Showing 30001 words to 33000 words out of 107087 words

Chapter 11 - AUREN GADO COMPLETE DOCUMENT Book by MATAR SOJA.txt

04 Dec 2024

5657

bazai tanbayi d'an uwana Wannan hakkin ba? Ta dalilin tsanar da kike yimata har tabar gidan nan bataji dadin rayuwa da mijinta ba why Mommy? Don haka itama Matar son taki tayi biyayya irin nata tagani.
Ibrahim banson rashin kunyar ka haka kaga Ahmed.... "Mommy enough, kidaina kwatance da yaya, ribar me yaci, kinga Amfanin Abinda duk yakeyi? See to avoid you and your wife, am going back to bangkok, zanje in kulada duk wani aiki da yayana yakeyi, bana ra'ayin zama anan, I don't need her idan tagaji tasan hanyar gidan Uban ta.


"Ibrahim, zan hadaka da kawun ku inni bazakaji magana taba. Wucewa kawai yayi, dama so yake kawai ayi fourty days ya yi gaba Amma yanzu baijin zai iya Kara ko kwana daya a garin kano gwara yatafi ko zai dawo dai dai.
Duk gurmin da Akeyi Fauziya ta shigo tana kallo, yana wucewa a zuciye ta nufo mommy cikin kallon tsana da kece sanadi, tace Wallahi bantaba sanin Abinda kikayi zai shafi farin cikina ba dana taka miki burki, kuma zanje in shirya inbi mijina. Ta buga mugun tsaki, "Fauziya karfa ki manta ni uwar mijin ki ce kike fadamin maganar da kikaga dama. uwar miji uwata ce ko uwar ubana ce? I beg give me a break. Ta yi gaba zuwa dakin shi dake part d'in .


Yana hada kayan shi, tayi sallama yayi wurgi da Abinda ke hannun shi saboda haushin takurar ta, ya juyo cikeda haushi, "can't you learn from Naziya, kintaba ganin tana bin yaya the way you are following me? Please have some shame.
"Oh baby yazaka hanani bin mijina, you are my husband Inada right akan ka, and ka daina hadani da Wannan village and stupid girl....... Wani irin kukan kura yayi a wuyan ta, tareda shake ta ya hada da gini idanun shi kamar na bakin kumurci, "what did you said? Cikin karaji, don't repeat that again if not kin gama numfashi a duniya, I promise you, kin ce hakki ko kinada hakkina? gani ki diba in kinada karfi, hakkin na karfi ne kizo ki kwata, useless, now get lost. Ya saketa tareda hankada ta waje,


Da mugun kuka tafita falon Wanda mommy naji tayi Saurin tarar ta, Fauziya lafiya Me Khaleel din ya miki? karki tabani kuma wallahi sai na fadawa daddy na ke kikaja Wannan aikin da kike taka ma dashi sai kin barshi. Tafita tana kuka, hannu ta dora aka, kunga yaro zaimin salalar tsiya, Allah sarki Ahmed da kana nan kaine kadai mai iya takawa yaron nan birki, Allah ya jikan ka yaron kirki Allah yakai haske kabarin ka.
Ta share kwalla tabi bayan shi,
Lokacin yagama shirya jakar shi, kallon kayan tayi tareda zubamai ido, yanzu Khaleel bangama war warewa a rashin d'an uwanka ba zaka tafi kabarni bayan kasan banda kowa sai ku biyu kacal, yanzu shi yatafi kai kuma zaka tafi kabarni.


Baice mata komai ba yayi hanyar bathroom, fita tayi tana fitar da hawaye, wayar ta ta dakko tafara kiran number wayar kawun nasu, yana dauka tasa mai kuka tareda fadamai komai akan zaman shi da Fauziya, da kuma tafiyar da zaiyi. Yace mata Yana zuwa kawai ya katse kiran.
Bayan hour biyu kawun ya iso lokacin yaci Ado cikin manyan kaya Wanda rabon shi dasu tun kafin mutuwar yayan nashi,
Lekowa mai aiki tayi tace Ana kiran shi a falon, ya ce tace yana zuwa, fitowa yayi, yasamu mommy gwanin tausayi gefen kawu akasa yau tunda tana neman taimakon shi. Sallama yayi yagaida shi, zama yayi a kasa kanshi akasa, fuskar shi ba annuri ko kadan, kawu yayi gyaran murya yace "Khaleel tafiya zakayi batareda sani na ba? "Aa kawu yanzu ma gidan naku nake shirin zuwa infada maka.Toh Amma me zakaje yi kabar nauyin da yake wuyan ka anan, nafarko Matar ka, na biyu mahaifiyar ka na uku company, sannan wasiyar d'an uwan ka, ko bazaka cika mai burin shi bane, domin yafadamin tun ranar da zai rasu saboda rashin natsuwa banyi maganar da kowa ba, sai Malam, dago kanshi yayi domin jin wane magana akayi harda malam zai shiga ciki, "Ya bar maka Amanar Auren Naziya, kuma munyi magana da malam tunda zance ne na wasiyya ya Amince sai dai muyi Addu'a ta fita takaba lafiya sai a daura muku Aure da ita.


Wani irin zufa Kebin ta kowane kofa ta jikin shi, yakasa koda motsi baya iya koda daga yatsar hannun shi balle ta kafar shi,
Kukan mommy ne yasa yadawo hayyacin shi , wallahi bazai yuwu ba, yaza ayi yaya ya Aura ya mutu kanin shi ya Aura, kuma dole ne ni sai nayi Rayuwa da Wannan yarinya mai kamar mayya, nidai ban Amince ba gaskiya bada yawuna ba.
Kallon banza kawun yayi mata kafin yace " ni nasan bazaki canja ba balkisu, kuma nasan ilimi yayi miki karanci da kin koma islamiyya, tunda bakisan Ibrahim zai iya Auren Naziya ba, kuma Ina so insani me yarinyar tayi miki, ko ince meye laifin ta? Ni tanada laifi A wurina kana ganin saboda soyayyar ta dana ya hadiyi zuciya ya mutu, banason ta kuma lashemin zuciyar Khaleel din da ya ragemin nidai bada yawuna ba.


"Yawun ki basuda Amfani a wurin mu don haka Khaleel gareka idan ka Amince kafin ka wuce kaje kaga malam Allah ya taimaka ya kuma tsareka, sannan zancen Matar ka Wannan kaidai ba jahili bane kasan hakkin Aure to don haka Kayi kokari Kayi Abinda ya dace ni natafi.
Yafada yana mikewa, tashi yayi jikin shi a sanyaye yabi kawun Saida ya shiga motar shi yadawo gidan, tana nan ta cika tayi tab. Kana jina Ibrahim, wallahi kar kasake inji kadawo min da Wannan yarinya mai farar kafa gida, karka sake ka Amince da Wannan Auren nafada maka.
Wucewa kawai yayi cikin dakin shi, ya datse key tareda zubewa akasa, wasu irin hawaye masu zafin gaske ne suka zubo mai, wainda baisamu yinsu ba tuntuni, Ashe maganar da Ahmed kullum yake fadamai zata kasance gaskiya, Wato akwai Abinda Allah ya boye shiyasa ya cusa mai muguwar soyayyar Naziya wadda bai taba yarda da itaba domin yasan is prohibited,
Yasha wahala yana kuma kan shan wahalar, zai iya rantsuwa da Al'qur ani yafi yayan shi son ta, Wanda baisan ya akayi soyayyar ta ta shiga zuciyar shi ba, how? when? Wani irin kuka yakeyi Am sorry yaya am sorry my brother da nasan zaka tafi kabarmin ita da na roki Allah ya cire min soyayyar ta ya barmin kai a rayuwa, Am sorry for loving your wife more than you brother, am sorry for feeling jealous idan kuna tare baka sani ba yaya, Inada kishin ta sosai yaya I use to cry behind door saboda zafin kishin ta, you are my brother but Ina kishin ganin ku tare, bansan ya akayi soyayyar ta ta shigeni ba, I love her more than the way you love her, I hate myself for that I swear to you, I control my feelings because of you.
You're dead because of hidden destiny, hawayen shi ya share tareda hadiye kukan, "I will make her happy yaya zancika maka burin ka, zanbata farin ciki fiyeda yanda Kayi mafarkin bata, zansata dariya fiyeda yanda take dariya idan kuna tare. Mikewa yayi ya zari key din hadaddiyar motar shi tareda goge fuskar shi da kyau ya fita cikin hanzari a falon da yabar mommy a nan ya same ta tana waya tana fadawa y'an uwan ta bakin labari, Modu ya rantse sai ya cakuda jinin ta da talaka........ . 🖊








"Comment share the free pages please and Wannan ne last free page ku biya ku karanta cigaban yanda zata kasance, ya za ayi da rayuwar Naziya shin zata Amince, shin zataso Khaleel, ya rayuwar su zata kasance da Fauziya, idan Naziya ta Amince da Auren Khaleel wace wainar mommy zata toya????? Muje zuwa yanzu za afara wasan this is just the beginning, let's go my fans 💃, ga masu bukatar biya kofa a bude take chart me up 09011251444








*Matar Soja*














🌻🌻AUREN GADO🌻🌻







*Matar soja ce*






Daga marubuciyar
KUSKURE NA
BARIKI AUREN SOJA
MUK'ADDARI
WANAKE AURE
ZANYI BIYAYYA Y'AY'AN GATA
And now AUREN GADO,














Ga masu bukatar Wnn littafi ku turo kudin ku ta Asusun banki na 7304736012 nafisa sani hassan Fcmb ko katin wayar ku ta Wannan number 09011251444, sai kuma y'an 🇳🇪 Niger ku tuntubi Wannan number domin biyan naku, +225 0748153903, littafina Dari biyar ne kacal 500 sai najiku nagode,




2⃣1⃣&2⃣2⃣




................ Tuki yakeyi cikin kwarewa tareda bin k'aidar hanya, ya riga yasan hanyar gidan nasu Naziya, tunda yazo sau biyu, har kofar gidan ya isa, lokacin yana mak'il da Almajirai, da Alama Malam na gida, fitowa yayi yana wani irin sheki da haske duk da ya rame saboda mutuwar d'an uwan shi, wani Almajiri ya Kira yace yamai iso wurin Malam yace mai Ibrahim ne kanin Ahmed, ko minti biyu ba ayi ba saiga Malam cikin fararen manyan kaya, tsohon akwai tsafta da kwarjini, yayi saurin dukawa zai gaida shi, a'a Ibrahima tashi shigo daga ciki,
Har tsakar gidan yajashi domin zauren akwai mutane, yanayi yana kallon tsarin wurin Wanda zuciyar shi ke ayyana mai komai, tsakar gidan akwai inuwar bishiya wadda a karkashin ta aka samai kujera ya zauna Malam ma ya zauna suka gaisa kafin Matar k'irki ta fito, d'an dukar da kanshi yayi ya gaidata ta Amsa tareda yi mai gaisuwa, kafin Malam yace Hauwa Kira min Naziya, kafin nan shukrah ta kawowa bako ko sobo ne mai sanyi. Wani irin lugude yaji zuciyar shi tayi jin ankira sunan ta, ta' aziya Malam yakuma yi mai tareda fatan Samun Rahamar ubangiji, yabishi da nasihohin da duk in zakazo wurin shi sai ya maka su. Shukrah ce ta kawo zobo mai sanyi a tsaftataccen sabon jug cikin na Naziya, ta Ajiye tareda gaida shi tayi gaba,
Fitowa naziya tayi cikin katon hijabin ta, kana ganin ta kasan ta rame sosai,
Sallama tayi, ya dago kanshi suka hada ido, Wanda tunda akayi rasuwar daga ita harshi basu hadu ba.
Allah ya gani bata son shan inuwa daya da gayen nan don kawai yaci Albarkacin Ahmed ne batada yadda zatayi dashi, Amma tunda yanzu mai rabawa ta raba shikenan ta huta,
Gaida Malam tayi batada niyyar gaida shi, saida Malam yace ga kanin mijin ki naziya, dama Ina so in samu lokaci muyi magana daku dukan ku, akan wasiyar da mijinki yabari, wani irin faduwa gaban su yayi duka shi tsoron reaction dinta yakeyi ita kuma batasan wace wasiyya bace.
"Ibrahim Alhaji Amadu yazo min da maganar kuma ni bazanyi jayayya da wasiyyar mamaci ba" don haka yanzu magana na wurin ku, Naziya mijinki yabar wasiyya d'an uwan shi ya Aureki, don haka idan kinfita takaba sai adaura muku Aure.
Wani irin kukan tasa tareda zama gaban Malam d'in. Kallon lafiya Malam ke yi mata, shikuwa wani irin tsalle zuciyar shi keyi saboda fargaba, "Malam don Allah karka Yarda nidai bazan koma gidan su ba, ni bazan yi Aure ba ni bana ma son shi kawai abarni haka, ni karatu nakeso inyi don Allah Malam karka hadani dashi.




Tashi kibani wuri Naziya banson shiririta, yaushe kika canja hali haka? tashi kafin ranki ya baci, wucewa tayi da gudu dakin Inna, Malam ya kalle shi, Kayi hakuri kaima bansan naka ra'ayin ba, Amma tunda kaine namiji in har ka Amince Naziya ita ba Matsala bace, kaje Allah ya maka Albarka yajikan d'an uwan ka, Ameen yace kawai zuciyar shi na wani suya, maganar ta ta bata son shi really touch his heart, wani irin zafi yakeji a kirjin shi, cikin dauriya yace Malam Wannan filin nakusa daku yaya Ahmed ya siye shi da sunan zai gina maka dakunan Almajirai batareda sanin kowa ba, bayan rasuwar shi Nagani a rubuce ya gama biyan contract din komai Allah bai nufa ya yi ba, inaso Inturo su, su duba yadda zasu tsara komai zanbar komai kafin intafi, zanje domin shigo da wasu kaya,


"Allahu Akbar Allah ya jikan shi yasa mutuwa hutuce a gareshi" Allah ya Albarkace ku baki daya. Ya Amsa da Amin, ya tashi yana farin cikin zai fara cikawa d'an uwan shi burin shi, duk da yatafi da ciwon maganar Naziya.
Bayan tafiyar shi ya kira Inna kulu da Naziya, ranshi a bace yace "Hauwa bansan cewa zan haifi yaron da zai yi musu dani ba, yau Naziya ke da nake yabonki kike kokarin watsamin kasa a ido, a gaban yaron nan kice bakya son gidan su bakya son shi, a Ina kika koyo Wannan d'abi'a? "Subuhanallahi Naziya me nake shirin ji"? Inna ni dai Don Allah ku yafemin Amma ni bana son komawa gidan nan nayi hakuri batareda nayi wa kowa korafi ba, yanzu idan na koma mutuwa zanyi, wallahi bana sonshi baida hali ba irin Ahmed bane, malam baka san shi ba.
Toh Hauwa tariga ta girma Y'ar taki, ni bazance komai ba tunda ta isa da kanta. Yafada tareda tashi yabar gidan kawai, a tarihin rayuwar shi itace ya' ta farko data farayi mai musu da gaddama.


"Naziya me kikeso ki yi"? Kin taba ganin ko Y'ar nan malam ya yi magana ta amsa shi bare ke? Wane irin abu ne nake gani ni kulu yau? "Allah Inna bana son shi ya zan iya zama dashi ni dai bazan koma gidan nan ba. Ta tashi tana hawaye tareda shigewa dakin su, kwalawa shukrah kira Inna Tayi, "gani Inna. Kiramin Y'ar nan a waya. Tasan wa take nufi don haka takira Aunty Raliya ta bata, Inna tace "kuzo kuyiwa Y'ar uwar ku magana ta canjo hali, nan tafada mata komai, tace karta damu za tazo tayi mata magana ita da Aisha. Dakin su ta koma tana kuka, tareda kudurin duk Abinda zai faru sai dai yafaru bazata taba Auren Khaleel ba, saboda tun farko jinin su bai hadu da juna ba, tayi hakuri ta zauna da Ahmed saboda tana son shi, Amma bazata taba Y'arda ta zauna da Khaleel ba, wai ma yaza ayi ta yarda da Wannan kwamacalar, bayan agaban shi yaga yanda Ahmed yake nuna mata so lokacin da suka samu sarari,
Shigowa shukrah tayi tace "Aunty wai fadan me Inna takeyi yi miki? Kuka kikeyi me yafaru? Rungume shukrah tayi tareda jin wani sabon kuka, "Shukrah bana son shi. "Waye bakyaso Aunty? " Khaleel, I hate him, bana sonshi wallahi bazan zauna dashi ba. "Ni Aunty bansan me kike fada ba.


"Ya za'ayi kisani tunda Auren ya koyo mata taurin kai, Naziya ki rufawa kanki Asiri karki wahalar da kanki a banza idan Malam ya karb'i lamarin nan ba mai canja shi, don haka na hore ki kiyi biyayya ki gama lafiya shine kawai.
Hadiye kukan ta tayi, dif jin fadan Inna, Shukrah ta tashi tabar dakin domin tasan ba hurumin ta bane, zama Inna tayi gefen ta tafara yimata nasiha akan bin duk abinda Malam ya zartar, shiru kawai tayi domin bata saba jayayya da iyayen ta ba, Amma zuciyar ta bata lankwasu ba, Sam bataji zata iya zama da wani kanin mijin ta ba, dama wani ne ba Wannan ba.


Yana tuki yana tunanin kalmomin ta," ni bana son shi. Kalmar datafi kona mai rai, don haka speed ya Kara, saida yagan shi cikin gidan su ya fito a zuciye, ya matsu gari bai Waye ba yagan shi yabar kasar nan, kwabewa yayi tareda watsar da kayan jikin shi ya zube akan kujera zuciyar shi mugun zafi da turiri takeyi, she is the first girl da ta kalli tsabar idon shi tace bata son shi, huci yake fesar wa saboda zafin zuciya.
Har zuwa dare ya kasa bacci shi kadai yasan ciwon zuciyar shi, a kwance yake dagashi sai boxer jikin shi na sheki kadaicin d'an uwan shi kawai idan aka barshi dashi wani Abu, amma yana ganin duk duniya ba wanda zai iya fahimtar halin da yake ciki, how he wish yayan shi na tare dashi, yafi son rayuwar shi fiyeda soyayyar Naziya, wadda ya Amince ta kashe shi akan yarasa d'an uwan shi gwara shi ya mutu, saboda yanzu ma ba Amfana zaiyi ba don ya dade da sanin bata kaunar ganin shi.
Turo kofar da akayi ne yasa yadago kanshi, fauzy ce, ta shigo cikin Sanyin jiki fuskar ta sharkab da hawaye, tana sanye cikin kana nan kayan bacci, kusan duk komai nata a bayyane yake Wanda shi ba abunda ya burgeshi ciki, domin zuciya ma saida natsuwa take samun wani feelings, halin da yake ciki ko tsirara ta shigo gaban shi ba tashi zaiyi ba.
Zubewa tayi kan jikin shi tasa mai kuka mai ban tausayi, "meye illa ta, meye aibuna da ka kasa bani koda sakon zuciyar kace? Khaleel Ina sonka why ni baka sona? nayi hakuri da duk wani halin ka, yau kusan sati biyu Auren mu ba wani kulawa baka ko zuwa gefen da nake, Khaleel nifa mutum ce Inada jini, ni lafiyayyar mace ce, dole in bukaci mijina please tauye hakkin yayi yawa, sannan me nakeji? Auren Naziya? "That village girl"?.
Tunda take magana jikin shi yayi mugun sanyi, yes she is right ba ruwan Ubangiji da halin da yake ciki, tunda igiyar Auren ta na wuyan shi bai kamata ya watsar da hakkin Allah ba, amma this her last statement mess up things. Wani irin wancakalar da ita yayi kasa tareda mikewa yana nuna ta da yatsa " look that girl, I value her more than you, she is more important to me right now, karki sake inji wani mum munan kalma daga bakin ki akan ta, duk wani Abu da ya shafi d'an uwana yanada muhimmanci A rayuwa ta, ko a mafarki naji kin kuma kiran ta village girl sai na saba miki.


Tashi tayi tareda girgiza kai " lallai Khaleel, tell me,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login