Showing 54001 words to 57000 words out of 72718 words
Chapter 19 - RABO AJALI COMPLETE DOCUMENT BY Aisha Ya'u kura.txt
ta riketa tana rarrashinta tace mummy dan Allah ki daina wannan ihun kinga mutane suna ta kara yawa,
oyiza ta hankaďa ta tace sun ci kutumar ubansu mutanen,
nan ta fara zage2 tana tsinewa mutanen da suka zo mata gaisuwa cikin ficewar hayyaci,
saida farida ta kirah alhj basheer yazo ya lallabata da kyar sannan tayi shuru tana ajiyar zuciya,
gaba ďaya ta dauki tunaninta kacokan ta maida shi gurin gano yadda akayi abin da ta shimfiďa ma Afeeyah ya dawo dakinta, yanzu su chummy basuyi ma diyarta lamuni ba suka zuke jininta ba tare da sun tambayeta ba,
lallai sun taro match dan wallhy sai tasan yadda akayi wannan kyallen ya dawo dakinta sannan kuma sai ta nuna ma su chummy bacin ranta,,
Tun ranar da salma ta mutu nutsuwa tayi ma oyizah tawaye,
kullum cikin mafarke2 take tana bakin cikin yadda akayi aka bada ďiyarta a cikin kungiyarsu ita kuma shegiyar kungiyar mai lakabin sabo da kaza baya hana a yanka ta, in ba haka ba ay sunsan yadda takeson yayanta kamar yar ranta,
a ranar da akayi uku ne ta fara shirin zuwa gurin meeting dan ta warware musu kuma a binciko mata dalilin da yasa wannan farin kyallen ya koma ďakinta.....
Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣2⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Karfe biyun dare suka hadu a gurin meeting kamar yadda suka saba,
oyizah na zaune gaban chummy bayan ta gama masifarta sai cika takeyi tana batsewa,
Chummy ta dafa kanta tace oyeee naji duk bayanan ki
, kuma na fahimci fushinki, amma kinsan mu nan duk wanda aka kawo baya tafiya ba tare da munsha jinin shi ba ko,
mistake din daga gareki yake tunda ke kika shimfiďa farin kyallen,
oyizah cikin fushi tace ba a dakina na shimfiďa ba my lord a dakin yarinyar da na bada anan na shimfiďa bansan yadda akayi ya dawo ďakina ba,
alhj sambo ya kalleta yace haba oyizah dan kin bada yarki daya shine kike ta wannan fushin,
ni yayana biyu na bayar da kannena biyu da nake matukar so,
a hassale oyizah tace abin da kake nema ne dole sai kayi wannan sacrifice din,
ni ay na riga na bada nawa wannan kyauta na bayar saboda kungiya taji dadi,
esther tace calm down oyee,
chummy tace barta ta cigaba,
ta manta duk abinda kungiya tayi mata ne, ta manta da irin rufin asirin da mukayi mata, ta manta da duk wani wanda zai tona asirinta mun kawar mata dashi saboda tasamu nutsuwa a gidan aurenta,
ta manta yadda muka mallaka mata alhj basheer
, ta manta yadda muka lalata rayuwar dan kishiyarta ita kuma muka mayar da ita matacciya alhali tana raye,
oyizah ta sunkuyar da kanta kasa tace am sorry my lord, ni ba fushi nayi ba,
kawai dai ina son in san wanda yayi min wannan aikin ne,
chummy ta janyo wani kokon tsafi ta fara bincikenta cikin kwarewa dan gano wanda ya canza farin kyallen,
a wannan lokacin kuma Afeeyah na zaune kan dadduma tana kallon gabas tana rokon Allah ya karesu daga dukkan sharrin masu sharri,
Babu irin duban da chummy batayi ba amma sam bata ga komai ba sai duhu da ya mamaye kwaryar, ajiye kwaryar tayi hannunta na rawa tace kaii oyee gaskiya na kasa gane ko waye, kar mu zurfafa bincike ko ma waye zamu gane shi wata rana, kedai kije ki cigaba da mulkinki kamar yadda kika saba tunda babu wanda ke taka miki birki,
cikin damuwa oyizah ta ďago da niyyar faďin damuwarta akan Afeeyah amma ta kasa,
daga ta bude baki zatayi magana sai taji wani abu na mata yawo a makoshinta, sai gab da asubahi suka fara bacewa suna komawa gidajensu,
har lokacin bakin oyizah naso ta furta sunan Afeeyah amma ta kasa,
gurin wata kwalba suka je wacce ke dauke da gunki a cikinta,
d'aga kwalbar chummy tayi tana dariya ta mayar ta ajiye tace haka kishiyarki zata dawwama babu motsi a duk inda take,
fanne da fanna dake cikin wata kwalba sukace saidai in bamu fita anan ba, wallhy muna fitowa zamu fasa kwalban nan,
oyizah ta buga glass din tace to dan ubanku ku fito mu gani,
fanne tayi dariya tace wit tym,
chummy tace rabu dasu oyee tafi gida sa'a na tare dake a ko da yaushe,
ta russuna kamar zata mata sujjada tace thank you my lord.....
Kwanan salma biyar da mutuwa har lokacin oyizah bata walwala, kullum sai tayi kuka saboda yawan mafarkin salma da takeyi,
alhj basheer da farida kaďai ke tausarta se kuwa a gurin meeting dinsu,
sam ta tsani ganin Afeeyah dan gani takeyi sanadiyyar Afeeyah ta rasa yarta, jira kawai takeyi ayi sadakar bakwai tayi wani aikin akanta dan wannan karan da hannunta zata kashe shegiya,
mugun shiri takeyi akan Afeeyah dan so takeyi tayi mutuwar wulakanci,,,,
Afeeyah kuwa hankalinta kwance yake dan kula sosai takeyi da mijinta da take ganin yar nutsuwa a tare dashi kwana biyun nan,
shi kanshi hankalinshi a kwance yake saboda daina ganin salma da yayi kwana biyu,
karfe 5 na yamma ta gama girkinta sukayi wanka suka shirya cikin kyakyawar shiga sai kamshi sukeyi, dakin oyizah suka shiga Afeeyah ta tsuguna ta gaisheta tayi mata ya hakuri,
ko kallonta oyizah batayi ba idonta nakan Affan tana hararar shi, boye fuskarshi yayi a bayan Afeeyah yana leken fuskar mummy da har lokacin bata daina hararar shi ba,
mikewa Afeeyah tayi tace sai anjima mummy,
oyizah ta bita da mugun tsaki tace za kici ubanki ne,
Ta wani corridor taja shi tace yau ta nan zamu bi,
kasan tunda nazo gidan nan ban hau gurin nan ba,
yayi dariya yace to muje amma fa mummy tace akwai su lions a gurin,
Afeeyah tace haba dai babu komai muje may be basa so ka hau ka fado ne,
runtse idonshi yayi yace muje amma bazan bude ido na ba, dariya Afeeyah tayi taja hannunshi suka hau can saman gidan,
sakin hannunshi tayi da sauri tana fadin Wowww amma gurin nan ya hadu,
bude hannunta tayi ta lumshe idonta tana shakar iskar gurin flowers sai kaďawa sukeyi,
da gudu taje bayanshi ta fara mishi cakulkuli tana faďin ka buďe idonka ka gani babu komai a gurin sai flowers masu kamshi, dariya yake ta kyakyatawa sannan ya buďe idonshi a hankali,
wasu shuďaďďun abubuwa ya dinga gani suna mishi yawo a cikin kwakwalarshi da kwayar idonshi,
sosai yake ganin abubuwan da suka taba faruwa a gurin kuma yake ganinsu kamar zanen cartoon,
fuskar zeenatu ce take mishi gizo yanata so ya gano ko wacece saboda dishi2 yake ganinta,
rike kanshi yayi dasauri bakinshi na rawa a hankali ya furta
U-M-M-A,..... ..
Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣3⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Maimaita sunan ya dinga yi yana ja da baya kanshi na juyawa saboda yadda abubuwan ke zuwan mishi cikin kwakwalwarshi,
a firgice Afeeyah ta kamashi tana faďin me ya faru,
girgiza kanshi yayi da karfi ya runtse idonshi yace dan Allah ki sakko dani ki kaini ďaki,
Afeeyah cikin tsoro ta rike hannunshi taja shi tana waigen gurin ko itama zata ga abin da yake gani,
daki ta wuce dashi ta zaunar dashi ta tsuguna a gabanshi har lokacin bai buďe idonshi,
a hankali tace ka buďe idonka,
kara runtse idon yayi yana girgiza kanshi,
Afeeyah tace a daki fa muke ka bude idonka ka gani babu komai anan,
a hankali ya fara bude idonshi har ya bude su gaba ďaya ya saukesu a kan Afeeyah,
Afeeyah tace kaga ni ba komai ko,
ya gyaďa mata kai, tace to me ka gani a can saman,
ya ďaga kanshi sama yace babu komai sai fan,
Afeeyah ta dawo kusa dashi tace ina nufin a sama inda muka je, rufe idonshi yayi shi kanshi yana son tuno abinda ya gani duk da bai gansu clear ba amma yasan ya gane fuskar ďaya a cikinsu,,
bude idonshi yayi dan ya kasa tuno fuskar da ya ambaci sunanta a sama,
kallon Afeeyah yayi yace ni ban ga komai ba,
Afeeyah tace kagani mana, baza dai ka faďa min ba ko,
ya tabe baki yace ni na manta kome na gani,
Afeeyah tace to shikenan, tashi muje muyi sallah magriba tayi,
ba musu ya mike ya bita fuskar da ya gani a sama tana ta mishi gizo amma sam ya kasa tuna ta....
Zaune take a gefen gadonta rike da turaren da kaka liman ya bata a hannunta tana shafa shi tana addu'a kamar yadda ta saba,
tofe jikin Affan tayi da addu'a sannan ta kwanta tana istigfari har bacci yayi gaba da ita,,,,
Mafarki*****
Tafe take a cikin gidan tana bin inda bata taba bi ba tun zuwanta gidan a zuciyarta tana yabawa da kyau da tsarin gidan,,
Kamar giftawar walkiya ta hango wani katon DAMO yana bin wata mata tana gudu tana salati haďe da ihun neman ďauki,
da sauri ta bisu tana addu'a zuciyarta cike da tsoron wannan damon dan bata taba ganin suffa irin tashi ba,
ja da baya tayi saboda yadda ta hango wannan damon ya hankaďa matar cikin wani kewayayyen flower bed ya haye kanta,
tun tana jiyo ihun matar har ta daina jiyowa saboda matar ta nitse ciki sai tashin kura mai karfi kawai take gani,,,
a firgice ta juya jikinta na rawa ta hango wannan damon ya fito daga cikin flower bed din yayi gurin fishpond, yana zuwa gurin ya rikiďa ya koma kifi ya shiga ciki,,
a hankali ta tako ta leka cikin ramin ta hango kifayen sun cure kansu sun zama kifi ďaya,
a gigice ta koma baya tana sauke numfashi tana fadin "innalillahi wa inna ilaihir rajiu'n," dan ganin yadda kifayen nan suka cure ba karamin daga hankalinta yayi ba,
cikin sassarfa tayi hanyar daki,
anan ne ta haďu da wani tashin hankalin dan ganin wata guntuwar halitta tayi a kofar ďakin oyizah tayi wuf ta shige ta kofa ba tare da ta buďe ba,
nan jikinta ya fara rawa ta leka ta window ta hango wannan halittar ta haye gado ta nutse cikin katifar,
wata dariya taji an saki mai karfi haďe da guguwar da ta fito da wani mugun bakin hayaki daga karkashin gadon,
da sauri ta juya zata koma ďaki taji haushin karnuka a bayanta, tana waigawa taga bakaken karnika sun fi ďari sun doso inda take suna haushi kamar zasu tsaga gidan,
a razane ta fara gudu tana fadin "hasbunallahu wa ni'mal wakil,"
bin ta karnunkan suka fara yi da gudu suna kara yin haushi,
tana zuwa kofar dakinta taji an taďiyeta ta fadi kasa sosai,
ja baya ta farayi tana kara karanto adduoi da karfi tana kuka,
wani irin tsalle wani katon kare yayi zai hau kanta,
a razane ta runtse idonta ta saki ihu mai karfi haďe da tashi daga baccin da takeyi,
Affan ta gani a zaune yayi tagumi yana kallonta,
kauda kanta tayi ta janyo wani zani a gefenta tana share zufar da ta jikata tana fadin
"'A'oothu bikalimaatil-laahit-taammaati min ghadhabihi wa 'iqaabihi, wa sharri 'ibaadihi, wa min hamazaatish-shayaateeni wa 'an yahdhuroon.""
Singlet ďinshi yasa a gefen kunnenta yana share mata zufar da take gangaro mata daga kanta,
juyowa tayi ta kalleshi tace har ka tashi, karfe hudu fa yanzu,
ya karkatar da kanshi gefe idonshi ya ciko da kwalla saboda mafarkin mahaifiyarshi yayi amma sam ya kasa tina mafarkin,
da sauri tasa hannu tana share mishi kwallar idonshi tace menene,?
A hankali ya kwanta lamo a jikinta yana kara zana fuskar zeenatu a cikin kwakwalwarshi,,
shafa kanshi ta fara yi tana karanto addu'a tana tofa mishi a kanshi har bacci ya ďaukeshi,
haka suka kasance a wannan daren Afeeyah bata koma bacci ba dan tana matukar tsoron ta runtse idonta ta kara yin wani mafarkin....
Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 5⃣4⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Washe gari sukuku ta gama aikinta,
sai da suka karya sannan ta kirah kaka liman tayi mishi bayanin abubuwan da ta gani a cikin mafarkinta,
cikin mamaki yace na faďa miki mugun tsafine dankare cikin gidan nan,
yanzu gurare uku zakiyi aikin kisa a ranki Allah na tare dake,
ki tabbatar yau kinsa an hake wannan flower duk abinda kika gani a ciki ki cire shi,
sannan ki tabbatar wadannan kifayen yau basu kwana a gidan nan ba,
kisan duk irin dabarar da zakiyi kisa a fitar dasu daga cikin gidan a wanke gurin ya zamana ba komai a ciki,
sannan guri na uku shine mai wuyar, yadda zakiyi ki shiga wannan dakin nata har ki iya bankade karkashin gadonta,
Afeeyah dai ta gama tsorata matuka idonta ya ciko da kwalla tace kaka duka suna da wahala, wallhy har yanzu jikina rawa yakeyi,
yace nasani jikata nasan suna da matukar wahala amma Allah zai mayar maki dasu masu sauki daga kin fara,
dan Allah karki ji tsoro zan tayaki addu'a ina daga nan, Allah zai taimakeki saboda niyyarki mai kyau ce, kisan duk yadda zakiyi ki bankade na karkashin gadon nan dan duk wasu alkadaranta anan suke, in mun gama da wannan zan fassara miki na karnunakan nan,
jiki a sanyaye Afeeyah tace to kaka nagode sai anjima, yace to sai anjima Allah yayi miki albarka tace ameen kaka...
Karfe 11am ta fito daga ďakinta ta fara bin hanyar da tabi cikin mafarkinta,
sannu a hankali take tafiya har saida kafarta ta sada ta da wannan kewayayyen flower bed ďin da farida ke raya shi da ruwa babu dare babu rana,,
karasawa tayi gurin flower ta leka ciki dan tasan duk dabarar da zatayi a hake mata gurin,
ta kai minti uku a gurin ta hango tanimu mai Guga rike da bokiti a hannunshi,
da karfi ta kwala mishi kirah ya taho da sauri ya tsuguna yace hajiya gani,
Afeeyah tace dan dan Allah a ina zaka samo fatanya inason a shiga cikin nan ne ayi min digging dinshi naga kamar ana gyara sauran kullum banda nan,
tanimu ya rike baki yace wallhy hajiya ko katakon gurin nan ba'a yarda mu taba bare ganye bare kuma har mukai ga hakeshi,
Afeeyah tace to saboda me, yace wallahu aalamu, nima ban sani ba,
Afeeyah tayi tsaki tace kira min mati naga shi ke kula da flowers din gidan,
da sauri ya mike yaje ya kira mati suka taho tare,
dakyar da yaudara tace ma mati yazo ya hake mata saboda alhj yace za'ayi shuka ne a gurin,
jin alhj ne yace yasa mati zuwa dauko fatanya ya bude gurin ya fara haka tun karfi,
gefe ta koma tana addu'a tana kallonshi, yana tsakiyar hakan ne ya jiyo taurin wani abu, da sauri ya dago shi da fatanyarshi ya fara girgijeshi kasar na kakkaba,
Afeeyah na hango kafar ta gane ta dabba ce, da sauri tace mati ajiye dan Allah ka samo min ruwa in dauraye hannu na,
dasauri ya ajiye yayi gurin pampo,
cikin azama ta karasa tayi bismillah ta dauko wannan damon tayi cikin dakinta dashi ta naďe shi cikin wani zani ta turashi karkashin gado,
tana komawa gurin ta tarar da farida na balbale mati da masifah,
Afeeyah ta karaso da sauri ta kalli fuskar mati gwanin tausayi tace ya akayi ne mati, mati yace hajiya saida na faďa miki ba'a taba gurin nan kika dage sai na hake shi, gashi yanzu hakan na min barazana da aikina,
Afeeyah ta kalli farida dake harararta sannan ta maida kallonta ga mati tace dama wannan ce ta dauke ka aiki,
ya girgiza kanshi yace a'a, Afeeyah tace to dan me zatayi sanadiyar aikinka,
naga dai wannan aikinka ne, ko alhj yasan baka gyara wannan flower,
mati yace a'a bai sani ba,
Afeeyah tace to maza ka cigaba da aikinka tunda dama dan albashi kakeyi,
farida tace ke kuma asuwa dan uwarki,
Afeeyah tace ni as uwarki dan ita uwar taki,
fareedah ta rike baki cikin mamaki tace mummy kike zagi,
Afeeyah tace uwata ce ita ko kuma kina tunanin uwa tafi uwa ne,
kai mati cigaba da aikinka in ka gama kayi watering din gurin ka rufe ni ina da abin yi,
farida ta hassala ta finciko Afeeyah da karfi tace wallhy yau sai naci ubanki a gidannan,
duka duka yaushe aka haifeki da zaki tsaya kina gaya ma mutane magana,
Afeeyah ta haďe rai sosai tace sakeni kar muyi creating sin a gurin nan,
farida tace baza'a sakeki ba,
Afeeyah ta buge hannunta da karfi tace dallah sakeni,
farida ta daga hannunta cikin fushi zata mareta Afeeyah tayi saurin rike hannunta tace karki fara wannan gangancin dan wallhy bazamu kare faďan nan yau ba,
ki bar ganinki katuwa wallhy babu abinda zaki dauka ajikina dan abun a zuciya yake, kuma sannan da kike cewa yaushe aka haifeni to bari kiji ko jiya aka diga maniyyi na na fito yau na fiki daraja a idon duniya saboda nayi aure kuma nasamu Apple of marriage, ke fa? har yanzu kina gida babu mashinshini bare har yayi yunkurin dauka, tayi wurgi da hannunta taja tsaki ta wuce ta barta tsaye idonta jajur....
Gurin Affan ta wuce yana zaune yana kallon kifayen dake cikin fishpond,
runtse idonta tayi saboda tuno mafarkin da tayi,
da sauri ta mike tayi hanyar ďaki tsigar jikinta sai tashi takeyi,
da sauri ya biyota dakin yana tambayarta me ya faru,
a hankali take maida numfashi tace wallhy na tsani ganin kifayen nan,
dan Allah muje gurin daddy yasa a fitar dasu daga gidan nan,
Affan ya bata rai yace kifin mummy ne fa, bazata bari a fitar dasu ba,
Afeeyah ta fara kakarin amai ta mike ta shiga bayi tana kakarin karya tana kuka kamar zata mutu,
da gudu ya tafi dakin daddy yana fadin daddy kazo Afeeyah zata mutu,
da sauri ya tashi ya fita yace tana ina, Affan yace tana bayi daddy,
da gudu ya shiga dakin ya tarar da ita kofar bayin tana haki kamar da gaske,
karasowa yayi da sauri yace me ya sameki, Affan yace daddy wai kifayen nan ne ke bata tsoro,
Alhj basheer yace wani irin tsoro kuma,
Afeeyah tace wallhy daddy kullum sai