Showing 114001 words to 117000 words out of 126031 words
Chapter 39 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt
a kansa da ta ke son cikawa, amma ba halinta bane. Aalimah ba son shi ta ke yi ba in ya yi la’akari da tsayin lokacin nan ba ta taba neman shi da ya ba ta hakkinta na aure ba. Wata zuciyar ta yi saurin kare ta da cewa “ita za ta nema ko kai?
A al’adarta ta iyaye da kakanni, miji ke kai kansa ga matarsa ba matar ke kai kanta ga mijin ba. Ko babu soyayya mata basa jurewa wannan. Kuma ta san kana da lalura, tsoron hakan ma na iya cire mata sha’awar komaiâ€.
Yana wannan tunanin ya ji motsinta tana shigowa. Daga kai ya yi ya dube ta a hankali, doguwar riga ce a jikinta (milk colour) samfurin Oman, yadin kamar na roba, don haka ya fiddo surar jikinta shapely, ta daure kanta da dankwalin rigar, gashin kanta ya kwanto ta baya. Ya samu kansa da kasa dauke ido a kanta. Wani magnet na jan idanunsa zuwa gareta. Ya kasa dauke ido a kanta.
Ba tare da ta ankara da irin kallon da yake mata ba a yau take ce da shi.
“Nan zan kawo maka lunch, ko in bar shi a dining?â€
Zuba mata idanu ya yi kamar wani maganadisu na fizgar zuciyarsa zuwa gare ta. Kamar wanda aka yi wa wahayi; ji ya yi duk wani nauyinta da shakkarta da yake ji, a yau ya kau daga idanunsa. Hannunsa ya mika ya kamo nata a hankali, tare da ambaton sunanta da sassanyan sauti daga can karshen makogaronsa. Sai jinta ta yi gaba daya a jikin Mu’azzam ba tare da ta shiryawa hakan ba, ya soma wani irin sunsuna ta tun daga wuyanta har cikin jikinta. Turaren da ya dade yana ji daga nesa nesa yana dimautar dashi yau ya samu completely a jikinsa.
Aalimar da ya dade yana kallo daga nesa nesa yana kintata laushin fatar jikinta da sulbin bakinta, yau ya samu kwance a jikinsa.
And the skin is softer than he imagined.
Samun kansa yayi da rungumeta sosai tare da manna ta a kowacce kusurwa ta jikinsa.
Ajiyar zuciya yake saukewa a jejjere kamar numfashinsa zai bar gangar jikinsa. Is that the feeling of being with a woman???
Idan kuwa shine it’s the most pleasurable, and most intoxicating feeling in the history of man ever.
A hankali ya shiga kurdawa ta wuyanta har ya samu ya kai bakinsa zuwa ga nata.
It is a kind of gentle kiss wanda ya hautsinasu cikin dan lokaci bakidayansu.
Jikinta rawa ya soma yi tare da tasowar dadadden al’amarin da ta jima tana kokawa da shi da karfin hali da karfin addu’a. Kamshin jikin Mu’az da wanda ke fita daga bakinsa na mouthwash din da yayi amfani da shi shi ne babban abin da ya ribace ta. A lokacin da ya soma kissing din tsakiyar bakinta sai komai ya kwace mata. Ta manta cewa, wannan Mu’azzam ne ba Aboulkhair ba. Yanayin yadda yake sumbatar tata ba ta taba jin irinsa a duniya ba. Ya zamanto cewa ta gama mika wuya ga duniyar Mu’azzam…
Yayin da tafiya ta yi tafiya sai Mu’azzam ya rasa kuzarinsa bakidaya. Duk kokarinsa ya kasa komai bayan kissing din, cikin sanyin jiki ya koma gefen gadon ya zauna yana mai dafe kansa... Ita kuma Aalimah barin dakin ta yi tana mai jin har abada ba za ta sake iya hada ido da Mu’azzam ba.
Kwana uku suna buyar wa juna, sai dai ya samu abincinsa a ‘dining’, ta daina shiga dakinsa, duk wannan karambanin ta daina, ta zama calm, cool kamar farkon zuwanta, ta san ba karamin tsallake rijiya da baya ta yi ba, kunyarta ya ke ji, yana ganin ya zama raggon namiji, wanda bai iya biyawa matarsa bukata, tana ganin ta zama mara aji da tayi saurin bada kanta ga Mu’az haka. Gashi babu biyan bukata, ta san ba komai bane tasirin magungunansa ne. Ita dama bata da tsarki so bata cikin irin damuwar da Mu’azzam ke ciki. Ta kasa zaune ta kasa tsaye a daren yau da sabon al’amarin dake sakadar zuciyarta a hankali a hankali a kwanakin nan, yana rarake ruhinta kusufa-kusufa tun ranar da wannan dan physical relationship din ya shiga tsakaninsu, ba komai bane sai yawan tunanin MU’AZZAM da son ganin shi. Da kasancewa cikin wani irin shauki a duk lokacin da ta ji muryarsa yana magana a waya koda Harrison ko motsin sa zai shiga daki. Ba abinda take son ji sai muryarsa, ba abinda take son gani sai fuskar sa, ba abinda take so sai kasancewa tare da shi muddin rayuwar ta.
*****
Tayi kwalliya cikin atamfa Ghana wax koriya shar, daidai lokacin da ta fuskanci yana fitowa cin abinci sai ta fito ‘dining’ ta zauna, ta gaji da buyan tana so ta ganshi ko daga nesa ne in ba haka ba bata jin zata kai daren yau a raye, ta zuba abincin amma ta kasa ci sai juyi take da cokali a cikin tangaran. Dai-dai nan Mu’azzam ya fito daga dakinsa yana waya. Kallo daya tayi mashi ta ambaci “Ya Allah†cikin zuciyarta, sannan kuma tayi gaggawar kawar da kanta kada kwarjini da haibarsa su yi mata lahani a idanunta.
Ya shirya cikin ‘American suit’ bakake wuluk kamar kullum, neck-tie din wuyansa na yau red ne, amma sai ta ga kamar yau yafi kowacce rana yin kyau. Kamar yau ya fara sanya suit a jikinsa. Kamar yau ta fara ganinsa. Yayi fes! Yayi fresh! Kuruciyarsa ta fito sarari. Har ya zo kusa da ita ya ja kujera ya zauna bata sauke ido a kan shi ba.
Yayin da shi kuma ya ja ‘food warmer’ gabansa ya bude, ya dauki plate zai zuba sai ta mike ta karbe shi ta zuba masa daidai yadda ta san yana bukata, ta koma ta zauna tayi shiru tana satar kallon shi daga karshen idanunta tana cigaba da juya cokali a cikin abinci. Zuciyarta tayi haske, ko ba komai a ce Mu’azzam mijinta ne kadai ta gama morewa. Tunanin matsalar da ke kwance cikin auren nasu ta sanya jikinta yin matukar sanyi.
Mu’azzam yana cin abincin nashi amma hankalinshi na kanta. Ta koma ‘cool Aalimah’ din ta. Dama an ce ‘kayan aro baya rufe katara’. Murmushi yayi ya girgiza kai ya cigaba da cin abincinsa.
Da ace tuntuni ya san common hug da kiss zai ladabtar masa da ita ai da bai zauna tana bashi wahalar data bashi a baya ba. Da tuni an dade da wuce wurin. Ta dube shi da alamar tambayar ko me ya sanya shi yin murmushi? Ture plate din gaban shi ya yi, ya sunkuya a gabanta dai-dai fuskarta kasa-kasa ya ce da ita,
“Da za ki zauna a haka yadda ki ke, ai da na ji dadiâ€.
Murmushi ta yi, don sarai ta gane abin da yake nufi. Ya sarke hannayensa biyu, ya kuma dora habarshi a kansu ya yi magana cikin sanyin murya.
“Aalimah, why do you want to change me (Aalimah, me ya sa ki ke son ki canza ni?)â€.
Da sauri ta cira kai ta dube shi, amma ta kasa magana, ashe ya ramfo ta tuntuni ita kadai ta ke shirmen ta?
Ya ce, “Answer me Aalimah, why? Me ya sa ba za ki barni a yadda ki ka same ni ba?â€
Hawaye suka ciko idanunta, ba jimawa suka garzayo kan kuncinta, hanky dinsa ya ciro daga aljihunsa ya mika mata. Da sauri ta karba ta share, sannan ta furta masa abin da ke cinta a zuci.
“Because I want another Aboulkhair in youâ€.
Da sauri ya girgiza mata kai cikin gamsuwa da amsar da ta ba shi.
“Aalimah!â€.
Ya kira sunanta cikin sanyin murya,
“Kama da wane ba ta wane! The fact that we belong to the same parents ba zai taba zama cewa za mu zama daya ni da shi a komai ba. Ki yi hakuri ki karbe ni a yadda nake, ni ma na fi son ki a yadda ki ke. Mai kunya mai kawaici mara hayaniya. Na kuma yi miki alkawarin zanyi miki duk abinda kike so gwargwadon ikona, amma ki daina aro personality din da ba naki ba kawai don kina so in canja daga yadda nake, zan kyautata miki iyakar iyawata insha Allahu but please accept me the way I was.
Na san ya fi ni kirki, ya fi ni dadin mu’amala, ya fi ni nuna miki soyayya. Aalima ki sani, ni ba ni da lafiya. Ina mai kokawa ne da kaddarar da ta same ni. Amma tabbas rayuwarmu tare na yarda cutuwa ce a gare ki. Aalimah na yanke shawarar in sauwake miki auren nan ko babu amincewar iyayenmu don ki samu farin ciki irin na kowanne ma’aurata. Iyayenmu su yi hakuri, na yarda ina cutar da ke a cikin gangar jikin ki da zuciyar ki.
Ni ma ba son raina ba ne zamowata a haka, I’m fighting with my destiny. Na san yadda zan bai wa su Daddy hakuri, in kuma nuna musu ba ki da laifi…â€.
Girgiza kai ta ke yi da sauri, hawaye na bin kuncinta. Hankalin ta yayi mugun tashi.
“Na zabi zama da kai Yaya Mu’azzam a cikin kowanne hali a yadda na same ka. Babu saki tsakaninmu har abada. Ina son ganin iyayena da malam cikin farin ciki kamar yadda nake son rayuwa taâ€.
“Ki sanya su farin ciki ki nakasa kuruciyarki Aalimah? I can’t give you sexâ€.
Da dukkan affirmation na zuciyarta ta daga masa kai, mai nufin, eh ta amince, zata zauna da shi haka. Mu’azzam bai san lokacin da ya bude mata dukkan hannuwansa ita kuma ta tafi a hankali ta shige, suka rungume juna suna hawaye da runguma mai tsananin karfi (tight-hug). Rungumar data bude shafin sabuwar rayuwa a gare su.
******
A haka suka ci gaba da rayuwar, sai dai su yi dan romancing a tsakaninsu. Wanda ke matukar wahalar da Aalimah a karshe. Ta rasa inda za ta sanya kanta a matsayinta na mace mai cikakkiyar lafiya. Rannan ta ce, bari ta kwaso magungunan Aunty Gumsu, watakila za su taimaka wa Mu’azzam ya ba ta farin cikin da gangar jikinta ke bukata.
Amma a karshe, matukar azaba suka sanya ta, wanda sai da Mu’azzam ya tausaya mata, ya kuma soma tunanin dole ne ya yi wani abu don inganta rayuwar aurensa.
A washegari ta ce da Mu’azzam za ta fita shopping ya ce ta bari ya dawo office sai ya kai ta, ta ce, a’ah ya sa Harrison ya kai ta da wuri ta ke bukatar shopping din. A yadda yake tattalinta ba ya son duk abin da zai bata mata rai, dole ya amince da tsarinta.
Ba ta ce da Harrison ya kai ta ko ina ba, sai asibitin Mu’azzam, tana son ganin Dr. Nebrass.
Da karramawa tsohon baturen ya karbe ta, a lokacin da ta gaya masa ita ce maidakin Engnr. Mu’azzam Raazee.
Ya ba ta wajen zama, ya kuma ba ta abin sha, amma ba ta sha ba, ya kuma ba ta dukkan hankalinsa don ya fahimci muhimmiyar magana ce ta kawota.
“Doctor I want my husband to live without the help of Anti-Androgensâ€.
Ta kifa kai a kan teburinsa ta saka masa kuka mai cin rai, wanda dole duk wanda ya ji ya fahimci tana cikin tsananin damuwa, ya tausaya mata a kan hakan, don ya san da ma hakan za ta faru.
Ba ta fito ta yi masa bayani baro-baro ba, saboda kunya ta diyan musulmi, amma ya gane dalilinta na zabar Mu’azzam ya zauna da lalurarsa yadda Allah ya bar masa ita, ba tare da sun daddaure shi da magungunan kashe tasirin androgens (sex hormones) a cikin jikinsa ba.
“It’s o.k Mrs. Raazee, its ok stop crying. Tunda kin zabi hakan shikenan. Daman maslahar taki ce, amma tunda kina ganin zaki iya jurewa it’s quite okayâ€.
Shi ne amsar da likita Nebrass ya ba ta. Ba haka taso al’amarin ya kasance ba babu yadda zata yi ne. Ta yi hakuri har na tsawon shekara guda da rabi, amma wutar son Mu’azzam da ke ruruwa a zuciyarta sannu a hankali, da kuma yawan physical relationship dake faruwa tsakanin su yanzu, da kwana da suke yi bisa gado guda kalmashe cikin juna, ya sanya ta kasa cigaba zuba masa ido kamar watannin baya.
*******
Dr. Nebrass, ya gaya wa Mu’azzam zai rage karfin anti androgens a jikinsa tunda yanzu yana da aure. Ba tare da ya gaya masa matarsa ta zo ta same shi ba. Mu’azzam ya yarda nan da nan, don shi kanshi al’amarin ya fara damunsa. Ba soyayyar Aalimah ce ta yi masa katutu ba, a’a, tausayinta ne. In don ta shi ne, yana jin dadin rayuwarsa a haka. Amma ya sani Aalimah tana cutuwa matukar cutuwa ba dan kadan ba, kawaicinta da alkunyar ta ke sa tana danne komai bata nuna masa gazawarta, tunda ya ba ta option na zama da shi ko a’ah, kuma ta zabi cigaba da zaman anyhow.
Aalimah ba za ta taba mancewa da wannan ranar ba. Rana mai dumbin tarihi a gareta. Ana tafka ruwan sama har da kankara kamar da bakin kwarya. Ranar da ta zama sirrin Mu’azzam, ya zama sirrinta shima, cikin wani yanayi mai ban mamaki a gare su bakidaya.
Tun abubuwa na tafiya gentle-gentle, har komai ya kwace wa Mu’azzam. Ya zama out of his control. Tsayin daren bakidaya za ta iya cewa, ko na minti talatin Mu’azzam bai barta ta huta ba. Har ita da kanta ta gane ba ta da wayo, abin da ta je ta sa likita ya yi masa.
Washegari ko da ya je office ma bai wuce awanni uku ba sai ga shi ya dawo a wani yanayi da dole ta amsa kiransa. Ya sake komawa office ba a yi closing ba ya dawo. Tsayin kwanaki bakwai a haka suke, tana kwarara kanta, tana karfafa gangar jikinta da zuciyarta. Ga dai biyan bukata ta samu, amma kuma shi Mu’azzam din tana tausaya masa. Ta kuma gane hakan zai iya zama barazana ga aikinsa, tunda ba ya maida hankali gare shi. Ba inda yake zuwa, ya daina kulla komai, in dai yana cikin gidan to aikin kenan, ko isasshen abinci ba ya iya ci, har ramewa ya yi, ita ma ta jigata ta rame. Don haka dole ta sake satar jiki ta sake garzayawa wajen likita Nebrass ta gaya masa kukanta, don an bai wa Mu’azzam query daga Chevron kan yana wasa da aiki yanzu, za’a iya sallamarsa ko rage masa matsayi daga yanzu zuwa kowanne lokaci idan bai gyara ba.
Dr. Nebrass ya zauna da taimakon wasu manyan likitoci ‘yan uwansa kan lamarin Mu’azzam. Domin sosai yake tausayawa Aalimah, ta damu da mijinta sosai, ya kuma gama fahimtar tana matukar son sa. A daya bangaren yana tausaya wa Mu’azzam din. Shekaru daidai kenan har goma sha biyar, yana rayuwa kan shan magani. Ya yi aure matar ta kasa jurewa. Ya warware maganinsa ya zama barazana ga aikinsa. Don sam Mu’azzam ya daina yin cikakkun awanni uku a office sai a jikin Aalimah. Daya daga cikinsu wanda ya zo daga asibitin Johns Hopkin, shi ne ya yi suggesting wani magani wanda yake ganin zai yi daidai da Mu’azzam, ya zauna lafiya da matarsa da kuma aikinsa.
Amma yana da matukar tsada. Amma da gudu Mu’azzam ya amince da wannan tsadadden maganin. Sai ya kasance Mu’azzam na yin sati ma bai bukaci sex ba, amma bayan cikar satin a duk ranar da abin ya juyo, Aalimah na ji a jikinta, amma ba ya wuce na kwana biyu, rabin albashinsa kuma na tafiya wajen sayen magunguna. Wannan ita ce rayuwar auren Aalimah da Mu’azzam a birnin Las Vegas.
Daidai wannan lokacin Aalimah ta fahimci yaron ciki a tare da ita.
A ranar data fahimci hakan, daki ta shige ta fuskanci alqibla ta yi sujudush-shukr ga Ubangijinta.
7/11/21, 9:41 PM - Buhainat: Don haka iyayen suka mika al’amarin kotun muslunci, inda kotu ta dankawa Aalimah mas’alar auren ta a tafin hannunta. Cewa in ta fi son zama da Aboulkhair za’a yi amfani da shari’ah, kotu ta yi wa Mu’azzam khul’i ta ci gaba da rayuwar aure da Aboulkhair, idan kuma ta zabi ci gaba da zama da mijinta uban ‘ya’yanta, to ta koma dakinta. Wannan karon babu wanda zai yi mata shisshigi. Sun ba ta dukkan damar ta da addini ya ba ta.
Aalimah bata yi wata-wata ba ta ce ta zabi Mu’azzam ya cigaba da auren ta sabida ‘ya’yan dake tsakaninsu da wasu dalilai da dama. Sannan ta nisa, kafin ta dago idanunta cike da hawaye ta nemi kotu alfarmar tana son Mu’azzam ya sake ta (ba khul’i ba), bata da ra’ayin sake zama da ko dayan su alhalin duk suna raye, in har da gaske addini ita ya bawa zabi a hannunta, to ta zabi Mu’azzam, a gefen hakan tana neman alfarmar ya sake ta, ba kuma don ta komawa Aboulkhair ba, sai don rabuwa dasu bakidaya yafi mata kwanciyar hankali. Ba zata iya kallon daya ba, alhalin tana auren daya. Tana kuka take rokon Alkali mai shari’ah ya roka mata Mu’azzam wannan alfarmar in har da gaske an damka mata ragamar auren nata a hannunta babu takurawar kowa cikin iyayen su. To wannan shine zabin ta.
Gabadaya iyayen sai suka sadda kansu kasa. Alkali kuma yace wannan tsakaninta da mijin ta Mu’azzam ne amma kamar yadda tace ya roka mata alfarma sai ya maimaitawa Mu’azzam alfarmar da Aalimah ta roka daga gare shi.
Koda aka waiwayi Mu’azzam kan wannan alfarma da Aalimah ta nema, daburcewa yayi, wata irin kidima ya shiga irin wadda bai taba shiga a rayuwar sa ba, daga bisani ya karfafi kansa da ya ga irin kukan da Aalimah take yi a gaban kowa, ya ce shi da hannunsa bazai iya rubuta saki a gareta ba, amma ta je ya warware igiyar aurensu guda daya (a fatar bakinsa). Tunda abinda ta zaba kenan. Kuma ta ce shine kwanciyar hankalin ta. Yana mata fatan alkhairi a gabadayan tsayin rayuwarta ta gaba. Daga haka ya mike ya bar kotun.
Mummy sai ta fashe da kuka, ta kifa kanta cikin cinyoyinta tana ta yi, wannan wace irin kaddara