsa; Commissioner of Police Isma’ila Dauda Kataki.
Sai da kwamishina ya ga sun nutsu, sun bashi dukkan hankalin su. Sannan ya soma da yi musu tunasarwa a matsayinsu na musulmi da ya rataya a wuyan dukkanin mu da mu karbi kaddara mai kyau ko mara kyau, mai dadi ko mara dadi, domin samun cikar imanin mu. Dukkansu sun gama mika wuya ga karbar koma me zasu ji a wannan lokacin, wanda ba irin hasashen da basu yi ba kafin kwamishina ya gama zagaye-zagayen sa, zukatansu kamar su fito daga kirazansu a lokacin da Kwamishinan yake gaya musu mummunan hatsarin motar da ya afku kafin a shiga boarder din dake tsakanin Najeriya da Nijar, tsakanin motocin guda biyu babbar (Jeep) da karamar mota (toyota Camry), wanda a take ya yi sanadiyyar rayuka uku. Sauran suka jikkata, mummunar jikkata, kuma su ba su san wadanne ne na wannan motar ba, wadanne ne na waccan motar ba. Gabadaya sun cakude ta yadda sai wadanda suka san su ne kadai zasu gane su. An dai kai gawarwakin guda uku matuary kafin zuwan ‘yan uwansu don su tantance su. Wadanda suka ji ciwo kuma suna karkashin kyakkyawar kulawa.
Sun samu wadannan I.D cards dinne guda biyu na shaidar gida da wajen aiki a aljihun motar Jeep da ta ragargaje na wani Aboubacar da wani mai suna Mansour. Shiyasa aka taho dasu Kano.
A take Malam Raazee da ‘ya’yansa suka soma ambatar, “Innalillahi wa’inna ilaihi raji’unâ€. Yi suke suna maimaitawa, wani ba ya jin na wani.
Kwamishina ya ci gaba da kwantar musu da hankali da tausasan kalamai. Ya fada musu su zo a je su tantance gawarwakin su kuma ga wadanda suka tsira a emergency unit na asibitin Malam Aminu Kano.
Ba su bata lokaci ba suka fito, a cikin mota suka tadda Aalimah ta kifa kai akan sitiyarin mota abin tausayi. Idanunta sun yi ja sun kankance. Fargabar halin da za’a ce mata su Daddy na ciki ya gama karar da dukkan kuzarin ta. Kafin ta dago har sun shigo motar jikin su yanata rawa. Suna masu kauda kai daga gareta. Ba wanda ya iya ya hada ido da ita. Motar ‘yan sandan da za ta yi musu jagora na gabansu, suka ce da Aalimah ta bi bayansu ba tare da sun yi mata bayanin komai ba.
A mutuary na asibitin Malam, ba su bi ta kan wadanda aka ce sun tsira ba, sai wadanda aka ce sun mutu!!!
Allah sarki! Kada ku so ku ga fuskar tsoho Ibrahim Sarhamu Raazee da manyan ‘ya’yansa a wannan lokacin. Shekarun su sun kara bayyana akan jajayen fuskokinsu. Azabtuwa suke a zuci da ruhi. Sun kasa shaida gawar kowa cikin ukun da aka nuna musu sabida yadda halittarsu ta jikkata. Wasu daga ciki hannu da kafa suka fita.
Eidrissa ne ya nuna daya daga ciki, ya ce ko mutuwa ya yi ya dawo wannan Aboulkhairi ne ba zai kasa shaida shi ba. sauran ba su da zabi ban da su amince a fitar musu da shi.
Da taimakon ambulance da kwamishinan ‘yan sanda aka tafi da gawar filin jirgi don yin cuku-cukun tafiya da ita Niamey. Malam ya ce a nuna musu rayayyun, inda likitocin suka kai su ga masu hatsarin.
Hailala suka saki da suka yi tozali da Dr. Mansour a gadon farko babu kafa guda, Daddy Ishaq na kwance cikin tsananin ciwo da karaya har biyar a kafa da hannu, bai san wanda ke kansa ba, sai Aboubacar wanda ke cikin wani irin hali na rai kwakwai-mutu-kwakwai.
Iyakar tashin hankali wadannan mutane sun shige shi irin wanda basu taba shiga a rayuwarsu ba. Duk abin nan da ake Aalimah ba ta sani ba, ta koma gida kamar yadda Oncle Oussama ya umarce ta yace in sun gama abinda suke za su kira ta ta zo ta dauke su. Ta kwantar da hankalinta an same su kuma babu wanda ya mutu amma sun ji rauni sosai kuma suna karbar kulawar gaggawa yadda ya kamata.
Da wannan dan kwarin gwiwar ta tuka motar a hankali kamar mai tafiya akan kwai ta koma gida, tana shiga ta wuce kitchen ta baiwa su Tabawa umarnin su dafa abinci za ta kai wa su mama asibiti, ga Hamoud da Mu’azzam can a falon Daddy su kai musu. Bata bi ta kan su Mu’azzam din ba, wadanda ke can falon Dr. Mansur sun yi zugum-zugum ko hira sun kasa yi a junansu tsakanin sa da kanin nasa Hamoud, Mu’azzam ya cure hannayensa wuri guda ya mikar dasu ya dora habarsa a kansu, banda sallah ba abinda ke tayar da su, ko ruwa basu iya sha ba tun shigowar su falon.
A lokacin ta samu ta rama sallolin da ke kanta, tayi wanka sama-sama, ta canza kayan jikinta. Suna gamawa Sabira tazo har daki ta sanar da ita, ta ba su umarnin su kai wa Mu’azzam da Hamoud falon Daddy, su kula dasu ko suna bukatar wani abu, ita kuma ta dauki na asibiti ta wuce gate ba tare da ta leka su Mu’azzam din ba, ta sanya a bayan mota ta tafi.
Malam Raazee da ‘ya’yansa sun yanke shawarar za su koma Niamey tare da Mu’azzam, don ya halarci jana’izar dan uwansa. Eidrissa da Hamoud su zauna tare da majinyatan kafin a gama jana’iza sai a san yadda za’a yi. In can za su koma da jinya to, in kuma Mu’azzam zai fita da su ne toh, duk da bai san halin da Mu’azzam din zai fada ba in ya fahimci ya rasa dan uwansa rabin-ransa, barin jikin sa, sanyin idaniyarsa, Aboulkhairi. Da haka suka bar asibitin suka bi motar ‘yan sanda tareda ambulance din zuwa filin jirgi. An yi sa’a akwai jirgi wanda zai tashi zuwa Abuja nan da awa daya don haka bazasu samu jinkiri sosai ba.
Kafin su isa airport, Aalimah Oncle Oussama ya kira a waya, yace ta dauko Mu’azzam daga gida ta kawo musu shi filin jirgi, zasu koma Niamey tare da shi, amma Kawu Eidrissa da Hamoud suna nan tare da majinyatan. Don haka ta fadawa Basma da Mama abinda Kawun nasu ya ce, ta tuko motar ta dawo gida don tafiya da Mu’azzam din kamar yadda Baffan nasu yayi mata umarni .
7/4/21, 10:50 AM - Buhainat: HARUNA TANKO
Da ATM card din Aalimah Mama ta biya duka hospital bill dinsu. Basma da ake jinya ita ta koma jinyar Aalimah. Ga danyen jego, ga jarirai sabuwar haihuwa har guda biyu. Abin duka babu dadi garesu ko ta ina. Abincin da masu aikin Mama ke kawowa babu mai iya cinshi. Duk kokari da kwarewar likitocin asibitin international sun kasa tsayar da cikin jikin Aalimah, dole aka yi mata tiyata aka cire shi babu rai, an gama masa halitta tsaf, don samun tata rayuwar. Abin gwanin ban tausayi.
In har kana da zuciyar imani dole ka kokawa iyalan RAAZEE a wannan hali na jarrabawar Ubangiji da suka tsinci kansu. Wanda basu taba tsintar kansu a kwatankwacin sa ba, Basma da jariranta da Mama sun warware, sune suke kula da jinyar Aalimah, yayin da Hamoud da Oncle Eidrissa ke kula da iyayensu da Aboubacar dake gadon asibiti. Duka daga ATM din Aalimah ake biyan duka asibitocin nan. Kafin sakon Mu’azzam ya cimmasu, na dauke marassa lafiyan daga Kano zuwa Amurka, tare da Hamoud.
******
Ranar da likitoci suka sallami Aalimah daga gadon asibiti, ranar ne Hamoud ya daga da su Daddy zuwa asibitin da Mu’azzam ya shirya musu jinya a garin Las Vegas, saukarsu a asibitin Southern Hills Hospital ke da wuya motar asibitin Southern Hills ta kwashe su karkashin kulawar likitoci zuwa asibitin. Dakuna na musamman Mu’azzam ya kama musu bakidayansu, kowanne dakinsa daban.
Tunda suka je ba su ga Mu’azzam ba, basu ji muryarsa koda a waya ba, asibitin ke ta dawainiya da su da bukatocin su tun daga airport, direban da ya dauko su ma na asibitin ne ba direban Mu’azzam ba. Ya kai majinyata asibiti, ya kai Hamoud gidan Mu’azzam ba tare da ya yi masa bayanin komai ba.
A gidan ne Hamoud ya tadda yaron Mu’azzam da direbansa Harrison inda yaron ya ce, zai dinga kawo masa abinci sau uku a kowacce rana bisa umarnin ubangidansa, direban kuma ya ce zai dinga kai shi asibiti wajen majinyatan duk sanda yake so, maigidansu an rike shi a asibiti tun jiya, shima ba shi da lafiya.
Duk kokarin Hamoud na su kai shi asibitin da Mu’azzam din yake sun ki. A cewar su ba’a yi musu wannan umarnin ba. Babu fuska ma daga gare su na a cika su da tambaya, they are very cautious akan aikinsu kowanne abin da ya kawo shi yake yi a gidan ya gama ya tafi.
Hamoud na takawa tsakiyar falon gidan ya ga gaba daya gilassan taga sun ragargazo kasa, duk wani abu na gilashi a fashe yake a gidan. Including talbijin dake manne jikin bango ta kwankwatse. Bai gama fita daga wanan mamakin ba sai da ya kutsa kai dakin barcin Mu’azzam.
Komai yayi raga-raga. Hatta kwan fitila bai tsira ba, da bed-side lamp, duk sun yi kwatsa-kwatsa ga jinin da ya tabbatar na Mu’azzam ne ya disa a wurare daban-daban.
Tsoro, mamaki, fargaba da tu’ajjibi suka cika Hamoud, rokon Allah yake cikin zuciyarsa ya sa ba Mu’azzam ne da kansa ya aikata hakan ba. To in ba shi bane wanene? Da sauri ya fito daga dakin ya rufe, ya nemi wanda zai iya kwana cikin dakunan dake kasa ya sauka a ciki.
Da safe da yaron Mu’azzam ya kawo masa karin kumallo ya tambaye shi dalilin da ya sa bai share gilassan dakin Mu’azzam ba, yaron ya ce, ba’a yi masa izinin shiga ba, amma ya share na falon kasa yanzu, jiya duhun dare bai barshi yayi aikin ba, amma shi zai iya shiga ya share na bed-room din tunda shi dan uwansa ne.
Hamoud ya karbi abin shara da mopper ya nade hannun riga ya shiga aiki, ya share dakin tas, ya goge ko’ina, ya feshe dakin da freshners, sannan ya yi wanka yaci abincin da aka kawo masa yayi shirin tafiya asibiti.
Ya samu su Daddy cikin kyakkyawar kama fiye da wadda suka zo a cikinta, an yi musu wanka, an sauya musu kaya, ga abinci mai rai da motsi suna ta ci, ya bi su daya bayan daya yana runguma yana hawayen farin-ciki. Sannan ya gaya wa Daddyn Mu’azzam abin da ya gani tun shigarsa gidan Mu’azzam.
Nan Daddyn ya ce da shi, kada ya damu, ya san likitoci suna kula da Mu’azzam yadda ya kamata yanzu haka, kuma sai ya dauki tsawon watanni zai fito daga hannunsu.
Cikin bayyanannen mamaki Hamoud ya tambayi Daddy Ishaq wanda ba ciwo ne kadai yake nukurkusar shi ba, ya maida shi ba umh ba uhum umh, ya fiddo tsufansa zahiri wanda jin dadi ke boyewa a baya, sai ido da dogon karan hancin su na iyalin Raazee kadai ya rage a fuskar ma’abociyar zati da kamala, illa rashin ‘Aboulkhair’ da Malam ya gaya masa. Koyaushe za ka same shi rike da carbi, rokon Allah kawai yake ya yi wa Aboulkhair rahama da gafara. Ya hada fuskokinsu da alkhairi. Yasa can ta fiye masa nan. Halin sa nagari ya bishi. Rayuwar duniyar bakidaya ta fice mai a ka.
“Daddy, Mu’azzam yana da disorder ne?â€
Ya tsinkayo muryar Hamoud can saman kansa yana tambayar sa. Cikin murya mai ban tausayi da bayyanar da kauna.
Daga masa kai kawai ya yi, hawaye na bin fuskarsa na tausayin Mu’azzam. Ya san tabbas Mu’azzam ya yi dauriya, ya yi dauriya, ya yi dauriya har an zo gejin da kwakwalwarsa ta kasa jurewa, ciwonsa ya tashi, da taimakon rashin magani da baya sha. Shine ya yiwa gidan sa wannan aika-aikar. Wadda rabon da ciwon ya sake tashi yayi irin haka anyi shekaru tara.
Hamoud gefe ya koma ya sharbi kukansa mai isarsa, tausayin Mu’az da kewar Aboulkhair ya lullube masa zuciya, yana sharar hawaye da hankicin sa yake fadin.
“Ubangiji ka saukaka muna! Idan laifi muka yi gare Ka Ya ubangiji Ka gafarta mana!â€.
Ya durkushe a wurin yana ta kuka. Daddy Ishaq ma na yi wiwi. Tunda aka fada masa rasuwar Aboulkhair bai yi kuka ba sai fa yanzu. Da Hamoud ya gaya masa halin da Mu’az ke ciki. Ga gabban jikinsa na zogi ta ko’ina, kashi yana hadewa da dan uwansa.
A fili yake fadin,
“Ya Arrahmanurrahim ka saukaka muna! Mun tuba Yaa Ubangiji mun tuba! Hamoud da gaske ne na rasa ABOULKHAIRI???â€
Hamoud babu baki sai kuka, da istigfari a fili da yake ta yi.
Likita ne ya bude kofa ya shigo jin koke-kokensu, ganin halin da suke ciki ya ce da Hamoud zai hana shi zuwa asibitin kwata-kwata idan raunata majinyatan zai dinga yi, maimakon ya karfafe su sai ya zo ya raunana su?. Da hannu biyu Hamoud yake rokonsa kada ya hana shi shigowa wajen Kawunninsa. Yana ta kuka a fili kamar ba namijin soja ba, sojan ma na sama. Likitan ya ce, to ya daina kuka a gabansu. Rantsuwa ya shiga yi masa kan ba zai sake ba, amma kar ya hana shi ganinsu. Tausayi ya sa likitan ficewa daga dakin. Ya sayo musu kofa a hankali.
******
Sauki na samuwa gare su a hankali a cikin gangar jiki, amma ban da a zuciyoyin su. Sun gaya wa Hamoud za’a sanya wa Daddyn Aalimah kafar plastic leg da zarar ya samu lafiya. Mu’azzam ya sakar musu katunan bankinsa na bankuna guda biyu; WellFargo da JPMorgan Chase ya ce komai a cira a yi musu, komai ake bukata a cira kawai. Wannan nauyin ya dora shi ne a wuyan tsohon likitansa kuma wanda za’a iya kira amintaccen sa a Las Vegas bakidaya duk da a haife ya haife shi wato Dr. Nebrass Sheldon, wanda ya yi retire shekarun baya, daga baya kuma ya bude private clinic nasa na kansa. Shi ne amintaccen Mu’azzam sabida dadewar da yayi karkashin kulawarsa tun farkon lalurarsa, shi ya daurawa alhakin kula masa da iyayensa da ya kawo asibiti kafin gushewar nasa hayyacin. Yana karkashin kulawar manyan likitocin kwakwalwa yanzu haka abokan aikin Aboulkhair, karkashin jagorancin Dr. Nebrass din wanda yayi gaggawar nema bayan dawowarsa kamar yadda Malam Raazee yayi masa umarni.
A baya Nebrass ya damkawa Aboulkhair file din Mu’az, kulawar sa da komai da ya danganci lafiyarsa ya koma hannunsa, amma bayan dawowarsa daga tafiyar da yayi zuwa gida Niger da rasuwar Aboulkhair zaune cikin kwakwalwarsa, dole ya nemo Nebrass da ya fahimci yana cikin risk na tashin ciwon sa a kowanne lokaci daga yanzu, da kuma rokon da Malam Raazee ya yi masa na ya kai kansa ga likitocin sa, in ba haka ba bazai bar su Daddy a hannunsa ba.
Ko kafin Nebrass ya iso gidansa don ya duba shi, kasancewar baya gari yayi ‘yar tafiya zuwa Orlando Mu’azzam ya riga yayiwa gidansa mummunar illah, ya ji wa hannayensa ciwo, yayi asarar dukiya mai yawa, ya shiga black episode na aggressive tendency sabida ya dade baya shan magani kuma ya kasa karbar reality na rashin Aboulkhairi na har abada a tare dashi....
Nebrass da Daddy sun san juna tsayin shekaru goma sha a baya, tun Mu’azzam na Boston yake dubashi kafin ya shiga jami’a a nan Nevada (Las Vegas). Wato tun dawowarsu Massachusetts sakamakon lalurar Mu’azzam, aka hada shi da Nebrass a matsayin mashahurin neuropsychiatrist din da babu kamar sa a U.S. Tsayin lokacin da Mu’azzam ya dauka yana karbar treatment a hannunsa ne ya haifar da aminci da girmama juna a tsakaninsu, Nebrass ya zama kamar Babansa sabida ya manyanta. A wani bangaren abokin sa. Sannan Mu’azzam na yi masa alheri sosai.
Daddy na kan gadon asibiti, ga dori a ko’ina a kafafu da hannayensa, amma sosai yake magana, yana kuma gane komai da kowa da ke kansa sabanin su Aboubacar. Nebrass ya sameshi a wannan ranar da daddare, ya gaya wa Daddy kudin account din Mu’azzam sun yi kasa sosai, jinyarsu da tasa (wadda ta fi tasu cin kudi) ya lamushe komai, jinya a turai ba wasa bace har ta rayuka uku ban da shi uban gayyar mai karbar (special psychiatric care), ya kara da cewa ya yi reporting din rashin lafiyar Mu’azzam a kamfanin su a matsayin sa na likitansa don haka sun bashi isashshen hutu har zuwa ya samu ingantacciyar lafiyar da yake ganin zai iya komawa bakin aikinsa.
Kamfanin man petir na Chevron na ji da Engnr. Mu’azzam Ishaq Razee sabida hazaqarsa da zurfin ilminsa, don haka yana daga cikin ‘yan gaba-gaban goshin da ake ji dasu a Chevron Corporation. Ya gayawa Daddy salary account din Mu’azzam baya hannun sa, Mu’azzam bai bashi ba, kuma a halin da yake ciki bazai iya tambayar sa ba, don haka kudi tafiya suke ba sa shigowa.
Daddy ya ce ya zo masa da waya ya kira Mummy Zulaiha.
Mummy, wadda ke can Niamey cikin sabuwar rayuwa ta dayanta Allah da jin tsoronsa hadi da jingine farin ciki baki daya a muhallinsa, ta amsa wayar mijin nata a can kuryar dakin Inna Bintou. Gaba daya Mummy Zulaiha ta zama kashi da rai don rama, idanunta kyawawannan sun zama abin tsoro sabida yadda suka zurma cikin kwarmin idanunta. Fatar bakinta ta bushe rayas, alamun babu isasshen ruwa da jini a jikinta. Sakamakon rashin cin wadataccen abinci na lokaci mai tsawo. Tsufan ta da gayu ke boyewa a yanzu ya fito sarari bakidaya kowa na ganinsa.
Daddy Ishaq yace.
“Ku yi shiri ke da Gumsu ku