Showing 105001 words to 108000 words out of 126031 words

Chapter 36 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt

Gumsu kan ba ta haushi wani lokacin, ta fiye wuce gona da iri, tana nufin ta fi-ta sanin abin da ya kamata ne? Ta ce,
“In kin tafi zan raka ta dakin nata aiâ€.
Gumsu tayi tsalle ta dire ta ce atafau sai ta kai Aalimah dakin da ya zam mallakinta za ta bar gidan. Mu’azzam mikewa ya yi zai wuce ba tare da ya ce komai ba. Kansa ya dau zafi sosai, ba ya son hayaniya, komai kankantar ta. Ita kuma Gumsu ya gama fahimtarta ‘yar hayaniya ce ba tun yau ba. Ba shi da zabi ban da ya lallabata ta bar masa gidansa. Ya ce ta biyo shi ya nuna mata dakin da aka yi furnishig din da sunan ‘yar tata. Da karfin gwiwarta ta bi bayansa.
Kwarai ta yaba da bedroom din, sosai furnitures din suka burge ta. Ga dakin kusa da dakin barcinsa. Duk wani motsi da daya yayi dayan zai ji shi. Hakan ya yi mata sosai. Ta je ta takura Aalima ta yi wanka a gabanta cikin ruwan turare na musamman, ta fiddo mata kayan da za ta sanya sababbi kar! A ledarsu, ta feshe su da turare, ta gyara mata dogon gashin kanta. Sannan ta rufe ta cikin lullubi ta kai ta har dakinta gefen gadonta.
Ta gama karance Mummy Zulaiha tsaf! So ta ke ta hana kusanci tsakanin Aalimah da Mu’azzam, amma ba ta san dalilinta ba, shiyasa ta dage sai ta kawo Aalimah dakin ta da kanta, cikin zuciyarta ta ce, “Allah ya fi kiâ€.
Ta zauna a gefen Aalimah ta soma yi mata huduba, ta ce, duk runtsi ta zauna a dakinta, ba ta yarda ta koma dakin Mummy ba, ta shiga rayuwar Mu’azzam ko ba ya so. Ta cire kunya ta kutsa kanta cikin rayuwarsa kota yaya, don in ta biyewa Mu’azzam zata shekara cikin gidan sa basu gaisa da juna ba, wanda wannan ba shine kudurin iyayen su a kan su ba; so suke ta canza Mu’azzam ya dinga walwala da farin-ciki kamar kowa. Duk abin da ta ke so ta dafa da kanta kada ta dogara da girkin Mummy, gidanta ne ba gidan Mummy ba, ta kasa zaman nata auren kada ta sake ta hana ta nata zaman auren.
A hankali Aalimah ta ce, “Aunty Gumsu ni wace ce da zan yi fito-na-fito da ita a gidan danta? Dan ma da ba son shi nake yi ba dole aka yi mun?†Sai kuka.
Gumsu ta ce, “Zauna nan wawuya ki yi ta dakon rashin so, tunda kin ga shi zai fishshe ki. Ki dubi Mu’azzam daga sama har kasa za ki tabbatar ba karamar kyauta ce Allah ya zabo ki cikin dubban mata ya yi miki ba. Ruwan ne ki karbi wannan kyautar da hannu bibbiyu, ruwanki ne ki yi wasarere da ita ki yi wa kanki asaraâ€.
Ta mike za ta fita, sai kuma ta juyo, ta dan rungumeta a jikinta ganin tanata hawaye ba kakkautawa.
“Take it easy my daughter. Insha Allahu sai kinyi alfahari da wannan aure. Mu’azzam is a genius you will soon come to love your husband fiye da son da ki kai wa kaninsa. Na zuba miki duka magungunan da na tanadar miki a lokar gadon ki, Enjoy yourself my daughterâ€. Ta yi murmushi sannan ta sumbaci goshin ta ta fita.


Ita ba karamar yarinya ba ce, ba kuma yau ta fara aure ba, sarai ta fahimci magungunan da Gumsu ke nufi. Wani siririn murmushi tayi mai kama dana tausayin kai. A ranta ta ce,
“Kin dai ajiye min sinadaran da zasu taimaka min wajen tafiya ta lahira duk ranar da ya waiwaye ni. Don ba ki san lalurarsa ba neâ€.


*****


Gida ya zama daga ita sai Mummy da Yesmin. Tunda maigidan ba zama yake a cikinsa ba sai lokacin barci. Haka kawai shi da gidansa an haramta masa zaman cikinsa. Wannan abu na ci masa tuwo a kwarya. A da, ba abin da yake so irin ya bude ido ya ganshi a falonsa ko a balcony din gidansa, hakan na sanya shi nishadi matuka. The unbelievably beautiful building of his house wanda mutanen Las Vegas suka kira fierfield terrace and the scent of his tidy green grasses na sanya shi nishadi. Amma yanzu ya zama daga gida sai office sai kan titi.
Wani lokacin zuciyarshi kan shawarce shi to ya dinga zuwa BAR mana don rage lokaci kadai ko ba don ya sha ba? Wata zuciyar sai ta ce, kai yanzu in aka ce ka doshi inda giya ta ke da sadaka sai ka je? Bayan ita ce silar mutuwarka a tsaye ba don ka mutu ba? Ka dai nemo wurin zuwa, amma ban da matattarar shan giya. Kowa ya debo da zafi bakin sa.


Aalimah na kokarin amfani da hudubobin Gumsu a zamanta da Mummy cikin gidan. Ta amince Gumsu mai kaunarta ce da zuciya daya. Sosai take girmama Mummy kamar uwar data haife ta. Bata saukowa kasa sam sai za ta nemi abin da za ta ci. In Mummy ta dafa nasu tana aje mata a food warmer in tanaso ta dauka. In bai yi mata ba ta dafa abinda take so. Tsakaninta da Mummy gaisuwar safe da yamma, tana shiga ta gaishe ta. Ta kuma zauna suna hira da Yesmin. Ita ma ta lura da abin da Gumsu ta gane Mummy ba ta son zamanta upstairs, ta fi son ta dawo nan dakinta su zauna tare don dai ba yadda zata yi ta gaya mata hakan ne. Dalilinta na hakan ne ba ta sani ba. Yesmin kan haura saman wajenta su yi hira. Tana nuna mata damuwarta kan karatunta da aka katse mata a Boston. A bakin Yesmin ta ji cewa Daddy ya sayar da gidansu na Boston dalilin dawowar su nan kenan.
Aalimah ta dade tana mamaki, a baya in wani ya ce mata Daddy zai taba barin rayuwar Turai ba za ta taba yarda ba, sabida yadda Turan ta ratsa jikinsu shi da ‘ya’yansa. Ta san Mummy dole ta zauna don ba za ta iya karbar rayuwa a Nijar da sauki ba. Don ma Yesmin ta sakaya ba ta ce an saki Mummy ba.


Tunda ta koma benen ba su taba haduwa da Mu’azzam ba. Ba wanda ya san da zaman dan uwansa, tana da toilet dinta cikin dakinta. Daga karfe shidda na yamma in ta yi wa Mummy gaisuwar yammaci ta dauki abinda zata ci a kitchen ta haye sama ba ta kara fitowa sai wayewar gari. Mummy kullum cikin observing dinta ta ke don ganin ko akwai wani sauyi a tare da ita? In ta zo mata gaisuwar safe ta dinga saka mata ido kenan, amma ga kwanciyar hankalinta ras ta ke ganin Aalimar kuma tana da tabbacin Mu’az bai dawowa sai Aalimah tayi barci, kuma sammako yake ya tafi office.
Sai kuma ta shiga damuwar ina yake zuwa haka after office hours? Kada dai shan giyar ya komama wa? Tunda bashi da lafiyar da zai nemi mata? Abincin safe kawai yake ci a gidan, wunin ranakun ba ta san ina yake samu ba, sai dai tana da tabbacin a WALDORF ASTORIA yake ci don baya cin wani abinci sai nasu kamar yadda ya saba a baya. Ba abinci ne damuwarta ba, inda yake zuwa sai dare ya nausa, shi ne damuwarta.


Mummy ba ta kara shiga cikin damuwa ba, sai da likitan Mu’az ya zo har gida ya same ta, cikin sirri yake gaya mata cewa, cikin satin nan jinin Mu’azzam ya hau, ko ta san me ye matsalolin sa na yanzu? Don hauhawar jini matsala ne babba ga mai matsaloli irin na Mu’azzam.
Mummy ta gaya masa iya abin da ta sani, cewa aure mahaifinsa ya yi masa ba da saninsa ba, kuma matar Aboulkhairi mai rasuwa. Har ma tana gidan ta tare. Nebrass ya yi rubuce-rubucensa, sannan ya tambaye ta ba’a yi masa wani abun da ba ya so? Ma’ana ba’a takura shi yin abinda zuciyar sa bata so? Mummy ta yi shiru, ko zamansu tare da shi itada Yesmin sarkin rikici ai ba ya so. Biyayya kawai yake mata ya takura kansa matsayinta na uwarsa ya danne ransa yake zaune da ita amma a kasan ransa baya so. Ya fi son kadaici. To amma in ta bar gidansa ina za ta?
A yanzu kam ba ta da karfin kama gida a U.S tunda ba ta aiki, sannan ba ta son yin nisa da shi, tana matukar tsoron abin da zai faru duk ranar da Mu’azzam ya kusanci Aalimah. Ita zaman gadi ta ke yi, idan Aalimah ta ki Mu’azzam wace mace ce za ta yarda ta zauna da shi a karo na uku? Kwarai tana tsoron zuwan wannan ranar. Amma Gumsu da kilbibinta ta raba musu daki ita da Aalimah.
Hawaye ta share, ta ce da likita Nebrass,
“Ni kaina ai damuwa ce ga Mu’azzam, amma likita ba ni da inda zan jeâ€.
Cikin mamaki Nebrass ya ce, “Ina mijinta? Yana nufin Baban su Mu’azzam?â€
A sanyaye ta ce, “Mun rabuâ€.
Kamar ya ce da ita, “Kuma aka ce dole sai kin zauna a kasar da ba taki ba?†Sai kuma ya yi shiru, ya soma ja mata kunne a fakaice.
“Mu’azzam dai yana son nutsuwa, yana bukatar sarari daga hayaniya inda hali. Ita kanta matarsa ta yi nesa-nesa da shi, in ba shi ya neme ta ba, Madame, lafiyar dan ki ita ce first, ya kamata ki duba wannanâ€.
Ya yi musu sallama ya tafi.
7/7/21, 8:09 AM - Buhainat: Damuwar Mummy ta nunku. Ta ga cewa komawa Nigeria ko Nijar ya zame mata dole kada wani abu ya faru da Mu’azzam da kyakkyawan treatment din da yake samu Ubansa ya ce ita ce sila.
Kuma a ranar Daddy Ishaq ya kira Aalimah a waya, ya ce ta kai wa Zulaiha wayar yana son magana da ita. A sautinsa ta ji fushi mai tsanani don Nebrass ya kira shi ya gaya masa komai.
Daddy ya soma fada ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, ya ce, in ta kashe Mu’azzam sai ya yi shari’a da ita. Mummy na kuka ta shiga ba shi hakuri, kuma ta gaya masa ba ta da kudin tikiti, sai karshen shekara take karbar kamashonta na banki, sannan tsoro ta ke ji kada wani abu ya faru da Aalimah, Mu’azzam zai rasa mata ta uku… ita kuma burinta shi ne ya zauna da aure ko da babu abin da zai shiga tsakaninsa da matar.
Murmushi Daddy ya yi, ya kuma fahimce ta. Ya ce,
“In dai tikiti ne zai saya musu ita da Yesmin, wannan maganar da ta ke yi kuma ba huruminta ba ne, tunda ko likitansa bai ce don me aka yi auren ba. Ta bar wa Allah komai kamar yadda kowa ya bar masa.
Da wannan nasihar da Daddy ya yi mata Mummy Zulaiha ta soma hada kayanta don barin Las Vegas. Yesmin ta fi kowa farin ciki, ko ba komai ta san Daddynta ba zai barta babu karatu babu aure ba. Kuma zata kasance cikin ‘yan uwanta, ita kuma dama damuwarta kenan.
Har karfe goma sha daya na dare suna zaman dakon jiran dawowar Mu’azzam don yin sallama da shi, wanda yau yayi nisan kiwo fiye da koyaushe, bayan Daddy ya aiko musu da ticket mai zuwa Nigeria ba Nijar ba. Wannan ya dan taba ran Mummy, amma da ta tuna babu aure a tsakaninsu sai ba ta ga laifinsa ba. Kamar tuni yake mata da hakan.


Mu’azzam bai tashi shigowa gidan ba sai karfe goma sha biyu na dare. Zai haye benen shi kamar yadda ya saba ya gansu a zazzaune kamar masu neman gafara.
“Lafiya Mummy ba ku kwanta ba?â€
Mummy ta harareshi kafin tace. “Abinda yakamata da magidanci kenan ya dawo gidansa lokaci irin wannan Mu’azzam? Ina kake zuwa sabida Allah? To ba wani abu ya hanamu kwanciyar ba, jiranka muke mu yi sallamaâ€.
Mummy ta fada idanuwanta sun yi rau-rau suna son zubar da hawaye. Jikinsa a sanyaye ya ciro kafarsa daga steps din daya soma takawa ya dawo ya samu waje a gefenta ya zauna.
Maimakon ya bata amsar waccan tambayar sai ya jefa mata tambaya shima.
“Mummy an yi muku wani abu ne wanda ya bata muku rai?â€
Girgiza kai ta yi, “Ko daya Mu’azzam, kana kula da ci da sha na, suttura da lafiyata daidai karfinka. Ko da samun ka ya ragu ba ka gaza da ni ba ta kowanne fanni. Na sani ba ka son a zauna kusa da kai, amma ko a fuska ba ka taba nuna min hakan ba duk da na sani. Zan koma cikin iyaye da dangi, ina rokonka in na bata maka a tsayin zamanmu ka yafe miniâ€.
Ta kai gefen mayafinta tana share idon ta, “Ka rike Aalimah da mutunci da amana, don Allah Mu’azzam ko don alfarmar mahaifinta…â€.
Sauraron Mummy yake yi attentively har ta yi shiru. Kafin ya ce,
“Ni Mummy zamanki bai takura ni ba, ni da ba zaman gidan nake ba? Ku ci gaba da zamanku har Allah ya huci zuciyar Daddy ya maida ke dakinkiâ€.
Girgiza kai ta yi, “Gara in tafi Mu’az, ya dau zafi da yawa, tafiyar tawa ce kadai za ta sa ya sauko har yayi tunanin maida ni dakin nawa. Na dinga zuwa muku ziyara insha Allah lokaci zuwa lokaci. Kayi min alfarmar bazaka sake yin dare irin wannan a waje ba. Saduwar alkhairi don tashin asuba za mu yi. Je ka turo min Aalimahâ€.
Ya yi dan jimm! Kamar bai ji abin da ta ce ba. Tana da tabbacin ya ji din, duk da haka ta sake maimaitawa,
“Je ka turo min Aalimah mu yi sallamaâ€.
Kamar ya ce, “Ba ga Yesmin nan ba?â€
Ya tuna cewa, sallama yake yi da mahaifiyar tasa, gara ya yi mata duk abin da ta ke so su rabu lafiya, don haka ya mike ya nufi kafar benen cikin takunsa kamar na saraki. Zuciyarsa na tsukewa da wannan umarni na mahaifiyarsa, wanda babu yadda zai yi da shi ta ko’ina, domin kamar da gayya ta yi shi, don ta sa su ga juna shi da Aalimahr da yake gudarwa kwana da kwanaki.
Kayan barci ne a jikinta masu sulbi ruwan shanshanbale. Kanta cikin hular sanyi fara sol wadda ba ta rufe ko rabin gashin kanta ba. Ta hadashi ta nannade kamar gammo a tsakiyar kanta, ta rufe rabin jikinta da bargo mai tsananin laushi da santsi. Barci ta ke sadidan a lokacin da Mu’azzam ya murda kofar, bakinsa dauke da sallama kamar ta rowa. Ba ta amsa ba, don haka ya idasa shigowa dakin yana mai cije lebensa na kasa. Kamshin wani sassanyan turaren wuta dana mata ya bugi hancin sa. Saida ya tsaya ya shaqa sosai yayi ajiyar zuciya. Da alama mai nauyin barci ce, ya lura in zai kwana yana sallama ba za ta ji shi ba. Karasawa ya yi har gaban ta ya dan janye bargon kadan daga jikinta.
Maimakon ya tashe ta, sai ya tsaya kawai yana kallonta. Bai taba yi mata wani kyakkyawan kallo ba sai yau. Mace har mace, wadda ko cikin abzinawa sai an tona, mai tarin nutsuwa, kamala, kunya, kawaici da ilmi. Yana iya tuno kyakkyawar rayuwar da ta yi da mijinta abin kaunarsa Aboulkhair. Don me iyayensu suka yi wannan bahagon hadin?
Aalimah na matukar ganin girmansa, shi ma haka, yana bata respect har guda biyu; na kasancewarta matar kaninsa da yake matukar so, da kuma wanda halayenta ababen yabo suka sayo mata a idanunsa. Bai shirya wannan zubar da kimar ba (rayuwar aure da ita) daga nan har zuwa inda Allah ya nufa da rayuwar kowannensu.


Aalimah ta yi wani dan juyi cike da jin dadin barcinta jin sanyi na shigarta tun daga tafin kafa, sakamakon dan janye bargon da Mu’azzam yayi daga jikin ta. Jikinta ne ya ba ta akwai mutum tsaye a kanta. Da sauri ta bude ido, wadanda suka kada suka yi jajir sabida nauyin barci, sai suka rikide suka bada wani irin yanayi mai motsa zuciya, bata yi aune ba sai samun idanun ta tayi kane-kane cikin na Engnr. Mu’azzam Ishaq Raazee, wanda ke tsaye saitin kanta ya zuba mata ido. Da mugun sauri ta yayibi zanin gadon ta rufe jikinta gaba daya. Juyawa ya yi yana mai sakin tsaki ya bar dakin yana mai ce da ita da murya ciki-ciki,
“Ki zo Mummy na kiranki a kasaâ€.
Dakinsa ya karasa cikin takunsa na nutsuwa da kasaita, lokar jikin gadonsa ya bude. Lokacin shan maganin sa har ya wuce yana can yana yawo a titi duk don kar ya hadu da Aalimah, gashi ya tashi a banza tunda Mummy sai da ta san yadda tayi ta hada su. Magunguna ne ga su nan birjik! Wadanda aka rubuta mood stabilizers su ya cira ya dauko gorar ruwa cikin karamin firjin da ke gefen gadonsa, ya watsa su cikin bakinsa, ya bi su da ruwa. A hankali ya kwanta bisa gadonsa yana maida numfashi a sannu. Saukowar da bai kara yi ba kenan sai asubahin wayewar gari. Shi da kansa ya tuka Mummy zuwa airport bai hada ta da Harrison ba.
Har da Aalimah aka tafi kai Mummy airport, don haka a hanyarsu ta dawowa daga shi sai Aalimah cikin motar an rasa mai yin ko motsin kirki a tsakaninsu. Aalimah ko numfashi za ta fitar sai ta tabbatar ta sake shi a hankali, yadda ba zai zama takura ga Mu’azzam ba. Ta san halinsa sarai, ba yau ta sanshi ba.
Suna isowa gida ta bude motar a hankali ta fita, haka nan a hankali ta rufe ta silently. Ta juya cikin takun nutsuwa ta shige cikin gida, ko kofa za ta bude a hankali ta ke yi, don sanin cewa Mu’azzam ya biyo bayanta.


******
Tafiyar su Mummy sai ya mayarwa da Aalimah gidan kamar maqabarta. Har zuwa washegarin ranar bata kara sanya Mu’azzam a idanunta ba. Ko motsinsa bata ji ba duk da cewa dakunansu na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login