Showing 30001 words to 33000 words out of 126031 words

Chapter 11 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt

yi kafin ya kwanta, kama daga wanka, brush, shan black tea, ya daura pajamas sannan ya shige cikin quiltdinsa da wayar Aalimah a hannunsa. ‘Yar kankanuwar waya Daddy ya saya mata kirar Iphone. Contact list shi ne abin da ya fara shiga, contacts din ba su da yawa, ba su fi ashirin ba. Ya ci gaba da scrolling contactsdin, akwai mamere, watau Mamanta kenan, mon pere (Babanta), sai Bhaiyya, wato Yayanta Aboubacar da harshen India. Sai ta Daddy, ta Basma, ta Khaleesat, Malam Raazii, Kawu Oussama, Kawu Edrissa, Balkissa Eedrissa, Grandma Kasisi, Grandma Bintou. Sai lambobin maza guda biyar wadanda ya ga ba zai jurewa zamansu ba.
Alex ya fara gogewa, ya goge Harrison, ya goge Mr. Edward Proffessor. Bai san cewa course tutor dinsu ne ba ma. Harrison kuma course mate dinta ne. Lambar da ta rage guda daya ce ta tsaya masa a makoshi, kuma ya kasa goge ta. Akwai bukatar ya dauke ta a tasa wayar, sannan ya goge. ‘MAHMOUD’. Ba don komai ba sai don ya kawo karshen alakarsu ko ma wane ne. Har wani heart ta makala masa bayan ta rubuta sunansa. Bai yi mamaki ba, don yarinya kamar Aalimah ba yadda za a yi a ce ba ta da mashinshini har zuwa wannan lokacin. But he’s jealous, in ya ce jealous to guda daya kenan. He is very-very jealous! Don ya lura ko ma wane ne wannan Mahmoud din ba yau ya fara son Aalimah ba, kuma bai fara don watarana ya daina ba.
Zuciyarsa ba ta gama tsinkewa ba sai da ya shiga message inbox. Sakonnin Mahmoud din ne rututu masu barazanar tarwatsa kwanyarsa. Bai iya ci gaba da karantawa ba ya hada su duka ya goge su daga doron kasa. Abu daya ya dan kwantar da hankalinsa, ba reply mai zafi daga Aalimah, ga dukkan alamu ba ta damu da yin rubutu cikin waya ba, babu wani social media da ta bude, she only text Mahmoud twice, saying that she saw his messages, she’s doing morethan fine. She will call him when she is opportune, he know how tedious her studies is. (Sau biyu ta yi ma Mahmoud sako, inda tace ta ga sakonsa, tana nan lafiya, zata kira shi in ta samu dama, ya san yadda karatunta yake da tsauri). Wannan ne kadai ya dan sanyaya ransa. Amma ya rantse gobe sai ya raba Aalimah da Mahmoud yadda zuciyarsa za ta buga ya mutu ya huta.
Ya dauki lambar Daddynta, mamanta da ta Yaya Aboubacar. Lambobinsa ya zuba cikin wayar tata, ya yi saving da Mon Amour (MY LOVE da harshen faransa), sannan ya yi mata downloading din whatsapp application. Da niyyar cewa shi kadai zai dinga mata magana ta cikinsa, not even Daddy karshenta kenan. Sannan ya koma cikin gallery na wayar, duka yawanci selfie ne ita da Basma a makaranta, wani a mota, he can guess that she adores Basma a lot (tasu ta fi zuwa daya).
Murmushi ya yi da ya tuna Khaleesat ko Daddy bai cika shiri da ita ba sabida I don’t care attitude dinta. Tafi shiri da Mummy. Ya dade yana kallon kyakkyawar fuskar da ta zame masa madubin zuciya daga jiya zuwa yau. Ta rusa duk wasu plans da ya yi wa rayuwarsa, ta kuma zamo babban kalubalensa na rayuwa a yanzu. Mallakarta is the greatest challenge of his life now. Ban da barci ya fi kowa iya sata da Aboulkhair yau ma bai runtsa ba kamar yadda ya ga dare da rana jiya.
Amma yau ya yi barci yadda ya kamata da wata irin nutsuwa da ya dade bai samu ba a rayuwarsa.
Washegari, Aboulkhair ya yi wanka ya shirya cikin shirt da wando ‘yan gidan Nordstrom, rigar orange ce da ratsin baki, wandon fari tas. Sumar nan ta sha taza ta kwanta luf a kansa. Samun kansa ya yi da zakulo turaren da ya fi kowanne kamshi mai sanyi cikin tarin turarukansa masu ban sha’awa, sannan ya fesa. Ya fi son shi fiye da dukkan turarukansa, saboda Mu’az ke ba shi (SAUVAGE Dior). Duk wani abu kuma da ya fito hannun Mu’azzam is preciousa gun Aboulkhair. Ya san dai ba yau ya fara fesa turare ba, amma shi kansa ya san wanda ya fesa yau bai fesa shi don radin kansa ba.Is meant for AALIMAH ta ji yana kamshi.
Wani murmushi yake saki shi kadai yana yi wa kansa dariya. Sanda ya fito su ma duk sun yi shirin makaranta suna dining suna karyawa har Daddy, sai Aalimah da ke ta shige da fice daga kitchen zuwa dinning area din tana miqo musu abubuwan da suke bukata.
Sosai ya ji haushi, amma bai ce komai ba har ya zauna. Shi ma ita ta yi serving dinshi ba tare da ta yarda sun hada ido ba.
Ya dubi Basma, “Ina mai aikin Mummy?â€
“Aal, ta hana ta zuwa by 6am ta ce ita za ta dinga yin breakfast, Easther ta yi lunch and dinnerâ€.
Ya dubi Daddy ko zai ce wani abu? Ya ga bai ce komai ba, sai shi ma ya yi shiru. After all ita mace ce kuma rainon Nigeria, she might be willing to do so. Shi kansa ya fi son cin nata abincin a kan na Easther, tunda ya ci pounded yam sau daya. Amma anya hakan ba zai zamo takura a gare ta ba?
Muryar Daddy ya ji yana yi wa su Basma fada kan su dinga shiga kitchen din da safe tare da ita za su fi sauri, kuma su ma su koya. Ajiyar zuciya ya yi cikin jin dadi.
Fara cin abincin ya yi, su kuma suka koma sama don dauko jakunkunansu da mayafansu. Khaleesat da Yesmin da ma uniform ne a jikinsu. Daddy ya riga su ficewa, su ma mota suka wuce don su jira shi, bai dade ba ya gama ya fito. Kofar direba ya shiga ya rufe, sannan ya mika hannu ya bude kujerar gefensa. Basma za ta shiga, ya ce, “No, koma baya, daga yau seat dinta neâ€.
Ta ce, “Who?â€
Harara ya galla mata ba shiri ta shige bayan don ta lura daga zuwansa zuwa yau he’s a changed person. Aalimah ba da son ranta ba ta zauna a gaban, ba ta so ko kadan su Basma su fahimci tsakaninta da Yayansu akwai wani abu, kunya ta ke ji sosai balle ta san Basma da digimi da maida allura garma. Sai da suka hau titi sosai ya dan juyo ya dube ta. Ta yi masa kyau sosai cikin doguwar riga ruwan kasa da veil dinta sakar kasar Kuwait. Takardun hannunta ta ke dubawa tana da gwaji yau (test). A duk lokacin da ya dube ta his feelings for her heightened bai san dalili ba. Cikin tattausar murya ya ce, “Babu gaisuwa Aalimah?â€
Ko su Basma da ke baya ba su ji abin da ya ce ba, sabida raunin muryarsa. Ba tare da ta dago ba ta ce,
“Bonjour?â€
Ya amsa, sannan ya ce, “What time is your interval (lokaci na hutu tsakanin wata lakcar da wata). Ta gaya masa.
Daidai lokacin da suka shigo Boston campus ya ajiye su ya juya. Ko da ya koma gida kasa hassala komai ya yi, sai tunanin Aalimah. Tashi zaune ya yi daga kan resting chair ta falon da yake kwance a kai, ya hau saman gidansu. Akwai wani balcony da galiban daddy ke zama da yamma ya yi karatun jarida a weekends can ya je ya zauna. Wayarsa ya lalubo ya nemo lambobin da ya yi saving jiya daga wayar Aalimah ya kira ‘UNCLE MONSOUR’. Gara ya fara yi wa kansa yakin neman auren Aalimah kafin Daddy ya gama yangarsa ya fara nasa.


Dr. Monsour Raazee, na zaune cikin ofishinsa da ke cikin sabuwar jami’ar Bayero yana marking takardun dalibai ya ga shigowar kiran mai dauke da lambobin kasar Amurka cikin wayarsa. Amma kuma ba Aalimah ba ce ba, kuma ba yayansa Ishaq ba, sannan it is not his darling son MU’AZZAM ISHAQ RAAZII, wanda sati ba ya shigowa ya shude ba tare da ya kira shi ya gaishe shi ba, musamman a ranakun karshen mako. To ko Aalimah ce ta canza layi? Haka ya mika hannu ya sanya ta a handsfree yana ci gaba da marking din da yake yi saboda tsabar kwarewa da aikinsa.
“Assalamu alaikum Uncleâ€. Ya jiyo muryar saurayin mai wani irin accent shi ba bature ba, shi ba balarabe ba, ba ma kuma za ka sanya accent dinsa a jerin na Hausawa ba duk da uwarsa cikakkiyar bakanuwa ce.
“Ameenwa’alaikumus-salam warahmatullah, da wa nake magana?â€
Kunya da jin nauyi da nadama baki daya sukayi rubdugu a kan Aboulkhair, a girmansa ba zai iya tuna rana ta karshe da ya kira wani cikin dangin mahaifinsa ya gaishe shi ba, tun suna yara Mummy ke gaya musu they don’t love them, they are always saying ‘baku da tarbiyyah’ don kawai ba sa sona!’
Ya runtse idonsa yana jin wata irin nadama tana ratsa shi. A shekarun girmansa kuma he is very busy with schools musamman da ya fara karatun jami’a ya bar iyayensa ma bakidaya ya tare a jami’a, sannan ga yanayin karatunsa, he hardly find time for himself ma balle ya tuna mutanen da suka shafe shi. Ko askin kansa ba ya samun damar yi sai gashin na neman rufe masa ido. Ko kadan bai dauko Mummy ba, sai idanunta da duhun fatarta, he is a perfect photocopy of his father. Mu’azzam ne mai kama da ita, sai dai shi kuma ya yi hasken fatar Daddy, bai yo yawan sumar kai ba, sannan he shaves regularly (yana yawan yin aski).
Ya yi nisa a tunani, wanda ya mantar da shi cewa ya kira waya har kawun ya amsa. Muryar Kawun nasa ya ji yana tambaya cikin sanyin murya,
“Ko ABOULKHAIR ne?â€
Ya cije labbansa cikin mamaki mai cakude da jin kunya da jin dadi duk a lokaci daya, ya ce,
“Ni ne Uncleâ€.
“I guessedâ€. Inji Dr. Mansour, “Ya ya ku ke, ya Babanka da ‘yan uwanka da mahaifiyarku?â€
“Suna lafiya Uncle, I’m sorry for not calling you. Nayi nadama uncle.Uncle na ji kunyarka, amma ka yarda da niban taba mantawa da ku ba. Bana tare da iyaye na, ina karatu a Louisiana shekaru hudu kenan. Yanzu ma hutu na zo, kuma nanda sati hudu zan koma.I need your blessing!â€.
Hausa yake iyakar iyawarsa tana subuce masa yana cakudo ta da turanci.
Dr. Monsour ya yi murmushi kamar yaron na kallonsa. Hamdala yake yi cikin zuciyarsa, addu’ar mahaifinsu da kalaman mahaifiyarsu ba su fadi a banza ba. Inna Kasisi ta sha cewa kowa ya daina damuwa da rayuwar Ishaq da ‘ya’yansa, idan ‘ya’yan na halal ne da kansu za su neme su. Malam kuwa ya sha cewa, “Da izinin Allah kan ‘ya’yansa da jikokinsa ba zai rabu ba ko bayan ransa. Ishaq da ‘ya’yansa da suka zama saniyar ware, yana rokon Allah ya karkato da hankalinsu gida, su rungumi ‘yan uwansu da iyayensu.
Kiran sunan yaron ya yi wanda ya fada cikin damuwa da shirun Kawun nasa.
Ya ce, “Aboulkhair, Aboulkhair! Kana jina?â€
“Eh Uncle, I’m still onlineâ€.
Ya ce, “Ka daina damuwa, I’m your father, an halicci iyaye da dabi’ar zama masu karbar uzurin ‘ya’yansu. Na ji uzurinka, kuma in gaya maka ban taba damuwa da hakan ba, tunda na san lafiya ku ke. Amma ka dinga koyi da dan uwanka wajen kula da zumunci. Ya fi ka yawan hidimomi tunda shi babban ma’aikaci ne, still ya rike danginsa kam-kam. He is not with us, but we are feeling him beside us. (Baya tareda mu, amma jinsa muke kamar a gefen mu). Sallar bara da ta wuce tare da shi muka yi sallar idi a Nijar, ya je Zinder (garin su Inna Kasisi), ya je Tessaoua (garin su Malam Ibrahim Razee), har Arlit (garin su Inna Bintou) ba inda bai je ya ga dangi su ma sun ganshi ba. Ga albarkar kakanninsa da iyayensa yana sha ta ko’ina, ba ka yi wa kanka kwadayin hakan?â€
Ya ci gaba da kawo masa ayoyi da hadisai da Allah ya yi umarni da zumunci, da kyautata shi, musamman ga maza kuma manyan jikoki a family. A karshe ya saka masa albarka, shi kuma ya yi alkawarin zai ci gaba da kiran kowa. Ya ce yana son kiran Maman Aalimah da yaya Aboubacar, amma bai sani ba ko sun manta shi?
Dr. Mansur ya ce, “You are welcome to call everybody within your family, babu wanda ya manta da ku ko don Mu’azzam. Allah ya yi muku albarka bakidayaâ€.
Bayan sun gama waya da Daddyn Aalimah ya dade a wurin, ya jingina da karfen balcony din zuciyarsa ta yi masa dadi. Sai kuma ya fada wani tunanin. Wato duk yadda yake da tabbacin ya fi kowa sanin Yayansa Mu’az har gobe bai zo rabi a sanin nasa ba! Abubuwan mamakinsa yawa gare su, kuma ba wanda ya isa ya san cikinsa hatta da iyayensu idan aka zo maganar abin alkhairin da yake yi a rayuwa. Sai dai ya tsinta nan da can kuma bai isa ya yi masa zancen ba, yanzu zai ce bai san maganar ba, ko ya ce ya kyale shi da unnecessary magana, ba ya son yin magana mai tsawo.
Ajiye tunanin Mu’azzam ya yi a gefe, don abubuwan mamakinsa ba masu karewa ba ne. He is just far beyond everyone’s assumption (ya wuce da sanin kowa). He is a patient, amma abubuwan da yake yi da yadda yake gudanar da rayuwarsa masu lafiya dari bisa dari ba za su iya ba.
Maman Aalimah Hajiya Aseeyaita ce mutum ta biyu da ya kira. Ita kam ba ta gane shi ba, sai da ya kara da bayanin kansa sannan ta gane. Sosai ta shiga janshi da hira, tana tambayar kannensa da mamanshi. Abin da ya ba shi mamaki, ba ta tambayi Aalimah ba, sai su Basma. Abin ya burge shi kwarai da gaske. Kawaici wani abu ne mai kyau cikin al’adun malam bahaushe, wanda Mamansa ba ta sanshi ba. A gaban kowa, kiri-kiri ta ke nuna son ‘ya’yanta da nuna babu ya su a duniya. Su ne kadai ‘ya’ya. Sannan ya kira Yaya Aboubacar.
Aboubacar sa’an Aboulkhair ne, bai fi watanni biyu Aboulkhair ya ba shi ba. Don haka hira sosai suka yi, irin ta ‘yan uwa. Ya ce ya gaida Aalimah duk da ba a fi kwana biyu ba sun yi magana shi da ita.
Yau dai Aboulkhair ya yi wa kamfanin wayarsa na VERIZON ciniki mai dumbin yawa, don bayan gama wayarshi da ‘yan gidan su Aalimah ‘yan Nijar ya hau kira, duk wasu manya a dangin ba wanda bai kira ya wanke kansa ba.
Inna Kasisi na yi masa tirjiya da hutsancinta, haka ya yi ta lallashinta har ta ware suka yi hira. Ya yi mata alkawarin he will keep calling kuma zai zo Nijar next hutunsa. Albarka kuma ya sha ta wajen malam da manyan Uncles dinsa. Ba su da riko ko kadan sai kaunar junansu. Ya kuma yi mamakin matsayin da Mu’azzam ke da shi a family dinsu. Ya raina kansa, don ba wanda zai yi magana da shi har ya kare bai tambayi Mu’az ba, bai fada mishi alherin da yake masa ba. A karshe da ya gama wayar Mu’azzam din ya kira. Yana dagawa cikin sauri ya ce da shi,
“At office, call laterâ€.
Murmushi ya yi yana jin kaunar Yayan nasa na kara ratsa shi.
A fili ya ce,
“Ni ma ba wani abu zan ce maka ba. I just want to hear your voice, (kawai ina son jin muryar ka ne) kuma na jiâ€.
6/28/21, 7:32 AM - Buhainat: 185




Zuwa lokacin azahar ta yi, dakinsa ya koma ya yi sallah, ba ya bukatar abinci don haka ya je ya yi sabgoginsa a cikin gari zuwa lokacin da Aalimah ta gaya masa tana da sarari. Yana yin parking kuwa ya gansu suna fitowa, daga dakin laccar tana rungume da folder.
Tsura mata ido ya yi tana nufo motarshi. A zuciyarsa tambayar kansa yake yi, me ya fi so a Aalimah? A gaggauce amsar ta halarto zuciyarsa… Yana son komai nata… komai ta yi abin burgewa ne a idonsa. He loves her dearly.
Har ta shigo ta zauna a gefensa bai sani ba. Sai da ta hada yatsunta biyu suka yi kas! A kunnensa. Kallonta ya yi, sannan ya dauko wayarta daga inda ya ajiye ta ya lalubo lamba ya danna kira. Ba ta ankara ba ta ji muryar Mahmoud na amsawa da sallamarsa, yana tambayar ina ta shiga kwana biyu? Kafin ta kwace wayar ya bada amsa,
“Ba ita ba ce, mijinta ne, kuma Yayanta, wanda ya bada sadakinta ga iyayenta. This is for your information not to call or text my wife againâ€. Ya datse kiran.
Aalimah ta ji ba dadi har fuskarta ta nuna.Mahmoud yana da mutunci a idonta ko don Yaya Aboubacar. Ko rabuwa za ta yi da shi ba za ta so su yi irin wannan rabuwar ba.
Kallonta yake kai tsaye cikin idanunta don ganin reaction dinta, amma ya kasa fahimtar komai ban da rashin jin dadin da idanunta suka nuna. Magana ta yi a hankali cikin rarrashi don fahimtar cewa so yake su yi rigima.
“Haba Yayan Basma? Abokin Yaya Aboubacar ne kuma…..†Ta yi shiru ta kasa ci gaba.
“…... Kuma saurayin kiâ€, yayi maza ya karasa mata. “Kawai ki fashe da kuka na raba ki da saurayinki…â€.
Turo baki ta yi cikin shagwaba, “…Ni ba saurayina ba ne, cewa zan yi muna mutunci ni da shi fa… Ni ba ni da saurayi…â€.
Ganin yadda yake kallon bakin nata admiringly ya sanya ta maida bakin nata ta kintse, ta kuma sunkuyar da kanta. Murmushi ta shiga saki kasa-kasa a sanda ya sanyaya murya ya ce da ita,
“Har NI?â€
Tafukanta ta kai ta rufe fuskarta tana murmushi,
“Kai ma Yayana neâ€.
“Ko?†Ya tambaye ta.
Bai jira amsarta ba ya ci gaba, “Za mu bambance hakan ranar da aka daura mana aureâ€.
Ta kara tusa fuskar tata cikin tafukan nata, cikin matsananciyar jin kunya.
Wayarta ya jefa mata kan cinyarta ya tada motar, “Na bude miki Whatsapp, Daddy ya amince min in dinga magana da ke ta waya, daga yau har zuwa ranar da zai karbi sadakinki. Idan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login