Showing 27001 words to 30000 words out of 126031 words

Chapter 10 - Aalimah Complete 1,2,3,4 Free Book by Takori .txt

haife shege. Zuciyarta ba ta taba kawo mata tunanin aure nan kusa ba.
Da wannan dalilin dama wasu da dama ya sanya tun safe ta ke yaki da zuciyarta a kan Aboulkhair duk da cewa dan uwanta ne, ta san ba zai cutar da ita ba. Amma ba a shaidar maza a wannan fannin, Mahmoud kadai zata iya shaida a cikin maza. Sannan shi da kansa (Aboulkhair ) ya tilastawa zuciyarta ta ji tsoronsa daga yadda yake behaving ga kannensa tun jiya. Sosai ta himmatu wajen yakice shi daga zuciyarta ta ke ta karatu tun safe. Sun yi lacca biyu suna da hutun awa daya kafin su koma wata, shi ne ta roki Alex ya yi highlighting dinta abin da ya shige mata duhu.
6/28/21, 7:32 AM - Buhainat: 07030137870






45


#####################################################


Mummy ta manta ba ita za ta kai Daddy aljannah ba, wannan buzuwar dai da ta raina wadda ba ta je makarantar boko ba, ko Abuja ba ta taba takawa ba, bayan danta ya share sama da shekaru ashirin da bakwai a kasar Amurka. Daidai da rana daya kuma hakan bai taba damunta ba, ba ta taba daga ido ta dubi wani abu da Ishaq ya mallaka ba. Wadanda ba su yi karatun bokon ba, Eedrissa da Oussama sun share mata hawaye, sun gama mata komai. Dole Kasisi ta ce me ake da boko?
Ita dai kam bai amfana ta da komai ba daga nata ‘ya’yan. Daya ya tsallake ‘boarder’ ya je ya kafa iyali a inda ba shi da kowa, saboda ya auri ‘yar Nigeria, sai shekara-shekara ta ke ganinsa. A hakan ma nashi da kyau shi, tunda mace ba ta hana shi kyautata ma iyayensa ba. Sannan yana matukar kokari wajen lika ‘ya’yansa jikin iyayensa da ‘yan uwansu. Dayan kuma tun da ya tsallake kasar da sunan aiki ya fidda kansa daga sahun ‘ya’yan da ta haifa, ya koma dan Zulaiha mijin Zulaiha. Kowa banza ne tunda bai yi rayuwa a America ba, har wadanda suka samar da kwan haihuwarsa a duniya.
Kuka Aboulkhair ya soma yi a hankali yana fidda shessheka, kukan tausayin mahaifinsa da yin Allah wadai da wannan hali da mahaifiyarsa ta rika a matsayin dabi’a. Wutar Allah yake hango masa karara. Yana kyautata zaton ko a waya Daddy ba ya kiran Inna Kasisi ya gaishe ta yadda ya kamata, kullum he is busy bautar iyalinsa da nemo musu kudi. Sau da yawa yana ganin mahaifinsa (Malam Raazee) yakira shi in ya ji shirunsa ya yi yawa, in suka gaisa sai ya ce,
“Na yi mafarkinka ne kai da takwara da Aboulkhairi, to nesa ba ta maganin kusa balle in ganku. Ina fatan dai lafiya ku ke?â€
Wadannan sune kalaman Kakansu duk sanda ya kira wayar Daddy, har ya haddace su. Sai ya kira shi sau goma bai kira shi sau uku ba. In ya ba su wayar kullum nasiha yake musu kan su ji tsoron Allah a duk inda suka samu kansu, su tsaida sallah, su bi iyayensu, su rike ZUMUNCI, in sun yi hakan za su shiga aljannah. Shi ma ya san halin ko’inkulan na Daddy ga iyaye da danginsa ya shafe shi, Mu’az ne kawai mai kula da lamarinsu duk da halin rashin lafiyar da yake ciki he’s doing well with Daddy’s parents and family. Rabin albashin Mu’az ya san inda yake kai su duk da Mu’az din bai so ya sani ba.
Kwantar da kai ya yi a kan cinyar Daddy ya yi ta kuka, gwiwoyinsa suna durkushe a kan carpet kansa a kan kafafun Daddy. Gani yake yanzu in ya zo neman auren Aalimah babu mai ba shi, tunda daga shi har Daddy halinsu daya. Shi ma Daddyn could not help yin kuka, kukan yake amma na hawaye ba mai sauti ba. Ya sanya hannunsa cikin sumar Abulkhair yana shafawa a hankali, yana mai tuno dukkan kura-kuransa yana yarda da su, tare da yin nadamarsu daya bayan daya.
Ko da halin Zulaiha a kan tabarbarewar zumuncinsa da kowa nasa da kokarin fin karfinsa da ta ke yi, most at times shi ma da sakacinsa. Ya yi mata riko irin na mijin bature da macen baturiya; wadanda ba su san kowa ba a rayuwa sai kansu da ‘ya’yansu.
“It’s ok Aboulkhair, stop crying like that, Allah zai gyara mana komai. Sannan yanzu na sa damba a rikon Aalimah sai inda karfina ya kare. Wannan sakona ne ga mahaifiyar ku ku gaya mata. Zan ci gaba da dakon igiyoyin aurenta saboda ta bani the most expensive gift of life. Wannan kuma ba komai ba ne sai ku din nan ku biyar. Duk abin da nake nema a ‘ya’ya na same shi daga gare ku. Kun zame min abokai a lokacin da ta raba ni da su. Kun zame min DANGI a lokacin da ta raba ni da su. You brought all the happiness that children brings to the parents. (Kun bani duk wani farin ciki da ‘ya’ya ke baiwa iyaye).
Amma yanzu ina ji a jikina akwai wani babban gibi da na rasa, duk wannan rayuwar farin cikin da nake tsammanin ina ciki, my life is incomplete. Ina jin wani wawakeken rami a wani gefen na zuciyata Abulkhairi. Bayan kowacce soyayyah dan Adam yana bukatarta fiye da soyayyar kowa. Wannan ba wata soyayya ba ce face ta UWA! I missed MOTHER’S LOVE which is like no other. I’m lucky she is alive (nayi kewar soyayyar Uwa, wadda babu kamarta, nayi sa’a tana raye) yau da ban san inda zan sanya kaina baâ€.
Aboulkhair ya share hawayensa, sannan ya kara dukar da kansa cikin cinyoyin Daddy, as if kansa zai kutsa cikin rigarsa ya shige cikinsa, shi kuma ya sake haifo shi.
“Daddy, ku ba ni auren Aalimah, I mean Aal… Daddy zai dinke komai. Zai faranta ran Inna Kasisi. Above all, I LOVE HER SO MUCH DADDY, I mean it, from the bottom of my heart…!â€.
Dariya Daddy ya kama yi, kafin ya ce,
“I knowâ€.
Da sauri ya dago ido yana yi wa Daddyn kallon mamaki, ya san dazu a office bai furta masa ba, sabida kunya yake ji, kuma ya san Daddy sai ya yi masa dariya, saboda ya sha cewa sai Mu’az ya haifi ‘ya’ya biyu zai yi aure. Sai ya zama cikakken medical doctor. He is now in year 4. Akwai kwararan shekaru biyu a gabansa kafin ya gama MBBS, sannan ya zo ya yi Specializing. Wannan na nufin; sai ya kwashe shekaru kusan hudu zuwa biyar kwarara nan gaba kafin ya mallaki Aalimah???
Ina ruwansa da auren Mu’az?Mutumin da aure baya cikin vocabulary dinsa. He can’t even develop emotion!Duk da lalurar da Allah ya jarrabce shi da ita, ya gwammace ya yi ta daureb kansa da kwayoyi, shi zai zauna ya yi ta jira ya yi aure ya haihu? Tunanin da yake ta yi kenan idonsa a kan mahaifinsa, wanda ke ta binsa da murmushin kauna kamar ya hadiye shi, saboda farin cikin da kalamansa suka jefa shi. Sun wanke duk wasu damuwoyi da suka lullube shi a ranar.
Wannan ne babban abin da zai yi ya gyara komai din, har Khaleesat da Basma ya yi musu nasu tanadin wanda ya san hakan ne kadai zai wanke dattinsa daga idanun ‘yan uwa da iyayensa, wanda ya yi shekaru ashirin da bakwai yana barbada musu a idanunsu.
“Kana mamakin ya aka yi na sani? Na sani tun daga lokacin da ka tasa ta a gaba sai ta cinye sakwara, bayan kai ne ka sa ta kasa ciâ€.
Zuru ya yi yana kallon Daddy, wato iyaye sun fi kowa karantar ‘ya’yansu.
“Amma Aboulkhairi…†Daddy ya ci gaba da magana, sannan ya dakata. Tattaro dukkan attention dinsa ya yi ya mika wa Daddyn, burinsa ya ce gobe zai nema masa auren AALIMAH.
Daddy ya ci gaba da magana, “Cire gaggawa daga cikin lamarin nan, domin ita gaggawa daga shaidan ta ke. A yanzu haka in na nema maka auren Aalimah da kyar za su ba ni. Musamman Yaya Oussama wanda shi ke ba da aure a family dinmu. I have wronged them so much. I’ve to cover my mistakes first, make-up my short comings, eradicate the inconveniences.(Na bata musu da yawa, dole in fara wanke kurakurai na tukunna, in wanke laifi na). Idan na je musu da nadama ta da kuma nema maka auren Aalimah concurrently (a lokaci guda) cewa za su yi abin da ya kawo ni kenan.
Don haka mu bi abin a hankali, mu fara gyara girgidadden zumuncin. Ina ji a jikina komai zai zama daidai ba da jimawa ba. But I want you to exercise patience, concentrate on your studies, make me proud with flying colours kamar dan uwanka. Shi ne babban abin da zai ba ni karfin gwiwar nema maka auren Aalimah. Amma yanzu ba ni da guts na yin hakan tunda baka da halin rike iyaliâ€.
Da sauri Aboulkhair ya dubi Babansa, damuwa kwance baro-baro a kan kyakkyawar fuskarsa, “Daddy, allowee dina ya ishe mu, ko aikin karfi zan hada da shi in ciyar da ita. Daddy don Allah…!â€
6/28/21, 7:32 AM - Buhainat: 07030137870




103








####################






Wani matsanancin tausayi irin na iyaye ga ‘ya’yansu ya kama Ishaq Razee. Ya san Aboulkhair fiye da kowa cikin ‘ya’yansa. Ya amince yana nufin kalamansa. Karatun likita kuma ba wasa ba, kada hidimar iyali ta dauke masa hankali, ya hana shi kuma rashin nutsuwa da soy ayyah su hana shi karatun. Gara ya kasa karatun a kan ya zama Mu’azzam, shi ga karatun, ga kwalayen masu karshen kima da daraja, ga kuma career mai matukar daraja, amma ba ya zancen auren. Nan da shekaru goma a gaba ma ba shi da niyya, shi kuma ba zai taba takura masa ya yi ba, uzurinsa ya kai uzuri, kwanciyar hankalinsa a hakan da yake rayuwa ya fi musu komai.
Idanunsa suka cicciko da kwalla, gab yake da ya zubar da hawaye sabida tausayin dan sa Mu’azzam.
Ga wannan mai lafiyar shi ma yana kokarin zame masa wani abin tausayin. Hannu biyu ya sa ya dago shi daga durkuson da ya yi a gabansa kamar mai neman gafara, nan kuwa Aalimah yake nema.
Zaunar da shi ya yi a barin jikinsa ya rike hannayensa, “Aboulkhairi, ni ta bangarena ba ni da matsala da zarar na dinke barakar da ke tsakanina da ‘yan uwana zan iya yi maka aure daga yanzu zuwa kowanne lokaci, in ciyar da kai, in ciyar da matarka, in suturta ku, in ba ku muhalli ku haifa min jikoki su ma in ciyar da su. In dauki nauyin kula da lafiyarku da karatunku har zuwa sanda za ku iya rike kanku. Matsalar daga iyayen Aalimah ne.
Sun dauki duk wani buri da suke da shi a kan babban dan su Aboubacar sun dora a kanta, they wanted her to be very well educated, kamar kakanta na wajen uwa Prof. Kashim.Mutuwarsa ta taba mahaifiyarta tun daga zuciya har kwakwalwa, she dropped her career and became a mental patient too, ta tsaya da burin danta Aboubacar ya zame mata magaji ga mahaifinta. Su biyu rak! Ya haifa,dan uwan nata Suraj yayi mata nisa.
Aboubacar ya ki yarda ya karanta pharmaceutical science, ainahin kwas din marigayi Prof. Kashim, sai mijinta ya shwarce ta da ta ba wa Aalimah damar da ta ke son bai wa Aboubacar. Yana so kada ta zama discouraged don ta haifi ‘ya’ya mata da yawa fiye da maza, yana so ta yarda mata ma ‘ya’ya ne kuma ta yi farin ciki da haihuwarsu.
Alhamdu lillah Aalimah ta fara kokari sosai a karatunta. Ka ga ya kamata yanzu in ce su cire ta daga makaranta su aura wa Dana? Shi kadai ya san yadda ya yi fafutukar da ya yi ya samo mata scholarship din nan babu ko sisina, ko kudin jirgi uwarta ta biya mata ba su karbi nawa ba. Hakan ya kamata Aboulkhair?â€
Da matukar sanyin jikin Aboulkhair ya girgiza kai, da zai iya, da zai so ya ce da Daddy “aurena ba zai hana burin iyayenta cika a kanta ba, zai zamo ne a step toward her achievements… zan zamo tsanin cikar burinta… zan taimaka mata ta duk hanyar da zan iya……â€. Maganar zuci yake bai san a fili yake yi ba. Saboda ya zama very infatuatedakanAalimah, ya kasa controlling emotions dinsa da damuwar zuciyarsa.
“Be strong my son, ina tabbatar maka za ka iya JIRA, musamman idan ba ka ganinta. I’m not against early marriage(bana kin auren wuri)sabida ni ma sanda mahaifina ya yi min na ji dadi, na tabbata ni dan gata ne, kuma iyaye irinshi kadan ne. Da kuma za’a samu yawaitar irinsa a duniya, da zina ta ragu a cikin al’ummah.
Mahaifiyarku ajinta biyar a sakandire na aure ta, yau ga ta da degree har da masters . So ni ta fannina na yarda aure da hidimar iyali ba sa hana goal attainment. Daga iyayenta ne, and their convenience. Ni ko gobe Mansour ya ba ka Aalimah zan biya sadaki. Amma na rokeka ka daga min kafa in gyara nawa ruguzajjen ginin tukunna. Kada ka dagula min al’amura. In kuma za ka yi min abin da na fi so shi neWAIT FOR HER!(Ka jira ta). Jikina yana ba ni matarka ce, kuma uwar ‘ya’yankaâ€.


Wani numfashi Aboulkhair ya zuka ya kuma dawo da shi da sauri. Dariya ta kama Daddy, amma ya gintse. Yana mamakin wane irin so ne haka ya kama Aboulkhairinsa cikin kwana daya rak? Tarihi ne ke maimaita kansa. Ya sani duk ‘ya’yansa maza shi suke gadowa a halayya dabi’a. Shi ma haka ce ta faru da shi a kan mahaifiyarsu the very first time he saw her, bai kuma nutsu ba sai da ya aure ta. Baya fatan hakan ta faru da Aboulkhair, tunda ba shi da ikon ba shi Aalimah a yanzu, rashin nutsuwarsa kuma daidai yake da tabarbarewar karatunsa, wanda ba ya fata…
“Would you keep encouraging me to wait? (zaka cigaba da karfafa min gwiwa wajen jiran?â€) Ya tambayi baban kamar zai yi kuka. Abin nasa har da shagwaba-shagwaba.
Gyada kai Daddy ya yi yana masa murmushin bada karfin gwiwa da son karfafa gwiwa.
“Yes, I will keep encouragingâ€.
“Would it take long?â€
Aboulkhair ya kara tambaya.
“No, five years is like a blink of an eye (kamar kiftawar ido shekaru hudun suke). Especially when a person makes himself busy with studies. Make frequent phone calls when he is far, but he should make sure the phone calls doesn’t distract or affect his study times, once in a day or twice in a week. And it shouldn’t contain deep emotional talks that would inturn arouse his fantasies. It ought to stick on “how are you†and “how is studies?â€
Dariya Aboulkhair ya shiga kyalkyalawa kamar babu gobe. Shi kansa Daddyn dariya yake yi, zukatansu suka yi dadi tamkar babu sauran damuwa a cikinsu.


Yana komawa dakinsa ya rufe kofa ya dauki wayarsa da niyyar ya kira Yayansa, amma sai ya duba lokaci, lokacin shan magungunan Mu’az ne yanzu, yana sha kuma zai yi bacci. Kamar ya kyale shi, amma sai ya ga ba zai iya ba, ya kamata yasan komai da ke faruwa tsakanin Mummy da Daddy daga bangaren kowannensu don yayi sulhu. Ya manta da situation din Mu’az da tunanin zai shiga lokacin barcin sa ya danna masa kira. Sai da ta kusa katsewa kafin ya daga.


“I’ve been expecting your call since yesterday, where have you been?†(nayi ta tsammanin kiranka tun jiya, ina ka shiga?â€


A cikin muryar akwai maturity, akwai nutsuwa da haiba, akwai gentleness, akwai kwarjini da kamala, akwai wani abu wai shi ‘class’ da sanin ciwon kai. Sannan it is so caring as well as affectionate ga wanda ake magana da shi. Shi ma wanda ya yi kiran respect ne da affection zallah a tashi muryar. Ya tattaro dukkan nutsuwarsa ya daidaita tone din muryarsa yadda ba zai zama boring ga mai saurare ba, sannan ya zauna a gefen gadonsa ya yi wa wayar rikon aminci, yadda ba za ta zame ba.
“Is Mummy beside you? Mummy na kusa da kai?â€
“No, ta shiga barci tun dazu. Ni ma I’m about to take medicines(gab nake da shan maganina) in kwanta, wani aiki ne ya dan tsare ni da ba za ka same ni ido biyu baâ€.
“Kayi hakuri da rashin kiranka tunda na iso, bana cikin nutsuwa, I metatedious threshold inthe house…†Ya warware masa komai; tun daga farko har karshe da nasa observation din na halin Momy tun suna kanana. Da irin kukan da suka yi dazu shi da mahaifinsu. Amma bai gaya masa he is in love da Aalimah ba, komai da lokacinsa.
Shiru Mu’azzam din ya yi, kamar ruwa ya cinye shi. He didn’t cry. Ba abu kankani ke sa Mu’azzam kuka ba, sannan ba ya jan magana da nisa, his words are specified, he is very selective and picky before he utter a word. Amma duk sanda ya furta magana zata kasance ta kunshi ma’anoni masu yawa a dunkule. Aboulkhair ya yi zaton sam ba zai yi magana ba har sai shi din ya gaji ya ajiye wayar, bai damu ba, sabida ya san dan uwansa fiyeda kowa a duniya. Ya san bynowzuwa yanzu ya gama tunanin yadda zai shawo kan matsalar iyayen nasu gaba daya cikin dan wannan lokacin da ya dauka shiru.
Daga baya Mu’azzam din ya kira shi.
“This is totally opposite with what she told me…â€. (Abinda ka fadamin kwatakwata bai yi dai-dai da wanda ta fada min ba). Mu’azzam ya fada cike da tausayin mahaifinsa.
Suka yi maganganu na maza masu hankali na dan gajeran lokaci, kafin Mu’azzam ya ce,
“Is the girl still in the house? (Har yanzu yarinyar na gidan?)â€
“Yes, she is, the nicest sister I ever met (eh tana nan, ‘yar uwa mafi dadin mu’amala dana taba haduwa da ita a rayuwaâ€.


“Greet her for meâ€.
(Ka gaishe min da ita)


“Za ta ji insha Allahâ€.
“As for Mummy (Game da Mummy, ofishin su sun kirata jiya, kyale ta kada ka kirata don ka rarrasheta, da kanta zaka ga ta dawo. Ka yi kokari ka gina kyakkyawar mu’amala a tsakaninta da yarinyar kafin ka koma makaranta. Ka nunawa yarinyar yadda zata yi hakuri da ita.Sukuma ka rabu da su za su shirya kansu a junansuâ€. (Yana nufin ita da Daddy)
Da haka suka yi sallama.


******
ABOULKHAIR DA WAYAR AALIMAH!
Sai da ya gama komai da ya saba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login