Showing 39001 words to 42000 words out of 72718 words

Chapter 14 - RABO AJALI COMPLETE DOCUMENT BY Aisha Ya'u kura.txt

16 Dec 2024

2299

mukai kasan mana,
farida ta dawo kusa da ita tace mummy lafiya, oyizah tace hmmm aure aka ďaura a cikin gidannan,
farida cikin kidima tace daddy ne yayi aure,
oyizah tace gara min shi yayi aure dan nasan duk wacce zatazo baza tayi karko ba,
farida tace to waye yayi aure, dai2 lokacin Affan ya wurgo kwallo yana bugawa cikin farin ciki ta kalleshi tace wancan saunan aka daura ma aure,
fareeda ta kwashe da dariya tace ita kuwa wannan wace dakikiyar ce ta yarda ta aureshi,
mummy tayi tsaki tace mune dai dakikan da tuntuni banyi tunanin nemo mace sakarya na haďashi da ita ba,,
Farida tace ban gane ba mummy,
oyizah tace ay kwakwalwarki bazata gane ba amma nasan in na faďa miki amaryar zata gane, Ay kwakwalwarki tasan Afeeyah yar kishiyar suwaiba ko?, farida ta dafe kirji tace farin sani mummy ita ya aura,
tace aka daura mishi dai, ta kalli Affan taga ya kara mata nuri sajenshi ya kwanta luff" yayi matukar kyau kamar yasan yau zai angwance,
da karfi ta kira sunanshi ya taho da gudu ya zauna kusa da ita,
ta kalleshi tace u luk very happy my son,
ya kara gyara zamanshi cikin murna yace am happy mummy yau za'a kawomin Afeeyah,
ta kalleshi sosai tace waye ya faďa maka, yace ni nace daddy ya kawomin ita mu dinga wasa ba jiya nazo zan fada miki ki mata girki mai dadi ba kika koreni,
oyizah tayi saurin dafe kanta da ya sara mata tace tashi ka tafi,
ya mike tsaye har ya fara tafiya sai kuma ya juyo ya tsuguno saitin kanta yace mummy zakiyi mata girkin,
a hassale ta dago ta daka mishi tsawa tace ubanka zan girka mata, wuce ka bani guri,
Affan ya wuce cikin tsoro yana waigenta kamar zaiyi kuka..
Farida ta dafata a hankali tace mummy meyasa kike damuwa naga Affan is under ur control dole itama in ta shigo ta zama a karkashinki, ni mummy kin bani mamaki wannan small girl din kike damuwa akanta, duka fa bata wuce 17 to 18,
oyizah tacee uhmm kawai ta mike tayi sama tana tunanin yadda zata fara bullo ma wannan alamarin...


A can gidan Malam Atiku kuwa tunda suwaiba ta samu labari take bala'i tana zaginshi, wai akan me za'a boye mata maganar auren saida aka daura za'a fada mata dan anga ba ita ta haifeta ba,
malam Atiku cikin fushi yace sannu uwata, wani abun zaki tsinana min in na fada miki, ko nairah dari bazaki kawo kice a siya mata cokali ba to niko saboda me zan faďa miki, aure ne an daura shi babu wanda ya isa ya warwareshi, nan fa suwaiba ta cigaba da bala'i tana aibata auren harda kuka saboda bakin ciki,
acewarta ita bata bakin ciki da auren musaki amma can cikin zuciyarta takaici ne dankare saboda tasan ko Affan zai dawwama cikin ciwon hauka Afeeyah ta gama warkewa, hangowa ta dinga yi da kausar ce da tuni yanzu alhj basheer ya fara jikata da kuďi,
daki ta koma bayan ta gama sababinta tana kukan rashin sa'arsu ita da diyarta,
malam Atiku ya fita ya barta, hajja kuwa ko dekowa batayi ba tana ďaki tana aikin rarrashi...


Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 3⃣9⃣ By Aysha Ya'u Kurah


Bayan isha'i Alhj basheer da kanshi yazo daukar Afeeyah,
suna zaune da hajja da Asiyah suna rarrashinta suna kuma bata shawara akan ta kula da mijinta duk haukarshi mijinta ne kuma aljannarta na karkashin kafarshi,
Asiyah tace yanzu kin zama kamar uwa a gareshi da taimakonki komai nashi zai fara daidaita,
dole ki jajirce ki manta da ke yarinyace ki rike darajarki da ta mijinki kuma karki yarda wani ya raina shi a gabanki, Nasiha sosai sukayi mata har malam atiku ya shigo shima ya daura ya kuma yi mata tuni da riko da adduoi, sannan ya umurceta ta tashi suje ga alhj basheer can yana jiranta,
mikewa tayi tana kuka Amirah ta miko mata sabon hijab dinta tasa Asiyah ta fesheta da turare ta riko akwatinta suka fito rakata,
dakin suwaiba ta shiga yi mata sallama ko kallonta batayi ba ta cigaba da cin tuwon gabanta tana yan wake wakenta,
tashi sukayi suka fita basu ko kulata ba,
motar alhj basheer suka nufah suka sakata a baya ta rike hannun hajja sosai tana kuka tace saidai hajja ta shigo su tafi, dakyar malam atiku ya lallabata ta saki hajja sannan alhj basheer yayi sallama dasu suka wuce hajja na kuka tana ďaga musu hannu sai kace wacce zata bar unguwar,,


Runtse idonta tayi da suka shigo harabar gidan tana karanto adduoi akan Allah ya taimaketa yayi mata jagora a cikin wannan sabuwar rayuwar da ta tsinci kanta a ciki,
alhj basheer ya fito ya buďe mata kofa yace mun iso diyata, Allah yasanya alkhairi a farkon shigowarki gidannan, ya kuma dawwamar da farin ciki a cikin zaman aurenku har karshen rayuwarku,
a zuciyarta ta amsa sannan ta sako kafarta kasa da bismillah,


Zubur Affan ya mike daga kan kujera ya karaso kofa yana faďin daddy na ya dawo, yana buďe kofar ya hangosu da Afeeyah suna tahowa ya rugo da gudu yana cewa oyoyo barbie, chakk" ya ďagata cikin murna yana jujjuyata ya karaso cikin parlon da ita yana fadin mummy kizo ga barbie nah daddy ya kawo min,
wani irin kuka Afeeyah ta fashe da shi yayi saurin sauketa yana nunama daddy hannunshi yana faďin ba ruwana daddy wallhy bani na sata kuka ba,
alhj basheer yayi dariya yace kai ka sata kuka nima babu ruwana bari ma in tafi kar ace har dani,
Affan ya zaro idonshi zaiyi ma oyizah magana tayi saurin jifanshi da mugun kallon da yasa shi ďauke kanshi ya ďago fuskar Afeeyah kamar zaiyi kuka yace ay bani na saki kuka ba ko,?
Afeeyah tayi banza dashi ta cigaba da kukanta,
alhj basheer yace zo nan diyata ki zauna rabu da shirmenshi,
Afeeyah taja kafarta a hankali ta zauna a kasa kusa da alhj basheer Affan ma ya biyota ya zauna kamar zaiyi kuka,
alhj basheer yace share hawayenki ki bude idonki ki gaisar da mamanki da kuma yayyinki,
oyizah tayi saurin cewa ta mayar da idonta abinda muna tare kullum yanzu,
alhj basheer yayi murmurshi yace haka ne,
ya kalli Afeeyah yayi mata yar nasiha ya kuma roketa da ta kula da Affan ta rikeshi amana sannan yace suje oyizah ta nuna mata ďakinta,
oyizah ta mike tace ma Afeeyah ta tashi suje,
kafin Afeeyah ta mike Affan ya mike yace barbie tashi muje ďakinmu,
Afeeyah ta mike tabi bayan oyizah da ya"yanta zuwa side din Affan,
saida tayi addu'a sannan ta shiga ciki ba tare da ta ďago kanta ba,
oyizah ta kalli Affan da ke binta a baya tace to bita zaizai wuce ka tafi daki,
Affan ya bata fuska yace ay nan ne yanzu ďaki na,
Salma ta daka mishi gigitaciyar tsawar da tasa shi fita da gudu, dariya suka watse dashi suka dawo da kallonsu kan Afeeyah,
oyizah ta ďago kumburarriyar fuskarta tana mata kallon banza tace "so called Amarya,"
farida ta kwashe da dariya tace su amarya man gyaďa,
salma ta hada rai tace kuna dariya ne, ay sai ta samu damar raina mu, mummy ki bata warning din da zaki bata mu wuce dan wallahi na mugun tsanar ganin yarinyar nan,
oyizah tace me kike ci na baka na zuba,
ta kalli Afeeyah tace nasan dalilinki na auren Affan bai wuce saboda dukiya ba, to kin makaro yarinya saboda ke da Affan kunyi ma juna nisa kamar tsakanin gabas da yamma saboda Affan is under my control sai abin da nace mishi,
Sannan kisa a ranki aikatau ne ya kawoki gidannan ba zaman aure ba,
salma tace gud mummy dama tunda "Gaje" mai aikin shegiyar mum din Affan ta tafi bamu kara samun mai aiki mai tsafta ba yanzu tunda mun samu wannan sai muyi manage,
oyizah kwarai kuwa, yanzu zan fara miki lissafin daily works din gidannan,
karfe 5 in kika tashi ba ruwana da sallarki in kinga dama kiyi in kinga dama ki barshi, fareeda tayi saurin cewa mummy wannan small gal din ma ay sallah bai wajabta akanta ba,
salma tace tell her ooo,
oyizah tace oho in taga zata wahalar da kanta tayi to tayi nidai amin aiki, girki shine first,
sai gyaran kitchen, gyaran ďakin yara, sai parlor,
tsakr gida da sauransu akwai maza masu yi,
Farida tace mummy wannan special secret flower bed din naki da nake bashi ruwa plss spare me ki kara mata shi a aikinta,
da sauri oyizah ta kai mata duka hade da yi mata dakuwa, farida ta toshe bakinta tace sorry mummy sannan ta fita da gudu,
oyizah ta gama lissafa wa Afeeyah duk aikin da zatayi a gidan hade da concrete warning na in ta saba aiki ko daya ne she will be in fr it,
Afeeyah dai gyada kanta kawai takeyi hawaye na kwaranya a idonta,
har sun sa kai zasu fita oyizah ta juyo tace lastly babu ruwanki da rayuwar Affan, ban yarda ku kebe tare ba bare har ki yaudareshi da wadannan shanyayun idanuwan naki,
salma tace haba mummy wannan mahaukacin meye zai rude shi,
oyizah ta harareta tace shi dutse ne ba mutum ba, mahaukata ma ay suna da feelings tunda akwai zuciya a kirjinsu, dan haka na horeki da kebewa dashi bare har--- ta yi saurin dafe kanta tace bana ma fata dan har abada,,,
salma tace har abada me, oyizah ta jata suka fita tace muje ďaki in faďa miki..


Suna fita Afeeyah ta fashe da kuka tana kiran sunan jabeer, kuka sosai takeyi har saida jiri ya fara dibanta sannan ta zauna bakin gado, saida ta gama tunane tunanenta sannan ta mike a zuciyarta tace Allah yasa yawan aikin da suka bani ya kasheni in huta,
drawer dake dakin ta bude zata sa akwatinta taga kaya masu tarin yawa wadanda ba dinkakku ba harda na bacci, cire hijab dinta tayi ta shiga bayin dake ďakin tayi wanka ta fito tana tsane kanta da towel,
tsawar da aka saki tayi daidai da bude kofar ďakin,
da sauri ta waigo tana kallonshi yana kokawa da mukullin kofar alamun yana saurin rufeta dan kar wani ya ganshi ......


Mrs tijjani shattima.....
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 4⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah


Kallonshi Afeeyah ta tsaya yi har ya rufe kofar ya waigo yana mata murmushi,
kau da kanta tayi ta janyo hijab dinta tasa ta zauna a gefen gado, karasowa yayi yana kaďa kanshi yana dariya ya tsuguna a gabanta ya daura hannunshi kan nata yace barbie yau kin dawo gidan mu ko,,
ta juyar da kanta gefe, ya taso ya zauna kusa da ita yayi narai2 da ido yace abokina ya faďa min kullum kina kuka da daddare meyasa kike kuka?


Afeeyah da idonta ya ciko da kwalla ta kasa ce mishi komai sai kallonshi da takeyi, hannu yasa ya share hawayen da ya digo a idonta yace ki mayar da hawayen nan dan Allah karkiyi kuka abokina zaice ni nasaki kuka in yazo,
Afeeyah ta kara fashewa da kuka a zuciyarta tana mai tausayawa ranar da Affan zai san jabeer ya bar duniya,
kukan shima ya fara yi kamar karamin yaro yana share mata hawaye,


wata tsawar aka sake saki mai firgitarwa kamar zata rusa gidan saboda kararta,
da sauri Affan ya shige jikinta ya kankameta haďe da runtse idonshi,
wani abu mai wuyar faďuwa yaji ya tsarga mishi a cikin kwakwalwarshi,
wani irin shauki ya dinga ji a can cikin jikinshi,
shi kanshi ya kasa fassara yanayin daya shiga a wannan lokacin,
Turashi Afeeyah ta farayi tana kokarin mikewa tasa kaya,
kara kankameta yayi dan bayason ya daina jin abinda yakeji,


kallon fuskarshi tayi a hankali taga idonshi a lumshe yana fitar da wani irin numfashi, tausayi ya bata sosai saboda yadda ya koma cikakken mutum a haka kafin anjima ya birkice ya koma tababbe,


a hankali ya bude idonshi da ya fara canza kala ya saukesu kan nata,
da sauri ta kauda kanta tace dan Allah ka sakeni in sa kaya bacci nakeji,


sakinta yayi cikin muryar lafiyayyan mutum yace "muje in tayaki sawa" cikin mamaki ta zaro manyan idanuwanta tana kallonshi,
murmushi yayi mata ya mike tsaye ya bude drawer ya dauko mata cotton night gown ya mika mata,
kasa amsa tayi tana mishi kallon mamaki, ajiye rigar yayi a jikinta ya hura iska cikin idonta yace ko ni zan sa miki da kaina,
tayi saurin kauda kanta ta ďauki rigar ta faďa bayi tana tunanin canzawarshi lokaci Guda,


tsaye ta sameshi gaban mudubi yana zana kanshi yana dariya,
ta mudubin ya hangota ya juyo da sauri ya janyota yace zo kigani na iya drawing mutum a mudubi, tsaya anan kigani,
Afeeyah ta girgiza kanta tace bacci nakeji,
ya girgiza kai a shagwabe yace ni sai kin tsaya,
Afeeyah ta haďe rai ta juya ta wuce kan gado ta kwanta,
zama yayi a kujerar dressing mirror yana kumbure2 yana kunkuni shi a dole an mishi laifi,


Ko kallonshi batayi ba tayi kwanciyarta ta shige bargo tana karanto adduoi,


muryarshi taji saitin kunnenta yana faďin
Niko?
Niko?
Ya faďi haka yafi sau goma Afeeyah tayi tsaki ta yaye bargon zata fara masifa hawayen da ta gani kwance a kuncinshi ya hanata, ta kalleshi murya a tausashe tace me nayi maka kake kuka,
ya kwanta kan cinyarta yace bake bace kika ki tsayawa inyi drawing dinki ba kuma kika tafi kika barni baki bani hakuri ba,
sai na fadama abokina ince barbien shi ta daina kirki yanzu,


Afeeyah tasa hannu ta share mishi hawaye tace kayi hakuri gobe zan tsaya yanzu bacci nakeji,
Affan ya ďago kanshi ya kalleta cikin ido yace ni bana jin bacci zaki rarrasheni inyi bacci,


Afeeyah ta dafe kanta kwalla ta cika idonta a zuciyarta tace ni kuma kaddara ta kenan, kwanciya tayi ba tare da ta bashi amsa ba tana hawaye tana hango da yanzu fa tana gidan masoyinta abin kaunarta jabeer,
hawa gadon Affan yayi ya kwantar da kanshi a bayanta, nan ta fashe da wani irin kukan da yasashi saurin kankameta yana rarrashinta,
runtse idonshi yayi yana sake jin abin da yaji dazu,


a hankali kwakwalwarshi ta fara daukar caji ya shiga shinshina jikinta yana lumlumshe ido,
kara matseta yayi lokacin da hannunshi ya sauka kan kirjinta a take ya saki ajiyar zuciya yana wani irin nishi,
cire hannunshi ta fara kokarin yi ta kasa saboda irin rikon da yayi mata, yafi minti biyar a haka yana sauke ajiyar zuciya yana sauraron kukanta da yake jinshi kamar waka a wannan lokacin,


mirginowa yayi ya ďago fuskarta idonta a rufe ya fara share mata hawaye haďe da bata hakuri,
bata bude idonta ba kuma bata tsayar da hawayen ba, kwantowa yayi ya haďa fuskarshi da tata yana gogawa a hankali,
cikin kuka ta bude baki zata fara masifah yayi saurin tura bakinshi cikin nata,
duk yadda taso fitar da bakinshi ta kasa saboda sam ya hanata damar hakan,


wani irin rikitaccan alamari ta dinga gani a tare da wanda tasan bashi da isashshen lafiyar kwakwalwa,
Shi kuwa Affan sam baya cikin hayyacinshi bare ya tantace a tsakanin duniyar mahaukata ko a ta lafiyayyu yake,
babu inda baya rawa a jikinshi, gani yakeyi kamar duk cikin wasa yakeyin abinda yakeyi sam ya kasa tsayawa da wannan wasan saboda ba kananan abubuwa yakeji na shauki a cikin jinin jikinshi ba,
a wannan lokacin duk iya kokarin turashi hade da kukan da Afeeyah takeyi bai sa ya daina ba saima shiga yin wasu abubuwa na daban da yayi dan a yadda yakejin kanshi in har ya daina wasannan da yakeyi to tabbas zai iya rasa ranshi,


wani irin kuka Afeeyah takeyi na takaici da bakar azaba tana kiran sunan jabeer dan abubuwan da Affan yake mata sun zarce tunaninta,


"Ni kaina danake dauko rahoto saida na tsorata nayi fitar da babu shiri harda buge kafa saboda sauri dan Affan ya matukar tsoratani yadda ya dinga sarrafa Afeeyah kamar cikakken mai hankali"


A bakin kofar na tsaya ina jiyo muku kukan Afeeyah wanda takeyinshi kamar ana yankata, sai karar ruwan sama da ake tsugashi kamar da bakin kwarya,,


barin kofar ďakin nayi na juya gurin da nake jiyo magana kasa2,


a hankali na karasa side din mummy wacce ta fito daga dakin alhj basheer,
tsaye na same ta a bakin kofar dakin da ta bawa Affan tana magana ita kadai tana fadin ina yaron nan ya shiga,
kardai yaron nan gurin yarinyar nan ya tafi, cikin bacin rai tayi kwafa ta kama hanyar side din Affan.......


Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:37] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 4⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah


Muryar alhj basheer taji da karfi yana faďin ina tea din yake ne safiya,
sai a sannan ta tuno da abinda ya fito da ita daga dakin har taga kofar Affan a bude,
hanyar kitchen ta nufa cikin gaggawa ta hado mishi tea ta koma dakin ta mika mishi, ya dafe kanshi yace ina maganin,
da sauri tace ba kai ka ajiyeshi ba,
yayi tsaki yace na manta inda na ajiyeshi duba min ko cikin drawer ko kan mudubi, cikin bacin rai oyizah ta fara duba maganin da kyar ta ganoshi a drawer gefen gadonshi ta mika mishi da sauri, ya kalleta yace yau ko ballo min maganin baza'ayi ba,
ta amsa ta babbalo mishi ta mika mishi tayi hanyar kofa,
Alhj basheer yace wai ina zaki je ne kiketa sauri haka,
juyowa tayi tace umm na manta ban bawa Affan maganinshi ba, yayi murmushi yace karki damu dazu da kuna gurin Amarya na shiga na bashi,
oyizah tace ka tabbatar dai2 ka bashi,
alhj basheer yace kwarai kuwa dawo kiyi min tausa,
oyizah ta dawo ranta a bace ta fara mishi tausa tana tunanin abinda ya kai Affan dakin da aka kai amarya,
wasu irin tunani ta dinga yi dan tasan illar kebantuwar mace da namiji a guri,
wani irin ihu tayi ta diro a gado tana fadin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login