Showing 102001 words to 105000 words out of 126031 words

Chapter 35 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt

zasu fara fuskantar sabuwar rayuwar da babu Aboulkhair a cikin ta. Ta samu hannayenta da rike kudin sadaqin kam-kam ba tare da sun yi shawara da ita ba. Wanda ke nufin; sun karbi auren Mu’azzam da hannu bibbiyu, ba tare da sun ba ta damar yanke hukunci tsakaninta da zuciyarta ba.




Ana tsaka da zub da kankara (snow) suka sauka a Las Vegas. Don haka ba karamin shiri suka yi wa ‘ya’yan Basma ba, suka kuma sanya su a bayansu ita da Gumsu suka goye da zani. Aalimah ko taya su hidimar yaran ta ki yi sai cin fushi ta ke. Daga lokacin tashinsu da lokacin saukarsu Daddy ya gaya wa Mu’azzam. Wanda har zuwa lokacin yake cikin halin rudu da kidimewa, ya yi kokarin ya fahimtar da Daddy ba zai iya wannan auren ba Daddy ya ki sauraronshi, ya ce,
“Auran nan Mu’azzam an riga an daura shi, ka yi hakuri kawai kamar yadda ta yi hakuri. Ka karbi kaddara kamar yadda ta karba. Ita ma ba ta so, amma ta nuna muna da ikon sanya ta ta yi, ta yi ko da babu son ranta. Haka nake so kai ma ka karba.
Ya kare zancensa da cewa “Mu’azzam ba ka san ta ya ya aka kulla auren nan ba, ba da son ran wasu a cikin gida ba. Burin su ka dawwama a haka babu aure saidai ka ga ‘ya’yan su na yi. A hakan da kake ka tsolewa wasu da dama ido suna kullin ka ba tare da sanin ka ba.
Ina so ka sani duk duniya bayan ni da mahaifiyarka sai Mansour a masu kaunarka. Ka fidda ni kunyar dan uwana mai kaunata da zuri’ata mai kuma kaunarka tsakani da Allah, ka rike Aalimah amana tsakaninka da Mahaliccin ka, in ka yi min haka ka gama min komai Mu’azzam, albarka ta gare ka ba za ta taba yankewa ba!â€.


Wadannan maganganu na Daddy sun firgita shi, sun sanyayar masa da jiki ba dan kadan ba.


Don haka Mu’azzam ya tattara damuwarsa ya hadiye. Babban jin dadinsa da ya kasance su Mummy suna cikin gidan. Ta samu abokan hira da taya ta zaman gidan. Don shi kam ba za a fara abin da ba za’a wanye lafiya tare da shi ba. Yana matukar jin dadin rayuwarsa a yadda yake yin ta, baya maraba da kowanne canji.
Ko Mummy bai gayawa su Basma na tafe ba, kamar yadda bai yi mata bayanin komai ba cikin abubuwan da suke tattaunawa da mahaifinsa. A ganinsa abin da aka dauka da muhimmanci shi ake tsayawa yi wa mutane bayaninsa, yadda suka ajiye ‘yarsu idan zaman ya ishe ta ya tabbata za ta yi musu waya su zo su dauke ta. Tunda shi an yi masa kandagarki da rabuwa da ita har abada.


Harrison ya tura ya dauko su a filin jirgi. Bai san da wanne ido zai kalli Aalimahn Aboulkhair wai a matsayin matar sa ba. Kasancewar Harrison ya san Aalimah bai sha wahalar gane su ba, ya shigar da kayansu booth yana ta yi wa Aalimah fara’a, shi a dole ya nuna ya santa, amma yadda ya ga fuskarta kamar hadarin da ya hadu ya nausa yayi gabas, dole ya hadiye sanayyarsa cikin cikinsa.
Mummy da Yesmin na barci a dakinsu da ke kasa suka ji tashin sautin su Basma. Da farko sun dauka cikin mafarki ne, amma da suka ji ‘ya’yan Basma na canyara kuka sun rasa inda za su sa kansu da wannan weather mai tsananin sanyi wadda ba su taba riskar kansu cikinta ba, dole suka yarda ba mafarki ba ne. Fitowa suka yi da azama sai kuma suka kwasa da gudu suka rungume juna.
Sun dade ba sa tare, sun dade ba su ga juna ba. Soyayyar Mummy da ‘ya’yanta ta motsa. Kwana suka yi a zaune. Duk da Mummy na sanyo Aalimah cikin hirarsu sai ta ga Aalimah din ta ki sakin jiki. Sai sunkuyar da kai ta ke ta kasa kallon fuskar Mummy. Sosai ta ke cikin rudu da damuwa, ita kuma haka za ta kare rayuwarta cikin auren ‘ya’yan mutum daya?
Gumsu ce ta fadi wa Mummy ko me kenan bayan sun sallaci asubahi. Mummy sai ta fashe da kuka wanda dukkaninsu ba su san ko na mene ne ba. Har sai lokacin da ta mike ta shige daki. Kukan damuwa ta ke dana farin ciki duka a lokaci daya, damuwarta shi ne ta san Mu’azzam ba shi da lafiya wannan ba karya ba ne. Ta san yadda aka wanye a aurensa na farko, tsoro ta ke ji kada a maimaita a kan Aalimah. Farin cikinta shine yau Allah ya cika mata burinta Mu’azzam yayi aure, ya zama cikakken mutum mai cikakkiyar rayuwa kamar kowanne dan adam. Babban farin cikinta kuma shine dawowar Aalimah cikin iyalinta. Don ta tabbata in ta kubuce musu sun yi asarar da ba zasu mayar ba.
Ta dade cikin tararradin sake yin aurenta tun bayan gama iddarta. Tana ganin kimar yarinyar domin a tsawon zamanta da Aboulkhair ba ta taba ganin wani hali na ashsha a tare da ita ba. Har gobe kuma tana jin kunyarta na mugun halin data nuna mata a baya, lokacin da Allah ya hada su zama tare a Boston.
Hakika tana son Mu’azzam ya yi aure amma ta wani fannin ba ta so Ishaq ya hada da Aalimah ba. Tunda ba su san me auren zai haifar ba. Ta so su ci gaba da zumuncinsu a haka, Aalimah ta samu miji mai lafiya kamarta ta aura, don tserar da zumunci da ganin mutuncin juna.
Ga shi sun ce an riga an yi auren, ba ta da wata kima gare su a yanzu balle har su yi shawara da ita kafin ayi. Za ta ci gaba da zama tare da Mu’azzam da Aalimah don ganin ba su kusanci juna ba, balle shakuwa ta shiga tsakaninsu. Har akai ga abinda zai bata komai. A ganin ta hakan kawai zata yi ta tserar da auren nasu.


Washegari tun karfe bakwai dai-dai Mu’azzam ya fito dining karyawa kamar yadda ya saba. Mummy kawai ya samu a dining din tana zaman jiransa, su suna can suna ta ramuwar barci wanda ba su samu sun yi ba a daren jiya. Ya yi shiri tsab cikin kayan sanyi bakake da jeans baki samfurin NEXT. Ya daure kafafunsa cikin bakin cambass. Cikin nutsuwa yake hada shayinsa wanda ya cikawa gahwah (coffe), amma kallo daya za ka yi masa ka fahimci cikin damuwa yake. Idan ya ce ba ya cikin damuwa kan auren nan da Daddy ya yi masa hakika ya yi karya. Ko ba komai wani nauyi ne aka dora masa wanda bai saba da shi ba.
Mummy ta yi gyaran murya ya dan daga manyan idanunsa farare kal! Ya dube ta, har wani sheki suke fitarwa na musamman da ba kowa yake lura da hakan ba sai wanda ya hada idanu da shi. Mu’azzam yana da kyau mai kayatar da idanu, mai sanyaya zuciya. Idan ka kalle shi za ka so ka maimaita ko don kyawun kwayan idanunsa. Sai dai kasaitar sa da jan ajinsa za su hana ka abokantake shi da sauri, idan ka samu ku ka gaisa ma ka gode. Bambancin sa da Aboulkhair kenan.
Wanda ya kasance mai faram-faram da son jama’a da yin haba-haba da su, balle makusantan sa. Matar sa tayi rantsuwa ta maya kan cewa babu mutum mai kirkinsa da saukin kansa a duniya.
Mummy har sau biyu tana gyara murya, amma ta rasa abin cewa, shi kuma hada shayinsa yake yi bayan gaisuwa bai ce mata komai ba. Ko yaya su Basma suka kwana bai tambaya ba, ta yi ta maza ganin cewa zai gama shan shayin ya tashi ne ya barta a wurin ba tare da sun tattauna akan zuwan bakin nasu ba, ta dube shi tace,
“Kana sane da zuwan su Basma?â€
A gajarce ya amsa “Eh’.
Duk suka yi shiru, yayin da shikuma yake sipping shayin a hankali.
Mummy ta sake cewa,
“Ashe aure Daddyn ku ya yi maka ni ba ni da labari?â€
Shiru Mu’azzam ya yi, kamar ba da shi ta ke magana ba. Ta ci gaba da cewa, “Shi kenan kuma don an sake ni ba ni da martabar da za a nemi shawarata kan al’amuranku? A kalla a ba ni hakkina na haihuwa ko?â€
Mu’azzam ya soma zama bored da maganganun Mummy, don bai ga wanda ya shafe shi a ciki ba. Tsakaninta da tsohon mijinta, shi me ye nasa a ciki saboda Allah? Karewa ma shi kansa ba a yi shawara da shi ba. Mikewa ya yi tare da aje kofin hannunsa ya yi baya da kujerarsa ya hau duba agogon swatch da ke daure a damtsen hannunsa.
“Mummy zan wuce office kuna bukatar wani abu?â€
Ta san in ta ce ta ji haushi ta wahalar da kanta a banza. Kewar Aboulkhairi ta zo ta lullube ta. Kawai sai ta soma hawaye, ta rufe fuska da tafukanta. Ta kifa kai akan teburin cin abincin ta na wani irin kuka mai ban tausayi.
Da yanzu yana nan yana lallashinta, da yanzu yana taya ta neman mafita ga damuwarta, da yanzu yana nan cikin damuwa da damuwarta… Da yanzu ya bata dukkan lokacinsa ya saurareta…. Sun tattauna lamarin yadda ya dace sun nemo mafita. Mu’azzam ya koma kujerar sa ya zauna ganin Mummy na wannan kuka. Wanda bai San musabbabinsa ba. Hankalinsa ya kai kololuwar tashi. Don shi har ga Allah bai ga cewa yayi wani abu wanda ba daidai ba. Ya kai hannunsa cikin sumar kansa yana cakudawa a hankali, ya ce,
“Mummy ki daina ganin laifina, ni ma ban san da zancen auren ba sai bayan da suka daura shi, Mummy I don’t want to talk too much…a kai, ba ni da masaniya a kan ala’amarin nan, me ki ke so in ce miki?â€
Mummy ta cire hannu daga fuskarta, yana ganin yadda hawaye ya wanke mata fuska. Hankalinsa ya kara dugunzuma ya tashi.
“Ba abin da nake so ka ce min, illa ka damu da damuwata Mu’azzam. Sau da yawa ina hadiye abubuwa sabida lafiyar ka, amma na lura bayan rashin lafiya cikin dabi’unka har da ‘hali’. Halinka ne Mu’azzam rashin damuwa da al’amarin kowa…!â€.
Zai yi magana ta katse shi, “Ni na san na yi rashin da ba zan mayar ba! Aboulkhairi, ban san muhimmancin ka ba sai da na rasa ka! Yadda ka damu da ni ni ban damu da kai haka ba! Ka taba cewa don Allah in so ka yadda nake son Mu’azzam. Yau ga ni ina kuka a dalilin rashin ka, Mu’azzam din da na kwallafawa rai ga shi a gabana, amma ban da bakin ciki ba abin da yake cusa mini.
Na hakura da aurena na shekaru sama da talatin saboda shi, amma ba ni da alfarmar tattauna matsala ta da shi…â€. Sai kuka ya kara kwace mata.
Ba abu kankani ke sa Mu’azzam kuka ba, amma dole yau Mummy ta sanya shi kuka. Ya ji yana mai kaico da yanayin halayensa lokaci na farko a rayuwar sa.
Abin da ba ta sani ba, rashin Aboulkhair ya kara taimakawa wajen cire masa walwala da yawan magana. Tun da ya fito daga asibiti walwala ta kara karanci agareshi. Da yana nan ko ba ya son yin magana in dai ya zo inda yake dole ya yi ta, ko ba ya son yin dariya sai ya yi. Zai so Mummy ta ci gaba da yi masa uzurin da ta ke yi masa kada ta gaza…. Zai so Mummy ta daina kwatanta shi da Aboulkhair ta kowacce fuska, domin Ubangiji da ya halicce mu sai Ya halicce mu da halaye mabanbanta, da kamanni daban-daban da personality iri-iri. Shi haka Ubangiji ya halicce shi.
7/6/21, 4:51 PM - Buhainat: 💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖💖






A wannan lokacin ba shi da abin yi ban da ya koma ya zauna, ya bata lokaci wajen lallashi da bata hakuri kawai, ba tare da ya yi mata bayanin cewa; shi ma in zai samu mai lallashinsa so yake yi. Ya fi ta damuwa a wannan lokacin, kuma ya fi-ta kewar Aboulkhair.
Koda ya je office yau a makare ya je, saida ya bada hakuri sosai. Yana shiga bayan yayi loosing tie din shi ya zauna a kujerarsa wayarsa ya fiddo ya sake tura wa Mummy text na ban hakuri sannan ya fuskanci ayyukan dake gabansa.


Bayan fitarsa Mummy ta dade zaune a wurin, har zuwa lokacin da text din Mu’az ya shigo mata, murmushi ya subuce a fatar bakinta sabida irin tausasan kalaman da yayi amfani da su duk da cewa ba masu tsayi bane, sai kuma tausayin sa ya lullube ta. Ta sani kwarai shima baya jin dadin yadda rayuwar shi ke tafiya, da gaske yana bukatar mace a gefen shi ba tare da ya san cewa rashin macen ne ya maida rayuwarshi incomplete ba. Ta samu kanta da yi musu addua Allah ya hada kansu shi da Aalimah tare da godewa Mansour cikin zuciyarta, don tana da kyakkyawan zaton wannan kokarin nashi ne ba na wani ba.
Ta share hawayenta ta koma daki. Basma ce kawai ido biyu tana shayar da ‘ya’yanta. Nan ta karbi mai sunanta daga hannunta ta zauna suka soma hira, hirar da ta tada Gumsu da Aalimah daga baccin gajiyar da suke yi. Aalimah ta mike ta nufi toilet don yin wanka. Mummy ta bi ta da kallo tana tausaya mata cikin ranta. Gaba daya ta rame, tayi zuru-zuru ta fita hayyacinta. Babu wata alama ta amarci a tare da ita. Kafarta ko lalle babu.


Kwanaki uku da Aalimah ta yi cikin gidan ba ta hadu da Mu’azzam ba ko sau daya. Yana riga kowa ficewa, kuma sanda zai dawo sun gudu daki sabida sanyi. Ba sa iya zaman falon duk da room-heater da ke aiki. Yana shigowa kuma da sassarfa yake hayewa upstairs din shi kada ma su samu damar ganin sa. Mummy da Gumsu ke musu girki, Aalimah ba ta umh ba ta umh-umh sai in sun sako ta cikin hirarrakinsu ta yi murmushi.
Idan a da tana kallon al’amarin matsayin almara ko mafarki, yanzu ta tabbatar reality ne. Cikin gidan Yayan su Mu’az ta ke, kuma wai a matsayin matarsa ta sunnah. Yayan nan nasu ita da Aboulkhair data ke matukar girmamawa da hidimar dafowa abinci da hadowa magunguna. Irin rayuwar da ta yi da Aboulkhair ake nufin ta maimaita da Mu’azzam! To ta ina? Ta ya ya? Da wacce fuska? Ta wace hanya? How could that be possible? Ko da a ce Mu’azzam zai ba da fuska (wanda ta tabbatar hakan impossible ne) ita wacce irin butulu ce ga Aboulkhair da za ta aikata hakan gare shi? Me yayi mata a rayuwa banda alkhairi da zata saka masa da auren Yayansa mafi soyuwa a gare shi?
Anya iyayensu na aiki da hankali da tunani a lokacin da suka yanke wannan shawarar suka kuma zartar da wannan hukuncin?
Irin tunaninnikan da Aalimah ke yawan yi kenan a duk lokacin da ta kadaice kanta cikin daki ko a toilet, don in tana tsakiyarsu ba sa bari ta yi tunanin komai, yanzun nan Basma za ta janye mata hankali da hira, duk dai don kada ta barta ta yi tunanin wanda ita ta san ya zame mata dole ta yi shi.
Satin su Gumsu biyu a LasVegas Daddy ya fahimci basu da niyyar komawa gida, sun je sun shantake abinsu Mu’azzam na jika su da jin dadi, kudi wannan atm guda ya basu suna sayen duk abinda ransu ke so, ita Gumsu sayayyar haihuwa take ta yi, Basma ‘ya’yanta da mijinta take yiwa sayayya da kannen mijinta ‘yan mata su Suhaima. A ranar da suka cika sati biyu Daddy ya kira ta yana ta fada kan su dawo haka, sati daya ya ce su yi amma sun je sun canza booking sun yi zamansu. Gumsu ta ce.


“Mummy ce ta ce mu kara sati don Aalimah ta sake sosaiâ€.


Cikin mamaki Daddy ya ce, “What? Da ma har yanzu tana gidan Mu’azzam? Na dauka tuntuni ta koma Kano? Ashe Zulaiha ba za ta taba yin hankali ba?â€
Ita dai Gumsu ta yi shiru, ta kuma shiga dana sanin ambatar Mummy da ta yi, ba ta san cewa bai sani ba, da ba za’a ji a bakinta ba. Ko da ta ke da surutu na barkwanci ta ke yi amma ban da na tsegumi da munafurci. Daddy ko sallama bai yi mata ba ya kashe wayarsa.
Sun yi booking za su tashi a washegarin lahadi, don haka suka zauna a falo suka ki yin barci suka kuma ki shiga daki suna jiran Mu’azzam ya dawo, don su yi sallama da shi. Mu’azzam, wanda gidansa ya zame masa kurkuku a yanzu, ba shi ya shigo ba sai karfe goma na dare.
Hannayensa biyu cikin aljihun bakar kwat din jikinsa, kafarsa daure cikin fararen cambass samfurin (NIKE), da dan gudu-gudunsa ya shigo zai haye upstairs din sa kamar yadda ya saba. Bai yi tsammanin ganin ko mutum daya a falon ba kamar yadda suka saba, amma sai ya gansu dukkanin su suna zaune zaman jiran shigowar sa ban da Aalimah kadai. Ga dukkan alamu kuma zaman ba na komai bane dakonsa suke. Dole ya dawo ya zauna a kujerar da ke fuskantar Mummy yana tambaya ko lafiya ba su kwanta ba? Basma ta ce,
“jiran ka muke yi mu yi sallama, gobe za mu koma gida insha Allahuâ€.
Kada kai ya yi irin na ‘to ni me ye nawa a ciki?’ Kafin ya dawo ya samu kujera kusa da Basma ya zauna, ya sanya hannu cikin aljihun kwat dinsa ya fiddo kudi ko kirgawa bai yi ba ya bai wa Basman, ta sa hannu ta karba tayi godiya, ya dauko wasu ya bai wa Gumsu. Gumsu ta harare shi shida kudin nasa, ta ce,
“Ni ba kudi nake so ba, kawai Malam ka kular min da ‘ya ta. Na ba ka amanar ta, ka tausaya mata, ba ta da kowa a garin nan sai kai. Ba zaman Mummy ta ke yi ba, zamanka ta ke yi, don haka ba zan tafi ba sai an ba ta dakin ta da Daddy ya ce a ba ta, ba dakin Mummy ya ce min ta zauna baâ€.
Mummy ta harare ta ta gefen ido,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login