Showing 102001 words to 105000 words out of 184930 words
Chapter 35 - SHU'UMIN NAMIJI Book Complete by Phatyma Sardauna.txt
yafaɗa, kuka tashiga yi tamkar wacce aka sanarmawa da ranar mutuwarta, yayinda wani abu yataso ya tokare mata ƙirji wanda batasan komenene shi ba kamar yanda batasan kukan me takeyi ba...
Driver yana parking motar Zaid yace yafita ya bashi waje, aikuwa babu musu driver'n yafita daga cikin motar..... Kansa ya kafa ajikin kujera haɗe da fidda wani irin zazzafan numfashi ta bakinsa, zuwa yanzu kam bazai iya jurewa ba, sam bazai iya jure raɗaɗi dakuma azaban soyayyar Zahrah dake damunsa ba, tabbas da ace zai iya to da yayi iya ka ƙoƙarinsa wajen ganin ya yakice soyayyarta acikin zuciyarsa amma hakan bazai yiwuba domin kuwa duk kowani kwanan duniya soyayyarta ƙara ninkuwa takeyi acikin zuciyarsa, zuwa yanzu soyayyar Zahrah babu inda bata ratsa acikin jikinsa ba,,,, a ƙalla yakai kusan 30 minute acikin motar yana saƙawa da kuncewa, da ƙyar ya'iya fitowa daga cikin motar kai tsaye yanufi babban parlour'nsa dake cikin guest house ɗin nasa, domin kuwa daga gidan su Zahrah guest house ɗinsa suka yiyo....
Yana shiga cikin falon ya faɗa kan doguwar kujera haɗe da lumshe kyawawan idanunsa, kansa ne ke saramasa yayinda juwa ke ɗibansa, lallai yazame masa dole yasamawa kansa mafita, yazama dole yafarka daga wannan mafarkin daya keyi tabbas al'amuransa a yanzu suna masa kama da al'amara,, tabbas yana buƙatar samun relief daga damuwar dayake ciki, amma sai dai babu amfanin shangiya a yanzu domin kuwa koda yashama bata basa wani relief ɗin da ya kamata, miƙewa yayi yashiga cikin ɗakinsa, kai tsaye wani ɗan drower yanufa haɗe da buɗewa, hanu yasanya ya ɗauko wata wayarsa ƙirar techno phantom 9 wanda dama yana ajewane saboda rana irin haka, kasancewar baifito da wayoyinsa ba duk yabarsu a gida,, yana kunna wayar ya laluɓo wata lamba haɗe da turawa lambar text message, yana ganin alamar saƙon ya isa inda yakeson yaje yayi switch off ɗin wayar haɗe da maidata inda ya ɗaukota kwanciya yayi akan makeken gadonsa wanda yasha shumfuɗa ta alfarma, cusa kansa yayi cikin pillow haɗe da soma fitar da numfarfashi akai akai....
A hankali taturo ƙofar ɗakin wanda kafun ma tashigo tuni ƙamshinta yarigata shigowa, sanye take da jan wando pencil wanda yayi matuƙar bayyana kyakkyawar surar jikinta yayinda rigarta yakasance baƙa me kyau, rigan irin masu faɗin wuyan nan ne hakan ne yasanya manya manyan breast ɗinta bayyana kansu tasaman rigar,, takalmine me uban tsini a ƙafarta yayinda ta tufke dogon gashin kanta da jan ribbon kalan wandonta,, kallo ɗaya zakayi mata kafahimci cewa wayayyar macece ƴar duma, shigarta kaɗai ya isa yabayyana maka ainihin ko wacece ita, saboda bashigane da mata masu mutumci sukeyi su fita ba kamar yanda ita tayi, domin kuwa ko ɗan kwali babu akanta, wani irin murmushine kwance akan fuskarta dake nuna alamar cewa tana cikin farinciki,, lumshe idanunta tayi haɗe da buɗesu alokaci guda, kallon surarsa kaɗai ya isa sanya mata nutsuwa, tajima tana tsumayi da kuma fatan Allah ya sake ɗaurata akansa, harta cire rai saikuma gashi yau shi da kansa ya gayyatota, lallai zata iya cewa a rana irin ta yau tafi kowa sa'a..
Duk da yaji ƙamshin turarenta acikin hancinsa hakan baisanya yaɗago kansa ba,,
Cikin taku irin na matan da suka goge wajen iya ɗaukar hankalin ɗa namiji tashiga takowa har zuwa inda yake kwance ya yinda juyawa ƙofa baya...
Hanunta tasanya a bayan wuyansa haɗe da soma shafawa a hankali,, cikin wata murya me sanyi dajan hankali tace "Man!"
Shiru yayi bai amsa mata ba, duk da kuwa cewa yanajinta,,, ganin bai amsa taba yasanya tayi murmushi haɗe da cire takalman dake ƙafarta ta hawo kan gadon,, bakinta ta sanya adai dai saitin tsakiyar bayansa tashiga tsotsa haɗe da shafa bayan wuyansa a hankali,,,, wani irin zubawa Zaid yaji tsikar jikinsa tayi, adai dai sanda take ƙoƙarin nuna masa wani sabon salo.... "Meenal!" yaƙira sunanta da wata irin murya wacce ta riga da ta cushe..
Murmushi Meenal tayi haɗe da mirginowa ta dawo gabansa suna fuskantar juna, lumshe idanunta tayi alokacin da tayi arba da kyakkyawar fuskarsa, wallahi tana matuƙar son Zaid komai nasa me kyaune daga ciki har waje, ba abunda yake ɗaukar hankalinta akan fuskarsa kamar wannan kyakkyawan sajen nasa dayake shan gyara da mayuka masu kyaun gaske..
"Nayi kewarka Man, ashe de kaima kayi kewata? katafi ka barni da tunanin daɗin da kajiyar dani, wanda har rana me kamar ta yau babu wani ɗa namiji da yajiyar dani kwatan kwacin wannan" Meenal taƙare maganar cikin yanayi na shagwaɓa haɗe da sake matsowa tashige cikin jikinsa,, ɗan guntun murmushi yasakar mata haɗe da soma ƙarewa fuskarta kallo, Meenal kyakkyawar yarinyace wanda kyawun nata kuma yazama na ɗan maciji, domin kuwa Meenal tantiriyar ƴar iska ce kuma cikakkiyar mazinaciya wanda idan ta kafamawa namiji ƙahon zuƙa duk nuƙu nuƙunsa sai ta jefasa cikin raminta, sai dai idan kuma shiɗin ya kasance gwaska na gasken gasken, tofa nan ne zasu dai dai ta, kamar dai Zaid da ta buga ta rawa yaƙi faɗowa raminta, domin kuwa shi ɗin ma ɗan iskane me lasisi san nan kuma gwaska ne me zaman kansa, wannan yasa Meenal takasa turasa a cikin raminta..
Hanu Meenal tasanya akan faffaɗan ƙirjinsa tashiga shafawa haɗe da cusa kanta acikin wuyansa cike da ƙwarewa take manna masa kiss,, tamkar wata mayya haka take sake shigewa cikin jikinsa..
Lumshe idanunsa yayi haɗe da cusa hanunsa cikin sumar kanta,, take yasoma sauƙe ajiyar zuciya akai akai domin kuwa gani yake tamkar Zahrah ce kwance haka a jikinsa,, idanu Meenal ta kafesa dashi cike da mamakin irin sauyawan da yayi, nafarko ta hango tarin damuwa acikin idanunsa yayinda na biyu kuma ta hango wani abu mai ɗaure kai acikin idanunsa,,, "Man!" taƙira sunansa cikin wata irin murya, idanunsa kawai ya jefa acikin nata idanun batare da yace da'ita komai ba,, dama haka takeso burinta shine yaɗaga kyawawan idanunsa ya kalleta,, take ta sauya salon nata kallon ta marairaice idanunta,, fuskarta ta matso daf da tashi fuskar lokaci ɗaya tasoma ƙoƙarin haɗe bakinsu waje ɗaya, kamar koda yaushe ƙin aminta da hakan yayi da sauri ya kawar da kansa gefe, saboda hakan baya daga cikin tsarinsa haɗa miyau da matan bariki, domin babu abu mafi saurin sanya shaƙuwa kamar haɗakar yawun baki, sosai kiss yake sanya shaƙuwa a tsakanin masu yinsa, domin haɗuwar yawun bakuna biyu wani sinadari ne na musamman,,,, bata damu ba domin dama tasansa bayawa mace kiss batakuma san dalilinsa na hakan ba, wan nan kuma ita duk ba damuwarta bane matuƙar zai kusanceta to zatafi kowa farinciki,,,,, hanunta ta sanya akan mararsa tashiga shafawa a hankali haɗe da ɗaura bakinta akan nipples ɗinsa, jawota yasakeyi jikinsa bayan ya cire mata ƴar ƙaramar rigar jikinta, kansa ya cusa acikin ƙirjinta yana me shaƙar ƙamshin turarenta, haɗe da sanya hannayensa a bayanta yasoma shafawa a hankali,, take Meenal tasoma sauƙe numfashi akai akai dama ƙiris take jira saboda akunne take ƙwarai... Lokaci ɗaya Meenal tarikice wasu irin salo take gwadawa Zaid masu sanya mutum ya fita a hayyacinsa, yayinda shima yagama ruɗata da nasa salon har saida yakusa sanyata shiɗewa,, amma kuma wani abun mamakin shine yanayin hakan ne cikin wani irin yanayi wanda baisan dame zai ƙira sunan yanayin ba, kwata kwata baijin wani abu mai suna sha'awa a jikinsa duk dakuwa irin romancing ɗinsa da Meenal keyi, lumshe idanunsa yayi haɗe da jawota yadawo da ita ƙasansa aniyarsa shine ya kusanceta amma kuma sai yaji zuciyarsa tashiga bugawa da sauri sauri yayinda Zahrah tashigo cikin ransa ta tsaya cak, take idanunsa suka haskomasa irin kallon tsanan da tayi masa ɗazu, nan danan yaji komai yafice masa arai, da sauri ya ture Meenal gefe haɗe da sanya hanu ya dafe kansa da yayi masa nauyi, da wani irin kallo Meenal da takai ƙololuwa wajen sha'awa ta bisa, meye haka yakeyi? badai halin nasa na wulaƙanci zai gwada mata ba? idan kuwa hakane Zaid yacuceta, saida yagama jefata acikin masifaffiyar sha'awarsa san nan yajuya mata baya, hanu tasanya ta rungumosa ta baya haɗe da soma goga masa breast ɗinta akan bayansa "Meke damunka Man? kada kabari damuwa ya hanaka jin daɗin rayuwa please" tafaɗi haka cikin narkakkiyar murya, hanunsa yasanya ya zameta daga jikinsa wani irin haushinta ma yake ji, miƙewa yayi direct ya wuce toilet ɗinsa ko waiwayota baiyi ba, baki sake haka Meenal tabisa da kallo harya shige cikin toilet ɗin,, kuka ta fashe dashi haɗe da matse cinyoyinta, tsakani da Allah take kuka domin kuwa iyaka cuta a wajenta shine abun da Zaid yayi mata...
Zaid kuwa yanashiga bathroom ya zame wandon dake jikinsa haɗe da nufar inda babban bathtub ɗin wankansa yake, ruwa ne me kyau da tsabta acikin bathtub ɗin, amma duk da haka saida ya zubar yakuma taran wani ruwan, turaren wankansa me daɗin ƙamshi ya sanya a cikin ruwan haɗe da shiga cikin ruwan ya kwanta a hankali,, lumshe idanunsa yayi haɗi da jingina kansa, zafi yakeji adai dai saitin zuciyarsa, tabbas yanaji ajikinsa cewa akwai abun da zai faru dashi bayan wanda yake faruwa dashi yanzu, "wace irin soyayya ce haka yake yiwa Zahrah me zafi?" tambayar da kullum sai yayimawa kansa kenan, lallai yau yasake tabbatar mawa kansa cewa yazama mutum me rauni, A she dama akwai wata rana da zai iya kasancewa haka? yaƙira Meenal ne don taɗebemasa kewa yakuma samu ya rage tarin sha'awar dake damunsa, domin kuwa har wani ciwo yakeji mararsa nayi masa, amma kuma sai gashi ya kasayin komai da Meenal, ashe ba Meenal ɗin bace muradinsa Zahrah ce, haƙiƙa yasake yardarwa kansa cewa abunda kake so shi yake wahalceka sannan kuma yasake tabbatar mawa kansa cewa ƘAUNA guda ɗayane tal aduniya, SO ne kawai yake da yawa, amma ƙauna ƙaunace,, kafun yaƙira Meenal yayi tunanin cewa idan tazo zata gusar masa da damuwarsa, sai kuma bayan tazo yaga ashe bazata iya ba, ashe yin sex da shan giya basune maganin damuwarsa ba, Zahrah har lau itace maganin damuwar sa,, anya kuwa zai warke daga damuwar nan tasa?
Yajima acikin bathroom kafun yayi wanka yafito jikinsa sanye da farar rigar wanka,, kallonsa ya maida kan gado inda yabar Meenal don ganin wani hali ta ke ciki domin kuwa sarai yaji kukanta lokacin dayake cikin bathroom,, dariyane taso ƙwacemai sakamakon ganin Meenal da yayi takure a can ƙarshen gado tana bacci, yayinda ta cusa hanunta na hagu a ƙasanta, sarai yasan Meenal jarabebbiya ce yanzu haka fingering tayi don samawa kanta relief, abun da yafi tsana kenan wato mutum yayi amfani da kansa don biyan buƙatarsa, amma kuma wannan halin Meenal ne,, kai kawai ya girgiza haɗe da nufan gaban dressing mirror ɗinsa, vaseline yashafa ajikinsa kasancewar garin ana ɗan yanayi na sanyi, saida ya feshe jikinsa da body spray kafun yasanya kayansa riga da wando na jeans masu kauri, sosai kayan sukai masa kyau, kuɗaɗe yaciro a cikin drower ɗinsa ya ajiye a kusa da Meenal daketa sharan bacci, kana yayi ficewarsa daga ɗakin, direct bai zarce ko inaba sai compound ɗin gidan, yanzu kam shida kansa yakeson yayi tuƙi, don hakane ma yazaɓi BMW blue colour amatsayin wacce zai fita da ita....
Dr.Sadeeq
Duk yanda Dr.Sadeeq yaso samawa kansa nutsuwa hakan yagagara domin kuwa sam zuciyarsa bata amince da zuwa wajen Zahrah da Zaid keyi ba, duk da yau yafara ganinsa aƙofar gidan su Zahrah'n amma jikinsa ya basa cewa ba yaune zuwansa na farko ba, amma bakomai zaiyi maganin abunne zai nisanta Zahrah da Zaid nisantawa me tsanani kuwa, da wannan tunanin bacci ya ɗaukesa...
Washe Gari.
Dasassafe Zahrah ta shirya tayi tafiyarta makaranta sai dai a ranta tana mamakin rashin ƙiranta da Dr.Sadeeq yayi, rabonta dashi tunjiya da yamma sunkuma rabu dashi akan cewa zai ƙirata sai gashi kuma har zuwa yanzu bai ƙirata ba, uzuri tayi masa akan cewa ko aikine yayi masa yawa domin tasan hakanan Dr.Sadeeq bazaiƙi ƙiranta ba...
Tana tafiya ba jimawa motar Dr.Sadeeq ta tsaya a ƙofar gidan nasu, fitowa yayi daga cikin motar yasha adonsa cikin blue ɗin shadda sosai kuma yayi kyau,, yaro ya aika cikin gidan yace yace ana sallama,, bajimawa yaron daya aika yadawo ya shaida masa ance me gidan yana fitowa.... Washe da baki Baffa yaƙaraso wajen Dr.Sadeeq dake tsaye " Maraba da Likita, dama kaine ai da kashigo ciki amma ka tsaya a waje sai kace wani baƙo"
Murmushi Dr.Sadeeq yayi cike da girmamawa ya sunne kansa ƙasa haɗe da durƙusawa ya gaishe da Baffa,, fuska cike da fari'a Baffa ya amsa gaisuwan,,,
"Aikuwa kayi rashin sa'a domin kuwa mutumiyar taka bata jima da fita a gidan ba, tatafi makaranta ko karyawa bata tsaya tayi ba, amma ina ga zaifi kyau mushiga daga ciki ko"
"A'a Baffa nan ɗin ma yayi, dama wajenka nazo ae"
"To to masha Allah, saimu zauna ae ko abisa dakalin nan" Baffa yaƙare maganar yana meyi mawa Dr.Sadeeq nuni da dakalin ƙofar gidan.
Duk yanda Baffa yaso Dr.Sadeeq ya hau kan dakalin su zauna ƙiyawa yayi, domin kuwa Baffa surikinsa ne baidace ace sun zauna gaf da juna ba kodan saboda kara da matuntawa,,
"Shikenan to tunda dae kaƙi zama, inajinka Allah yasa dai lafiya?"
Kansa yaɗan sosa haɗe da sakin murmushi "Lafiya ƙalau Baffa dama akan maganan aure nane da Zahrah..." sai kuma yayi shiru ya kasa ƙarasa maganar dake cikin bakinsa, gani yake tamkar idan yafaɗi maganar kai tsaye Baffa zaice masa yayi gaggawa ko kuma yace yayi rashin kunya...
"Ka kwantar da hankalinka Likita kafaɗi duk wani abu dake ranka" Baffa yafaɗi haka ga doctor ɗin..
"Am dama...dama inaso ne kabani izini nasake turo magabatana dan sukawo sadaki san nan kuma a tsaida ranar aure"
"Alhmdlh to ai wannan abun farinciki ne Likita, wannan ae bawani abun damuwa bane, nabaka dama ka turosu aduk sanda kakeso, sai de kuma zakaɗanyi haƙuri, saboda zansa lokacin da ɗan tsayi saboda kasan ba a yin aure kai tsaye haka dole sai anɗanyi mawa yarinya sayayya, ina fata hakan bazai sosa ranka ba?"
Murmushin jin daɗi Dr.Sadeeq yayi haɗe da cewa "Naji daɗi sosai Baffa, amma kuma maganar sayayya basai kun wahalar da kanku ba, domin zuwa yanzu gidan da zamu zauna baya buƙatan komai, saboda haka don Allah kada kusa kanku a wahala"
Murmushi Baffa yayi haɗe da cewa "Ƙwarai mungode da wannan ƙoƙarin naka, amma sai de nace kayi haƙuri, duk da cewa mahaifin Zahrah baya raye ni ƙaninsa ina raye kuma niɗin ma ubane a wajenta, zan yi amfani da ɗan abun da nake dasu wajen ganin namata kayan ɗaki iya dede ƙarfina, kamarde yanda kowani uba keyiwa ƴarsa, wannan shine kaɗai gatan da zamu iyayi mata a yanzu" Baffa yafaɗi haka da iyaka gaskiyarsa..
Ajiyar Zuciya Dr.Sadeeq ya sauƙe, haƙiƙa shi Zahrah kawai yakeso bawai wani abu na daban ba, kuma shi baiso akawota da komai, domin musamman ya ware mata ɓangarenta, kuma tuni yabawa wani abokinsa me saida furnitures a Dubai order akan akawomasa setin kujeru dakuma gado harma da duk wani abu wanda yasan zai ƙawata ɗaki,, amma tunda yaga Baffa yadage akan cewa shima zaiyi iya nasa ƙoƙarin shikenan zai ware wani ɗaki na da ban idan yaso sai a sanya kayan da Baffan yayi mata acan,,, cike da mutuntawa Baffa da Dr.Sadeeq sukayi sallama....
Baffa na shiga gida ya kalli Inna dake zaune,, "Salame inajin fa tafiyana yola yagabato idan banje jibi ba to zanje gata insha Allah"
Fuska ɗauke da mamaki Inna ke kallonsa, "Yola kuma Malam?"
"Ƙwarai kuwa, kinga fitana ɗin nan to yaron nan ne Sadeeq yazo min da maganar cewa inbasa dama yaturo magabatansa don sukawo sadaki akuma sa rana, to ni dai nace yaturosu duk sanda yakeso, yanzu dole zanje yola insanya fili dakuma gonan nan namu na gado a kasuwa idan aka siya intarkata kuɗin nan nasamu nasaiwa yarinyarnan kayan ɗaki dakuma kayan aikace aikace kamar de yanda kowani iyaye kemawa ƴarsu dan baiyiwuwa ace mu miƙata haka"
Ajiyar zuciya Inna tasauƙe haɗe da gyara zama " Duk naji batunka Malam, amma kuma mezai hana kabar shi mijin nata yayi mata komai, ae naga yana da halin da zai iyayi mata fiye da wannan ma"
Murmushi kawai Baffa yayi shi kam tun ba yau ba yasan cewa bakoda yaushe ne Inna take gane karatun da'ake biya mata ba, don haka baiƙara cewa da'ita komai ba yawuce ɗakinsa, domin yasan kozai shekara a wajen yanason ganar da'ita tofa bazata fahimcesa ba,,, Inna kuwa baƙin ciki ne yakamata ina ma laifin yace zaiƙara jari da kuɗin, sai yace wani wai zai siyawa Zahrah kayan ɗaki,, haka taita ƙananun maganganunta babu maijinta ma balle yatanka mata......
Da yamma Dr.Sadeeq yaƙira Baffa yasanar masa cewa Baffansa zaizo da dare donsu tsaida magana, duk da cewa Baffa yayi mamakin sauri irin na Dr.Sadeeq ɗin amma saiya share yace Allah yakawosu lafiya,,
Hargida Baffa yaje yasanarwa Alhaji Umar abun da Dr.Sadeeq yace, kuma dama Alhaji Umar ɗin tuni yasan da maganar saboda duk abun da yafaru Baffa yanazuwa ya sanarmasa har kawo lefen da akayi ma Baffa yasanar masa,, sosai Alhaji Umar yayi murna yakumace zaizo gidan Baffa'n da dare a ƙarɓi baƙin dashi......
Kamar yanda Dr.Sadeeq yafaɗa hakane yakasance domin ana idar da sallan Isha Baffa Amadu da wani shaƙiƙin amininsa suka zo gidansu Zahrah,, sosai Baffa da Alhaji Umar suka musu tarba na mutunci,, zama sukayi haɗe dayin magana ta fahimtar juna, nan Baffa Amadu ya miƙa sadakin Zahrah ga Baffa naira dubu ɗari (100,000) bawani ɓata lokaci Baffa yasanya lokacin aure wata ɗaya, aikuwa take kowannensu yacika da farinciki haka sukayi sallama cike da girmama juna.......
(Team Dr. Saiku fitarmana da ankon biki, nasan duk Baba Zaid ze saya mana auren Zahrah'nsa ne ae 🤣🤣😜)
*4/Junuary/2020*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
~Fatymasardauna~
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 78 to 79*
Zahrah na zaune a ɗakinta Inna takutso kanta cikin ɗakin.
"Idan kin gama rubuce rubucen banzan naki kije Baffan ki nanemanki!" Inna tafaɗi haka