Showing 6001 words to 9000 words out of 126031 words
Chapter 3 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt
ce masa ‘Yaaya’, ka dinga respecting dinsa. Wannan ne babba abinda ya ja hankalin Mahmud ga son hada jini da iyalin Dr. Mansour Raazi. Tsakanin Daddy da yaransa auzinanci suke yi ko yaren Temachekwato harshen Inna Kasisi, Mama ce kadai ke musu Hausa da Turanci. Wani lokacin ma tana musu Margiduka ba wanda ba sa ji. Duka yaran gidan sun saba da shi, suna kula shi kamar Yayansu Aboubacar, banda Yayarsu Aalimah.
Wata mutum guda daya a gidan Dr. Mansur Razee mai wani irin halina seriousness irin na Babanta. Ba ta da hayaniya, ba ta da sakin jiki da mutane. She’s very authoritative ga kannenta, kuma sosai suke jin tsoronta. Shi kansa Yaya Aboubacar wani lokacin sai ya ji tana commanding dinsa. Abin yana ba shi dariya sosai. Kafin ya ankara, ya zama infatuateda kan Aalimah,so much so that, in ya wuni bai ga giftawarta ba, sai ya yi ta zarya kamar zararre a cikin gidan ko ya tambayi Sultana cikin hikima. Sau tari yarinyar kan ce masa, ‘karatu ta ke yi’, kuma ‘ba’a yi mata magana in tana karatu’. Ta hakan ya gano cewa; karatu is the best hobby for Aalimah, kuma da shi zai yi amfani ya jawo hankalinta gare shi.
Aka yi sa’a Aboubacar ya tafi Yamai a safiyar wata litinin zai halarci daurin auren daya daga cikin cousins dinsa dan Kawu Saddam wato jikan Inna Bintou. A ka’ida kuma Aboubacar ke yi musu extra lesson kullum bayan sun dawo daga islamiyya wadda ita ma a nan cikin New Site ta ke, don haka Daddy ya dora alhakin koyarwar a wuyan Mahmoud kafin dawowar Aboubacar.
Wannan shi ne mafari, mafarin soyayyar Aalimah da Mahmoud Sulaiman Kaita.
Ta samu Mahmoud irin mazan da ta ke burin aura, wato yaro dan boko mai kwakwalwa da nunawa macen da suke so soyayyah a fili kamar duk duniya ba wata macen sai ita. Kafin dawowar Aboubacar sun shaku fiye da zato, sai daga baya ya fahimci ko me suke ciki.
A zuciyarsa ya yi musu fatan alkhairi, amma a fili ya dora wa mu’amalarsu ido, har ya fahimci tsaftacciyar soyayya ce suke yi wa juna, Mahmoud ba yaudarar kanwarsa yake da niyyar yi ba, har ya gama hidimar kasarshi ya koma garinsu Katsina, shi da Aalimah remains in contact ta wayar Yaya Aboubacar ba tare da sanin Mama da Daddy ba wadanda ya san ba za su taba amincewa aurar da Aalimah a daidai wannan lokacin da ko sakandire ba ta gama ba, shi kuma yana son abokinsa da Aalimah don ya san in har ta aure shi to ta yi miji, wanda zai rike masa ita da daraja da mutunci har karshen rayuwarta.
Dalilinsa kenan na kyale su suka ci gaba da contacting juna ta wayarsa. Don Aalimah a lokacin Iyayensu basu bata damar mallakar waya ba. Bayan komawar Mahmoud garinsu, ba da jimawa ba ya samu aiki da hukumar zabe ta kasa a can Katsina, ita kuma Aalimah ta gama jarrabawar fita sakandire a shekarar. Ba jimawa sakamakonsu ya fito, tana daga cikin zakarun gwajin dafin da (BUK staff school) ta yaye a shekara ta 2015.
A wannan lokacin ne Maman su Aalimah wato Aseeya ta samu mijinta da takardun banki,mai dauke da sunanta na fixed deposit account da ta bude da gadon mahaifinta. Kudi ne zunzurutu da a iyakacin rayuwarsa bai taba mallakar ko da rabinsu ba. Ta gaya masa kudurin da ta ke da shi, wato tana son kai Aboubacar karatu jami’ar da mahaifinta marigayi V.C ya yi a kasar America. Tana so Aboubacar ya gaji Babanta. Watarana ya zama kamarsa....as the only male child she have (a matsayin sa na Da namiji daya kwal data mallaka).
Murmushi Daddy ya yi ya dube ta sosai cikin idanunta, sannan ya soma magana.
“Aboubacar bai da sha’awar hakan, bai da sha’awar ilmi mai zurfi,abinda yake mafarki kawai(is to become a banker), amma kina da wani dan, da zai iya cika miki wannan burin. Amma fa in za ki kauda kowanne irin tunani ki bada kwarin gwiwaâ€.
Da mamaki ta ke kallonsa,
“Duk ‘ya’yana mata ne Daddy, he’s the only male one....â€.
“… Mace ma mutum ce!â€
Ya yi hanzarin katse ta.
“…Amma me rauniâ€. Ta ba shi amsa.
“Idan za a yi ta kallon rauninta ba za’a ba ta damar bada gudunmawarta ga al’umma ba. Musamman in aka fahimci cewa tana da motive a kan neman ilmin. Don haka in har amincewa ta da shawara ta ki ke nema, to Aalimah ce za ta tafi karatu ba Aboubacar ba. Shi ya ci karfin duk wani karatu da zai yi a gaba, tunda yana da kwalin degree. Duk wani abu da zai kara karantawa a gaba ado ne kawai ga na bayaâ€.
Mama ta yi shiru tana tunani, kafin cikin sanyin jiki ta ce,
“Daddy ka fahimce ni, ba kasancewar Aalimah mace wajen karatu ne abin dubawa ba. Yadda tafiyar mace wani waje bata halatta ba tare da muharrami ba. Aalimah ba mu yi mata aure ba, mu dauke ta mu kai ta kasa irin America mu ajiye mu ce ta yi karatu babu idon kowa a kanta babban kuskure ne duk irin tarbiyyarta.
Ubangiji ma sai ya tambaye mu. Na sani bokonka mai zurfi ne, irin wanda ke hana ku daukar hakan da muhimmanci, amma hakan zai zama mana damuwa a gaba, kada garin neman gira a rasa idoâ€.
Ta karasa cikin karyewar murya.
Murmushi Dr. Mansur ya yi ya ce,
“Na fahimce ki, na kuma fahimci abinda kike so na fahimta, ni ma ba zan amince ta zauna a hostel ba, hannun Yaya Ishaq zan damka ta. Ta zauna cikin iyalinsa.
Fadamiki ne ban taba yi ba, ya sha cewa in ba shi ita ya hada da yaransa su Basma ya rike ina cewa, sai ta gama makaranta. Ni ma kuma akwai nawa tanadin da na dade ina yi don haka kudin nan naki ki yi tunanin business din da za ki fara da su, ni zan dauki nauyin makarantar Aalimahâ€.
Nan Mama ta nuna ba ta yarda ba, ta san ba shi da wannan halin, amma ya ce ta kyale shi.
Abinda Mama bata sani ba shine;Federal Scholarship ne ya samo mata ta hanyar wani abokinsa shugaban scholarship board na kasa, tare suka yi karatu, wato Dr. Obi Olayinka. Da mama ta dage tana so ta bada tata gudummawar sai ya ce, to ta saya mata ticket, amma duk sauran shirye-shiryen Babanta ne ya yi mata.
Sai da komai ya kammala, admission da komai, sannan ya kira dan uwan nasa ya sanar da shi komai. Ishaq din ya ce da bai yi wahalar neman scholarship din ba ma ya yanke shawarar sanya su ita da Basma daga aljihunsa a wannan shekarar, amma tunda ta riga ta samu shi kenan ya sako ta a jirgi ta taho.
Ranar da Aalimah za ta taso kuma tafiya ta kama shi daga office dinsu zuwa California zai kwana daya, don haka ya tura wa Dr. Mansour adireshin gidan nasa, ya ce ta dauki drop har gida.
Zulaiha tana wajen aiki sanda za ta iso, yaransa maza kuma duk ba sa gari. Wannan shi ne tarihin su Aalimah da asalin tahowarta kasar America. Kafin ta taho ta je Maiduguri da Yamai ta yi sallama da kakanninta da ‘yan uwanta. Inna Kasisi kam abin bai yi mata dadi ba ko kusa, yadda ba ta son rabar Zulaiha, haka ba ta son kowa nata ya rabe ta, balle Aalimah wadda ko a cikin jikokinsu ita ta daban ce, mai kyakkyawar tarbiyyah da sanin ya-kamata. Suna ji da ita fiyeda sauran jikokinsu. Tsoronta Allah tsoronta kada ta koyo dabi’un ‘ya’yan Zulaiha da kullum ke sanya ta cikin takaicin wai cikin zuri’arta suke.
*****
Aalimah, ta ja dogon numfashi a yayin da tunaninta ya zo nan, tana kallon su Basma na shigowa falon, babu kamannin ‘ya’yan Auzinawa ko na Malam Bahaushe ko kadan a tare da su, sun fi kama da ‘ya’yan kasar Somalia. Fatar Babansu da ta mamansu bahaushiya ta cakude ta ba su wata irin colour da complexion mai ban sha’awa. Ga su da tsayi da mulmulallen jiki tubarkallah. Sunshades a idanun Basma da Khaleesat, dogayen wandunan jeans na mata da rigunan Armani collection a jikin kowaccensu. Khaleesa ta kusa kamo Basma a tsayi, babu dankwali a kansu gashin Abzin din ya kwanta a kafadunsu.
Basma a gaba, sai Yesmin biye da ita, sannan Khaleesa, Aunty Zulaiha da Daddy suka biyo bayansu.
Tsayawa ta yi a kofar kicin din ta harde hannayenta a kirjinta tana kallonsu da murmushi irin na ‘yan uwantaka. Khaleesat ce ta fara ganinta, ta zare sun shade dinta ta mutstsika idanunta ta ce,
“Daddy, am I dreaming? She looks so much like Aalimahâ€. (Daddy Mafarki nake yi? Ta yi kama sosai da Aalimah). Sannan ne hankalin kowa ya kai gare ta.
Aunty Zulaiha kam shaf! Ta manta da zuwanta, sai yanzu ta tuna. Take fuskarta ta sauya, ta wuce upstairs kai tsaye.
Basma ta yi cilli da jakarta ta yi kanta da dan banzan gudu, saura kadan su sha kasa su duka biyun, tana kakabin murna. Daddy ya wuce kujerun falon ya ajiye suitcasedinshi, yana rike da falmaran din suit din jikinshi. Gogaggen dan boko wanda ya ga jiya a Amurka yake kuma ganin yau, ga furfura nan tsilli-tsilli a kanshi, amma tsammani za ka yi Balarabe ne ba ba’abzine ba. Dogon hancin nan zur! Kamar na Babanta.
Kujera ya samu ya zauna a gajiye yana kallon Aalimah da ke tahowa, Basma da Khaleesa sun sako ta a tsakiya har gabansa, sun bi sun rirrike hannunta, bakinsu kamar zai tsage don farin ciki, kan kujerar suke kokarin zaunar da ita kusa da Daddyn, amma sai ta zame ta zauna a kasa daura da kafafunsa ta soma gaishe shi cikin harshen Hausa.
Cewa yake, “Tashi-tashi ‘yata ki zauna a kujera, kin sha hanya. Ki yi hakuri I couldn’t make it taking you from airport, I went to California for a meeting, dawowata kenan. Ina fatan kin ci abinci kin huta?â€
Murmushi ta yi, ta ce,
“Babu damuwa Daddy, kuma na ci abinciâ€.
Ya kalli Basma ya ce, “ Basma bani jakar canâ€.
Ta dauko jakar ta kawo masa babu ko russunawa kamar ta mikawa sa’anta, Aalimah ta ji wani iri a ranta. Budewa ya yi ya fiddo wasu takardu ya mika wa Basma, ya kuma mika wa Aalimahn wasu irinsu. Ya bawa kowaccensu biro ya ce ta sanya hannu karkashin dokokin jami’ar da za su je. Sai a lokacin ne Aalimah ta ga admission letter dinta da kwas din da Babanta ya zaba mata.
Zukar numfashi ta yi ta fesar, tana rokon Allah ya fidda ita kunyar iyayen ta, ta sha ji a bakin Yayanta Aboubacar how complicated pharmacy is (tsaurin kwas din harhada magunguna) lokacin da Daddy ya ce ya karanta shi don shine abinda Kakansa Prof. Kashim ya karanta ya kuma zauna akan (proffessorial chair) dinsa har mutuwar sa, ko don ya farantawa Mama, Aboubacar ya fitittike ya ce shi ba zai iya ba, Accounting yake so.
Nasiha sosai Daddyn ya yi musu a kan su tsare mutuncinsu, su maida hankali kan abin da ya kai su. Bai yarda da yin saurayi ko friendship da maza ba, duk kuma ranar da ya ga hakan zai cire kowaccensu ne ya yi mata aure. A karshe ya yi musu addu’a, ya gaya musu jibi za su fara registration.
3094856450
Sumayyah Kabara
Firstbank
Price 1&2 N400
6/28/21, 7:31 AM - Buhainat: 🌹 *Aalimah* 🌹
*
*SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI*
FREE PAGES 6
Ta jima a jikinsa tana ba shi hakuri, sannan ya ce ya hakura, amma in tana son zaman lafiya ta daina kawo masa wadannan sababbin halayen da ta billo da su, kuma ta zauna lafiya da Aalimah don zamanta daram a gidansa, tunda ba tare suka hada kudi suka sayi gidan ba. Duk ta ce ta yarda, sannan suka yi dan gajeren romancing dinsu suka fito, suka tadda yaran duk sun sha wanka sun shirya gwanin sha’awa. Daga Basma har Khaleesat kayan Aalimah ne a jikinsu. Sun dan matse su sabida duk sun fita garin jiki. Don ma dai manyan riguna ne dinkin Nijar. Ta hadiye wani abu da ya tokare ta a wuya, ta kama hannun Yesmin suka fita. Ta dauka motarsa zai nufa ya shiga ya tafi inda za shi, sai ta ga ya ce duk su shigo tashi motar.
Mummy kamar ta yi kuka don ya rushe duk wani plan da ta shirya. Ta shirya a ranta ba wani traditional wears da za ta saya musu, kuma ba za ta sai wa Aalimah wani abin kirki ba, kwancen su Basma za ta dawo ta tattara mata. Ta san ba shi da sanya ido, ba abin da zai fahimta. Amma yanzu ta san ya ruguza komai.
Chevrolet din Daddy suka shige dukkansu. Ya zauna a mazauninsa ya sanya belt, sannan ya tsaya yana dan duba abu a wayarsa,da alama adireshin inda zai je yake dubawa a yanar gizo. Sannan a tsanake ya dauki hanya. Aalimah sakin ido da baki da hanci ta yi sosai tana shan kallon birnin Boston, don tunda ta zo ban da makaranta, babu inda ta ke zuwa.
Su Khaleesa na ta hira a tsakaninsu ba ta sa musu baki ba, wani lokacin ma ba sosai ta ke fahimtar maganganunsu ba, sabida yanayin accent dinsu. Sun iya Hausa, amma ba sa janta da nisa, wato jefi-jefi suke yinta. Ta lura Mummy ba ta da walwala sosai tunda suka taho duk da Daddy na yi mata hira. Tafiya suke sosai kamar za su bar cikin gari, kafin Aalimah ta ga sun hau wani titi da aka rubuta Newbury street Boston. Sun yi tafiya sosai a cikinsa kafin su karkata ya yi parking a kofar wani katafaren shago a samansa an rubuta Riccardi. Tunda Mummy ta fahimci shagon African Germents ne na maza da mata ta sake gyara zamanta cikin motar tana duba Ipad dinta.
Daddy ya dan dube ta ya ga ba ta da alamar fita sai ya mika mata hannu ya ce,
“Give me the credit cardâ€.
Ba musu ta dauko a jakarta ta ba shi abinsa.
“Ba kya bukatar komai?†Ya sake tambaya cikin kwantar da murya.
Ba tare da ta dube shi ba, ta ce,
“A nan dai babu, su shiga su fitoâ€.
Ya kada kai ya bi bayan yaransa wadanda har sun shige shagon sun hau elavator. Abubuwa kadan suka tsitstsinta a Riccardi don kayan maza na Africa sun fi yawa. Basma ta ce, Daddy ya kai su wani shagon again. A cikin mota ya zauna ya kira waya ya yi magana da wani abokinsa dan Nigeria, mutumin ya hada shi da matarsa suka yi magana, sai ya ja motar. Wannan karon kan titin Harrison Ave Daddy ya shiga.
Tun daga nesa Aalimah ta hango dogon ginin da ya tabbatar mata wannan karon su Basma za su samu har ma fiye da irin kayan da suke so. Daddy ya yi parking a parking lot suka firfito, wannan karon ma banda Mummy, Aalimah, ta daga kai tana karanta sunan shagon, ‘ZAINAB SUMU PRIMITIVE MODERN’. A cikin shagon nan su Basma sun yi siyayyar kaya da jewelleries har da na banza. Da ta ga Aalimah ta ki daukan komai ita da kanta ta dinga daukar mata duk abin da ta daukar wa kanta. Sai dai tana bambanta colour. Ta fahimci Aalimah na son ‘dark colours’ sabida kalar fatarta don haka komai ta daukar wa Aalimah mai turuwa ne sosai, sai ta daukar wa kanta lighter one. Hatta Yesmin sun gwangwajeta da kayayyaki daidai jikinta, sun samu kaya iri-iri, na Nijar, na Najeriya, na Senegal, na Arab da na D’jbouti. Daddy shi yake nuna musu wasu ma ya ce su kara. Sai da Khaleesat ta ji tausayin creditcard dinsa, ta ce su barshi haka, amma shi ko a jikinsa. Ya basu suka zare kudin komai, za su fito kenan wani Bature ya biyo su da gudu ya ba su wani littafi yana tallata musu malldin The Germent District, ya tabbatar musu za su samu shagon beyond their expection, za su ji shi kamar suna cikin Africa in dai batun tufafi ne. Basma ta ce a je, Khaleesat ta ce, sai dai wani lokacin, Aalimah ta ce su tausaya wa Daddy su barshi haka. Hannu ya dora a kan kafadunta ya bubbuga.
“If you like atamfa, lets go Aalimah, kada ki ji tausayin wannan Daddyn he loves you more than his moneyâ€.
Dariya suka yi suka shiga mota suka tafi. Aalimah dai ta kafe a barshi haka sai wani lokacin. Ganin ta dage suka yarda.
Sai da suka yi nisa Mummy Zulaiha ta yi gyaran murya, su kam har sun manta Mamansu na cikin motar saboda rashin motsinta. Daddy ya dan dube ta ya maida idonsa kan titi. Duk kokarinsa na fahimtar matarsa ya kasa. Ta zame masa ‘alqibla-less’. Ta dan motsa dan kyakkyawan bakinta tana magana, “Mu shiga kasuwa daBURLINGTON MALL zan yi cefane da tawa siyayyarâ€.
Bai ce komai ba ya karkata kan motar ya nufi kasuwar da ta fada, su suka taya Mummy da tura sayayyar da ta ke yi a shopping bag, har ta gama cefanen kayan abinci kala-kala nau’i-nau’i suka sa a bayan mota. Daga nan sai suka wuce Burlington Mall din ta yi ta sayayyar kayan gayunta, su ma ba a barsu a baya ba duk wani abin amfani na mata na tsaftar jiki da kayan shafa da kamshi sun saya, Daddy na ta biya, sannan suka taho gida.
Kafin su iso gida Mummy ta saki rai sosai tana ta jan mijinta da hira, su ma yaran tana kula su har Aalimah. Shi dai kallonta yake yana mamakinta. Ta zame masa kamar wata mai ‘Multi personality disorder’ yanzu ta ke daidai anjima za ta koma wata majanuniya. He loves his wife as such! Wato yana son matarsa a duk yadda ta ke. Take-away suka yi na KFC kafin su shiga gida don already dare ya yi, kuma duk yunwa suke ji mai girkawar ma Mummy ta gaji tibis. Tun a lokacin ta soma regrettingkorar Easther da yanzu kafin su dawo sun tadda komai yana jiransu a kan dining. To wai ma da ta yi gaggawar korar Easther how sure is she (wane tabbaci ta ke da shi na cewa) Aalimah ta iya girkin da za su iya ci har mijinta? Damuwa karara ta bayyana a