Showing 27001 words to 30000 words out of 72718 words

Chapter 10 - RABO AJALI COMPLETE DOCUMENT BY Aisha Ya'u kura.txt

16 Dec 2024

2283

dan adam wanda Allah ya ara ma lokacin tsafi ko wani abu to ba abun tsoro bane dan idan Allah ya tashi tarwatsasuu a lokaci daya zaiyi ba tare da bata lokaci ba...


Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣8⃣ By Aysha Ya'u Kurah


Sati ďaya ya rage bikinsu,
lokacin yayi daidai da kammala jarabawar su Afee,
Fitowarsu kenan daga exam hall ita da safnah kowannensu sai share zufa yakeyi, skul mosque suka wuce sukayi sallah suka zauna bin inuwar gurin saboda gajiya, hira sukeyi duk akan jarabawar da suka zana yau kuma ta karshe,
sai da suka fi minti talatin sannan suka mike da niyyar tafiya gida,
a dai2 gate din fita makaranta suka tsaya ganin anyi cincirundo kan wani yaro ďan ss2, Afeeyah tayi tsaki tace dadina da skool dinnan son gulma dan Allah ji yadda aka wani zagaye yaron can kowa so yakeyi yaji abinda ya sameshi, safnah tace may be abin da ya sameshi babba ne dan kuka yakeyi sosai gunin ban tausayi,
Afeeyah tace to Allah ya kyauta muje ko, safna tace ga "Zulaikha Sambo" can tahowa bari tazo muji me ya faru,
Afeeya tayi tsaki tace dan Allah safnah mu tafi wato kema kin fara son jin abinda bai shafeki ba ko,
kafin safnah tayi magana zulaikha ta karaso gurin su, safnah tace Zully me ke faruwa a can gurin, zully tayi fuskar tausayi tace wallhy mahaifiyar waccan yaron ce ta rasu yanzu aka zo aka faďa mishi, safnah tace ayyah Allah ya jikanta mutuwar mahaifiya ay babbar cuta ce tanada zafi sosai walhy,
Afeeya da jikinta yayi sanyi tace Allah ya rahamsheta mu kuma yasa mu cika da imani, suka amsa da ameen,
safnah tace ay mune abin tausayi Afee, gara ke tun kina karama kika rasa taki yanzu zaiyi wuya wata mutuwa ta girgiza ki,
zully tace kwarai kuwa,,
Afeeyah tayi murmushi tace har gobe ina tunawa da mamana duk da bawani daďewa mukayi tare da ita ba, wallhy kullum na kalli hotonta sai na zubar da hawaye,
mutumin dake debe min kewar tunaninta tun ina karama shine wanda bana fatar rasa shi har karshen rayuwata,
ta kalli safnah tace kikace babu mutuwar da zata girgiza ni, to wallhy kinji na rantse da Allah bana fatan mutuwa akan yaya Jabeer amma ni nasan duk ranar da aka ce min ya mutu to nima binshi zanyi in kuwa lokacina baiyi ba to walhy ko in haukace ko in zama marar amfani,
dariya suka saka sosai safnah tace ay ke baki da hankali,
da in mutum na mutuwa ana binshi kuma Allah baya sa dangana da duk wadanda suka rasa makusantansu suma sun dade da mutuwa,


Afeeyah tayi tsaki tace dan Allah ya isa haka maganar mutuwar Allah yasa mu cika da imani,
suka amsa da ameen sannan suka wuce zuciyar Afeeyah a dagule dan ta tsani zancen mutuwa...


Ranar haka Afeeyah ta wuni sukuku,
wasu irin muggan tunanin mutuwa takeyi, da taga abin bazai fishsheta ba sai ta ďauki qur'ani ta fara karantawa,
a haka jabeer ya tadda ita,
gaisheshi tayi haďe da ajiye alqur'anin a mazauninshi,
kusa dashi ta dawo ta zauna ta zuba mishi ruwan da hajja ta ajiye mishi ta mika mishi tana kallonshi, kallonta yayi shima da ya karbi ruwan yace yau naga duk kin wani natsu ne ko wani ne ya taba min ke,
ta gyada mishi kai,
ya ajiye ruwan hannunshi yace to menene, ko kina son wani abu ne,
ta kara girgiza kanta,
ya bata rai sosai yace akwai damuwa a fuskar nan kinada wanda zaki faďawa da ya wuce ni,
tace um um,
yace to fada min da sauri kinji, idonta ya ciko da kwalla muryarta na rawa tace ba komai,
hajja tace iskanci ne kawai fa da shagwabar banza yau ko abinci bata ci ba saboda abin ya motsa,
jabeer yace dan Allah hajja kiyi shuru karki kara bata min ranta, tashi muje waje ki faďa min kinji,
ta mike jiki a sanyaye suka fita,
a zaure suka tsaya ya kalleta yace ki mayar da kukan nan kar ki bari ya zubo, in naji abinda ke damunki ya cancanci kuka sai in tayaki muyi tare kinji,
ta gyada kai har lokacin kwallah na makale a cikin idonta, yace to inajinki waye ya taba min ke,
ta shagwabe fuska tace ni ba abinda ke damuna kawai dai ina tunanin mutuwa ne,
ta shige jikinshi sosai tace yaya jabeer ay bazaka mutu ka barni ba ko,
ya sa hannunshi ya kankameta hade da lumshe idonshi yace mutuwa lokaci ne Afee babu wanda yasan ranar mutuwarshi,
ta dago kanta tace ni nasan lokacina yaya jabeer,
jabeer ya tallabi fuskarta yace wace irin magana kikeyi,
tace ni nasan duk ranar da ka mutu to nima zan mutu,
yace to ke waye yace miki zan mutu, tace ba kowa ina dai fada maka ne,
yayi dariya sosai yace to naji,
ta marairaice tace dan Allah yaya jabeer karka mutu kabarni kai kadai nake dashi a duk duniyar nan,
kai kadai kake understanding dina, kuma kai kadai kake tolerating dina, kai kake sani dariya kuma ka hanani kuka,
dan Allah ka dinga yi mana adduar in mutuwa tazo ta daukemu lokaci ďaya kaji,
yayi murmushi ya share kwallar da ta zubo daga idonta a zuciyarshi yace yaro yaro ne, ya kalleta yace naji amma ki daina kawo mana maganar mutuwa ke da zaki zama amaryata ranar Saturday,
kar in kara ganin hawayen nan kinji, tace too,
yace yauwa babynah, kin san meye, ta girgiza kai tace a'a,
yace banaso in faďa miki sai kin min alkawari,
tace alkawarin me, yace alkawarin bazaki yi kuka ba, kuma bazaki damu ba, kuma zaki min addu'a,
tace umm nayi alkawari Allah ya bani ikon cikawa,
yace ameen baby,
ina zanje daura gobe amma fa gobe zan dawo in shaa Allah,
Afeeyah ta karkatar da kanta gefe tace ni um umm wayau kamin wallahi na kwance alkawarin,
yayi dariya sosai yace ba'a kwance alkawari yarinya, dan Allah kimin hakuri gobe kawai akwai abinda zanyi mai muhimmaci, kuka ta fara yi tana bubbuga kafa tace wallhy ni bazan yadda ba saidai mu tafi tare, ya rike baki yace ina zamu tafi tare, tace daura mana,
yace haba Afee nah yanzu kinaso in ďaukeki mu tafi gurin su kaka liman tare, ay sai suce amaryar ma bata da kunya,
ta turo baki tace naji ay sau ďaya zasu ce, ya daura hancinshi kan nata yana gogawa a hankali yace haka zasu dinga faďa kullum,
jikin Afeeya ya mutu sosai saboda yadda yakeyi da hancinshi kan fuskarta, ta kalli idonshi dake lumshe ta fara kokarin kauda fuskarta,
hanata yayi ta hanyar daura bakinshi kan nata a hankali yace I love uu to d moon nd bck baby,
ta sunkuyar da kanta kasa tace I love u too yayana,
yace to tunda u love me ki barni inje I promise you komin dare in na shigo gari zanzo in ganki kinji,
ta kalli cikin idonshi tace ko biyu na dare ne fa zan jira ka,
yace na yarda baby kiyi fatan Allah ya kaini lafiya,
tace to Allah ya kaimun kai lafiya ya dawo min da kai lafiya, yace ameen Afee nah,
sun daďe tare a ranar suna hira kamar kar su rabu,
Da kyar suka rabu gurin 11 ya tabbatar mata zai shigo ya ganta kafin ya tafi,.
rakiyar kura suka dingayi har saida ya gaji ya kaita har cikin daki ya tabbatar ta kwanta sannan ya tafi gida cike da nishadi, ya yi matukar kosawa Afeeya ta zama mallakinshi, shi yasan auren Afeeyah shine lst dream dinshi, yasan yana aurenta ya gama samun komai a rayuwarshi,
da wadannan tunaninkan masu dadi bacci yayi gaba da jabeer da gidan Bara'u...


Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 2⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah


Tun 5 saura na asuba jabeer ya farka jikinshi duk da ya jike da zufa, duk sanyin a.c dana damuna basu hanashi yawan jin zafi a yan kwanakin nan,
bayi ya shiga yayi wanka da ruwan sanyi ya ďauro alwala ya fito yayi nafila ya zauna jiran a kira sallah..


Yana idar da sallah ya zauna kan kujera ya lumshe idonshi kanshi na kallon sama,
Allah kaďai yasan tunanin da yakeyi a wannan lokacin,
sai 8 ya mike jikinshi a sanyaye ya gama shiri cikin farar shadda, yayi matukar kyan da bai taba yin irinshi ba shi kanshi saida ya faďi da ya kalli madubi,,,
saida ya gama shiryawa tsaff har zai fita daga ďakin sai kuma ya dawo ya dinga kallon ko ina ko akwai abin da ya manta bai dauka ba, drawer ya buďe ya dauko driving licences dinshi har zai rufe drawer sai yaga wasu takardu,
daukosu yayi ya dubasu yayi murmushi ya mayar dasu mazauninsu ya rufe drawer yasa kai ya fita daga ďakin,


A parlor ya tadda babanshi zaune yana karyawa ya tsuguna ya gaisheshi, ya amsa da fara'a yace sammako zakayi kenan,
jabeer yace eh baba ina son in dawo da wuri ne shiyasa,
Abida ta fito rike da cup din kunun gyaďa da plate din alale ta zauna kusa da mijinta, jabeer yace ina kwana ummi,
tace lafy lau jabeer yau dai kaka liman yayi kira irin wannan sammako hka,
jabeer yayi dariya yace na kosa inje in ga uwargidana sarautar gida shiyasa,
ta gutsiri alalen ta kai bakinta tace kace ka kosa kaje kuyi faďa har ku gaji,
yayi dariya yace kamar kin sani,
dai2 lokacin Amirah ta shigo parlorn cikin uniform itama rike da break dinta a hannu ta gaisheshi ya amsa yace miko min naki kije ki zubo wani, Amirah ta turo baki tace yaya fa nayi latti dan Allah kasa Dayyaba ta zubo maka,
alhj bara'u yayi mata dakuwa yace gidanku, zubo abincin ne zai hana ayi miki dukan latti, ajiye mishi kije ki zubo wani,
Amirah ta ajiye tana kunkuni ta wuce kitchen ta zauna ta zuba wani kunun tana sha tana mita,
shima jabeer kaďan yasha kunun ko alalen ma bai taba ba ya mike yayi sallama da iyayenshi sukayi mishi fatan Allah ya tsare hanya,
har ya shiga mota yaji kamar ana kwala mishi kirah,
fitowa yayi ya nufi parlon yace gani baba, alhj bara'u yace ban kira ka ba jabeer saidai ko umminka,
Abida tayi dariya tace muna tare a zaune zan kirashi baka ji ba,
ta kalli jabeer dake tsaye yana kallonsu yana murmushi tace ni wai me ma zakayi a daura ne ka kirkiri tafiyar gaggawa,
alhj bara'u yayi dariya yace zuciyarki ce ta kirashi kenan dan tayi mishi wannan tambayar,
jabeer yayi dariya kamar zai faďa musu sai kuma ya fasa yace ziyara kawai zanje yi ummi,
tace to Allah ya bamu ladan tare, duk sukayi dariya haďe da cewa ameen,
kallon babanshi yayi yace baba akwai maganar da zamuyi dakai akan wasu takardu suna nan a ďaki na in na dawo in shaa Allahu zamu tattauna, alhj bara'u yace Allahumma yashaa ka gaida Baba da Goggo,
yace zasu ji sosai ya fita Amirah ta biyoshi da gudu tana mishi bye bye,
hararta yayi yace Allah yasa a fasa miki jiki da dukan latti,
tayi mishi gwalo ta shige mota tana dariya tana daga mishi hannu,
shima motarshi ya shiga ya tada ya fita yana gaisawa da baba ado da sauran masu aikin gidan..


Hanyar daura ya ďauka ba tare da ya tsaya yaga Afeeyah ba saboda yana gudun bata mishi lokaci da zatayi dan yasan in har ya shiga to bazai taba tafiya da wuri ba,,
Karfe 10 da mintina ya isa gidan kaka liman, bayan ya huta yaci abinci da furah suka dinga hira dasu Goggo, basu fara aiwatar da komai ba sai da sukayi sallar azahar sannan suka fita shi da kaka liman,
suna tafe yana mishi bayanin irin mugayen tsafin da akayi ma Affan wadanda aka binnesu a cikin gidan, kaka limann yace saboda rashin imani irin na matar nan har kafin fita gida tayi mishi dan kar ma ya fita wani ya ganshi yayi mishi addu'a ko ya taimaka mishi, sannan ta katangeshi daga dukkan adduar mutane ta mantar da mutane ciwonshi in ba waďanda suke kusa dashi ba,
jabeer ya jinjina kai yace ay ni ban ďauka zaluncinta har ya kai haka ba walhy kaka, amma in shaa Allahu karshenta yazo,


wani kauye suka je a cikin kasar Nigar mai suna "Tsatsunburum (s Burum)"
kauyen bashi da nisa da zangon daura, gaba da gidan sarki sukaje kaka liman yace ya tsaya anan,
jabeer ya kalli gurin,
a katange yake da wata katuwar bishiya a ciki, kaka liman ya fito ya shiga gurin jabeer na binshi a baya, ashe wata katuwar rijiyace a cikin gurin mai cike da tarihi,
kaka liman ya kwance ledar da ya zo da ita ya fito da wasu layu da magunguna ya fara haka rami ya binnesu sannan ya ďauko wata gora a cikin jakarshi da magunguna a ciki yasa hannu a cikakkiyar rijiyar ya debo ruwan cikinta sannan suka fito daga gurin,
jabeer dai kallon gurin yakeyi ga rubutu a jikinshi amma rubutun ya fara gogewa,
ya kalli kaka yace kaka amma wannan rijiyar tana kunshe da tarihi ko,
kaka liman yace kwarai kuwa,
abin al'ajabi ya taba faruwa a gurin nan,
ya nuna mishi wata bishi dake dan nesa kaďan da gurin yace kaga waccan bishiyar, jabeer yace eh kaka, yace to daidai saitinta da gurin kiwon shanu ne, shanaye da yawa ake kiwo a gurin, "akwai wata saniya guda ďaya kullum aka bata abinci sai taki ci haka ruwa, saidai a ganta kullum da yamma tazo nan gurin da muka shiga kafin a katange shi ta daďe a gurin har sai dare take komawa cikin yan uwanta, kullum haka takeyi sam bata cin abincin da ake basu, ana cikin haka rannan sai mai shanun ya dinga binta a baya dan ganin abinda takeyi a gurin, yana zuwa gurin yaga ta kafa kanta a wani ďan tsukukun rami tana shan ruwa, tana gamawa yaga ta kwanta karkashin bishiyar nan lokacin tana karama sosai a gurin take bacci har dare sannan ta koma cikin yan uwanta, in takaice maka dai wannan saniyar tunda ake kiwonta bata taba cin abinci ba wannan ruwan shine ya zamo ruwa da kuma abincinta sannan wannan bishiyar ta zamo gurin hutu a gareta har ta mutu a gurin, bayan ta mutu ne mutane suka haka wannan ramin ya zamo rijiyar da bata taba kafewa ba duk wahalar ruwan da akeyi a garin tofa wannan rijiyar na nan da ruwanta sannan wannan bishiyar tana nan bata taba fadi ba shekaru fin 100 dan nima labari aka bani,
jabeer yace ikon Allah shine aka katange ta, kaka liman yace kwarai kuwa kuma cikin ikon Allah ruwan cikinta yana zama waraka ga duk wanda ya yarda da Allah kamar yadda ta kusugu take,
jabeer yace Allah ya kara ma Annabi daraja, kaka yace ameen jabeer shiga muje dan zan ga Aminina "Maina dogon yaro" shima akwai abin da zai bani daga nan mu wuce cikin daura mu karasa,
jabeer yace to kaka, suka shiga mota suka wuce jabeer na kallon girman bishiyar yana tasbihi ga Allah...


Sai bayan magriba suka gama komai suka dawo gida a gajiye,
dakyar jabeer ya iya taba abincin da Goggo ta kawo mishi sauri2 dan yana son ya dauki hanyar gida komin dare,
babu yadda basuyi dashi ba akan ya kwana yace samm bazai kwana ba dan gobe da wuri yake so fara aiwatar da aikin cikin gidansu Affan wanda shine mataki na karshe na aikin,,
sai da yayi isha' sannan kaka liman ya fito yayi mishi rakiya yana kara nuna mishi yadda zaiyi amfanin da maganin yana kuma mishi faďa akan yayi taka tsantsan da oyizah,
jabeer ya shiga mota yace in shaa Allahu kaka zanyi duk yadda kace, mun gode sosai, kaka liman yace to Allah ya tsare kayi tuki a hankali ďan boko, jabeer ya tada motar yace baka da matsala tsoho, yaja motar suna ďaga ma juna hannu, saida yaga kulewar motarshi sannan ya juya gida,
haka kawai ya tsinci gabanshi da tsananin faďuwa,
a waje ya zauna yana bin sawun motar jabeer da kallo yana mishi adduar Allah ya kiyaye hanya...
[15/12 09:34] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 3⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah


★ 9:54pm ★


Tun bayan magriba hadari mai tsananin duhu ya taso yana kokarin haduwa a gabas,
iska ce mai dadi taketa kaďawa a wannan lokacin har zuwa karfe 9:32pm, lokacin ne hadarin yamma ya kusa haďuwa da na gabas, iska mai karfin gaske haďe da guguwa da walkiya su keta tashi ta ko'ina kamar zasu tashi gidaje da motocin biladama,
yaf yaf ruwan feshi ke busawa a cikin iskar,


A wannan lokacin gudu jabeer yakeyi cikin motarshi yana Allah Allah ya isa kano kafin goma ko kuma goma daidai,
wuce motoci yakeyi yana tafiyarshi cikin kwanciyar hankali yana wiping yayyafin dake sauka a kan glass din motarshi, karfe 9:50 ya rage saura k.m baifi 15 ba ya shigo garin kano, murna ya dinga yi dan yasan in shaa Allahu kafin 10:30 zaiga Afeenshi,
har ya dauko wayarshi zai kirata sai ya fasa so yakeyi kawai ta ganshi kafin lokacin da ya daukar mata..


Wani haske ya gani ya gifta gabanshi hade da girgiza mai karfi wacce tayi sanadiyyar fitar tayar motarshi ta gaba,
runtse idonshi yayi sosai yana kalmar shahada saboda yadda yaji shi a sama motar na juyawa sosai, wasu masu trailer sukayi parking gefen hanya suna salati cikin tsoro saboda yadda motar ke wulwulawa a sama,
saida tayi minti uku a haka sannan ta daki wani katon dutse ta tarwatse a kasa dai2 lokacin ruwa mai karfi ya tsuge haďe tsawa, mutanen gurin kowa ya kunna full light dinshi suka karasa kusa da motar jiki na rawa saboda basu taba ganin accident irin wannan ba,
ba karamin dagargajewa motar tayi ba, nan da nan suka fara kokarin ciro mutumin da suka gani a gaban motar, da kyar suka iya ciro jabeer saboda wani karfe da ya shige cikin hancinshi ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login