Showing 144001 words to 147000 words out of 184930 words
Chapter 49 - SHU'UMIN NAMIJI Book Complete by Phatyma Sardauna.txt
iyaye da kakanninmu kenan!" Dr.Bilal yafaɗi haka yana me tattara nutsuwarsa ga Dad.
Gumi kawai Alhaji Ma'aruf ke sharewa sai ambatan
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!" yakeyi gaba ɗaya ji yayi duniyar tayi masa nauyi.
"Doctor menene mafita?" Dad yatambayi Dr.Bilal cikin sanyayewar guiwa.
"A yanzu kam dai bamu da mafita Alhaji Ma'aruf, sai dai mujira muga me Allah zaiyi, wataƙila Zaid zai iyakaiwa kwana uku batare daya farka ba, wataƙila kuma ko nanda kwana biyu ya farka, amma yazama dole ku kula dashi, yanzu bakamar da bane, yanzu abu kaɗan na ɓata masa rai zuciyarsa zata hau zafi, sannan kuma idan ya yawaita yin tunani to fa akwai babbar matsala, yazama dole ku tsaya akansa ku lura, akwai magungunan dazan rubuta muku, idan yatsaya akansu insha Allah zasu taimaka masa sosai."
Sai alokacin Alhaji Ma'aruf ya ɗanji sanyi acikin ransa.
"Nagode ƙwarai Dr.Bilal kuma Insha ALLAH zamu kiyaye sosai!" Dad yafaɗi haka yana me miƙewa tsaye. Musabaha sukayi da Dr.Bilal kafun ya fice acikin office ɗin.
*****
A daddafe ta tashi tayi sallan isha. Tana kan sallayan bata tashiba yashigo cikin ɗakin, idanunta ta zuba masa, bada kayan da yafita ya dawo ba, yanzu rigane da wando na jeans ajikinsa, kallonsa takeyi kamar wani wanda bata taɓa ganinsa ba, shima kallonta yayi haɗe da yi mata murmushi, ya wuce cikin bathroom, mintuna kaɗan yafito daga cikin bathroom ɗin.
"Kizo kici abinci" yana faɗa mata haka yafice daga cikin ɗakin.
Wani irin kunyan sa ne yaka mata, amma kuma babu yanda zatayi, abundake cikin zuciyarta ta faɗa.
Miƙewa tayi sumi sumi ko hijab ɗin dake jikinta bata cire ba ta fita zuwa falo.
Zama tayi akan sofa kusa da inda yake zaune, haɗe da takure jikinta waje ɗaya, shawarma ne da gasashshen kifi (roasted fish) ya sayo musu, tura mata plate ɗin yayi gabanta.
"Kici sai kisha magani" yafaɗi haka fuskarsa ɗauke da ɗan murmushi, kallonsa tayi kamar zatace dashi wani abu kuma saita fasa tasoma cin abincin da kaɗan kaɗan. Shikuwa sannu a hankali yake sipping country yoghurt ɗinsa yana me kuma latsa wayarsa.
Haka suka zauna shiru babu me cewa da ɗan uwansa ƙala.
Tana kammala cin abincin ya bata wasu magunguna daya shigo dasu, babu musu ta amsa tasha. Ganin yatashi yabar falonne yasanya itama ta tashi ta koma ɗaki, wanka tayi kana ta fito ta sanya wata sleeping gown wacce ta tsaya iyaka cinyarta, ko guiwa bata ƙarasa ba, sosai rigar tayi mata kyau ta kuma fito da farar fatarta fili, dogon gashinta ta kama ta tubke a tsakiyar kanta haɗe da ɗaureshi da ribbon, turarenta me daɗin ƙamshi ta shafa, tana nan tsaye a cikin ɗakin yaturo ƙofar ɗakin yashigo.
Wani irin yawu ya haɗiye a maƙoshinsa, sanda idanunsa sukayi masa tozali da ita, sosai tayi kyau acikin rigar, ga fararen cinyoyinta sun bayyana kansu a fili, da ƙyar ya iya daure zuciyarsa, murmushi kawai yayi mata haɗe da kawar da kansa gefe, shi kaɗai yasan me yakeji acikin zuciyarsa, yana tsananin kishin matarsa, kamar yanda yake tsananin sonta.
Kan gado ta koma ta kwanta, agogon hanunsa yacire haɗe da cire rigarsa, 3 guater jeans yasanya..
Zama yayi a gefen gadon haɗe da jawo laptop ɗinsa yasamo dannawa, dama yanada ayyukan da suka masa yawa yanaso ya ɗan ragesu, bayaso ya kwanta shiru tunani ya damesa.
Hanu tasa ta share hawayen dake fitowa daga cikin idanunta.
"fushi Dr.Sadeeq yakeyi da ita kenan?" tambayar da take ta yiwa kanta tun ɗazu kenan, bazata iya jure fushinsa akanta ba, duk da baifito ya nuna mata hakan afili ba, amma duk wasu alamu sun nuna hakan, bayason yi mata magana me tsawo sannan kuma baya sake mata kamar yanda ya saba, idan tabarsa haka batayi masa adalci ba, ayanzu bata da wani wanda ya wuce mata shi, shi ɗinne dai komai nata, bazata iya ɗaukar fushinsa akanta ba.
Aikinsa yake cikin nutsuwa amma kuma gaba ɗaya tunaninsa akanta yake, ba abun dayafi damunsa kamar cutar hawanjini dake da munta, yasani sarai cutar hawan jini bata da kyau tana cutarwa sosai, musamman ma ga yarinya kamarta hakan yasa yake tsananin tausayinta.
Baizataba saiji yayi ta rungumeshi ta baya, haɗe da ɗaura kanta akan wuyanshi, me makon tace wani abu sai kawai ta fashe masa da kukan shagawaɓa.
Lumshe idanunsa yayi har a cikin zuciyarsa bayason kukanta idan tana kuka hankalinsa tashi yake.
Jawota yayi ta dawo gabansa.
"Menene?" yatambayeta yana me ɗora idanunsa akanta.
"Bazan iya jure fushinka ba, dan Allah kayi haƙuri wallahi inasonka banason kajuyamin baya, banda kowa sama da kai, idan kajuyamin baya bansan yanda rayuwata zata kasance ba, kayi hakuri kaji!!" kuka take sosai alokacin da take faɗar maganar.
Wani irin sanyine yaji yana ratsa zuciyarsa kalmar "Wallahi tana son shi" da ta faɗa yafi komai da ɗaɗa masa rai, yaji daɗin maganar sosai, amma sai ya dake bainuna mata hakan afili ba.
"Ni nace miki ina fushi dake ne?" abunda yatambaya kenan.
Da sauri tashiga kaɗa kanta alamar "Eh"
Cike da mamaki yace "yaushe nace haka?"
"Kaine kake bani abinci abakina harsai na ƙoshi, amma yau turamin abincin gabana kayi kace naci ni kaɗai, sannan tunda kafita baka dawo gidan nan ba, gashi kazo baka kulani ba saima laptop ɗinka daka fara latsawa, kasabarmin bazan iya jurewa ba, dan Allah kada kayi fushi dani naroƙeka, bazan iya samun nutsuwa ba matuƙar baka tare dani, bazan iya zama dakowa ba bayan kai, inasonka sosai!"
Tunda ta fara maganar yake kallon ɗan ƙaramin bakinta hartakai ƙarshe.
Jawota yayi jikinsa, haɗe da sake lumshe idanunsa, sun kai kusan mintuna uku a haka, babu wanda yasakeyin magana kafun ta ɗago kanta daga cikin ƙirjinsa. Buɗe idanunsa yayi ya sauƙesu acikin nata, kallon juna sukeyi cikin wani irin yanayi me wuyar fassaruwa, ahankali ta matso da fuskarta daf da tashi haɗe da lumshe idanunta, bakinta ta buɗe ahankali ta ɗaura harshenta akan lips ɗinsa, jiyayi kamar anjona masa shocking ajikinsa, ahankali ta tura harshenta cikin bakinsa tana me yawo dashi, kasa jurewa yayi cikin hali na zaƙuwa ya kama harshenta yashiga tsotsa.. Sosai suke kissing ɗin junansu, numfashinsu har ƙoƙarin ƙwace musu yake. Igiyar dake gaban rigarta yaja take rigar ta buɗe ta gaba, sake lumshe idanunsa yayi haɗe da fitar da wani irin numfashi me sauti alokacin da idanunsa suka sauƙa akan breast ɗinta, kansa ya cusa acikin ƙirjinta yana kai mata kiss tako ina.. Cikin mintuna ƙalilan Dr.Sadeeq da Zahrah suka fice a cikin hayyacinsu babu ma kamar doctor, gaba ɗaya idanunsa sun rufe numfashi kawai yake fitarwa ta bakinsa... Soyayyar su tayau ta da bance, yau tsantsar soyayya ya gwada mata wacce tasa ta manta komai acikin duniya har batasan sanda hawaye suka gama wanke mata fuska ba, shi ma kansa yau yazautu da tsananin kulawan data basa, ita kanta mamakin yanda yake shiɗewa akanta take, sai dai kuma idan ta tuno cewa ko wacce mace da irin baiwar da ALLAH ya mata saitaji sanyi acikin ranta, ko a iya nan aka tsaya, zata ta godemawa ALLAH ...
Cike da shagwaɓa ta ture kanshi dake kan breast ɗinta. "So kake ka ciremin nipples ɗina ne wai?"
Duk da haryanzu yana acikin magagin duniyar daɗin dayashiga bai sake saba amma saida yayi dariya.
"Dama Nipples yana fita ne?" shima yatambayeta cike da mamaki, domin a iya tsawon rayuwarsa shi bai taɓajin inda akace nipples yafita daga jikin breast ba.
"To bakai bane tun ɗazu fa kaketa sha, kuma zafi yakemin!" araunace tafaɗi maganar.
"To ba nipples din bane yace yana sona!" yafaɗi haka yana me kwaikwayon yanayin maganarta.
Dariyane yakamata sosai, da ƙyar ta samu ta zame hanunsa dake kan breast ɗin nata, tana ƙoƙarin tashi yayi saurin kamota ya kwantar da ita, kwanciya yayi asamanta haɗe da sakarmata duka nauyinsa.
Ɗan ƙaran wahala tasake haɗe da lumshe idanunta.
"Ina da nauyi ne? ke ɗazu da kika hau kaina ai bance kina da nauyi ba"
"To ae ɗazu banice na hau kanka ba kaine ka ɗaukeni ka ɗaurani akan ka batare da nace inaso ba"
"To amma dana ɗauraki wayace ki sakemin duka nauyinki harma da kama min....."
Da sauri ta sanya hanu ta toshemai baki bataso ya faɗi abun da tayi masa, ita kanta batasan tayi masa haka ba alokacin tana wata duniyarne na daban. (Khair uwar gulma harkin baza kunnuwa kiji metayi ko, to bazakiji ba nima banji ba balle ke😂)
"INASONKA!!!" Zahrah tafaɗa cikin wata irin murya me ɗauke da tsananin shauƙi.
"Nima INASONKI!!!" shima yafaɗa cike da tsananin ƙauna, wani irin kallo sukayiwa junansu, cike da sha'awar juna suka sake haɗe bakinsu waje ɗaya.......
(Zahrah da Doctor fa sun zama one love ga soyayya ga jaraba, doctor ya koya mata🤭)
*Vote*
*Vote*
*Voted please🙏*
*(Comment and vote please my lovely fans, my wattpadians idan kun karanta kuna min vote kunji😥)*
*Happy New Month*
*Saturday 1/January/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 105*
*ZAID*
Kwanansa biyu acikin asibitin kafun ya samu ya dawo cikin hayyacinsa, sai dai kuma tunda ya dawo hayyacinsa baice da kowa komai ba, ko su Dad ɗinsa da sukeyi masa ya jiki, da kai kawai yake amsa musu, shikaɗai yasan meyakeji acikin jiki da zuciyarsa.
Zaune yake akan gadon asibitin yayi jigum, babu wani abu dake yi masa daɗi acikin duniya, Matakin daya ɗaukarwa zuciyarsa yayi masa tsauri sosai, a haƙiƙanin gaskiya yasan yaudaran kansa yake, cire soyayyar Zahrah acikin zuciyarsa, ba abu bane me sauƙi, yana sonta so sosai, so irin wanda ba a misaltashi, so ne dayakai ƙololuwa, ko ina acikin zuciyarsa tambarine na ƙaunarta, rumtse jajayen idanunsa yayi haɗe da sanya haƙuransa ya ciji laɓɓansa, dai dai lokacin aka turo ƙofar ɗakin aka shigo, ko kallon bakin ƙofar baiyi ba, balle yaga waye ne yashigo cikin ɗakin.
Turus haka Afrah taja ta tsaya tana me ƙaremasa kallo, mugun tsoronsa takeji, yanzuma Momynsa ce tace tazo ta duba ya jikin nasa shiyasa ta shigo, amma da bazata shigo ba. Karambani irin na Afrah yasanya taɗan matsa kusa dashi cikin murya me sanyi tace.
"My Dear yajikin naka?"
Da sauri ya buɗe jajayen idanunsa ya watsa mata su, take jikin Afrah ya soma rawa, tsananin tsanarta tahango acikin ƙwayar idanunsa, yanayin yanda taga idanunsa sunyi ja shi kaɗai ya isa firgita mutum, da sauri ta juya tafice a ɗakin, zuciyarta cike tab da sabon tsoronsa, gani take kamar zai tsaidata ya jibgeta, aitana tsintar kanta a wajen ɗakin tashiga sauƙe ajiyar zuciya akai akai...
Shikuwa idanunsa ya maida ya rufe, wani irin ɗaci yakeji acikin maƙoshinsa, yayinda ransa yakai ƙololuwa wajen ɓaci, hakanan shikam Allah ya ɗaura masa tsanar yarinyar dako sunanta ma baisani ba, anzo anwani ƙaƙa ba masa ita amatsayin mata. "Shegiya me ƙananan idanu, daganinta munafukace" yafaɗi haka acikin zuciyarsa, jingina kansa yayi da bango, yaci gaba da tunanin yanda zai samawa rayuwarsa salama...
*****
Gyara zama Husnah tayi haɗe da miƙa duk wata nutsuwarta ga Zahrah.
"Kina mamakina ko Husnah? nasan dole dama zakiyi mamaki, amma kuma idan kika yi tunani me kyau tawani wajen baizama abun mamaki ba"
Zahrah tafaɗi haka da iyaka gaskiyarta, saboda ita yanzu tama daina mamakin kanta kwata kwata.
"Dole ne zanyi mamakinki Zahrah, wani irin so ne haka kikeyiwa wanda ya tozarta rayuwarki? bazan tuna miki abun da Zaid yayi miki ba, saboda na tabbata har kikoma ga Allah bazaki daina jin ciwon abun da Zaid yayi miki acikin zuciyarki ba, a gaskiya bana ma tunanin kinacikin hankalinki Zahra, saboda baidace ace kina da aure akanki, kuma kina zancen wani daban ba mijin kiba"
Husnah tafaɗi haka cikin yanayi dake nuna ranta ya ɗan ɓaci da jin kalaman Zahrah.
Wani irin murmushi Zahrah tayi haɗe da sanya hanunta akan kafaɗan Husnah.
"Nasan dole zakiji haushina Husnah, amma kafun ke kiji haushina ninafara jin haushin kaina, ada nayi tunanin cewa banda hankaline, amma daga baya nagane cewa so so ne, kinsani nima kuma nasani so bayashawartarka kafun yashiga zuciyarka, so baruwansa da anzalunceka ko kuma kazalunta, shidai so so ne a kullum haka yake baya tambayarka shawara idan zai saka ka aikata wani abu, hakanan baya kuma sanjawa, shi ɗinne dai akullum akuma ko da yaushe yana nan, nasan Zaid yacutar dani, amma kuma ina matuƙar jin tausayinsa acikin zuciyata, tabbas da ace inada iko ko wani hali dana sanjawa Zaid rayuwarsa nasan Allah zai bani lada" Zahrah taƙare maganar tana me cije laɓɓanta.
Kallon baki da hankali Husnah tashigayiwa Zahrah.
"Ki sanja masa rayuwa fa kikace, anya kuwa kina cikin hankalinki Zahrah?" Husnah tafaɗa cike da mamaki.
"Inacikin hankalina Husnah ban haukace ba, ada nima nayi tunanin ko na haukace ne,sai kuma nagane bahaka bane" hanunta ta ɗaura akan hanun Husnah..
"Zaid bai taɓa tunanin haka zata kasance dashi ba Husnah, yayimini fyaɗe ne bisa bin umarnin zuciya dakuma gangar jikinsa da yayi, yamin fyaɗe ne saboda yanaji ajikinsa cewa sha'awata ce ke damunsa, Allah ba azzalumin kowa bane saidai wanda yazalunci kansa, ada nayi kuka sosai Husnah, nayi nadaman sanin Zaid acikin rayuwata, sannan kuma naji ƙunci da ciwon abun da ya aikata a gareni, ada inatunanin cewa fyaɗen da Zaid yayi mini yatashi abanza, saboda banida wani wanda zai tunkaresa, har yaƙwatarmin haƙƙina a wajensa..." ɗan tsagaitawa da maganar tayi haɗe da sakin wani murmushi, cigaba tayi da cewa.
"Nasani ko badaɗe ko bajima Allah zaimin sakayya, amma kuma bansan tawani hanya zai saka minba, ashe tahanyar da Zaid yabi ya yaudareni ta hanyar Allah zai sakamin, kinsan wace hanyace?" Zahrah ta tambayi Husnah.
Cike da zaƙuwa Husnah ta girgiza kanta alamar "A'a"
"SO! naso Zaid so me tsanani, shine namijin dana fara bawa soyayyata tunda nazo duniya, haka kuma shine namijin da na aminta dashi ɗari bisa ɗari, bantaɓa tunanin cewa ze iya rumtse idanunsa yaketamin haddina cikin rashin tausayi da imani, hadda wulaƙanci ba, nayi kuka harnagaji alokacin da Zaid ya lalatamin rayuwata, Zaid yayi amfani ne da soyayyar da nakeyi masa wajen cutar dani, Allah daya tashi sakamin Sai yasanya masa soyayyata me tsanani acikin zuciyarsa, yakuma nesantashi dani, tsananin soyayyar da Zaid kemin shine sakayyar da Allah yayimini, sannan kuma alhakina, na bibiyarsa sosai, Zaid yana sona, son da bazaiyi mishi amfani ba, nayi masa nisa tayanda bazai iya samuna ba, inada tabbacin cewa ayanzu yana cikin tsananin halin nadama wacce bazata amfaneshi da komai ba"
Ɗan numfasawa Zahrah tayi haɗe da duban Husnah.
"Kina ganin Zaid yacancanci samun mace mai hankali da nutsuwa, wacce zata gyara masa rayuwa ko a'a?" ta tambayi Husnah.
Harara Husnah ta wurga mata haɗe da taɓe bakinta...
"Mazinaci, fasiƙi, ɗan giya, ta'ina ya dace da mace me hankali da nutsuwa, ae sai dai ko yasamu wata daga cikin karuwan ƴan matansa ya aura, sai su ƙare rayuwarsu a haka, amma wace me hankalince zata yarda ta aureshi" Husnah tafaɗi haka da iyaka gaskiyarta.
Murmushi me ciwo Zahrah tayi haɗe da cije laɓɓanta, kanta ta girgiza kana tace....
"Zaid bai cancanci zama da karuwaba Husnah"
Dasauri Husnah takalleta haɗe da cewa.
"Meyasa kikace haka?"
"Sauyin rayuwa yake buƙata, dole yana da buƙatar wacce zata tsaya akansa ta basa kulawa, zuciyata tanayimini wani hasashe na daban" Zahrah tafaɗi haka tana me kafe Husnah da idanu.
Harara Husnah takuma wurgawa Zahrah haɗe da taɓe baki, cikin takaici tace.
"Amma dai kinsan mazinaci sai mazinaciya ƴar uwarsa ko, taya zakina haɗa kamilar mace da wani taƙadarin ɗan iska Zaid, cab hmm gwamma ma kisake tunani, me kuma zuciyarki take hasasho miki akan sa?" Husnah ta kuma tambaya.
"Kece zaki iya Husnah, banda wata wacce ta wuceki, banda wata ƙawa sama dake, amma bansan yazaki ɗau abun ba amma nasan....."
"Mekike son cewane wai Zahrah? naga kinata wani kwalo kwalo, ki faɗi abun da kikeson faɗi kai tsaye" Husnah tafaɗi haka ta hanyar katse Zahrah daga maganganun da takeyi.
"Ke yakamata ki auri Zaid Husnah, ko saboda nima, zaki samu lada sosai ba ɗan kaɗan ba...."
Cikin tsananin mamaki Husnah tamiƙe tsaye daga zaunen da take, wani irin kallo tashiga yimawa Zahrah, cikin wata irin murya dake ɗauke da tsananin ɓacin rai da takaici tace.
"Ni" tanuna kanta da ɗan yatsarta. "Allah ya sauwaƙemin, bantaɓa tunanin zaki zomin da irin wannan zancen ba Zahrah, ashe dama bakyasona, bakya ƙaunata? nagode ƙwarai da kikanunamin hakan adai dai wannan gaɓan, amma inaso kisani idan mafarki kikayi cewa ni Husnah na auri ɗangiya mazinaci to kigaggauta yin sadaka!" taƙare maganar cike da ɓacin ran abun da Zahrah ta gaya mata...
Haka Husnah ta suri jakarta tayi tafiyarta Zahrah naƙiranta ko waiwayowa batayi ba, balle ta tsaya sake sauraranta.
Jingina bayanta tayi dajikin wata bishiya wanda suke zaune a ƙasanta, wasu siraran hawayene suka gangaro takan kumatunta.
"Kowa kallon mahaukaciya yakeyi mata, to sai yaushene wasu mutanen zasu gaskata cewa soyayya ba ƙarya bane? sai yaushene wasu mutanen zasu gane cewa ita soyayya babu ruwanta da illa ko aibin mutum? menene laifinta don taji tausayin Zaid? So baƙarya bane, kuma duk inda so yake akwai tausayi, haka kuma akwai tsananin sha'awa." Ƙaran wayartane ya katse mata tunanin da takeyi, dasauri ta share hawayenta haɗe da ɗaukar wayar takara akan kunnenta..
"To" kawai naji tace haɗe da jefa wayarta ta acikin jaka, tashi tayi daga inda take zaune haɗe da gyara mayafinta, jakanta ta ɗauka ta nufi inda Dr.Sadeeq ke jiranta.
Tun daga nesa daya hangota yaketa zuba murmushi, komai na Zahrah'nsa me kyaune, tafiyanta ma kaɗai abun ɗaukar hankali ne, duk da cewa ba dagangan take hakan ba, haka asalin takunta yake