Showing 66001 words to 69000 words out of 72718 words
Chapter 23 - RABO AJALI COMPLETE DOCUMENT BY Aisha Ya'u kura.txt
samun saukin Affan,
chummy ta kalli oyizah cikin mamaki tace ya akayi haka ta faru,
oyizah tace nima ban sani ba, komai na kayan aikina an kwasheshi a karkashin gado babu komai a gurin sai kasa,
sai kuma kwalbar nan da yan iskan yarannan suka fasa nasan shiyasa zeenatu ta farfaďo,
chummy tace na sakeyin wacce tafi tada karfi kin ganta can,
oyizah cikin mamaki tace to ya akayi haka,
chummy tace ni nafi mamakin na dakinki da wanda kika birne a bakin damo,
oyizah tayi saurin ďago kanta tace nasan wanda zaiyi min wannan aikin,
wannan yar iskar yarinyar ce zatayi min, wallahi I will not spare her,
yanzun nan zanje asibitin da take in kasheta,
chummy tayi murmushi tace daďina dake garaje,
bakya tunani kafin kiyi abu,
waye ya faďa miki suma yanzu zasu zauna,
, ai sun riga sun san sirrinmu so sai munyi da gaske ta karkashin kasa musa ki koma gidanki sai ki aiwatar da ayyukanki cikin kwanciyar hankali,
oyizah ta gyada kanta tace wallhi wannan karan mai zafin zanyi duk saina kashesu in mallake alhj da dukiyarshi muyi zaman mu tare har karshen rayuwarmu,,,
chummy tace yauwa ashe kin gane,
yau da daddare zamu fara aikin, kinsan akwai ďan tsoho da kika kawo to dashi za'ayi miki aikin, yanzu tashi muje gurin Dodo BELAH mu dawo kafin lokacin meeting yayi,
oyizah ta mike zuciyarta wasai dan a tunaninta komai nata zai koma normal tunda CHUMMY tayi assuring dinta,,,
oyizah sarkin sa'a........
Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Kwance take kan kirjinshi ta cukwikwiyeshi tana kuka mai ban tausayi tana faďin
"meyasa ka tafi ka barni na tsawon lokaci, meyasa baka daukeni mun tafi tare ba ka barni cikin wannan wahalalliyar duniyar mai cike da azzalumai marasa tsoron Allah,
ta tsunguna a kasa kukanta ya tsananta tace dan Allah yaya jabeer karka sake tafiya ka barni,
ba karamin wahala nake sha ba saboda rashinka,
I grew up in your arms plss led me die in it, plsssss,
ďagota yayi suna kallon cikin idon juna taga wani haske mai matukar kyau a cikin kwayar idonshi,
a hankali taji yana faďin tafiyata bazata taba zama wahala agareki ba,
naso kasancewa tare dake amma Allahn da ya hallicemu bai halicceki dan ni ba shiyasa ya ďaukeni domin ki kusanta da wanda yake makusanci na hakika a gareki,
dama ni ba mazauni bane zuwa nayi in nuna kamannina in koma ga ubangijin talikai,
tabbas nasan lokacin da nake da rai baki da wata matsalar rayuwa, yanzu kuwa nasan ko baki gama sanin meye rayuwa ba kinsan kadan daga ciki,
mu'imuni ako da yaushe Allah na jarabtarshi ta kowane bangare, duk wanda ya kansance cikin farin ciki a kullum to tabbas ya binciki kanshi domin duniya kurkukun mu'imuni ce sannan aljannar kafiri,
kafiri marar tsoron Allah, ko wanda ke sabawa Allah shi kaďai ne ke samun farin ciki marar yankewa a duniya,
akwai lokacin da zamu shiga farin ciki amma cikin lokaci kalilan sai bakin ciki ya maye gurbin wannan farin cikin,
to ki sani duk musulmin dake yawan shiga cikin jarabawar Allah lallai ba karamar soyayya bace tsakanin wannan bawan da Allahn shi, domin shiga kunci ga musulmi kankarar zunubi ne,
wasu kuma zaki ga basu da wata damuwa komin zunuban da sukeyi ba shi zai hana Allah ya barsu cikin farin ciki ba, sannan kome suka nema suna samunshi kamar su suka tsara rayuwarsu, to wadannan Allah ya barsu da kansu ne har sai sun tuba,
kullum mu'imunin kwarai yana cikin jarabawar ubangiji masu tsananin rabo su ke cinye jarabawar dari bisa ďari,
ya share mata hawayen idonta yace zanso Afeeyata ta zama daga cikin masu cinye jarabawar ubangiji a koda yaushe,
zanso ki daina yawan zubar min da hawaye domin hawayen basu kara komai sai wahalarwa ga kyakyawan idanuwanki,
zanso ki manta batun soyayyata a matsayin wanda zai aureki ki sanya soyayyar yaya a zuciyarki domin samun tsaftattaciyar addu'a daga gareki,
ki kular min da Affan kamar yadda zaki kula dani domin ni da shi bamu da wata maraba kuma nasan zai kula dake kuma ya kaunace fiye da yadda ni nayi, ki yawaita istigfari domin istigfari yana kusanta bawa da ubangijinshi kuma mai yawan yinshi zai kasance kullum cikin nutsuwa da walwala,
cikin sheshshekar kuka Afeeyah ta buďe baki zatayi magana jabeer ya sa hannu ya rufe bakin yace karki ce min komai ga Affan can yana jiranki zaku tafi gida, nagode sosai da ziyara,
cikin kuka ta cire hannunshi a bakinta tace dan Allah yaya jabeer ka tsaya kaji abinda zan faďa maka,
girgiza kanshi yayi yana mata murmushi hasken hakoranshi suka rufe idonta ta durkushe a gurin tana kallonshi cikin hasken tana kuka sosai tana kiran sunanshi,
wata sassanyar iska ta shiga kaďawa a gurin har hasken jabeer ya bace ma ganinta,
runtse idonta tayi tana kuka sosai tana faďin dan Allah karka tafi ka barni,
Hannu taji cikin nata ana murzawa a hankali sannan taji saukar ruwa a kan hannun,
a hankali ta fara buďe idonta da yayi mata nauyi sosai ta saukesu kan Affan dake zaune kusa da ita kanshi a kan hannunta yana zubar da hawaye,
lumshe idonta tayi hawaye na zuba ta gefensu ta fara tuno mafarkin da tayi akan jabeer,
meyasa ya tafi bai tsaya yaji abinda zance mishi ba, meyasa be bari nasan abinda zan faďa mishi ba,
shikenan bazan kara ganinshi ba har in koma ga Allah,
to ni yaushe zan mutu, wayyo Ya Allah ka dauk---- Affan yayi saurin toshe mata baki da hannunshi yasa hannu yana share mata hawayen dake gangarowa daga cikin idonta,
buďe idonta tayi ta kalleshi tasa hannu ta ďan ture hannunshi cikin muryar kuka tace kukan me kakeyi,
da mamakinta sai taji ya kwanto jikinta yace kukan abin da kikeyi,
a hankali tace ai bakasan kukan da nakeyi ba,
ya ďago jajayen idanuwanshi yace nasan har duniya ta naďe bazaki taba yin kukan komai ba in ba na rashin jabeer ba,
cikin mamaki ta kureshi da ido hawaye ya kara zirarowa a cikinsu cikin rawar murya tace kasa--- ya fashe da kuka yace nasani Afeeyah, nasani,
nasan jabeer ya tafi ya barni,
nasan bazan sake ganin fuskarshi mai dauke da murmushi a kullum ba,,
nasan bazamu sake haďuwa mu rungume juna mu faďa ma juna damuwarmu ba,
bansan me yasa mutuwa ta zabi jabeer ta barni, bansani ba Afeeyah,
ya karasa fadi yana kuka kamar karamin yaro,,
kuka suka dinga yi babu mai rarrashin wani a cikinsu,
saida sukayi mai isarsu sannan Affan ya ďago ya kalleta murya a dashe yace nagode, nagode da abin da kikayi min,
kau da kanta tayi tace ka gode ma Allah da kaka liman,
ya juyo da fuskarta yana kallon rinannun idanuwanta yace kullum cikin gode musu nake,
godiyarki ta daban ce Afeeyah, babu wanda zai dauki kasadar da kika ďauka a duniyar mu ta yanzu,
kinyi mana abin da ko dan uwa na jini bazai iya yi mana shi ba, bamu da wata kalmar da zamuyi amfani da ita gurin gode miki, Afeeyah tace karka gode min na cika kudirin jabeer ne, wannan shine burinshi na karshe, saboda wannan kudirin aka kashe min shi,,,
Affan yace nasan komai Afeeyah kuma in shaa Allahu wacce ta kasheshi ba anan duniya ba ma har a lahirah bazata taba samun kwanciyar hankali ba,
Afeeyah tace tun a duniya nakeson Allah ya wulakanta min ita, wallhi da nasan ita ce silar mutuwarshi na rantse da bazan kyaleta ba da nayi mata abun da zata gwammaci mutuwa da rayuwa,
Affan ya share mata hawaye yace ki kwantar da hankalinki nasan yanzu duk inda take a cikin bala'i take,
Afeeyah ta girgiza kanta tace da hannuna nakeson in kasheta kuma yau dinnan,
Affan yace hmm nima naso hakan tun ranar da na dawo cikin hayyacina,
nan ya bata labarin komai harda dawowar umma da bacewar oyizah,,,,,
cikin mamaki Afeeyah tace zatayi abinda yafi haka muguwa azzaluma, Allah ya isa tsakanina da ita,
in shaa Allahu sai tayi mutuwar kask---Affan ya katseta da sauri yace wannan adduar bata kamace ki ba, Allah yasan yadda zai tafiyar da irinsu ki zuba ido ki jira lokaci,
Afeeyah tayi shuru tana kallonshi kamar ba shi bane tababben bawan da baya taba maganar da zaka iya fahimta a da,
Allah mai iko......
Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Daren ranar suna zaune gurin meeting bayan sun dawo daga gurin dodon tsafinsu,
gaba dayansu suna sanye da jajayen kayansu da suke amfani dashi,
bayan sun gama tsaface tsafacensu sai chummy ta mike taje ta shigo da ďan tsoho,
a tsakiya suka sashi kamar yadda suka saba,
kewayeshi ta farayi tana yan sirkullenta a kanshi sannan ta zauna,
ďaya bayan ďaya tsohon yake bin mutanen gurin da kallo,
yana zuwa kan oyizah ya tsayar da idonshi kyarr a kanta baya ko kiftawa,
kureshi itama tayi da ido cikin rashin tsoro ta daka mishi tsawa tace daina kallona, idon wannan tsohon ko rawa baya yi ya fara motsa bakinshi da babu hakori ko ďaya a ciki,
oyizah ta kalli chummy tace my lord plss mu gama da tsohon nan mu cigaba da abinda ke gaban mu,
chummy bata kalli oyizah ba ta cigaba da haďe haďenta na tsafi cikin wani katon koko,
mikewa tayi ta iso gaban tsohon ta ja hannunshi da karfi har yana bigewa ta jona mishi wani abu mai tsini kamar kibiya a jijiyar hannunshi tana kallon cikin kokon,
a firgice ta juyo tana kallonshi ta kuma maida idonta cikin kokon dan gasgata abin da ta gani a ciki,
da sauri ta saki karfen taja baya saboda yadda ya dauki zafi kamar tana rike da garwashi,
wata irin dariya tsohon nan ya saki yace jinin nawa ya isheki haka, in kina bukatar kari kizo ki diba san ranki dan ko zaki dibi cikin tanki bazai kare ba,
su oyizah duk suka marmatso suka leka cikin kokon,
a gigice suka ja baya saboda ganin wani bakin ruwa mai kaurin gaske a ciki,
oyizah murya na rawa tace my lord kiyi wani abu plss wannan kamar ba mutum bane,
cikin su esther da alhj sambo ya ďuri ruwa suka ce kwarai wannan ba mutum bane,
cikin dakewa chummy tace ko ma waye shi tunda yazo nan bazai taba fita ba,
ta dauko wata sanda mai mugun kyalli ta nufi wannan tsohon dashi,
tana karasowa gaban shi ta ďaga wannan sandar ta saita cikin idonshi ta turata ciki, ga mamakinta sai ganin sandar tayi ta rabe gida biyu, daya a cikin idonshi ďaya a hannunta,
sa hannunshi yayi ya zaro sandar yana dariya ya mika mata yace haďata guri ďaya,
a harzuke ta yar da sandar hannunta ta koma ta shirya kanta sosai tace yau ko waye tsohon nan sai na gama dashi,
ta bayanshi ta bullo ta sa farcen hannunta ta shako wuyanshi ta baya, da azama ya juyo ya sanya nashi faratan a makogoranta,
wani irin kakari ta farayi tasa kafarta ta haureshi yayi baya, nan suka fara b'ace b'ace suna faďa sosai,
ba karamin wahala chummy take sha ba amma saboda tsabar ta dahu da tsafi kuma bata so mabiyanta suga gazawarta haka ta jajirce suka cigaba,
wani lungu ta shiga a cikin ďakin ta fito rike da wani magani ta bace tana kokarin watsa ma wannan tsohon,
sam bata san yana kallonta ba ta ďaga wannan maganin zata zirara mishi yayi saurin juyar da hannunta ya zuba wannan ruwan a tsakiyar kanta,
wani irin ihu ta saki ta faďi kasa tana ta shure shure nan take kanta ya fara zagwanyewa, tun tana ihu mai karfi har ta koma yi a hankali gaba ďaya mummunar halittarta ta canza kama,,
a gigice su oyizah suka fara ja baya hankalinsu a tashe babu wanda a cikinsu yayi kokarin zuwa gurin wacce suke kira mai taimakonsu, itama yau gashi ta kasa taimakon kanta,
mikewa wannan tsohon yayi yana kallon su oyizah,
mai da hankalinshi yayi gurin alhj sambo yace alhj sambo Bana, minister mai fuska biyu,
a fili fuskar kamala a zuci ta zalunci,
ina son kayi ma kanka hisabi ka zabi hukunci cikin jerin abinda zan lissafo,
na farko ko in kasheka anan in kaika gida da kayan jikinka, ko kuma in barka ka koma gida ka fito media ka faďi ko me kakeyi sannan ka fadi adadin mutanen da ka bayar akasha jininsu,
alhj sambo cikin rudewa yace kayi min rai dan Allah,
dan tsoho yace Allah shi ke da rai bani ba,
alhj sambo yace ka rufamin asiri wallhy na tuba,
har abada bazan kara aikata irin wannan aikin ba,
dan tsoho yayi dariya yace zunubin da kayi baya kuma fa,
kayi kisan kai, shirka, da sauransu duk dan ka samu mulki,
haka nake so kaje gidan talabijin ka sanar musu da halinka,
alhj sambo ya girgiza kanshi yace mutunci na zai zube,
dan tsoho yace ai gara ya zube a duniya, alhj sambo yace dan Allah ka kasheni anan kawai gara suga gawata,
dan tsoho ya girgiza kanshi yace a'a bazan yi kisa ba gara a hukunta ka kafin kaje ka tarar da na ubangiji,
kuka sosai alhj sambo yakeyi yana mishi magiya akan ya kasheshi ya huta amma tsoho yayi kememe yaki,
alhj sambo da yaga babu sarki sai Allah sai ya amince da abinda tsoho yace mishi ya kimtsa ya bace yayi gida hankalinshi a tashe,
kallon sauran yan gurin tsoho yayi ya dinga neman wacce tayi silar zuwanshi gurin bai ganta ba, girgiza kanshi yayi yace in kere na yawo,,,
sannan ya kalli su esther da suka tsure yace kuje Allah yasan yadda zaiyi daku itama waccan ogar taku banyi niyyar yi mata komai ba saida tazo cutar dani,
yana kaiwa nan ya bace,,
da sauri su esther sukayo kan chummy da ake iya hangen komai na tsakiyar kanta,
dagota sukayi suka ga komai na kanta na zuba a kasa,
a firgice suka saketa suka fara tattara kayansu,
wata a cikinsu mai suna HADASIYYA ta kalli kujerar tsafin chummy, muguwar zuciyarta ta sak'a mata ya kamata ta gaji kujerar itama ta zama 1 daga cikin matsafan da ake ji dasu ta samu mabiya tayi mulkinta san ranta,
murmushi tayi ta ajiye kayan hannunta tayi gurin kujerar,
tun kafin ta karasa karnikan gurin da eagles suka dinga kuka irin nasu na dabbobi,
tana taka step din gurin esther tasa ihu tace Hadiscos karki zauna,
nan hankalin sauran yakai kanta suka haďa baki suka dinga rokonta akan kar ta zauna taxo su gudu,
inaa wanda yayi nisa baya jin kira domin dai hadasiyya gani take bakin ciki suke mata dan karta fisu matsayi,
tana daura mazauninta akayi sama da ita,
wani irin girgiza ďakin ya farayi yana cilli da duk wanda yake cikinshi,
saida ya gama cillar dasu sannan ginin ya ruso gaba dayanshi kan ragowar chummy, "hmmm duniyar chummy ta kare"
saura oyizah ko ina ta shiga....
Sauki sosai ya samu a gurin Afeeyah har an sallameta ta dawo gida,
tana matukar samun kula gurin zeenatu da Affan duk da ba wani sabo sosai tayi dashi ba,
gyara sosai alhj basheer yasa ayi a gidan da saukar alqurani saboda shi har a lokacin a tsorace yake dan yasan indai safiya na raye to bazata taba barinsu ba,
farida ma ta nutsu sosai dan islamiyya ta koma ta zama saliha gwanin ban sha'awa, tsakaninta da zeenatu ba raini sai matukar girmamawa,
haka suna girmama junansu ita da Afeeyah....
3mnts later
Alhj Bara'u ne tsaye a ďakin jabeer yana duba wasu takardun Asiyah da jabeer din ya amso mata ana sauran sati biyu ya rasu,
cikin drawer ya bude ya gama bincikosu ya gansu can kasan kayanshi,
har zai rufe drawer sai yaga wasu takaddu a tsaftace cikin file dinsu,
dariya yayi yace jabeer kenan sarkin ajiyar takardu,
daukosu yayi ya rufe drawer ya budesu yana binsu da kallo,
cikin mamaki yace wannan ai takardun kadororin alhj basheer ne,
fitowa yayi daga dakin ya rufo kofar ya kaima Abida takardun Asiyah sannan ya wuce gidan Alhj basheer....
Mrs tijjani shattima.......
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 65 By Aysha Ya'u Kurah
A parlor suka zauna sai da suka gama gaisawa sannan Alhj bara'u yace wasu takardu na gani a dakin marigayi kuma da sunanka a jiki,
alhj basheer yace takardu kuma,
alhj bara'u ya mika mishi yace kwarai kuwa,
alhj basheer ya amsa ya duba su cikin mamaki yace ikon Allah,
wadannan takardun sune silar shigan iyalina cikin tashin hankalin nan alhj bara'u,
nan ya bashi labarin kyautar da yayi ma Affan, ya daura da cewa ashe jabeer ya bawa ajiyarsu,
tabbas nasan safiya tayi neman takardunnan bata gansu ba,
kai gaskiya nagode alhj ubangiji Allah ya jikan jabeer ya kai rahama kabarinshi,
alhj bara'u yace Ameen,
nan suka cigaba da hirarsu hankali kwance,,,,,
Fitowa tayi daga inda take makale kullum a cikin gidan bayan ta gama jin hirar alhj basheer da alhj bara'u,, tunda ta gudu daga gurin tsafin su kullum a gidan take yini a makale bacci ne kadai ke mayar da ita wani kurgugun daji inda take hada kulle kullenta,
dariya tayi sannan ta shiga parlourn ta dauki takardun tayi kissing dinsu tace me ya rage min tunda na samu wannan,
bari kawai in tafi inje in fantama hankali kwance,
a hankali ta fito daga parlorn ta make jikin window tana jiran alhj ya shigo ta fita,
tana tsaye a gurin ta hango Afeeyah da cikinta dan wata hudu da kwanaki har ya fito sosai kamar dan wata bakwai, Affan na tsaye kusa da ita ya daura hannunshi kan cikin yana mata magana kasa2 suna dariya,
wani bakin ciki ne ya turnuke oyizah saboda tuno cewar Afeeyah ce silar fitarta daga gidannan,
itace silar rushewar komai na farin cikinta,
kwafa tayi cikin bacin rai tace wallhy bazan bar yarinyar nan ta dawwama cikin farin ciki ba,
dole in dawo da shirina gobe in tarwatsa rayuwarta kafin in bar kasar nan gaba daya....
Washe gari tun takwas na safe ta gama