Showing 63001 words to 66000 words out of 72718 words
Chapter 22 - RABO AJALI COMPLETE DOCUMENT BY Aisha Ya'u kura.txt
ciwon ido,!
nan ya takaita mishi duk yadda akayi ya auri Afeeyah da kuma irin taimkon da tayi mishi,
zaman dirshan Affan yayi yana kuka sosai yace kaka babu mamaki itama bazata rayu ba don gata can sun ritsata a daki zasu kasheta,
innalilliahi W.I.I.R kadai kaka liman ke iya fada yana sauraren kukan da Affan keyi,
a hankali yace ka kwantar hankalinki Allah zai kareta ko don Rabon dake jikinta,
karar da tayi ne yasa shi saurin kashe wayar ya mike zai fito yaji mahaifinshi ma ya fito, jingina yayi da bango yana zubar da hawaye har suka fita da ita suka sata cikin mota,
kara kira kaka liman yayi Affan ya dauka yace ta kasheta kaka, gashi can sun tafi kaita asibiti da daddy,
da sauri kaka liman yace bata mutu ba,
na fada maka bazata mutu ba sai wannan rabon ya taka duniya, kayi saurin bin su karka sake ka barta ita da wannan matar dan zata iya yi mata illah, kuma karka nuna ma kowa kaji sauki domin yin hakan kamar ka bata goma ne daya bata gyaru ba,
da sauri Affan ya fita, musababbin binsu asibitin kenan,
ajiyar zuciya nayi dana gama tariyowa sai kuma nayi gaba har zuwa inda na tsaya muku wato inda Affan ke kuka yana fadin sai ya dau fansa....
Allah ya baka ikon karasa yakin nan Affan domin wannan kawar Bilki Nabayin Hatsabibiyace.....
Mrs tijjani shattima......
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣0⃣ By Aysha Ya'u Kurah
Tafe take cikin motarta tana neman tsohon almajirin da zata bashi sadaka ta saceshi ta kaima chummy suyi bandaro da jininshi domin ta samu sa'ar kashe Afeeyah,,
tana karya kwanar Gyaďi2 ta ga wani tsohon almajiri tukuf da kwaryar bara a hannunshi,
parking tayi ta sakko ta dunkule dubu biyu hade da farin kyalle ta bashi,
godiya ya dinga mata sannan ya juya mata baya, nan take ya bace ma ganinta,
cikin murna ta shige mota dan duk tunaninta hakanta ne ya cimma ruwa,
da murnarta ta koma gida ta wuce dakinta ta rage kayan jikinta, muryar Alhj basheer taji yana kwala mata kirah da karfi,
da sauri ta fito dan jin abinda ya faru, kauda kanshi yayi dan a yan kwanakin nan sam baya kaunar ganin fuskarta wani lokaci ma tambayar kanshi yakeyi daliilin da yasa ya aureta,
mutunta ta kawai yakeyi saboda darajar aure da kuma yarshi, badan haka ba da tuni yayi ma kanshi katanga da ita,
kallonshi tayi tace alhj ka kirani kuma kayi shuru,
yace eh baki zanyi daga cameroon zuwa anjima,
ina son ayi musu girki, ta bata rai dan ta tsani wani dan uwan alhj basheer ya rabeshi tace to naji sannan ta wuce daki tace wallhy taliya zan kwaba ma tsinannun..
Har bayan magriba baki ba su zo ba sai da akayi isha'i sannan motarsu tayi parking a kofar gidan Alhaji Basheer Balarabe (BB), su hudu ne suka fara shigowa, mata biyu maza biyu,
a parlon suka zauna alhj basheer ya tsuguna ya gaisar da baffa da dayan bakon cikin girmamawa, sannan ya kalli matan suka gaisa ya kure daya daga cikinsu da ido yace kamar nasanki,
tayi dariya zatayi magana oyizah ta fito tana ya tsina,
dakyar ta gaida baffa shima dakyar ya amsa dan kar ace bai amsa ba,
sannan tabi matan da kallon raini tace sann--- muryarta ta sarke saboda ganin Gaje da tayi,
cikin mamaki tace gaje,
gaje ta dago tace na'am,
oyizah tace long time ina kika shiga haka tsawon shekaru uku babu ko zuwa duba mu,
Gaje tace walhy kuwa aure nayi shiyasa, oyizah ta tabe baki tace na miki murna,
bari a kawo muku abinci,
Baffa ya kalli alhj basheer yace labarin zeenatu har yanzu shuru ko?
Alhj basheer yace wallhy kuwa baffa, amma mun baza addu'a ana nan anayi kuma muna sa ran in shaa Allahu zata bayyana,
oyizah tayi murmushi a zuciyarta sannan a fili tace alhj in ta mutu fa,
shekara uku mutum ya bace har yanzu babu labari ay ni ina ganin ta mutu,
Baffa ya galla mata harara yace bashiru ina ganin Allah ya amsa addu'armu dan kuwa na samu labarin inda zeenatu take,
saboda firgici oyizah saida ta kusa karya kujerar da take kai, zaro ido tayi tace kana da labarinta,
Baffa ya kalli cikin idonta yace kwarai kuwa inada labarinta mai karfi ko kuma ince ina tare da ita ma,
alhj basheer ya dafa kafar Baffa cikin rawar murya yace tana ina Baffa,
kafin baffa yayi magana an murďa kofar palourn an shigo, da sauri alhj basheer da oyizah suka daga idonsu ya sauka kan zeenatu da tayi wata irin muguwar rama,
da sauri ya mike yana fadin z-e-e-natu, Abida da yadikko dake rike da ita suka nemi guri suka zauna, gabanta ya karaso ya kamo hannunta saboda ya gasgata ita din ce,
murmushi Abida tayi tace ita ce alhj zeenatun ka ce matarka kuma uwar danka,
Allah yayi zaku kuma ganawa,
alhj basheer ya tsuguna a gabanta idonshi ya ciko da kwalla yace ina kika shiga zeenatu,
idonta ya ciko da kwalla ta kalli gurin da oyizah ta sankare a tsaye tace na shiga cikin ukubar da bawa baya iya fitar da danuwansa bawa saidai Allah ya fitar dashi,
an so kasheni amma da yake shan ruwana bai kare ba sai gashi Allah ya dawo dani bayan mutuwar danayi ta dan lokaci,
mikewa tayi a hankali kamar zata fadi saboda rama, ta karasa kusa da oyizah tace ribar me kikaci a wannan izayar da kikayi mana,
me kika samu mai amfani bayan tafiyarmu,
meyasa zuciyarki ta zabi ta dinga kisan kai akan abun duniya da zaki tafi ki barshi a duniyar,
meye ribarki dan na mutu ni da ďana ke kuma kina rayuwa keda yayanki,
ki sani safiya Allah na kare wanda yaso a lokacin da yaso, kin---- oyizah tayi saurin katseta cikin tsawa tace duk wadannan maganganun na menene,
ina ruwana dake da zan kasheki, me kikayi min,
ta fara kukan munafurci ta matso kusa da alhj basheer tace sharri zatayi min dan kawai ta shiga duniya ta kwaso cutar kanjamau shine zata ce ni nayi niyyar kasheta,
alhj inda zan kasheta da Affan shekararshi nawa ina kula dashi ban kasheshi ba,
ba'ayi min godiyar kula dashi ba sai dai a bini da sakayyar sharri,
kan alhj basheer ya ďaure sosai yace wai meke faruwa ne, zeenatu zata fara magana
"Affan ya fito yace ni zan faďa maka duk abinda ke faruwa daddy"
cikin mamaki suka mai da kallonsu kan Affan,
karasowa yayi ya rungume zeenatu yana faďin baki mutu ba umma,
ta dago fuskarshi tana shafawa tace kaima baka mutu ba, ashe kana nan da ranka Affan,
kuka sosai suka dinga yi na tsawon mintuna,
alhj basheer ya janyo Affan cikin mamaki yana shafa kanshi yace kaji sauki ne Affan,
Affan ya gyaďa kanshi yace na dawo cikin hayyacina daddy,
Allah ya kwatoni daga hannun wannan azzalumar da take kiran kanta matarka,
farida da shigowarta parlon kenan ta karaso da sauri ta buge hannun Affan tace karka kara zagar min mahaifiya,
Affan yayi mata wani irin kallo yace kice kar in kara zagar miki matsafiyya ba mahaifiyya ba,
oyizah ta sa kuka tace alhj kanajin sharrin da danka yake min, ko da yake bazan ga laifinshi ba dan nasan mahaukaci ne shi baya cikin hayyacinshi,
alhj basheer dai kanshi ya ďaure yace dan Allah karku rikirkitani, ku fada min abinda ke faruwa,
Baffa ya kalli Affan yace zauna Affan bari mu fara jin komai daga bakin mahaifiyarka
sai muji naka..
Mrs tijjani shattima....
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣1⃣ By Aysha Ya'u Kurah
A hankali zeenatu ta fara jawabinta kamar haka...
Ranar asabar bayan sallar isha'i ina zaune a daki sai naji kamar ana ihu acan sama gurin shan iska,
da sauri na mike na isa gurin dan duk tunanina Affan ne a gurin shi da jabeer dan mun rabu dashi zaije gurin jabeer,
ina isa gurin naga wasu kartin maza zaune kan wani jan kyalle da wani jan kaya a jikinsu,
juyawa nayi da sauri zan koma daki saboda sun matukar bani tsoro,
ina juyowa naga safiya cikin jajayen kayan itama tana dariya,
da sauri naja baya ina ambaton sunanta sai naji saukar sanda a tsakiyar kaina,
dishi2 na fara gani ina salati ina neman dauki gurin Allah,
cikin karaji naji muryar safiya tana fadin kunji ko addu'a takeyi na faďa muku wannan sai kunyi da gaske saboda nasha yin aiki akanta yana lalacewa,
jin haka yasani sake bude wani shafin na addu'a, sai naji sun ďaga ni, daya ya bankareni yana faďin zo ka shake mata wuya muga ta inda addu'ar zata fito,
da sauri ya matso ya matsemin wuya inata kakari na hango wata katuwar wuka a hannun safiya tana faďin wannan gara kawai mu kasheta sai mu kaita asha jininta, tana kokarin daura wukar a wuyana muka ji ihun Affan,
da sauri ta yar da wukar su kuma suka sakeni na faďa kan wani farin kyalle,
daga nan ban kara sanin inda kaina yake ba saida na ganni gaban wata mata wacce halittarta kaďai ta isa ta tsoratar da mai rai,
ajiyeni tayi a wani daki tana faďin yau dake zamuyi dinner,
tana fita naga wasu yara su biyu sun shigo dasauri suka tanbayeni wa ya kawo ni nan,
cikin rawar murya na ce musu kishiyata ce,
daya daga cikinsu tace nasan oyee ce dan bata da mutunci tunda ta kawo uwarta kowa ma zata kawo,
dayar tace har wani karamin yaro ma ta kawo lokacin da take neman cikin ďa namiji,
cikin sauri suka ce in tashi zasu fitar dani, da sauri na mike ina tambayarsu su bazasu tafi ba,
amsar da suka bani tasani zubar musu da hawaye sukace sunfi shekara ashirin a haka, yanzu gangar jikinsu ya riga ya zama kasa,
wani hanya suka nuna min nayi saurin bi na dawo jikina,
dakyar na iya mikewa ina kallon sanda suka dauki Affan zasu jefoshi daga sama su karasa shi dan kar ya tona musu asiri,
da sauri na fito dan kar su ganni na sakko kasa ina bin bango ina neman wanda zaizo ya taimaki ďana dan karsu kasheshi,
a kofar kitchen na hadu da Gaje ta dawo daukar sakon da safiya ta aiketa dashi,
da sauri ta rikeni tana tambayata,
dakyar na iya takaita mata, na kuma ce dan Allah ta dauko min Aff--- ban karasa faďi ba naji karar saukar mutum kasa da karfi, tun daga lokacin ban kara sanin inda kaina yake ba sai kwana biyar da suka wuce,,
ta karasa tana kuka mai tsuma zuciya,,
Ajiyar zuciya Gaje tayi tace kwarai abun da ya faru kenan dan tana faďuwa nayi saurin janta store saboda jin muryar madam da nayi ta sakko nemanta,
munfi minti talatin a store sannan na daukota na fito da ita da sauri dan kar wani ya ganni,
ina fitowa naga wani me keke napep a kofar gidan alhj bara'u, dasauri na karasa nasata nace ya kaini dorayi gidan kawu na,
bai tsaya musun kudi ba saboda ganin halin da muke ciki,
tafiya sosai mukayi har muka iso nace ya jirani,
ďakin matar kawuna na kaita nace dan Allah su kular min da ita kafin gobe da safe,
ba musu tace ba komai saboda sunsan irin alherin da hajiya ke musu,
sai kusan goma na koma gidan,
ranar a tsorace na kwana,, washe gari ina tashi na tattara kaya na nayi ma madam karya nace mata mahaifina bashi da lafiya acan nijar,
kudi ta bani tace Allah ya bashi lafiya tare da jaddada min in dawo da zarar ya samu sauki,
amsata kawai nayi na fita daga gidan na wuce ďorayi,
a ranar muka wuce nijar ni da hajiya dan nasan acan ne zata fi samun kulawa saboda kawuna malamine,
babu irin addu'ar da ba'ayi ba amma sam babu sauki dan ko motsi batayi,
A can na barta na dawo jigawa ina wani aikin, har Allah ya hadani da wani mukayi aure,
yau kwanana biyar da zuwa gida na tarar ta farfado,
shekaran jiya ne ta matsa ita akaita can gidansu a cameroon,
bamu so mu kaita ba har saita kara samun sauki amma malam yace lallai mu kaita saboda ta samu nutsuwa,
a can cameroon da muka je ta labarta ma mahaifinta komai shine yace a shirya a taho nan kano domin a fayyace komai dan kar aja lokaci a kuma kullo wani mugun abun da zai fi na da..
Cikin tashin hankali oyizah tayi kukan kurah ta shako wuyan zeenatu tana fadin ni zakuyi ma sharri wallahy yau sai na kasheki,
da sauri Affan ya taso ya banbare mahaifiyarshi a jikin oyizah ya shiga dukanta yana haki yana fadin duk abubuwan da tayi mishi da kuma wanda tayi ma Afeeyah da kuma kisan da tayi ma jabeer,
shaketa yayi idonshi yayi jawur cikin ďaga murya yace me jabeer yayi miki kika kasheshi,
kakarin wuya oyizah keyi idonta sun firfito waje tana girgiza kanta,
babu wanda yayi yunkurin hana Affan har farida da kuka yaci karfinta saboda jin mugun alkaba'in da mahaifiyarta tayi,
zeenatu ce ta taso da sauri ta fara banbareshi a jikinta saboda kar yayi kisan kai,
dakyar ya rabu da ita yana haki idonshi cike da kwalla,
mikewa oyizah tayi ta ruga dakinta da gudu tana haki kamar zata mutu,
tana shiga ta bankade katifarta da katakon, tana dagawa taga babu komai cikin ramin sai kasa,
da sauri tasa hannu tana tone kasar ciki kamar mahaukaciya tana fadin ina kuke, waye ya kwashe ku,
wayyo Allah na shiga uku na lalace,
buga kofar ďakin taji anayi da karfi kamar za'a ballata,
a hankali ta leka ta windon don ganin ko waye,
yansanda ta gani tsaye su kusan shida da mace daya,
dariya ta saki wacce da gani kasan ta takaici ce ta jawo jakar kayan tsafinta nan da nan ta bace daga ďakin....
Mrs tijjani shattima...
[15/12 09:38] Anty aisha ya'u kura: ◆◆ RABO AJALI ◆◆ 6⃣2⃣ By Aysha Ya'u kurah
Yan sandan sunfi minti goma a tsaye suna bugawa ba'a buďe ba,
cikin sanyin jiki alhj basheer ya taso ya dauko wani key yasa ya bude,
wayam suka gani ba oyizah ba sawunta sai katon ramin karkashin gadonta ne yayi musu sallama a idanuwansu,
alhj basheer idonshi ya kara ja yace jikina ya bani zata gudu dan shaidancinta bazai kare anan gurin ba,
da kun bar Affan ya kasheta mun huta dan yanzu wallahi bazata kyalemu ba,
malam maina ya taso yace ka kwantar da hankalinka in shaa Allahu babu abinda zai faru,
zamu toshe duk wata kafar da zata samu shigowa rayuwarku da addu'a,
alhj basheer ya sharce gumin goshinshi yace to Allah yasa, Ameen duk mutanen gurin suka ce,
Alhj basheer ya kalli Affan ya dawo kusa dashi yace Affan dama duk abinda kakeyi kana sane,
Affan ya girgiza kanshi yace ranar da mummy tayi niyyar kashe Afeeyah ranar na dawo hayyacina da taimakon Allah da taimakon Afeeyah,
nan ya kwashe duk labarin da kaka liman ya bashi na irin kokarin da Afeeyah tayi akansu ya fada musu sannan ya kuma faďa musu dalilin da yasa mummy ta kashe jabeer,,
ya share hawayen fuskarshi yace daddy dalilin da yasa kaga naki tafiya in bar Afeeyah a asibiti kenan saboda nasan muna barin gurin zata karasa ta,
doctr musah ma yasan na samu sauki saboda washe gari da mummy ta matsa sai mun tafi naje na sameshi na fada mishi komai nace ya taimakeni ya dauketa yace su zasu dinga jinyarta,
da kyar ya yarda dan a tunaninshi ban samu sauki ba shirme nake mishi,
muna tafiya yace min yaje dakin dan ya gasgata maganata sai ya tarar ta cire pillow tana kokarin kashe ta,
hankalinshi ya tashi a lokacin sai ya tabbatar naji sauki shine ya shirya plan din za'a kaita dakin hutu,
alhj basheer ya jinjina kanshi hawaye na fita a idonshi yana faďin ku yafe min, duk ni na jawo muku da na shigo da safiyya cikin iyalina,
gashi bata tsaya kai na ba har saida ta taba ya'yan makota na, dan Allah kuyi min afuwa ku dau duk wani hukuncin da ya dace a kaina,
zeenatu tace ka daina kuka alhj ba laifinka bane RABO ne ya shigo da ita rayuwarka, Rabon salma da Farida zai iya AJALIN duk wanda ya hana wannan auren a lokacin,
cikin kuka alhj basheer yace tabbas ya ko yi ajalin mahaifiyarta dan taki amincewa da zancen,
ashe safiyar ce ma ta kasheta da hannunta,
Affan yace har Anty salma itace silar mutuwarta dan jiya da mukayi waya da kaka duk ya faďa min hatsaririkan da Afeeyah ta tsallake a gidan nan,
mamakin alamarin kowa ya dinga yi haďe da ganin jarumta da jajurcewar Afeeyah,
Abida dai banda kuka babu abinda takeyi dan mutuwar jabeer ta dawo mata sabuwa fill a yau,
tabbas da an barta ita da hannunta zata kasheta ta huce takaicin rabata da nagartaccen ďanta mai cike da Haiba da tayi..,
Cikin kuka fareeda ta matso kusa da Affan tace dan Allah Affan ka yafe min abin da nayi maka wallahy sharrin shaidan ne da kuma ganin mummy nayi,
Affan ya janye kafarshi ya galla mata harara,
cikin tsawa alhj basheer yace tashi ki bamu guri yau dinnan zaki bi uwarki dan ban sani ba ko ke din ma ta tsafin ce,
fareeda ta rushe da kuka tana bashi hakuri, a hankali zeenatu tace alhj laifin wani baya shafar wani,
duk wanda yaga farida yaga jininka dan haka hannunka bazai rube ba ka yanke ka yar ba,
alhj basheer yayi saurin cewa saidai kuwa in bai isheni da wari ba,
yanzu ke kina so in zauna da jinsin matsafa a gida,
Baffa yace bashiru hakuri zakayi ya' dai taka ce dan haka dole ka riketa ku koya mata tarbiyar da addini ya koyar kuma ku aurar da ita,
nan suka cigaba tattauna maganar cikin tsananin al'ajabi....
Cikin tashin hankali oyizah ta bayyana a gurin tsafinsu,
kuka sosai takeyi a gaban chummy tana faďa mata duk yadda akayi har dawowar zeenatu da