Showing 3001 words to 6000 words out of 126031 words

Chapter 2 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt

da Ishaq Ba’abzine (kamar yadda suke kiransa). Abin nan da Turawa ke kira ‘love at first sight shi ya afku tsakanin Ishaq da Zulaiha.
Zulaiha baka ce (black beauty), yarinya danya sharaf ‘yar saandire. Iyayenta ba ‘yan boko ba ne, ‘yan kasuwa ne. Har Kano Ishaq ke zuwa daga Zaria wajen Zulaiha. Wata irin zazzafar soyayya ce ta shiga tsakaninsu, wadda ta sa iyayenta gwammacewa su cire ta daga makaranta su yi mata auren, don kuwa ta yi watsi da karatun ta kama Ishaq. Sai aka yi sa’a shi ma nashi iyayen ba masu tsattsauran ra’ayi ba ne a kan karatun, suka yi musu aure.


Hankalin iyayeyn Zulaiha bai tashi tashi ba sai da iyayen Ishaq suka ce Nijar za su tafi da ita can main house din su. Sun dauka tunda yana Nigeria bbai gama karatun ba haya zai kama su zauna. Daga karshe ba su da yadda za su yi, sun aminceAURE ba inda ba ya kai ‘ya mace, suka amince Ishaq ya tafi da matarsa kasarsa ta haihuwa, ya baro ta tare da iyayensa ya dawo makaranta ya ci gaba da karatunsa cikin kwanciyar hankali, tunda ya mallaki abin da zuciyarsa ke so.
A irin zaman amincin da ake yi tsakanin Inna Kasisi da Inna Bintou, ‘ya’yan wannan sune na waccan, sai ya zama cewa, Zulaiha surukar Bintou ce ba surukar Kasisi ba. Ita ke kula da al’amarinta tunda mijinta ba ya nan. Malam Razee bai ragi Zulaiha da komai ba ta fannin bukatunta tamkar mijinta na kusa da ita, makarantar da ta ke yi ma ta kudi ce, wadda shi ya sanya ta a can Yamai, har ta gama sakandire.
Sai dai sam Inna Bintou ba ta jin dadin surukuta da Zulaiha, sabida baudaddun halayenta;Yarinya ce mara godiyar Allah da fadin rai. Duk abin da suke mata a raine ta ke kallonsa ba ta godewa, ba ta jan jikokinsu a jiki, ba yaron da ya isa ya shigar mata daki. Ba ta taimaka musu da komai na hidimomin gida, ga ta da girman kai da raini ga kowa. Inna Kasisi kawai ta ke shakka a gidan, don ita kam ko kusa ba ta daukar raini, tana da zafi. Hatta ga ‘ya’yanta, mijinta ma lallaba ta yakeyi. Ita da kanta ta fahimci wasu daga halayen Zulaiha ba tare da Inna Bintou ta ankarar da ita ba. Don haka ta kara jan girmanta ta rike tamau a idanun Zulaiha. Ba ta shiga duk wata sabgarta, in taro suke yi a gidan na abin da ya shafi ‘ya’ya da jikokinsu, Zulaiha ba ta shiga sam, kullum tana killace kanta tana yi wa kowa kallon bai isa ba.
Malam Ibrahim bai san ko daya daga halayen Zulaiha ba, sosai yake kyautata mata iyakar iyawarsa, tunda yana ganin an rabo ta da iyayenta da kowa nata. Matan kuma babu wadda ta taba dosarsa da irin wannan zancen, don bai raine su da tsegumi da gutsiri tsoma ba.


Haka Inna Bintou ta yi ta hakuri da Zulaiha. A shekarar ne Ishaq da Mansour suka kammala karatunsu suka dawo gida. Kwarai Mansour ya ji dadin zaman Nigeria, ya ji yana son ci gaba da zama a can, musamman da yake ya yi nasa kamun shi ma a Nigeria. Don haka ya yi hidimar kasa a can kafin ya koma Nijar, yana gamawa jami’ar Ahmadu Bello ta dauke shi aiki a tsangayar Mass Communication a matsayin assistant lecturer, sabida kyawun takardunsa. Ishaq shi kadai ya koma Nijar da zama wajen iyaye da iyalinsa.


A ‘ya’yan Inna Bintou mata sun fi yawa, na Kasisi maza sun fi yawa, izuwa wannan lokacin manyan ‘ya’yan Inna Kasisi Edrissa da Oussama sun zama manyan attajirai a Yamai (Niamey) daga sana’ar da suka gada daga wajen mahaifinsu, wato shigo da shinkafa da sauran kayan abinci daga kasar Faransa zuwa Niger. Sun buge gidan mahaifinsu sun gina katon gida na zamani, ginin attajiran Nijar. Gidan ya zama mai sassa daban-daban, sassan iyayensu mata, sassan Malam, sassan matansa, na ‘ya’ya maza da sassan ‘ya’ya mata (jikoki), kasancewar yawancin jikokin gidan a gidan Malam Razee suke rayuwarsu. Gida mai cike da kyawawan ‘yammata da kyawawan samari kamar kana cikin birnin Punjabta kasar Hindu.
Gidan Ibrahimu Sarhamu Razee kenan.
*****


ASALIN SU
Asalin kakansu Malam Ibrahim Razee ba dan kasar Nijar ba ne, iyayensa larabawa ne na sahara, wadanda suka fito usul daga saharar TOMBOUCTOU. Ita Tombouctou karkashin kasar Mali ta ke, larabawan ta ma’abota sanin addini ne masu yawo a kan rakumansu cikin kasashen Africa suna neman ilmin addinin musulunci a duk kasar da suka ji labarin ta shahara wajen yada musulunci. Ba su da wata sana’a sama da kiwon dabbobinsu.
A irin yawon neman ilmi da suke yi sun shiga manyan kasashen Africa masu yawa, irin su Mouritania, Sudan, Ethiopia (Habasha), Somalia, Algeria, Libya, Senegal da Malawi. Daga karshe suka shigo Chadi, suka gangaro kasar Niger. A daidai wannan lokacin Niger ta samu ‘yancin kanta daga hannun Faransa a shekara ta (1960). Lokacin da suka samu kansu a Niger sun yada zango a Tessoua inda mahaifin Malam Razee ya tabbatar musu da ya ga gurin zama sabida albarkar wajen da habakar dabbobinsu. A lokacin ita kanta Tessoua kauye ce kayau, ba ta kai ga zama jiha ba.
Mahaifin nasa ya zama babban malami mai bada karatun buzu a Tessoua, a hannunsa duka ‘ya’yansa suka yi karatu, wadanda dukkansu maza ne. Ibrahimu shi ne babban dansa. Yahayya ke binsa, sai Lamin, Hassan da Hussain. Wadanda ya haifa da matarsa daya tilo ‘Zainabou’ wadda ya aura a nan. Buzuwar Tessoua ce ta asali iyaye da kakanninta.


Barkowar ‘yancin kai Nijar, da yaduwar sabbin sana’o’i bayan kiwo a tsakanin matasa cikin manyan biranen Nijar da makobtansu, irin Mali da Chadi, ya sanya wa Ibrahim Sarhamukwadayin barin gida domin neman na kai. Ya kuma roki mahaifinsa da ya ba shi dabbobinsa ya yi jari cikin tarin dabbobinsa, ya ce ba zai taba raba shi da kiwo ba, amma zai ba shi wani abu daga ciki, sannan zai ci gaba da yi masa kiwon rabi kafin ya dawo. Kiwon dabbobi da rakuma shi ne abin da suka gada daga iyaye da kakanninsu, ko bayan ransa bai yarda su watsar ba. Ko ba ya nan kannensa za su yi masa a Tessoua.
Ibrahim Razee ya shiga Yamai (Niamey) da kafar dama. A lokacin da matasa daga kowanne sassa na Africa ke silalowa cikinta, sakamakon (territoire de la capitale) wato capital territory da aka yi mata bayan Faransa ta ba su ‘yancin kai ranar 3 ga watan Agusta 1960.


Kasuwanci iri-iri ya gwada a kasuwar Nouhou market, inda daga karshe na hatsi wato kayan abinci shi ya fi karbarsa. Ya je garin Zinder duk kan sana’arsa ya ga Kasisi ya aure ta, ya tafi da ita Yamai. Sai da Kasisi ta yi haihuwa biyar ya auri Bintou, ita kuma daga Arlit. A lokacin mahaifinsa ya jima da rasuwa, lokaci-lokaci yana zuwa gida ya ga ‘yan uwansa da mahaifiyarsu, wadanda duka sun yi aure sun hayayyafa a can su ma, Yahayya shi ne ya gaji mahaifinsu wajen bada karatun buzu, shi ne kuma yake rike da ragamar gidan da sana’arsa ta kiwo. Duk da a lokacin Ibrahim bai yi wani karfi ba a hakan yana taimaka wa ‘yan uwansa sosai.
Wani zuwa da ya yi da iyalinsa bayan auren Bintou da haihuwarta ta fari, ya tarar da rasuwar mahaifiyarsa.
Wannan karon tunda ya bar gida ya dukufa neman na kai, ya mallaki karamin gida a unguwar (Liberte), unguwar talakawa ce a Yamai. Zamani na kara habaka, masu sana’ar kayan abinci suka gane wa sabuwar hanyar shigo da shinkafa da sauran kayan abinci na alkama irin su macaroni, taliya daga kasar Faransa zuwa manyan biranen Nijar ba Niamey kadai ba. Sai dai ita din ta zame musu cibiyar kasuwancin. Wannan shi ne silar arzikin Malam Ibrahim Sarhamu Razee da tarihin zamansa a babban birni (Niamey), kuma asalin su Aalimah, iyaye da kakanninsu.
*****


A Yamai Zulaiha ta haifi danta na fari, wanda Ishaq ya radawa sunan mahaifinsa ‘IBRAHEEM MU’AZZAM’, shekarar Mu’azzam daya Ishaq ya samu aikin da ya kai shi kasar Amurka a Niger Consulate America. Suka tattara suka koma kasar Amurka shi da iyalinsa.
Ya jima yana aiki a consulate na kasarsu kafin hanyoyi su bude masa sosai, ya koma karkashin siyasar gwamnatin kasar mai tabbataccen aikin gwamnati a hannunsa, ya ajiye aikin consulate a gefe ya zama dan kasa mai zaune da cikakken lasisi. A can ya haife sauran yaransa hudu daya bayan daya; Abulkhairi, Basma, Khalisat da Yasmin. In ka hada harYayansu haifaffen Yamaisun zama su biyar kenan.
Bayan dawowarsu Amurka Mummy Zulaiha ta ci gaba da karatu, inda ta yi digirinta a fannin tsimi da tanadi (Economics). Yanzu haka MummyZulaiha Raazee ma’aikaciyar banki ce da (JPMorgan Chase). Girman kai da fadin raisai abin da ya karu cikin halayenta. Al’adunta duk sun juye sun zama na al’ummar da ta ke zaune da su.
A hakan kuma ta raini ‘ya’yanta mata guda uku, mazan kam Babansu na matukar kokari a kansu, a halin yanzu yana jan su a jikinsa yadda ya kamata.He’sspending most of his leisure time with them yana dora su a kan tafarki mai kyau tun bayan mummunar kaddarar data shigo rayuwarsu. Da ma an ce ‘ya mace ta Uwarta, Da namiji na Ubansa.


Suna daukar lokaci ba su je Yamai ba, amma in suka je din suna jimawa. Suna kuma zuwa Kano wajen dangin Mummy, saboda mugun hali irin na Zulaiha ko nata dangin ba ta ja a jikinta, ba ta taba daukar wani nata ta kai inda ta ke ba. A haihuwar Basma ne shi Ishaq ya biya wa mahaifiyarta da Yayarta da Inna Bintou suka je, Inna Kasisi ta ki zuwa, don ba ta son duk wani sha’ani da zai hada ta inuwa daya da Zulaiha, zuciyarta ba za ta dauka ba.
*****


3094856450
Sumayyah Kabara
Firstbank
Price 1&2 N400
6/28/21, 7:31 AM - Buhainat: 🌹 *Aalimah**🌹
*SUMAYYAH ABDULKADIR TAKORI**


07030137870


FREE PAGES 3


MANSOUR RAAZEE
Sanda Yayansa Ishaq ya koma gida Yamai, shi kuma jami’ar ta rike shi don ya yi mata aiki bayan kammala hidimar kasarshi. Ya je ya ga iyayensa, ya kuma gaya musu samun aikinsa a inda ya yi karatu, atafau Inna Kasisi ta ce ita ba ta yarda ba, tunda babu Ishaq ya dawo gida ya nemi aikin ya yi aure. A nan yake gaya musu ya samu mata a Zaria abokiyar karatunsa. Nan ma Inna Kasisi ta yi tsalle ta dire ta ce ba ta yarda su kara yo mata wannan auren ba, ga Zulaiha nan da aka auro ba dadinta suke ji ba.


Mansour, ba shi da abin da zai ce da mahaiafinsu a duniya sai Allah ya ji kansa, ba don ya mutu ba. Yadda yake din bai yi karatun zamani ba, amma wayewarsa da rayuwa da yadda yake tafiyar da tsarin rayuwarsa babu matsi babu takura ga ‘ya’yansa, in har ba addini suka kauce wa ba, wane wani Farfesan. He is very soft on them (shi mai tausasawa ne a garesu). Shi ya tsaya masa ya auri ‘Aseeya’ diya ga shugaban jami’ar na wancan lokacin.
Aseeya ‘yar ajinsu e wadda ta fi duk ‘yan ajin kankantar shekaru. Babanta V.C, uwarta Dr. duk a jami’ar Ahmadu Bello. Asalinsu ‘yan Maiduguri ne daga kabilar Margi, aiki ya kawo mahaifinta A.B.U Zaria inda mamanta ta yi doctorate dinta a Microbiology, ta fara lecturing a nan itama, shi kuma yana matsayin V.C.
A nan cikin A.B.U aka haife su ita da Yayanta Suraj, ajinsu daya ita da Mansour Raazee a tsangayar aikin jarida.
Da fari haduwar jini ce tsakaninsu da aron note da yin tutorial in jarrabawa ta matso wanda ya rikide ya koma soyayya tsantsa. Tun abin bai yi nisa ba iyayenta suka so su dakatar kasancewar Mansour bakon haure. Suna tunanin watarana zai dauke musu ‘ya, ya mayar kasarsu.
Amma da Malam Ibrahim Sarhamu Razee ya tako da kansa tun daga Niamey shi da manyan ‘ya’yansa Oussama da Edrissa suka zo har Maiduguri nema wa dansu auren Aseeya, Prof. Kashim, kasa badawawannan farin ba’abzinen dattijon mai kama da Larabawan Hijaz kasa a ido ya yi, sabida haiba da kamalarsa. Ya kuma yi duk iya binciken da zai yi a kan Mansour, inda ya tarar asali kam sai dai ya gaya wa Aseeya, tun kafin zuwan Malam Ibrahim.
Ba da jimawa ba aka yi auren Aseeya da Mansour, suka tare a gidansa da jami’ar ta bashi, shekara na zagayowa ta haifi Da namiji, ya sa masa suna Aboubacar.
Sai da Aboubacar ya shekara bakwai aka haifi ‘AALIMAH’, ita ma sai da ta shekara biyar aka fara yi mata kanne; Sultana, Suhaima da Sabrina.
Har inda yau ke motsi Baban Aalimah Malamin jami’a ne mai matsayin Dr., Amma sun bar Zaria sun koma jami’ar Bayerota Kano bayan rasuwar mahaifin Aseeya, wato Prof. Kashim, mahaifiyarta ta koma Maiduguri cikin danginta.
Wannan ya tayar da hankalin Aseeya ta ce ba za ta iya ci gaba da zama cikin A.B.U ba, tana kallon kofar gidan da iyayenta suka rayu, hakan yana dawo mata da memories na rayuwarta tare da su. Har sai da ta samu matsala a kwakwalwarta (anxiety). Duk son da Mansour ke wa A.B.U haka ya barta ya koma Bayero don kwanciyar hankalin maidakinsa.
A sannan ne suka fahimci wani babban jigo nasu a Nigeria ya fadi (Prof. Kashim), ta ajiye aikinta da ta ke yi a gidan talbijin, sai abin da Mansour ya kawo, kusan komai da ta saba na rayuwarta dainawa ta yi. Da aka raba musu gado ta yi wa nata adani sosai a banki da wani kuduri a zuciyarta.
Yana kai ta Maiduguri akai-akai wajen mahaifiyarta da danginta, kuma suna zuwa Yamaiwajen nashi iyayen a duk sanda suka samu hutu.
A sannu Inna Kasisi ta fahimci Aseeya ba halinta daya da Zulaiha ba, they are totally opposite in every aspect.
Sonsu ta ke da zuciya daya, tare da girmama ko da kare ne in dai daga Nijar ya fito, sabida son da ta ke wa mijinta,. Yayanta Suraj ya bar kasar tun mahaifinsu na raye, tun daga zuwa karatu a kasar Canada ya yi zamansa a can musamman da mahaifinsu ya rasu, mahaifiyarsu ta koma Maiduguri, bai kara sha’awar dawowa Nigeria ba.
*****


Aalimah tun suna kanana suka taso da fahimtar cewa, mamansu is a mental patient, sannan suka fahimci Babansu na tsananin sonta. Tana daukar lokaci lafiya kalau don tana kan shan magani, amma in abin ya tashi ba Babansu kadai ba su kansu suna jin jiki. Babu duka babu zagi sai kuka. Za ta kwana ta wuni tana kuka kamar ranta zai fita babu gaira babu dalili. Ta bar shiga komai nasu, ta bar yi musu girki. A irin wannan lokacin Babansu ke yi musu komai; wanka, girki, shirin makaranta, wankin uniform da dukkan hidimar da uwa ke yi wa ‘ya’yanta.
Da Aboubacar ya soma hankali shi yake kula da Maman. Baban ya kula da su ita da su Sultana. A haka suka taso da wata irin shakuwa matsananciya tsakaninsu da Babansu, Mamansu tana da tsauri a kan tarbiyyarsu, hakan ba ya nufin ba ta sonsu, amma tana da zafi. Ba su nemi komai sun rasa ba, amma ba su da wadatar da sauran ‘yan uwansu na Yamai ke da shi.
Babansu bai dogara da komai ba sai albashinsa, sannan ba shi da halin rokon ‘yan uwa wai don sun fi shi wadata. Ya dogara da kansa ya tsare wa iyalinsa komai na bukatun rayuwa daidai misali, irin na kowanne cikakken dan boko. A halin yanzu Dr. ne shi a jami’ar Bayero a tsangayar kimiyyar sadarwa.
Aalimah na matukar son zuwa Yamai, ta iya harshen mahaifinta sosai don kusan duk wani hutu mai tsawo a can ta ke yinsa. Inda za ta hadu da ‘yammatan family sa’anninta su Balkissa ‘ya’yan Kawu Oussama su yi ta dabdalarsu tun suna yara. Ko a cikin jikoki Aalimah ta daban ce a wajen Kakansu. Sakamakon ita kadai ya sanyawa sunan mahaifiyarsa.
Yana sonta son da ba ya iya boyewa, kowa ya kwana da sanin hakan a familyn, Aalimah ce ta gaban goshin Mallam. Kuma shi ya zaba mata wannan suna na Innarsa (Aalimah) wato mai ilmi.


‘Margi’ da ‘Abzin’su suka hadu suka haife Aalimah, don haka na bar wa mai karatu ya siffanta kamannin Aalimah Mansour yadda yake so. Babu wanda ya damu da yin wani abu wai shi auren zumunci a wannan family kowa yana kawo wanda yake so ne ya aura, don haka babu rikici babu rashin fahimta, kansu a hade yake kamar tsintsiya. Sai dan abin da ba a rasa ba, wanda ba ka rasa shi a kowanne extended family, shi ma ya fi yawa a tsakanin faccaloli (matan ‘ya’yansu), amma jikokin gidan da ‘ya’yan gidan kam kaf dinsu kansu a hade yake.


Haduwar Aalimah da Mahmoud ta faru ne tana ajin karshe a sakandire ta staff school inda ta yi sakandire. Mahmoud abokin Yaya Aboubacar ne, tare suka yi karatu a nan B.U.K. Mahmoud bakatsine ne, wanda ya fito daga karamar hukumar Kaita ta jihar Katsina.Da suka zo yin hidimar kasa aka kai shi wata makaranta da ke daura da sabuwar jami’ar Bayero.
Daddyn su Aalimah ya san irin abotar da ke tsakanin Aboubacar da Mahmoud, don haka da Aboubacar ya zo yana nemawa Mahmoud alfarmar zama tare da shi a nan boys quartersdinsu wajen mahaifinsu, Daddyn ya amince, amma kuma ya ce masa ya gaya wa Mahmoud dokarsa ita ce; karfe tara na dare yake rufe gida, in ya amince ya zo ya zauna babu laifi.


Zaman Mahmoud Kaita a gidan Dr. Mansur Razee zama ne na aminci. Ya samu iyalin Dr. mutane masu karamci, tarbiyya, tsantsar ilmi da son junansu. Dole duk wanda ke gaba da kai a haihuwa ka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login