Showing 27001 words to 30000 words out of 107087 words

Chapter 10 - AUREN GADO COMPLETE DOCUMENT Book by MATAR SOJA.txt

04 Dec 2024

5661

Allahu zaka tashi kaji, likita kuyi aikin ku mana,. Yafada cikin tsawa, "Alhaji muna bakin kokarin mu Amma zuciyar shi tariga tagama kunbura shiyasa yake Aman jini, tunfarko yasan yanada ciwon zuciyar yabari tunani yashige shi Wanda yafi karfin zuciyar.
"Karka kawo min hauka nawa zanbiya ayi mai aiki, inba zaku iya ba infita dashi waje. Mommy ce ta shigo tana kuka tareda matsowa kusa da gadon da yake" Ahmed meke damun ka? Me yafaru dakai? Don Allah katashi.
Rikota kawai yayi dakyar ma yanzu yake fitarda numfashi, "ki ya fe min mommy na. Ya fada daya bayan daya yana riko hannun ta gam Wanda tanajin rikon cikin jijiyoyin ta rikone mai matukar karfi irin na fitar rai, koda takalle shi kafin tace wani Abu sai dai ganin jinin tayi yana Kara fitowa tareda kafewar idanun shi sama, kafin ya saki Hannun ta. Suman zaune tayi na wucin gadi kafin likita da kawu su gama magana su juyo, zarah ma tashigo, wani irin tsinkewa jinin ta yayi domin ba tantama Ahmed dai rai yayi halin shi,
"Innalillahi wa Inna ilaihirrajiun. Kullu nafsin za'ikatul maut. Kowane rai tabbas ne zai daddani zafin mutuwa don haka sai muyi fatan cikawa da imani, Ahmed dai yatafi yabar Wannan duniya mai cikeda rudani.
"Aunty Ahmed yatafi" Zarah tafada tana dora hannun ta saman kai, kawu wani irin zuface ta karyo mai tuni ya ciro hular kanshi yana fifita, "ya Allah" Kawai ya iya fada saboda sarkewar kalmomin bakin shi, saida zarah ta jijjiga mommy, kafin ta fasa kuka"wayyo Allah na ni balkisu Ahmed tafiya Kayi kabarni, why Ahmed why?
Rufeshi likita yasa Akayi da farin zanin gadon, yace Alhaji sai hakuri Ahmed lokaci yayi. Dakyar kawu ya iya saita natsuwar shi yana goge gumi kamar ya hadiyi kunama, ya ciro wayar shi a Aljihu ya yakira Khaleel, " kana Ina? "Yanzu na shiga gida kawu zan dakko Matar yaya. "Stay there muna zuwa. "Why yaya yac.... "Just do as I said, yafada cikin fada kafin ya katse kiran.
Shi ya hada komai yayi clearing aka basu Ambulance Abunka da kudi cikin minti kadan suka tafi da gawar su,
Mommy kamar ta haukace ji take kamar a mafarki wai Ahmed dinta ne ya mutu. Aunty zarah ido yayi Hulu Hulu.


Naziya tun fitar su take kan dadduma, zuciyar ta bugawa takeyi da karfi takasa ko motsawa, su kuwa Amare suna hakimce kowacce taci Ado kamar masu gasar gwal. Sun hakimce a falon,
A harabar kuwa Khaleel ya kasa gaba ya kasa baya saboda tashin hankali, ga umarnin kawu, yana daskare jikin motar yaji kukan Ambulance, wani irin kallo yake wa motocin su mommy, ganin yanda Aunty zarah ta riko mommy sannan kawu shima ya fito kai ba hula, ya maida idanun shi akan Ambulance yana kallon nurses din suna bude motar, ganin sunfito da mutum rufe da farin kyalle ya zube kasa war was, domin baya bukatar Karin bayani akai. Masu aikin ne suka ruga wajen shi domin jin faduwar tashi Tim.
Mommy ta tafi luuu itama tana shirin zubewa, shima ya mutu ko zarah? In ya mutu shima ni tawa ai takare kenan. Tafara sambatu, zarah ta riketa tana jijigata a'a Aunty bai mutuba, kai ku shiga dashi ciki, kawu dai nata gawa yasa aka shige dashi ciki, hakama Khaleel anyi ciki dashi,
Wanda tuni hankalin kowa ya kawo kan abinda yake faruwa banda Naziya, domin Amarya Salifa ita kanta jikin ta yayi mugun sanyi, wane irin Abu ne haka Auren ta jiya miji ya mutu yau,
Kukan da mommy ta fasa yasa Naziya fitowa jiki na tsuma da carbi, ganin mutum kwance akasa ga kawun su zaune agaba ya dafe kai yasa tafito jikin ta a mace tana sand'a kamar barauniya.
Kukan dasu Aunty zarah dasu Salifa keyi yasa ta gano duk Abinda yake faruwa. Dabas ta baje akasa kamar kurma, kafin kace me, tuni ji da ganin ta sun dauke.


Koda ta farko, taga dakin ta makil da mutane harda su gwaggon nin ta dasu Aunty Raliya da kuma matan kawu.
Zabura tayi tana kallon jikewar da jikin ta yayi da ruwan da aka rika kelaya mata,
Ganin ta zaburo Aunty Raliya ta riketa, "Naziya bi a hankali ruwa ne a hannun ki. Kallon hannun tayi, tareda kallon mutanen tace mafarki nakeyi ba mutuwa yayi ba ko? Aunty bai mutuba ko? Ku fadamin Ina yake?
Dafata kanwar malam tayi tace "ki yawaita Inna lillahi Wa Inna Ilaihir Raji'una Naziya. Tafiya takuma yi luuu. Suka kwantar da ita, kowa na share kwalla,
Khaleel kuwa saida akayi da gaske ya farfado, lokacin angama hada gawar Ahmed, zabura yayi kawai, ko digon hawaye yakasa fitowa a idanun shi.
Kannen shi ne yaran kawu maza suka rikeshi "yaya Khaleel bi a hankali karka fadi. "Let me go. Yafada cikin fada. Kafin ya fisge ruwan yafice cikin Sauri lokacin za adauki gawar zuwa makwanci, harda malam yazo gidan yau.
Cikin sauri yace "kawu kubari inyi mai Addu'a, fuskar shi ba ko Alamar hawaye domin ance kuka wuri yake samu watarana zuciyar shi ta cushe ta inda bako digon hawaye dake shirin zubowa.
Kowa yasan na zuci yakeyi Wanda ke cin zuciya, don haka malam yace "Ibrahima, ka saki zuciya Kayi kuka bakyau hadiye Abu yana illata mutum cikin sauri.
"Malam muje akai yayana makwancin shi. Yafada yanasa hannu ya daga makarar gefe daya domin yasan idan shine yayan shi zaiyi mai har wankan karshe, Amma tunda bai samu yimai ba shine zai sakashi cikin Kabari tareda samai kasa da binshi da Addu'oi.


Yabawa kowa mamaki yanda ya sakawa kanshi jarumta, har zuwa makabarta, inda da hannayen shi yasakashi cikin Kabari, tareda yimai kallon karshe, Wanda anan zuciyar shi ta karye ya fara fitoda hawaye, shikenan yayan shi yatafi, gatan shi Wanda saboda shi yadawo Nija, da ana dawo da hannun ago go baya da ya canja tsarin rayuwar Dan uwan shi , da ya hanashi shiga bakin ciki, Amma me komai mukaddari ne baida Wannan damar komai, yanda Allah yatsara haka zai kasance.
Lallabo shi akayi dakyar zuwa gida malam da sauran y'an uwan su, harma da mutane gari Wanda kowa mutuwar Ahmed din ta girgiza shi, Wanda sai ka mutu ake sanin halayen ka, wasu nacewa dazufa sun gaisa a masallaci, Wanda ita rayuwa haka take yanzu kana nan Anjima baka sai wani kuma, rai bakon duniya, Allah yasa mucika dakyau da imani.......... 🖊








"Kai jama'a bantaba k'isa ba a littafina irin Wannan don haka nikaina na koka na girgiza Wanda nasan watarana saidai labarina nima zantafi, ya Allah Kayi mana kyakkywan karshe kasa mucika dakyau da imani don darajar ma aiki, S. A. W🙏








*Matar Soja*
















🌻🌻AUREN GADO🌻🌻







*Matar soja ce*






Daga marubuciyar
KUSKURE NA,
BARIKI AUREN SOJA,
MUK'ADDARI,
WANAKE AURE,
ZANYI BIYAYYA, Y'AY'AN GATA, And now AUREN GADO,














Ga masu bukatar Wnn littafi ku turo kudin ku ta Asusun banki na 7304736012 nafisa sani hassan Fcmb ko katin wayar ku ta Wannan number 09011251444, sai kuma y'an 🇳🇪 Niger ku tuntubi Wannan number domin biyan naku, +225 0748153903, littafina Dari biyar ne kacal 500 sai najiku nagode,


*my fans masu maganar Ahmed yabar k'wanshi, ai mommy zataji dadi gwara tayi nadama ta har Abada tasan Allah yabata yaro mai yi mata biyayya har bayan idon ta, kuma shine zai zamar mata tabo har karshen Rayuwar ta don haka muje zuwa dama bahaushe yace in kana mugunta bakayi wa kanka ba to baka cika mugu ba*


Last 🆓 page




1⃣9⃣&2⃣0⃣








.............. Naziya kuwa Abin kamar a mafarki haka take ganin shi, koda ta farfado manya suka natsar da ita sunayi mata nasiha, sai Ajiyar zuciya takeyi takasa koda fitarda hawaye, Saida Akace mata har an sallace shi an dangana shi da makwancin shi ne ta fasa kuka, shikenan yanzu bazata kuma ganin shi ba, haka rayuwar su tazama tarihi Auren ta dashi yazama tarihi, Wannan wace irin kaddara ce ta bullo a cikin Rayuwar ta? Istigifari ta farayi domin kar Imanin ta yayi rauni, Amma kowa yasan bakaramin ciwone a zuciyar taba rashin mijin da kukayi Aure wata biyu yatafi yabarka, kowa ya tausaya mata, har kanin Baban su Ahmed din na gidan sunzo, mommy kuka take tana birgima, cikin masifa Aunty Fatima tace "Wallahi bilkisu kukan ki baida Amfani ai saiki tashi kiyi farin ciki, Ahmed yatafi yabar miki duniyar, ba Auren kece raini ba! yau gashi yabar miki matan duka, kiyi Addu'a ma ko jika ace yabar miki jikin Y'ar talakar da bakyaso, kin hana yara sakat ai munsan komai kallon ki mukeyi kawai kijira Abinda zai biyo baya, wallahi sakamako na zuwa. Matar kawu ce uwar gidan tace "Aa Fatima kubarta haka rashin d'a tayi kuma kuzo ana zama kuna tada fitina. "Nayi shiru Matar yaya".
Kuka Momy ta fasa, yanzu take data sani mara Amfani Ina ma Ina ma, Allah yasa Naziya tanada ciki, Allah yasa zata ga Abinda zai cire mata kewar d'an ta mai hakuri, Kuka takeyi mara Amfani domin batada damar maida hannun agogo baya.
Khaleel kuwa zazzabi mai karfi ya rufeshi Saida likita yazo ya kuma dubashi, su Malam na tausar shi tareda mai nasiha mai ratsa zuciya, kabi d'an uwan ka da Addu'a shine kawai soyayyar da zaka nuna mai yanzu.
Gefen Amare Fauziya tafi d'an natsuwa domin mutuwar ta taba zuciyar ta don duk shashancin mutum yau ace Wanda kasani yafadi ya mutu, dole kaji jikin ka yayi sanyi idan akwai Imani a tareda kai.
Gefen Amaryar Ahmed mommyn ta da y'an uwan ta nafama akan ta shirya takaba tace atafau bazata yimai takaba ba tunda ko kwana basuyi ba tare, maganar har taje kunnen mommy, bata iya cewa komai ba domin ta shiga rayuwar kurame na wucin gadi, Naziya kam bazata iya bude baki tace wai mijinta bai kusance taba, domin akwai Alkunya kuma ko saboda soyayyar datake mai tareda hakkin igiyoyin nan uku dake wuyan ta dole tayi mai takaba, in akwai Abinda yafi haka ma zatayi mai domin ita tasan tayi rashi babba Wanda maida irin shi zaiyi wuya, ita ai jitake ma ta rufe shafin Aure a rayuwar ta.
A cikin kwanakin uku zuwa bakwai bamasu sauki bane ga duk makusantan mamacin, tun daga kan mommy, Naziya, Khaleel da duk wasu masoyan Ahmed,
A dakinta take tanayi mai takaba mai tsabta tareda binshi da Addu'oi dare da rana, kuka kuwa kullum dare sai tayishi rayuwar da sukayi dashi batada tsawo Amma yabar mata memories da zasu rika tuno mata dashi har karshen Rayuwar ta.


Seven days


Khaleel Ko part d'in shi bai zuwa tun ranar da fauzy ta shigo ko kallon ta baiyi ba, Abinci ma baya iya ci ya rame a fuskar shi sosai daka kalle shi, Aunty zarah ce ta shiga dakin shi yana zaune rikeda waya karatun Alqur'ani mai girma natashi, idanun shi a rufe, sanye yake cikin jallabiya fara, "Ibrahim" kazo Alhaji na Kira ta fada tareda juyawa, tashi yayi yana sa stop tareda rike gefen jallabiyar shi ya fita, a katon falon ya samesu dukan su har Naziya tana nade cikin hijabin ta, gefe daya Maman Salifa ce da ta Fauziya duk suna hakimce sai kuma Amaren a gefe, Wanda shi tun ranar da aka kawo su bai sasu a idoba, Kawu da malam ne zaune a kujera sai kannin kawun mata biyu gefe, mommy ce tayi shiru kamar ruwa ya cinyeta, kana ganin ta kasan mutuwar ta tabata. Kawun ne yace "Malam Abubakar na taraku ne anan saboda Abubuwa uku na farko dai Ina Kara mika ta'aziya ta gareka Ibrahim domin kai Kayi rashi, Allah ya Kara maka dangana tareda ikon daukar nauyin da aka dora a wuyanka, na biyu akan maganar Matar Ahmed, sun kirani akan zasu tafi da ita gida domin bazata iya yimai takaba ba, don haka ga Malam muji shima idan zai tafi da Ita uwar gidan ne gida. Saurin dago kanshi yayi ya kalli gefen ta, sai yanzu yaga yanda ta rame tareda yin zuru zuru, gwanin tausayi, ya ce Kawu duk yanda kukayi daidai ne. Abinda ya iyacewa kenan,
Addu'a malam yayi kafin yabisu da nasihohi ya karayi musu ta'aziya, ya dora dacewa Idan so samune Naziya ta zauna a dakin ta, Amma a yanzu saboda dalilai masu yawa zan mayarda ita gida tayi takabarta, Allah ya gafartawa Ahmed.
Wani irin daci Khaleel keji a zuciyar shi, yarasa wane irin tunani zaiyi baida kalma daya da zai iya furtawa a halin yanzu,
Kukan mommy ne yasa suka kalle ta, ba Wanda yaji tausayin ta har Khaleel din ma, domin tsawon kwana bakwai din nan baya ko kallon gefen ta.

Toh Hajiya bilkisu Ahmed ya tafi, Amaryar da kika buga kirji kukayi mai yau tace bazata iya zama dashi ba, sannan Inada yakinin mugun halin ki ne yasa itama Matar tashi za a tafi da ita, domin ni Nafi kowa sanin halin ki bazaki taba canzawa ba, da zaki canza da mutuwar yaya na zata fara canzaki, mundade muna daukar mugun halin ki yau kinga ni, Allah yasa ki dauki darasin idan har akwai sauran kwakwal akan ki.


"Ya isheka Modu karka manta d'ana na rasa babban dana duk Wanda yayi kukan mutuwar nan Kara yayi min, sannan maganar bakin hali, naji abarni da kayana duk ko wacce tafi ruwa gudu cikin su, ni Abarni da zafin rashin d'ana kawai, tafada tana mikewa cikin zafi tayi daki tana kuka mara madafa.
Ko dago kai Naziya batayi ba Saida malam yace "su shukrah na nan zasu hada miki kayan ki su taho dake, ni zantafi dalibai na jirana a gida. Ya musu sallama yatafi. Saura y'an uwan kawai da iyayen matan, Maman Fauzy tace toh Saura mu yaza'ayi da yarinya tun da tashigo ace bata samu kwanciyar hankali ba.
Cikin zafi yace "Zaku iya tafiya da ita in kun so I don't need her.
Yafada cikin fada da kuma iyakar gaskiyar shi, "dama momy ta Aurota idan kunga bazaku iya zama ba ga hanya.
Cikin rawar jiki tace " no mommy please kuje ni Ina nan. Tafada domin tana matukar kaunar Khaleel, bayan ta aureshi da kyar ta yaya zatayi sake ta fita, don haka tuni ta kashe bakin uwar, salifa ce taja uwar ta gefe, "mommy nidai kinga kisa kawun su yasa Khaleel ya Aureni tunda anayin Auren gado, kinga yafi ma Ahmed din haduwa mommy wallahi zan zauna in ya Yarda. "Y'ar gari nima tunani na kenan ai kinga yaron ya Tara dukiya kan dukiya gatashi gata uwar shi gata d'an uwan shi yanzu, ke fa uwar shi duk cikin mu tafimu kudi shegiyar, bari mukoma inyi magana.


Jiki na rawa suka koma falon lokacin Naziya ta mike tayi daki inda su Aunty Raliya ke hada mata kayan ta, daga Khaleel sai kawu sai gwaggon nin shi, mommy dasu zarah na daki,
Zama Maman Salifa tayi tana Washe baki "Alhaji Inada magana. Suka zuba mata ido kafin yace "munajin ki. "Yauwa nace ba, tunda dai ga d'an uwan shi mezai hana ayi tunani mai kyau a bashi Salifa sai a hada Auren gado. Wani irin saurin dago kanshi yayi tareda watsa musu kallon kun haukace ya ce "kuna hauka wallahi kun haukace, toh kusani kune sanadin duk Abinda ya faru a rayuwar d'an uwana, koda ace mata sunkare a duniya bazan taba Auren Y'ar kiba, don haka kawu ni natafi Inka gama domin one more minutes a nan zanyi Abinda bashi bane. Yafada yana wucewa a zuciye,
"Toh kunji sai ku tashi kubamu wuri, inji daya daga cikin matan, shigewa dakin mommy sukayi jiki a sanyaye,


Dayar tace "yaya dakasa baki ya Auri Wannan Y'ar mai Hankali, itace Matar Aure ba wa'innan y'an barikin ba. "Zamuyi Wannan maganar ba yanzu ba kubari mu gama war ware rashin da mukayi sannan shima Khaleel baya cikin natsuwar shi yana bukatar natsuwa, company su ma manager din ne ke kulada komai tunda ba Ahmed.
Dakin mommy su zarah ke lallashin ta domin sunsan koma meye ita tafi kowa rashi, har suka samu tayi shiru tana Ajiyar zuciyar, Shigowar kawar tata yasa tace kuna nan Hajiya? Eh kawata ai na canja shawara, nace ai basai na dauketa ba kawai tunda zumunci mukayi niyyar hadawa tun farko ko yanzu bata baci ba tunda kanin shi na nan sai a hadasu Auren gado kawai.
Kallon su tayi kawai domin tasan Waye Khaleel kuma yanzu bata isa ta tunkare shiba sai bayan komai ya natsa, amma Ajiye mata biyu irin Salifa da fauzy Abun Alfaharin tane a matsayin surukai.
Zarah ce tace, "ai yanzu saidai abari komai yanatsa kafin Wannan maganar ta taso, kuma Karku manta yanada wata Matar fauzy kuma kinsan Y'ar waye. "Badamuwa nidai inzai Aure ni zan zauna da ko mata goma ne Salifa tafada, domin itafa kawai tasa rai.
"Oh Allah kasa mu zamo iyaye nagari ga ya'yan mu Amen.




Kwana ki natafiya Naziya yanzu tana gidan su duk kayanta dake gidan ankwashe har wainda bata moraba, tafara warware wa Amma kusan kullum cikin yiwa Ahmed Addu'a take da sadaka idan tasamu hali, har Azumi takeyi litinin da Al hamis domin Allah yakai ladan kabarin shi. Khaleel kuwa haryanzu bai dawo dai dai ba, fauzy tayi binshi har tagaji bai komawa kanta, ko fuskar shi bata gani. Yau yana kwance a katon falon mommy ta shigo ciki ita kanta ta rame, "Ibrahim, wai kai wane irin yaro ne, yazaka sawa yarinya ido tun kawo ta gidan ku bayan kasan akwai hakkin ta akan ka, kai bazakayi koyi da halin d'an uwan ka ba, Ahmed dina ba haka yake ba, idan har kaunar da kakewa d'an uwan ka gaskiya ne Kayi koyi da halin shi.
Dagowa yayi tareda cewa " koyi nakeso inyi da Rayuwar da kika dora shi akai mommy, Ina ganin yadda yayi Rayuwa batareda Matar shiba, kuma kece kika sashi, ke kika hana yaya na ya sauke hakkin da ya dakko har yabar duniya, mommy kina tunanin Allah

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login