Showing 6001 words to 9000 words out of 81703 words

Chapter 3 - 💖 Sakon So ♥️ Book Complete m Shakur ( By Ubeera ) .txt

M Shakur   

28 Dec 2024

2473

Kausar da Abdallah? Yazaci su basu damu kullum suna ganin ubansu haka bane? Nasan yawahala arayuwan nan na………” “Hajiya!” Mustafa yakira Hajiya ahankali dayasa ta kalleshi murmushi yamata yace “in sha Allah zanyi magana dashi yau bari naje” tashi yayi ahankali yay sama sukuma duka yaran har Anty Binta sukazo suka zagaye mahaifiyar tasu kowa yay zugummm kunsan ance yara mata dabanne akwaisu da tausayi da jinkan mahaifiyarsu duk lallashinta suka cigaba da yi kowa na bata baki.






Yana zaune agaban study desk dinshi har lokacin yana sanye da jallabiya ya kunna desktop dinshi ga coffee a mug yana kurba yana aiki akai knocking kofar dakinshi tareda bude kofan gabadaya aka shigo hakan yasa yadaga kanshi dasauri yakalli kofar danko Hajiya bata shigomai daki kai tsaye batare daya bata izinin shigowa ba balle kuma wani na gidan, ganin Mustafa yasa yasaki wani kalan coool smile taredajan kujeran dayake kai baya yamike tsaye yakaraso inda Mustafa ke tsaye gaban kofan yana murmushi yabashi hannu tareda cewa. “Wata sabon gani” murmushi Mustafa yayi yakarbi hannunshi yace “I missed my best best besssst friend my one and only childhood friend, Imrana waikai baka tsufa ne for God sake look at me look at you, jibeni kaman wani yayanka”?Dan murmushi yayi akunyace yace “common don’t start with this your blabbing mushiga ciki wants some coffeee”? Ciki babban dakin suka shiga Mustafa yazauna kan lallausan carpet din dakin dakeda wani kalan shegen taushi kaman gado shikuma Abee yawuce dauko flask na coffee da mug Mystafa nabinshi da kallo yace “jibeka kaman yayan Abdallah ba Babanshi ba” tsiyayamai coffee yayi yabashi batare dayace komiba hakan yasa ya amsa yana kallonshi yakai baki yadan kurba sannan ya ijiye, ahankali Abee yace “Ya Jiddarh how is the course going”? Dan yatsine fuska yayi yace “nima wlh retire zanzo nayi kwanan nan kaman kai, aikin soja barinma na Nigeria is exhausting and energy draining, you know what they say problem no dey finish for naija” murmushi dukansu sukayi atare Abee yakai mug na coffee bakinshi yanasha ahankali shima Mustafa yanasha yana kallonshi 1yr kenan da tafiyanshi Jiddah one year kenan rabon dayasashi a idanu gani yayi Abee yawani kara kyau wlh kaganshi zaka dauka matashi ne dake tsakiyan lokacinshi kawai maturity da yanda yake daukan kanshi ne zaisa kagane Babba ne mutumin nan ya kwan biyu aduniya but other than that yamafi wani lafiyayyen matashin kyan gani da kyawun jiki kaman daga sama yaji saukan tambayan Mustafa akunne shi. “When are you getting married again Imran”? Chak ya tsayar da mug din dayakai bakinshi zai kurbi coffee yakai kusan 2min ahaka ko motsi baiyiba sannan gently yazare mug din ya ijiye ahankali kan tray din kafin yamike tsaye Mustafa nabinshi da kallo yawuce gaban desk dinshi yaja kujera yazauna yacigaba da aikin dayakeyi acikin desktop din batare dayace uppan ba, dan murmushi Mustafa yayi ajiyan zuciya yasauke yakarasa shanye coffee cikin mug dinshi sannan ya ijiye cup din yamike tsaye shima ahankali yakaraso tsakiyan dakin ya tsaya anatse yace “kayi avoiding this question for good 13yrs but this time Imran ko bakaso you must answer me” yay dan shiru yatako zuwa bayan kujeran dayake zaune ahankali ya tsaya taredakai hannayenshi yadafa kafadanshi yace “duk wanda yashigo cikin gidanku abu nafarko dazai gani shine one bigggg happy family, ga Hajiya da yaranta dakuma jikokinta sun cika gidan leaving happily kansu ahade but trust me that still person dayayi tunani u people are happy family will take him just a day to realize you guys are not happy, dan behind that happiness is one huge big sorrow dayay surrounding zuciyan kowa all because of you Imran, kowa is not happy, your family supported you throughout the difficult time dakai going through arayuwanka, everything, kullum suna cikin battling da PTSD dinka, burinsu yanzu daya ne kasami mata kai aure ka natsu yaranka su sami uwa eh Imran” dan lumshe idanu Abee yayi sannan ahankali yabudesu tareda juyowa hada idanu yayi da Mustafa dake kallonshi kaman yaune yafar ganinshi, wani abune yaji ya tsayamai azuciya hakan yasa yasake lumshe idanu kawai yay shiru ahankali Mustafa ya tsugunna agabanshi tareda kamo hannayenshi yarike hakan yasa yabude idanunshi ahankali, ahankali Mustafa yace “talk to me I am your friend, I am here for you, talk Imran” kadawa idanunshi sukayi sukai jaaaa kaman bashiba ahankali muryanshi harta dishashe yace “I don’t wanna get married again! I don’t want tooo” yay shiru tareda sake lumshe idanunshi dan murmushi kadan Mustafa yayi ahankali yace “bakason kasake wani aure because you feel you are betraying Muna (Maimuna)”? Murya chan kasa yace “kowa knows how deeply you love Muna Imran, soyayya kukai kaida muna soyayyan da tun kuna yara tun bakusan ciwon kanku ba, soyayya ce dakuka farata tun baby class, primary school har secondary school, kaida Muna are just like Zara da wata, duk inda aka ganka anga Muna akaga Muna anganka, I remember lokacin nan kuna kare secondary school aka muku aure sabida kun ishi mutane da soyaya” Mustafa yayi murmushi ahankali murya chan kasa yace “is not easy to loose the love of one’s life along with 2 of your beautiful children Abdulhamid da Asiya, I know you are suffering I know your heart is shattered but trust me Imran this is not what Muna wants for you kana wannan miserable life din rayuwan kadaici kullum daga office sai masallaci sai gidan Hajiya for the past 13yrs kana tunanin Muna and your two marigayun yara wants that?” Wani kalan gaggauran ijiyan zuciya yasauke har lokacin idanunshi a lumshe dazaka iya dauka ko bacci yakeyi, ahankali Mustafa ya matse hannunshi yace “13yrs kenan da aka kashe maka mata da yaranka biyu tun kana shekaru 36yrs yanzu you are 49 Imran me kake nufi you will not move on ahaka zaka karasa rayuwanka kana zaman kadaici kullum mahaifiyar ka your old mother cikin kuka take kullum kanninka su Binta cikin kunci suke yaranka ma haka all because of you shin kamusu adalci kama dattijuyar 70yrs old Mom naka adalci da at this stage babu abinda take bukata banda farin ciki, kama Muna adalci datake sonka sama da rayuwanta eh Imran”? Wani kalan ijiyan zuciya mai zafi ya fuzar sannan yabude idanunshi ahankali yakalli Mustafa murya chan kasa yace “kowa zan aura Musty kasan cutar da ita kawai zanyi, my heart my soul my whole body and everything belongs to only one woman which is Muna, bazan taba iyason kowace mace ba kuma arayuwana, I cannot love again, kota Auren gangan jikina kawai aka aura, I can’t love again, bazan taba samun wata kaman My Muna ba” murya chan kasa Mustafa yace “kai Allah ne? Kasan gaibu ne? Did you know what tommorow holds for you don’t say that Allahn daya baka Muna can give you wacce tafi Muna” ajiyan zuciya yasake saukewa murya chan kasa still Mustafa na kallonshi yace “how are you even surviving Imran all this years? Tayaya kakai har war hakama bakai aure ba? Imranan dana sani dakenan duk shakara Muna ke haihuwa, I remember lokacin damuke trainning na sojoji a chan jaji kusan duk bayan 2days kake sabewa tabayan katanga kadawo gida just to come and ease yourself da iyalanka eh? I know you best friend naji bazaka tabaso wata ba but you are punishing kanka, grieving Mamaci daban sannan halittun da Allah yamana ajikinmu daban, yudaya baya hana daya grief Muna as much as you want but you are suffering, for the past 13yrs rabonka da wata mace idanba kanason kai loosing sanity naka loose focus bane kanemi mata kai aure” fuzar da iska yayi ahankali yace “I am sorry Musty but bazan taba iya neman wataba, and the suffering I am suffering lemme suffer it I deserve it, bayan aurenmu danake cema Muna I want to become a soja bataso she stop me but nakiji sabida it has been my childhood dream nazama soja, Muna was always scared idan aka turamu for assignment kada akashe mata ni not knowing bani Zaa kashemata ba itane za’a kashemin, had it been I listen to her I went for another course instead of becoming a soja da yanzu My Muna na raye, so lemme suffer I deserve it I have been selfish and stubborn and a bad husband to her” baki Mustafa yabude zaiyi magana Abee ya nunamai kofa da hannu kai tsaye yace “leave me alone Musty leave my room” kallonshi Musty yayi idanunshi sunyi jajir yasan idan ya tsaya zai iya sawa yanzun nan ya birkice kuma yau ya birkice babu wanda zai runtse agidan nan ga Dr shi baya Nigeria yayi dan tafiya hakan yasa ahankali yadaga hannunshi yace “okay I rest my case best friend saida safe” yajuya yay kofa yabude Anty Binta yagani gaban dakin idanunta sunyi jaaa maida kofan yayi yarufe kaman jira take kawai tafada jikinshi ta kankameshi tana kuka ahankali janta yayi saida sukai wajen bene sannan ta tsayarda kukan tareda dago fuskanta tashare idanunta ahankali tace “please kada kagayama Hajiya yanda kukayi wlh zuciyanta zai iya bugawa” Gyadamata kai yayi tareda murmushi yace “I know wife muje” sauka sukayi zuwa dakin Hakiya dake nan akasa a falo dan bata iyawa da benen nan tana ganin Musty cikeda murna tace “yakukayi dashi Mustafa ya aminci zaiyi Auren”? Dan murmushi Musty yayi yace “eh Hajiya amman yace adan bashi lokaci ya kammala project dindayakeyi a company shi” dan murmushi Hajiya tayi one thing is dudda tsufanta babu wanda yakaita sanin halayen yaranta kawai tasan bahaka sukai dashiba ne amma she knows what to do.
EPISODE 4️⃣






Sister Nace ba 100k din nan dakike ajiya, na siyan GOLD Dinnan…? Yawwa Ashe Kingane, nacikin akwatin NAN…… yawwaaaa Su😂


Nasamo miki wani hanya da zaki anfana dashi, kiyi kudi, kiyawata kasashe daban ban afadin duniyan nan, ke infact harma kisiyi gwala-gwalai dashi harsai kingaji… kinsan bana kawoo muku abun banxa. Sai wanda zaki anfana saboda inasan fans dina suma su dan-dana soft life dinnan fa😂😘


Haba Zainab kinkwantar da hankalinki, xan fada mana😂 saurin mea kikeyi🌝


To ita wannan sannan danajea ngama bincike akai sunan shi AFFILIATE MARKETING…. Dayawanku kunsan Affiliate marketing, musammam Art student..


But duk dahaka Bari inyi masu ooni bayani🌝


Affiliate Marketing sanaa ce da mutun zai siyarda kayan wani sannan abiyashi ribar tasa (hold on nasan xakice ai wannan kaman siyarda abayane abiyaka, nidai gaskia bazn iyaba😐) ki kwantar da hankalinki oo, ya kina mun haka🥹 ba kalan wannan sanaar bace fa, wannan yamafi shi dadi sannan ga sauki. Shide wannan Digital Products e xaki na siyarwa instead of physical, wannan yana nufin bama sai anga fuskarki ba kokuma kinfita daga dakin ki, akan gadanki ma sai kiyi abunki Kuma abiyaki, Yaya yakea.?? Am getting to it😂 wannan platform ne daxakiyi registration dasu, kice musu Kinasan kifara siyarmusu da kaya (Digital Product). Nasan anan ma xakice to idan nayi registration dasu taya xan nemo masu siyan kayan.?? Karki damu After Kinyi Registration su xasu nuna miki tayanda xakina samo mutanea harsu dinka siya.


Sannan duka sati ake payout which means Duk iya siyarwan dakikayi ranan Asabar nazuwa zasu bki kudinki. Idan misali kindau kayan 50k kina siyarwa, kinga 25k nakine. Mudauka asatin kinsiyarma da 20 people, kinga Asati kinada 250k🤯 Awata Kuma 1miliyan nea dake🥵 (Not bad ma sanaan daxaki fara da kudi kalilan)


The best part is ribarki idan kinsiyarda guda daya 50% ne maana rabin kudin nakine, sannan akwai inda zaki kai suna sponsoring dinki xuwa kasashen wajea ko kuma suna baki mota iya adadin kayanda kika siyar.


Registration dasu beada wani tsada ..
Anoda best part of it shinea from January to April idan kika siyar da kaya guda 300 zasu baki dan kareriyar waya ( 14 pro max). Idan kikayi 400 sales zasu biya miki kijea Maldives (wata kasace) idan kuma kikayi 600 sales zasu baki Sabuwar Mota Corolla.


Idan kinasan karin bayani ga number nan xan ajea kiyi mata magana. 09133427208 instagram handle @western_hemisphere_ https://bit.ly/3XleqfK




4:30 yabude kofar dakinshi yafito sai zuba uban kamshi yake kana ganin kasan yay wanka dan yasaka wata milk jallabiya gogaggiya mai bala’in laushi yasaka hula fara kwankwasa kaji hadisi, dakin Hamza yafara shiga yatadashi sannan yashiga dakin Abdallah yatadashi yace yay maza yay alwala kafin yagama tada mutanen gidan, fita yayi yawuce dakin Kausar, ahankali yabude kofan da sallama yashiga yakai hannu yakunna wutar dakin tana kwance kan gado ta kudundune cikin bargo tana shargan bacci karasawa gaban gadon yayi ya bubbuga mata katifa ahankali yace “Kausar” bude idanunta tayi cikin muryan bacci tace “Abeeee” hannunshi yamika mata yace “get up and pray” gently tasa hannunta takama nashi hakan yasa yadagota ahankali ta tashi zaune sannan takarasa yaye bargon tamike tsaye tawuce bayi, fita yayi ya tsaya gaban dakin da Maman Aneesarh ke ciki yay knocking yace “Rahama” cikin muryan bacci tace “natashi Ya Imran” knocking dakin da Anty Binta tasauka yayi itama tace ta tashi sannan yasauka kasa direct dakin Hajiya yayi tunda ya hango wuta dakin yasan ta tashi amman dudda haka sallama yayi yabude yashiga zaune take kan lallausan dadduma da charbi ahannunta hannu tadagamai alamun addu’a take mikewa yayi yafita daidai Hamza da Abdallah sun sauko kasa suka wuce masallaci.




Hamza da Abdallah sun rigashi dawowa daga masallaci danshi dama yana tsayawa yay azkar sannan yagaisa da mutan unguwa idan ana bukatan wani abu a masallacin ya saya, wajajen 7 yashigo gidan da sallaman shi chan ciki, gabaki dayan yaran gidan na falo dukansu an musu wanka looking neat dukansu sun saka kayan makaranta little Aneesarh ne kawai bata fara school ba, kuma duka yaran dsame school suke duk sun zauna suna jiran breakfsat dan iyayensu na kitchen, zama yayi akan kujera one sitter wanda wajen kusan shine wajen zamanshi na ka’ida duka yaran tahowa wajenshi sukayi sannan suka duka atare sukace “Assalamu Alaykum Abee good morning” dan murmushi ya sakan musu yace “wa’alaykumus salam children morning” daidai nan Abdallah shima yashiga saukowa kana ganinshi kasan yay wanka yasa kananun kaya masu kyau da sneakers akafanshi dawata jaka na LV abayanshi sai key mota kaganshi sak ubanshi yana zuwa gaban Abee yace “good morning Abee” “morning Abdallah what time kakeda lectures yau” yana gyara agogon hannunshi yace “Abee by 8 ne yanzu 7 harda minti goma bari nai sauri idan lecturer ya shiga baya kara bari wani yashiga” yay maganan yana mikewa zai wuce Abee yace “go and have breakfast kafin kafita” strictly Abee yay maganan daidai nan Hajiya tafito tace “Alhamdulillah ai yau uban naka nagida naga ta yanda zaka tafi makaranta bakai kari ba yaro kwata kwata bayason cin abinci” turo baki yama Hajiya yajuya yawuce dinning danyi kari Abee yadauke idanunshi daga kanshi yajuya yakalli Hajiya data zauna kan 2 sitter dake facing nashi ahankali yace “ina kwana Hajiya” “mun tashi lpy Imran” ahankali yace “Alhamdulillah Hajiya” yadanyi shiru sai chan yakalleta yace “me kuke bukata agidan”? Anatse Hajiya tace “fruits ne kawai babu amman akwai kayan abinci da komi lastweek ai kasa Hamza yayo chefene” gyadamata kai yayi yace “magungunan kifa”? Tana kallonshi tace “basu kareba har yanzu” daidai nan su Anty Binta suka fito daga kitchen zasu fara jera abinci a dinning Hajiya tace “ku kawo nan muci anan dan Allah ni wlh bason cin abinci wajen nan nakeba” kawo abincin sukayi duk suka gaida yayan nasu Sajida yafara kallo batare daya amsa gaisuwanta ba yace “when are you going back to your husband house”? Murmushi tayi tace “Yaya dazaran yadawo daga lagos zaizo yadaukeni next week yace zaizo ni wlh banma gaj…..” mugun kallon daya mata yasa tahadiye maganan yakalli Zainab kafinma yayi magana da sauri tace “Yaya Imran ni sai ranan Friday kaga yau monday” dan dariya Hajiya tayi tace “yara duk sun zo sun taremini gida sun hanani sakat” turo baki Zainab tayi tace “bamason rabuwa dake Hajiya” dasauri Hajiya tace “aure kam yagaji haka ingayamuku” daidai nan Anty Binta takalli Abee tace “mezan zuba maka akwai waina da pepper soup na cowtail, saikuma chips da egg, akwai kuma dumamen tuwo da kuka sai shayi da kunun gyada” ahankali yace “I want masa da shayi” murmushi tayi tashiga zubamai daidai nan Hamza ya sauko ya shirya cikin suit yayi kyau Hajiya dake kallonshi tace “kai lpy kaci suit yau”? Murmushi yayi yakalli Ya Imran da ake bama abinci yace “yau zamuyi baki a office za’a kawo wasu yan makaranta excursion suga company namu idan Ya Imran yayi welcoming nasu nine let’s just say tourist dinsu to kinga I need to look good” tabe baki Maman Aneesarh tayi yadaga mata gira daya Hajiya ta kalli Abee daya fara kurban shayi ahankali anatse tace “zakuyi baki shine kai me kampani gabaki daya ko shiryawa bakayiba” ahankali yazare kofin shayin daga bakinshi yace “idan nagama zan shirya” zama Hamza yayi yakarbi abincin da Anty Binta ke bashi yace “wlh yaran nan naku suyi sauri inba hakaba babu makarantan dazan kaisu saidai ku ku kaisu” Hajiya ta dubi Anty Binta dake bama yara abincin tace “wai ina jikata Kausara ne jama’an gida”? Dan dariya daga Binta, Sajida, Zainab da Maman Aneesarh sukayi, Maman Aneesarh tace “Hajiya kin manta shiryawan Kausar ne” Zainab tace “manyan yammata yan 100 level JJC saida gayu” daidai nan Abdallah yatashi daga dinning yace “nina tafi” atare kowa na dakin yace “Allah kiyaye hanya, Allah bada sa’a Doctor” karasowa wajen Abee dahar lokacin shayi yakesha baima taba wainar da aka zubamai ba yace “Abee natafi” hannu Abee yasa a aljihu 10k yaciro yabashi dasauri yakarba yana murmushi yace “thank you Abee” ahankali yace “drive safe” murmushi yayi yace “I promise Abee” yajuya dasauri yawuce daidai nan Kausar ta sauko tana sanye da doguwan rigan atampa mai kyau tasaka bakin safa akafanta da flat shoe sannan tarike milk hijabinta ahannu, da dankwalinta a hannu, da jaka da ribbon a hannu tana shigowa ajiyesu tayi akan kujera tazo wajen Abee da sauri tabashi ribbon din tace “Abee kamamini gashin” baki Hajiya tasake tace “yanzu kiwuce duka matan dake dakin nan kitafi wajen ubanki yamiki parking gashi dakecin abinci” turo baki tayi tawuce tabama Zainab tace “samin Anty” murmushi tayi takama gashin da baida wani tsawo tace “kawo kallabin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login