Showing 6001 words to 9000 words out of 107087 words
Chapter 3 - AUREN GADO COMPLETE DOCUMENT Book by MATAR SOJA.txt
tunda zancen yaje kunnen mommy ba fashi, yafada Yana dariya,.
Fita yayi daga dakin yayan nashi yanajin wani iri "Aure? Gaskiya bai shirya ba infact zaiyi ne saboda yayanshi ya insisting kuma koda baison Abu Idan yayan shi na sonshi dole shima ya soshi, Allah kadai yasan iyakar soyayyar da yake wa d'an uwan nashi, kwanciya yayi a kujera a dakin nashi Yana mai runtse idanun shi, so yake ya tuna komai na fauzy da quality's dinta just for Ahmed, Amma first thing da yafado mai a rai yasa ya zabura tareda girgiza kai, "no no no why her?
Cikin Sauri ya dauki wayar shi domin ya k'aryata tunanin shi, fauzy ya Kira, kamar mai gadin wayar ta ta dauka jikin ta na rawa "oh my goodness darling you call me? Tafada tareda Sanya kukan farin ciki, tundazu take kiranshi yaki dagawa har wani zazzabi takeji saboda damuwa tana yimai wani irin so mara misali. Tun isowar ta ake tarairayar ta Amma duk natsuwar ta bata tare da ita,
"Yes I call. Yafada Yana gyara zaman shi domin baisan ma mai zaice ba kuma. "Tank you darling for calling, please Ina so inganka kasan is hard for me kwana daya bansaka a idoba I can't. "Is OK zaki iya zuwa gidan mu gobe yanzu dare yayi. "OK am coming tomorrow tank you darling. Tafada tana buga tsalle tareda rungume filo, tasan yafara damuwa da ita tunda har yake so taje gidan su yanzu, hakurin ta ya fara aiki yanzu. Kwanciya tayi tareda Addu'ar gari yawaye ta ganta agidan su.
Gefen Naziya ta shiga gida da takaicin khaleel, domin yaron mugun d'an wulakanci ne, inba wai gizo idanun ta ke mata ba kamar kallon kyama yake mata, bayan duk unguwar su an shaida tsabtar su, duk da suna fama da Almajirai Inna kulu nada kokarin ganin ta tsabtace gidanta sosai,. Kwance take tana juyi shukrah ta matso gefen ta akan Y'ar madai daiciyar katifar tasu, tace "Aunty lafiya? "Hmm bakomai. "Aa Ina kallon yanda kike ta juyi tundazu kinkasa bacci, meke faruwa ne? "Kawai Ina tunanin yanda zan zauna da Ahmed ne tareda kanin shi shukrah dazu sunzo, baida k'irki irin Ahmed ya cika girman kai da nuna shiyayi karatu a kasar waje. "Ni kuwa Aunty kallon Arziki sosai nakeyiwa Yaya Ahmed fa. "No yafada min Yana da ubangida mai kirkine watarana motocin yake zuwa dasu, "nidai Aunty Ina tantama domin ko tsarin jikinshi ya isa ya nuna Yana cikin hutu. "Ni kuma me zakice dani? Tunda kowa kallon Y'ar masu kudi yakemin a school ko in munfita, halitta ce kawai. "Hmm tom kiyi bacci Ki kyale wani kanin shi Bashi zaki Aura ba.
Washe gari Karfe goma tayi mata a gidan su khaleel cikin tangamemiyar motar ta ta yayi, da kanta ta tuko kanta, da taimakon shi ta zo gidan domin unguwar su ba boyayya bace, momy ta zage sai rawar kafa takeyi an shirya mata tarba Kala Kala, cikin adon jan material doguwar Riga dinkin yayi na yayan masu daula, taci gwala gwalai wuya da hannayen ta tana zabga sheki da kamshi. Ta hadu ba sauki domin ta iya caba ado. Tasamu tarba gefen momy, Wanda koda tazo gidan bai tashi baccin safe ba,
Momy sai Ina ta saka Ina ta Ajiye takeyi da ita, sai zare idanun ta takeyi taga inda zai bullo. "Huh khaleel na bacci haryanzu bai tashi ba, kinsan da gajiya a jikin shi.
Shigowar Ahmed ne yasa Momy tace "ka duba d'an uwan ka ko ya tashi ga bakuwar ta iso. Gaisawa sukayi Yana Kara ganin wayewar ta da kudi Wanda yasan ba yanda za ayi Naziya tazo gidan nan saboda shi, banbancin yayan talaka kuma y'an gidan mutunci kenan da kuma ya'yan masu kudi. Yanzu meye Abun burgewa a nan mace ta nuna rawar kafa akan namiji, idanun fauzy ya gama budewa gaskiya and zasuyi kusan sa'a da Khaleel like he said, wucewa yayi Yana daya sanin bashi goyon baya akanta,.
A kwance ya sameshi Yana kallon saman pop, "oh you wake up? So kazo fauzy is here. "You see tunda Asuba mayyar ta tanbayeni address nafada mata don uwar ta a gidan mu zata karya? Dariya Ahmed yayi, "Auzubillahi yada zagi? "That's why Yaya bana sonta wallahi batada kamun kai Sam ace Karfe goma ta zo wurin saurayi saikace ba iyayen ta a gidan. "Yanzu dai katashi kayi fresh up kafito tana jira mother in law dinta ta bata big welcome. Tashi yayi ya shige bathroom, like Always Saida ya kwashe hour guda kafin ya fito Wanda shirin nashi ma Saida ya kwashi rabin hour cikin guntayen kayan nashi kamar yanda ya saba.
Cikin takun kasaita da shan kamshi ya fito falon, fuskar shi Sam ba fara'a, "ga shinan yaron kirki ya fito. Mommy Tafada tana mikewa tareda taroshi kamar wani kwai jitake kamar ta goyashi saboda so, jikin fauzy na rawa tace "hy darling kamar ta ruga ta rungume shi takeji. "Tashi kuje dakin shi zakufi sakewa bari insa a hado muku breakfast akawo ciki. Cikin sakewa tace "Saidai baby ni ai mommy kin cika min ciki tun zuwana kike duramin ciye ciye, Tafada tana Dariya, "Allah Y'ar nan, to bakomai ai gidan kune nan.
Zama yayi a falon fuskar shi a cakude yace "ke iyayen Ki basa gidane kika fito early morning? Kallon fuskar shi tayi tareda yin murmushi duk da tasan maganar banza yafada mata ranta bai baci ba, "mommy na nan dady na nan kuma sun san inda naje. "Really? Kuma basuyi kokarin hanaki ba? "Why zasu Hanani? Bayan su masu goyon baya na ne akan duk Abinda nakeso kasan cewa sun san komai akan ka dady na a shirye yake da katuro neman Aure na, please khaleel ka cika mun burina I promise zaka sameni yanda kakeso zan share maka damuwar ka duka zanbaka gatan da mata basa iya bawa mazajen su just give me chance.
"OK zanturo tunda mommy ta Amince dake and my brother too yanzu kije gida zanturo. Tsalle ta buga tareda Dane shi ta rungume shi kam" don Allah da gaske zaka tura? Oh my god khaleel zanyi suman dadi yau. Tafada tana share hawaye, ban bare ta yayi a jikin shi ya ce "oh come on a gidan surukai kike fa behave yourself.
"Farin ciki ne yamun yawa baby muje mota indakko wa momy tsarabar ta please, Tafada tana riko hannun shi, jinta takeyi kamar anyi mata bushara da gidan Aljannah....... 🖊
*Matar Soja*
🌻🌻 *AUREN GADO* 🌻🌻
*Matar soja ce*
Daga marubuciyar
KUSKURE NA
BARIKI AUREN SOJA
MUK'ADDARI
WANAKE AURE
ZANYI BIYAYYA
And now AUREN GADO,
🆓 page
5⃣&6⃣
..,.......... Kaya na kece raini ta kawowa momy tsaraba Wanda tayi ta godiya kamar zata goyata, bayan tafiyar ta bata da wani zance sai na "Ibrahim khaleel bikin ka zamu gwan gwaje ba karya kaga Abun Arzikin da ta kawomin tun ba ayi Aure ba? Wucewa yayi cikin dakin shi domin shi yanzu daya sani yake mara iyaka daya Amince mata tazo gidan su har Mommy ta ganta, yanzu ya boni shikam.........
Wasa wasa Saida aka kwashe kusan sati daya bai kuma daukar wayar taba ta Kira ta turo msg yafi hamsin Yana shareta, momy tayi nacin zancen turawa gaisuwa Yana ja baya, domin shidai bai shirya ba infact baya ra'ayin zama da fauzy she is not his choice zai cutar da itane kawai, bazata taba samun kanshi yanda take soba. Bikin Ahmed da Naziya ya matso gefen gidan su shikadai ke shirin shi da Abokan shi Yana cikin tsananin farin ciki, momy tace bazata wahala akan Y'ar talaka ba, yan uwan tane dai suka fara cika gidan, musamman Aunty zarah, Wanda itace kanwar ta da sukazo hali daya, komai na Aunty zarah sai a hankali tana son gayu da babbar harka.
Duk akwatunan da Ahmed ya hada momy ta sa anrage duk wani gold tasa ancire ansa passion wai basu san darajar su ba talakawa ne. Baida yanda zaiyi saidai farin cikin shi daya Khaleel ya hadomai Nagani na fada a bangkok, don haka sunkai sun boye sai in ta tare, duk wani event mommy ta soke wai yarinyar da ba wayayya ba yaja musu Abun fada bada itaba, don haka ya hakura domin Albarkar Aure yake nema in Allah ya mallaka mai ita burin shi ya gama cika, sannan farin cikin shi daya itama tace bata son wani bidi'a walima ta isheta da za ayi a gidan su,.
Khaleel yana gefe baya cewa komai he just feel boring baiga Abun burgewa a yin Auren ba ba wani Abu da ya bashi sha'awa da har zaiji yanason yayi Auren ma, fauzy sarkin naci tazo tun Ana jibi Bikin ta tare duk inda Aunty zarah ta shiga suna tare gaba daya yabi d'an uwan nashi sun kauracewa gidan suna part din Ahmed saboda jama'ar da suka cika na momy, yaki ko Yarda su hadu da ita, ta d'an ji sanyi ganin tana cikin gidan su kuma no matter what sai sun hadu kafin ta koma gida, ita da ta samu daurin gindi a wurin uwar miji ma, ita kanta tasan mommy batason Auren Ahmed domin ta gama bata labarin ta tas.
Rana bata karya inji bahaushe, Alkawari ya cika, inda Aka daura Auren Ahmed da Naziya akan sadaki mafi daraja, sai muyi fatan Allah ya kade fitina, tunda aka daura Auren ya baro taron ya dawo gidan tareda kulle kanshi cikin dakin su, zazzabi yakeji mara dalili tareda jin wani irin bakon Al amari a tattare dashi, Ahmed nata neman shi, Saida ya kirashi ya dauka yafada mai cewa yana gida, dawowa yayi shima tareda barin Abokan shi ya same shi a dukun kune cikin bargo,
Cire babbar rigar shi yayi ya zauna gefen gadon tareda cewa "bakada lafiya ne? "Fever ke son kamani, "sorry namiji, kasan me? Yafada yana gyara zama, tashi Khaleel yayi ya jingina a jikin gadon yace what my brother? "Burina yacika khaleel, today Naziya is legally mine, but am worried me zata fuskanta a cikin gidan nan, how is she going to react after she find out about everything? "Like what brother? Like our wealth, this big mansion, and mommy. Yafada yana rage murya cikeda tausaya wa kanshi, kamar yarone yaga alawa Ana mai kwalelenta haka yakeji yanzu, yasamu farin cikin shi Amma baya cikin farin ciki.
Matsowa yayi sosai kusa da d'an uwan shi yace "Yaya this is the time da zakayi fighting back, ka tsaya akan ra'ayin ka, you have to talk brother, fight for your love, and Aunty Naziya will be happy bazaka samu Matsala da itaba, in tace zata sama yayana hawan jini bazan raga mata ba cos batasan irin fighting da kakeyi akan soyayyar taba. "Hmmm you known, nafison momy ta barni in zauna a gefen mu, bana son Naziya ta shiga cikin damuwa nasan zata sha wahala Idan akace zata zauna cikin gidan, she can't handle it, bata saba da irin wannan rayuwar ba. And mommy is our mother dole mubi Abinda takeso Auren Naziya da A hannu na yake Dana hakura for mommy happiness, but Allah kadai yasan mai ya boye a cikin Al' amarin,
Yafada cikeda damuwa, Dariya khaleel yayi mai d'an sauti wadda ta Kara bayyana kyanshi sosai, "Yaya this my Aunty is very lucky, tasamu miji mai sonta sosai Anya zaka kuma Aure nan gaba like the way mommy is planning? " no Khaleel bana son Naziyata ta zauna da kishiya Ina so tayi rayuwar y'anci ne, Ina son inganta cikin hutu da walwala, khaleel na gama tsara irin yanda nakeso rayuwar Naziya ta kasance, I love her beyond your imagination, ka tayani son Naziya kaima kamar yanda nake sonta.
Sundauki dogon lokaci yana daukewa yayan nashi damuwa ta hanyar k'arfa famai guiwa, Saida friends suka fara kiranshi ya Fita tareda barin khaleel cikin damuwa, Alwashi ya dauka mai girma akan zai taya yayan shi fighting akan duk Abinda zai daga mai hankali bazai so yaganshi cikin damuwa ba,.
Bai kuma Fita a gidan ba ko sallah a part din yakeyi ya koma ya kwanta, yarasa abunda duk ya Cire mai walwala da natsuwa bayajin dadin jiki da zuciyar shi baki daya, he just fee like going back to bangkok, baisan mai ke hana shi sukuni ba. Sai Karfe Tara Ahmed ya kuma shigowa dakin ya tsaya a kan shi tareda cewa "brother what is wrong? You look very dull. "I don't know Yaya kawai bana jina cikin natsuwa. "relax nima haka nakeji tundazu but now am fine, your Aunty is here khaleel, finally Naziya is here. Zama yayi tareda rungume Khaleel din yana fitarda hawayen da yarasa na menene ke fitowa daga idanun shi.
Saida ya d'an natsu yace let go and welcome your sister in law. Mikewa yayi ba musu, ya bishi sanye cikin kana nan guntayen kayan da ya canja tundazu.
Gefen Naziya kuwa tunda suka sako kai cikin wannan tafkeken gidan gaban ta ke faduwa gashi gwaggonnin tane suka rakota su uku bisa ga umarnin malam domin baison gayyar tsegumi, kanta a duke yake tunda motar da ta dakko su ta shigo, cikin Y'ar rakiyar ta daya tace "t'irk'ashi wannan gidan mutum daya ne ko dai gidan y'an yankan kai? Sauran suka fara salati, shikenan malam saida Y'ar nan yayi, irin wannan gidan saikace wata unguwar? Saurin daga kanta tayi ta saki baki tareda dafe kirjin ta tana karanto Addu'ar tsari a cikin zuciyar ta, jikin ta shegen rawa yafarayi. Har motar ta tsaya Abokin da ya dakko su yace "Hajiya kufito mu shiga ciki ko? Kamar way'enda kwai ya fashewa a ciki haka suka fito ji sukeyi kamar ace ar su ruga, shi ya musu jagora kowaccen su Addu'ar da duk tazo bakin ta takeyi, rike take da tsintsiyar hannu irin wainda ake rikewa na share dattin daki a wurin sabuwar Amarya bisa ga Al Ada, nasan wasu sun san wannan Al Ada akan ce ta share duk fitinar d'akin kafin ta zauna cikin dakin ta.
Daya cikin gwaggon nin nata tace "kawo Abar nan inrike da ita zankoma Y'ar nan domin ko takarda bazaki shara ba a gidan nan, "Toh ai gidan da waje ma babu ko Alamar d'aud'a bare ciki, ai wajen ma ni yafi dakina tsafta, haka suketa sambatu tsakanin su. Ita kuwa jitakeyi kamar ta ruga da gudu saboda tsoro, wasu irin zafafan hawaye ne ke zubowa akan kyakkyawar innocent face dinta. She is regretting today, wayace ta Amince mai? wayace ta yarda da Auren shi? gashi yayi mata karya yakawo ta gidan da bata taba zuwa kusa da irin shiba.
A falon mommy ce hakimce itada y'an uwan ta, Zarah ce ke gefen ta da kuma uwar y'an kanzagi fauzy, sunayin Sallama mommy tace Zarah kusa katuwar tabar mar nan akan carpet din Idan sun tafi a fita a Y'ar da ita a waje kar k'uma ta shigo mana gida.
Sunji komai a kunnen su jikin su na rawa suka karaso akan tabarmar suka zauna tareda gaida su cikin girma mawa, cikin su daya tayi karfin hali tace "Hajiya toh ga Amanar Y'ar ki nan Allah ya tayaki riko.
"Ni Amanar me zaku bani saikace wata kishiya ta, to kuji infada muku tun mijina nada rai ko zance bai taba zuwa ba bare ayi zancen yimin kishiya, don haka karma ku fara ku jira Wanda ya Auro ta yazo kubashi...... Yauwa ga shi nan ma, Tafada tana nuna shi domin yana fitowa yaji zancen momyn wani irin zafi tareda damuwa zuciyar shi ta shiga. Khaleel ma yaji komai kuma he is not happy da irin yanda mommy takeyi ga su fauzy dake musu wata irin Dariya kamar sunga kashi itada zarah, wani irin baci ran khaleel yayi da Sauri ya matso tareda kallon Fauzy, " ke wace iri ce uban me kikeyi a gidan mu haryanzu baki tafi ba?
"Aa banson shirme Ibrahim, ya yarinya tazo maka k'ara zaka hauta da fada? "Mommy angama Bikin tazo ta wuce gidan ubanta tom. Jikin ta na rawa ta zabura ta nufoshi kamar zata fada jikin shi "no please na dauki permission wurin mommy na ta yarda inyi kwana biyu baby just for you..... "Oh come on, ke meyasa bakisan..... Saurin dafashi Ahmed yayi domin bayason more humiliation agaban y'an uwan Matar shi Dama ita kanta, yanzu yana tunanin how he is going to face her ne ma.
Shiru yayi tareda juyawa da Sauri ya yi cikin dakin shi dake part din momy, ranshi yayi mugun baci dole ya koyawa wannan fauziyar hankali gobe.
Fadin zuciyar Naziya da tunanin ta bata lokacine ma, daya daga cikin y'an uwan mommy ne tace "ku muje in nuna muku part d'in ta, Tafada tana mikewa kafin ya yar ta ta kuma kwab'a, sanyi Ahmed yaji domin yama d'askare yakasa ko motsi.
Suna shiga suka ware idanu domin basuga ko tsinken da sukasa aka kawoba, wadda ta rakosu ce tace "wannan dakin mijinta ne gidan su na waje a can akasa da kayan ta, kamar tasan me suke tunani,
Domin sunga gadajene na kasar waje ba irin nasu d'an wambai ba.
Cikin sauri sukace "tunda munrako ki Naziya mu zamu koma dare nayi, Allah yabada zaman lafiya da hakuri kinji ki rike tarbiya da mutuncin malam Dana kulu domin kinsamu tarbiya dai dai gwargwado kinsha nonon hakuri da kuma mutunci, Allah ya kade fitina. Suka juya cikeda sanyin jiki, riko daya daga cikin su tayi tasa kuka "Don Allah gwaggo karku tafi kubarni ni kumayar dani gida wurin Inna bana son nan gidan. Tafada tana kuka mai cikeda tausayin kanta da Rayuwar ta, daga shigowar ta harta karanto irin Rayuwar da zatayi a cikin wannan gidan.
Shigowar Ahmed