Showing 24001 words to 27000 words out of 107087 words

Chapter 9 - AUREN GADO COMPLETE DOCUMENT Book by MATAR SOJA.txt

04 Dec 2024

5659

ai wasu basu san dadin irin shiba, oh zaka iya cin Abincin mu na Nigeria ba kyankyasai ba. "For the first time a lokacin yaji wata irin dariya tazomai, shima Ahmed Saida ya dara, "ke Waye yafada miki sunan su kyankyaso? " oho nidai ai mutum ba Abinci yakeci ba sai tarkace, daga kunama sai k'wari.
"Hmm, kawai yace yafaracin Abincin shi batareda yace tak ba yaci sosai saida ya kusa cinyewa tace "little brother inkara maka ne? Dago kanshi yayi ya kalleta wani iri kafin yace "am OK Aunty babba tanks. Ya mike, "Wow Wato kasan Aunty karama na zuwa ko? Harara ta watsawa Ahmed d'in tareda daukar hijabin ta ta Mayar, zata wuce. "Wait my Hajiya ai muje a yimin wanka ki karasa ladanki tukuna.
Kokarin tafiya takeso tayi, khaleel yace "Yaya please let her go kafin mommy ta ankare. "Muje intayaka tafada kai tsaye, domin batasan meye matsalar shi na yimusu karan tsaye ba yanaso ya hanata sakewa a lokacin da ta samu damar ta,


"Toh munafuka Y'ar gidan masu kwana kan buzu, zoki fita shashasha, ko kunya an narkawa yarinya dukiya kinzo kin shige, zo ki wuce, kai kuma Ahmed idan ka wuce iyakata banyafe ba, kaima khaleel dakai ake haduwa anamin bita da kulli, kuzo ku shirya ku tafi daurin Aure, in mace ce matsalar ka Ahmed na zabo maka ta kece raini ba wannan Y'ar shilar ba, koma daka nayi baki. Da gudu ta fita while khaleel ya wuce Abinshi batareda ya tanka ba Ahmed ma haka ta karaci sababi tareda turo masu aiki su Kara gyara duk Abinda aka bata a turare shi.
Saida ta shaki kukanta ta tashi tayi wanka ta caba Ado wayar ta ta dakko taga sakonnin shi da basa taba rabuwa da wayar ta, "Am sorry matata idan muka dawo zankira ki mu fita shakatawa kinji. Dariya tayi kamar dagske yanzu mommy nace wa Ahmed zai sunne kai, "my gentle man. Tafada cikin nishadi, so hana ganin laifi,




Biki yayi biki ko Ina ba masaka tsinke a cikin babban birnin na kano a yau Auren yaran manyan mutane guda hudu at once, ga kuma Y'ar masu kasa Wato fauziya,
Daurin Aure ne Wanda ya jirkita garin ba kadan ba manyan baki ta ko Ina, kawu wakilin Angwaye Wanda baisan da zancen Auren Salifa ba sai ranar Auren, ya fara fada kamar zai Ari baki, har cikin gidan yazo ya kirata "Hajiya bilkisu halina na nan, yanzu saboda Allah yaro Aure wata biyu kisa ya karo Aure? Hajiya bilkisu kiji tsoron Allah. "Toh nidai bani nasa yaron nan Karin Aure ba ka kirashi ka tanbayeshi. "Koda bani na haifeshi ba jini nane nasan halin Ahmed nasan tirsasashi kikayi kuma Ina gargadinki da kibi a hankali. Shigowa Khaleel yayi ya zauna tareda gaida kawun yace "don Allah kasa baki ta bar yarinyar ta tare a part d'in ta kafin wata tazo kuma kawu ai itace uwar gida yakamata ace ita tafara shiga wancan gidan. "Yanzu kokarin kai karata kakeyi Ibrahim, Wato ya turoka kazo kasa kawunku ya yanke ni toh ka koma ka fadamai wallahi sai Salifa ta shiga Wannan gidan kafin Wannan Y'ar gidan malaman ehem. Tayi fuuu ta shige, ya so ya cire son zuciya ya agaji yayan shi amma mommy, Hmmm. "Khaleel ku shirya mu wuce ka Kira d'an uwan ka, mu ake jira,. Yafada domin lokaci natafiya kuma suntara manyan Kasa harda mai kano baki daya, kuma zai dawo mata idan komai ya natsa.


Andaura Auren fauziya da Khaleel sai kuma Salifa da Ahmed, Wanda akan sadaki mai matukar tsada akan miliyoyin kudi, domin gadarar mommy, Wanda Ana gama daurin Aure angwayen suka dawo dakunan su kowa kajishi shiru, ba wani motsi, lokacin da aka Kira mommy andaura ta rangada guda tareda kawayen ta, kannin mijinta ne suka iso suna Allah Sanya Alkhairi badon sun soba, babbar tace Ina uwar gidan Ahmed d'in? Tana nan zuwa anjima za akawo ta. Mommy tafada da gadara, "Hmmm Allah ya shiryeki bilkisu Wato harda yayan mu bai duniya baki canja bakin hali ba ko?, to wallahi sai Kinga sakamako idan kika cutarda Y'ar mutane. "Toh ku dama wayake taku dama ai duk kannin miji y'an bakin ciki ne don haka ni yau banda lokacin ku nayiwa ya'ya na AUREN GATA.
Taci gaba da guda, dakin Ahmed suka nema inda suka sameta zaune yan uwan ta sunzo tana ta walwalar ta ta fauwala wa Allah, Wanda ta mugun burgesu zama sukayi a dakin suka sake sosai sukasha hira anan suke fada mata su gwaggwnin mijinta ne, ta saki jiki ta kula dasu itama dasu Aunty Raliya sai hira sukeyi.
Damuwar ta kadan ce zuciyar ta na wurin Ahmed batasan halin da yake cikiba Wanda saida yakira likita ya dubashi yace "gaskiya Ahmed idan zuwa gobe bakaji sauki ba kazo Asibiti ayima xray saboda ciwo a kirji yanada matukar Matsala.
Godiya yayi yasha maganin shi ya kwanta yayi bacci sosai har magrib.




Taro ya ragu zuwa Karfe bakwai duk taron Naziya sun watse sai ita kadai, yau ta yabawa d'an gin Ahmed harda y'an gidan kawu gefenta suka tare sun share mommy da gayyar ta, yanzu bakajin komai sai kai da kawon su Aunty zarah iyayen ango,
Takwas aka kawo Amare Wanda kafin Wannan lokacin ba Wanda yasan inda angwayen suke.
Main house aka shigo dasu cikeda guda Wanda tanaji, a take wani kuka yazo mata, shikenan rayuwar da tafara mafarki watace zatayi da mijin ta, shikenan sun samu third party tunkafin su mori Auren su.
Saida suka gama feshe feshe kafin kai Amaren gefen su wainda kowacce cike take da tata salon rashin kunyar hade da rawar kai.......... 🖊




*Matar Soja*


















🌻🌻AUREN GADO🌻🌻







*Matar soja ce*






Daga marubuciyar
KUKURE NA
BARIKI AUREN SOJA
MUK'ADDARI
WANAKE AURE
ZANYI BIYAYYA
Y'AY'AN GATA
And now AUREN GADO,


















Ga masu bukatar Wnn littafi ku turo kudin ku ta Asusun banki na 7304736012 nafisa sani hassan Fcmb ko katin wayar ku ta Wannan number 09011251444, sai kuma y'an 🇳🇪 Niger ku tuntubi Wannan number domin biyan naku, +225 0748153903, littafina Dari biyar ne kacal 500 sai najiku nagode,
















🆓 page


1⃣7⃣&1⃣8⃣




........... Sai Karfe goma sha daya suka shigo main house, mommy na zaune sai faman jiran su takeyi,ta gwada numbobin su ba Wanda yake shiga, tanata sababi Su zarah na tausar ta, da sallamar shi ya shigo cikin falon while khaleel na biyeda shi cikin shigar shadda bugaggiya Y'ar gaske fara dal, "ko kin ga y'an rainin hankalin ko sai yanzu zasu shigo gida kusan Karfe goma sha daya. "Ahmed ne ya matso gefen ta tareda zama yana gaida Aunties dinsu, tareda cewa sorry mommy muna tareda Abokai ne. "Which abokai? Kai inkanada Abokai shi Wannan miskilin nadasu ne? Kun bar ya'yan mutane sukadai suna jiranku kamar masu gadi.
Carab ya bude baki a karon farko yace "jiran me sukeyi mana? Bayan ba ayi budar kai ba, sai su jira nan da sati daya idan an yi budar kai sai muje wurin su ni bacci nakeji, Yaya good night. Yafada batareda ya jira Amsar suba ya wuce Abinshi, ido kawai Ahmed yabishi da shi, bakin mommy a sake tace "Allah ya hadani da yaron banza, kai kuma bazaka tashi ka wuce dakin Amaryar taka ba? "Mommy gaskiya ne ita baza ayi mata budar kan ba? " ubanka kaji tashi ka wuce ko ranka ya baci yanzun nan, shima zanje in same shi. Mikewa yayi domin baijin dadi sosai dauriya yakeyi kuma Allah yagani bayason kowa yasan halin da yake ciki yanzu.
Yana kallon kofar dakin shi kamar yashiga yakeji yasan halin da take ciki, Amma ba hali mommy ta kasa ta tsare. "Za abiyoka da kazar Amarci nasa anyi muku gashi mai kyau. Ko amsawa baiyi ba ya fita, a zaune Amaryar tashi take tayi dai dai cikin wasu irin fitinannun nighties duk jikinta a bayyane gata ba wani shahararren kyau ba, sai faman tauna chewing gum takeyi tana kas kas kamar wata tsohuwar karuwa.


Tundaga falon ya hango ta kafa daya kan daya tana jijjiga, zai iya cewa yaune karo na biyu ganin shi da ita Wanda baima san ta Ina zai fara yimata magana ba, domin ko ganin farko bai wani mata kallon arziki ba, don haka ko yanzu yana shigowa ya dauke kanshi ya wuce ta gaban ta. "Kai, tace cikin zafi. "Kashi ka wuce? ace ankawoni tun Karfe takwas kowa ya watse ya barni baka shigo ba sai yanzu? kuma ka ganni kamar wata Kashi ka gani. "Oh sorry ya fada batareda ya kalle taba domin bai sha'awar hakan, murmurshi tayi tareda matsowa tana karkada jikin ta da shirin rungume shi, yayi saurin ja baya tareda cewa "please bacci nakeji sosai kuma kaina naciwo, am very tired please let me go. Ya wuce da sauri yabarta tana cizon yatsa, batasan da yanajin lafiya yau sai ya nemo Matar sonshi yaci Amarci kota halin Yaya, Amma bayajin dadi shikadai yasan me yakeji a jikin shi. Yana shiga dakin shi ya datse gam batareda ya jira wani Abu ba, idanun ta sun nuna mai zata iya mai fyade inyayi wasa ta karasa shi, saida ya kwabe ya zube kan gado domin yayi sallolin shi a waje, ya janyo wayar shi yafara neman ta, tana kan dadduma tana lazumi taji Karar wayar, tasan shine don haka cikin Sauri ta mike ta dauka, Ajiyar zuciya yasauke yace "Y'ar Aljannah." Ina wuni, ta gaidashi cikeda tausayin kansu domin yama fita zama Abin tausayi, "ba lfy my wife, ko in zo ne? " aa. "Why?" mommy na falo suna hira. Hmm! zaki tayani hira har safe? eh, Amma hakkin Amarya fa? "Don't say that again sai kisa inji guiltiness akan ki" naki hakkin fa? " ni na yafe. "Nikuma fa? Ni Ina bukatar hakkina Naziya, kinsan cewa ba Abu bane mai sauki namiji yayi ido biyu da Mace kamar ke ya kawar da ido ba, mommy ce ta tsaya min akan layi da tuni munfara lissafin wata biyu cikina. Rufe idanun ta tayi gam saboda kunya kamar yana ganin, "shy girl, nasan kin rufe ido.
Hira sukasha sosai yana yi yana bata hakuri tareda alkawura masu yawa.


Gefen Amarya ta cika ta batse momyn ta ta Kira tana kuka tafada mata angon yaki ko shigowa dakin ta, a daren Karfe biyu ta Kira mommy tana sababi, "nifa ba dutse nakai muku ba yarinya ce shakaf mai jini a jika don haka kari nji kar ingani, zancen wulakan ta min ya'. Tayi ta bata hakuri kafin ta gwada kiranshi yana busy, ta hakura ta barwa safiya, banzar kuwa kazarta ta yaga iya son ranta ta sha baccin ta nak, domin tasan dai dole yagama gudun shi yadawo mata domin a shirye take tsab.
Fauzy ma tasan halin kayan ta batasa akaba tasani tunda dai ta shigo, a juri zuwa rafi wata rana tulu zai fashe, Amma zama daram itada Khaleel tunda buri ya cika.


Gefen shi ma baccin shi yasha har safe batareda tunanin wata kaya fauzy ba,sai Asuba ya fito da shirin zuwa masallaci, ya samu mommy zaune itada bata tashi da wuri, tace Yauwa ku nake jira kuyi sallah kuzo kaida d'an uwan ka Ina jiran ku yanzu, fita yayi kawai Abun shi yasan tatsuniyar gizo bata wuce ta k'oki.
A masallaci suka hadu, saida suka idar yace "her excellency is calling. "Who? "Your mom. "Oh ba MAMAN ka bace kai? Shiru yayi kawai, domin shikam baisan me zaiyi mommy ta canja ba, ciki suka shiga yana mai nasihohi masu ratsa jiki da taba zuciya, suna saka kafa tafara sababi "nikam yau zanyi maganin ku duka sai kunfada min inkunada wata uwar bayan ni, Ina muku gata yara kuna watsa min kasa a ido, toh yau dukan ku Ina bukatar ku dakin matayen ku banason jin rashin kunyar ka Ibrahim. Sannan kai tunjiya Ina kiranka kaida ubanwa kake waya? Da ka kwashe tsawon dare kana busy? "Mommy kiyi hakuri, nida Naziya ne. "Innalillahi, Wato tanan ka bullo Ahmed kuna hadewa ta waya, ita kuma munafuka kamar salaha, mayya ta lashe min kurwar yaro to wallahi zanyi maganin Abun, karyar buzu tsohon ta yakeyi, mu munsha tabara mun sha yaseen , ta rangada mata Kira, Wanda duk tanajin komai.
Da sauri ta fito da hijabin sallar ta tace "gani momy. "Ni ba uwar ki bace ta cikin bukka munafuka, ke kin kaini bango hakurina ya kare akan ki inba zuciyar kare kikeda ba kizo ki koma gidan ubanki, ace mace don rashin zuciya miji bai neman ki baidamu dakeba saboda kin rab'i Ac kin like kin manne kamar kaska, ke wa ya iya da bakin nacin talaka? zo don Allah kibarmin gida Ahmed dai yayi Aure aje aci gaba da cin tuwon dawa da gero.
Tafada tana nuna mata hanya.
Kuka takeyi tunda momy tafara magana Wanda Wanda duk sauran bakinta sun taso, fauzy ma data bugo sammako ciki taji komai, tana dariyar mugunta tareda komawa ta Kira Salifa tazo kar ayi bata, domin tasan da zaman Naziya kuma tasan komai akai don haka tasan zatayi farin ciki yau idan taga Abinda mommy tayi,


Dafe kirjin shi yayi yana mai wani irin zafi tuni numfashin shi yafara seizing batareda kowa ya luraba, domin kan Khaleel na kasa idanun shi kamar wuta saboda bakin cikin halin mommy, da kuma irin cin zarafin da takeyiwa Naziya.
Zubewar da yayi Tim yasa khaleel ya zabura yayi kanshi, Wanda yabawa sauran damar ganin Abunda ke faruwa, har mommy tuni tayi dif kamar ruwa ya cinyeta,
"Yaya" khaleel yafada cikin tashin hankali, ya tarai rayoshi, saidai tuni jini yafara bin hanci da bakin shi, wani irin zubewa Naziya tayi jikin ta na rawa kukan da take ya tsaya ba Abinda take kallo sai jinin dake fita a fuskar Ahmed, cikin tsananin jarumta da mazantaka khaleel ya cirashi da gudu yayi waje yana mai kwalawa driver Kira yakawo mai key, yasaka shi cikin motar tareda rungume shi cikin tashin hankali driver yaja suka fita a guje domin gari yayi haske,
Mommy daskarewa tayi tana jin numfashin ta kamar zaifita saboda tashin hankali, Ba Abinda takeso duniya sama da ya'yan ta da kuma dukiyar ta, batasaon rasa kodaya a cikin biyun nan, don haka ganin yanayin Ahmed yasa tajita kamar ana zarar ranta. Saida zarah ta jijjigata ta dawo dai dai, "zarah muje wurin dana ingan shi, kar yarona ya mutu muje inga halin da yake ciki.
Ita ta dakko mata key da hijabi suka fito, su fauzy na tsaye turus basuda niyyar motsi, sanin halin khaleel yasa suka Kira driver yafada musu inda suke, Naziya kuwa kuka takeyi kamar zata mutu, idan ta kalli jinin dake kwance inda aka dagashi, hijabin jikinta ta zare cikin rudu ta goge kasan tiles din tsab tana kuka, Aunty Raliya ta Kira tana kuka tafara fada mata, ta lallashe ta tareda cewa "kiyimai Addu'a Allah yabashi lafiya ba kuka ba, banason shirme. Toh Aunty. Ta datse kiran tana mai dauro Alwala ta koma kan dadduma hannayen ta a Asama domin neman sauki wurin mai duka.




Gefen mommy koda suka isa Asibiti daidai da zuwan kawu modu domin Khaleel ya kirashi, hawaye yake sharewa tareda sintiri, kawun na zuwa yace " Meya same shi khaleel? " d'an uwana Kawu yana Aman jini hanci da baki suna ciki har yanzu basuce komai ba, ya mugun fita hayyacin shi, matsowa Mommy tayi jikinta na rawa "Ibrahim me yasamu d'ana?. Dago idanun shi yayi ya kalle ta cikin kallon kece sanadi mommy. "Look at it mommy kinga irin ta ko, d'an uwana na cikin Wannan halin because of you, mommy don dai ke uwata ce Amma in wani ne bazan taba yafe mai ba, now just pray d'an uwana ya tashi lafiya I promise dole abashi farin cikin shi that's enough! hakurin shi yayi yawa. "Ibrahim ' kawu ya daka mai tsawa, "me yasa kake fadawa mahaifiyar ka magana haka, me yafaru? Matsawa yayi cikin karyewar zuciya, ya fada jikin kawun ya saki kuka mai zafi Wanda ba Wanda zaice jarumin namijin ne ke irin Wannan kukan.
Bubbuga bayan shi kawu yayi " ya isa insha Allahu zai tashi lafiya, Kayi shiru haka. Fitowar likita ne yasa ya yi saurin share hawayen yace "lafiya doctor yaya na fa? "Please kaine Khaleel?. "Yes". Come your brother is calling you.
Bin likita yayi da Sauri kawu ya bishi shima, mommy zata shiga likita yace su tsaya waje mutane zasuyi yawa a emergency.
Jinin ya tsaya kadan sai Wanda ke bin hancin shi kadan kadan, yana isa yaja gefen rigar shi ya goge mai, "yaya please ka cire damuwa zaka tare da Matar ka I promise you kaji. Wani irin numfashi yaja mai wuya tareda fitarda murmurshin dole.
Yace "kawu", tareda mika hannu yace ga Amanar d'an uwana, kawu don Allah ka kula dashi ka tsaya mai akan komai, inason yayi farin ciki, kawu don Allah make him happy kar ya shiga damuwa idan bana nan, Khaleel take care of Naziya, where is she? Please call her, ka kawo min ita Ina so in roketa gafara please go and bring her. Ja da baya yayi tareda girgiza kai, " no no no stop that yaya nothing is going to happen to you, bari inkawo ta please yaya kadaina magana haka ciwo ai ba shine mutuwa ba, I don't like this, stop it. Am sorry Khaleel. Yafada yana mai kallo mai cikeda sakonni, fita yayi da sauri yana yi kamar zai tashi sama, riko hannun kawu ya kuma yi, "kawu don Allah kar Kabari Naziya ta fita agidana ko bani, kawu kabawa Khaleel ita ya Aura nasan zai bata kulawa saboda soyayyar da yake min please kawu". Mugun sanyi jikin kawun yayi domin Abun ya tsorata shi, a'a Ahmed kadaina irin Wannan maganar, haka d'an uwana yatafi yabarmin Amanar ku, bangama saukewa ba zaka bani wata, Insha

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login