Showing 15001 words to 18000 words out of 198792 words

Chapter 6 - ZEE-BABY-1-AND-2 COMPLETE HAUSA NOVEL By hausanovels001.txt

27 Nov 2024

5765

da zan rufa narasa ya zanyi ganin wayarsa yake kawai na matsa jikinsa na kwantar da kaina kirjinsa na zagaya hannuwana ta bayansa na rumgumesa gam na cusa kaina kirjinsa ina sabke ajiyar zuciya har tsawon minti uku sosai naji dadin hakan sanyi ya fara raguwa hannuna na dora saman wuyansa ina shafawa ashgwab'e na kirasa"Dr Sardauna ko gezau baiba yaci gaba da wayarsa yana driving d'insa duk da ta matseshi sosai ya bar tane saboda zafin da yaji ajikinta saida ya gama wayarsa ya ajiye wayar ya gangara yai parking can k'asa k'asa cikin daddar muryasa dan shi bai fiye taratsiba yace" wlh nidai an hadani da jaraba Dan ubanki ni sa'an kine meye zaki bani kike, kiran sunana bakin yaune kikeda damar hakan gobe ko ance ki nufi inda nake wlh bazaki zo dan ni bana yinki sam ya fadi yana janyeta jikinsa niko dama raguwace wajan zazzabi banida hakuri kuka na saka masa na Kara shigewa jikinsa" Dan Allah mai Suna Abbu kayi hakuri sanyi nakeji na fada ina karkarwa tsaki yaja ya tabe baki inda yake ajiye magani ya duba cikin sa'a ya samu ya dauka ya ballo biyu ya dago kanta ya bata ya bude gora ruwa ya kafa mata abaki Tasha kallon maganin takeyi kamar tace ya kara mata dan yau daya da bata taunaba batajin dadi rikeshi nayi gam ina goga fuskata saman wuyansa ina hucin zazzabi Dan nasaba alallabani kamar yada ummi takemun gashi ajirgi ma Ahukhuya ya lallabani k'asa nayi da murya, " mai sunan Abbu ka lallabani idan banida lfy lallabani akeyi na fada, ina had'e face d'inmu ina hawaye bakin cikin yama Dr Sardauna yawa bugemun baki yayi ya ingijeni " ke Dan ubankin tashi ki koma bayan mota ki kwanta yar iska jarababiya rashin tarbiyar zaki Nuna akasar Hausa jarababiya kawai zakici uwarki jikina ba na banzaye mata bane irinki naji zafin maganar sosai amma babu yada na iya saboda

ina bukatar gumi wlh har suma nakeyi idan haka ta faru banyi zuciyaba nasake dawowa jikinsa na rikesa gam ashagwab'e nace" Dr Sardauna kayi hakuri ceton raine zakayi wlh Nima idan ba doleba babu abin da zan da wannan lusarin jikin naka mai sufar mata niko na fadane Dan na bata masa azahirima bantaba ganin cikeken namiji mai cikar halita irinsaba wani Bacin raine yazo masa baisan lokacin da ya sharara mata mariba ya harbata ya matan da wata Amana janyeta ya wurgata baya " ni zan nunamiki ni Dr Sardauna bana cikin lusaran maza sai nasaki kinfadi haka da bakinki idan hakan bata faruba kice ni ba dan halak bane yau kinci darajar mahaifina amma kijirani wlh sai kinyi nadamar fadin hakan kuma daga yau bake bani idan kika sake shiga sabgata wlh zakiyi nadamar zuwanki duniya yar iska mashayiya ya fada yanama motar key ya fizgeta da karfi yana sharara gudu ransa abace yana kisama irin azabar da zai mata wacce itace ta karshe tabbas yasan daga ita bazata sake fatan shiga rayuwarsa ba Dan ya tsani yarinyar bata da tarbiya bata cikin irin mutanan da yake hulda dasu jiyake kamar ya tatara ya koma gidansa,Wanda bayada niyar hakan sai bayan yayi aure,

Naji ciwon maganganu da ya fadamun amma naji dadin yada yaji ciwon lusarin da nace masa murmushi nayi nima ina tsara yada zan Rama abun da yamun da karfi nace " Dr Sardauna na tsaneka bakada kirki yada ya karawa motar gudune yasa nayi mugun tsorata naja bakina nayi shiru Dan fah duk abinda nake masa wlh inajin tsoransa kwanciya nayi na rufe idanuna narasa mekemun dadi duniyar ma naji ta isheni amma da na tuna sati dayane zanyi sai naji farin ciki driving yake ransa abace sigari ya kunna yanasha cikin nutsuwa tunda na farajin kaurinta na kife kaina na toshe hancina ban yada yagane banason warin ba, haka dai har muka shigo garin Katsina abinda yasa ko na gane waya naji yanayi akofar wani makeken get muka tsaya yayi honr mai gadi ya bude masa ya danno hancin motar cikin gidan masha Allah duk suna tsatsaye harabar gidan parking space ya shigar da motar yai parking Mahabeer yanufo gunsu fitowa yayi gani iyayan NASA yasa ya bude mata motar ya bata hannu kin kamawa tayi ta murguda baki ta fito ai tana hango Mahabeer ta nufi gunsa tana dariya shima dariyar yakeyi ya ware mata hannayansa ta fada kirjinsa tana farin ciki Dr Sardauna ko kallo basu isheshiba ya wucesu Khalisat da ke tsaye kusan ghaisha ganin Sardauna ya nufo gun ta zuba masa idanu ta dan kallesa ta lumshe idanunta tana sabke ajiyar zuciya, gunsu Daddy ya nufa zee baby ko sai tabara takewa Mahabeer ashagwabe tace" Ahukhuya nayi missing dinka wancan mugun yayi ta dukana azaba iri iri ran Mahabeer yayi mugun baci ya kamo fuskarta yana shafawa idanunta masu mutikar haske ta zuba masa tana wani marerecewa " my zeena kiyi hakuri karki sake shiga sabgarsa kinji Rabin raina? " insha Allah my Ahukhuya na? dariya sukayi atare Daddy yace" Mahabeer kawota mana taga dangi mai ran karfe yace barni da ja'irin yaroAunty hauwa sai farin cikin takeyi jitake kamar Faisal dinne, gun jama'ar suka Iso kowa kallonta yakeyi saboda tsabar kyawunta da kuma tsantsar kamar da sukeyi da Dr Sardauna kan Daddah tayi da gudu itako toni ta fara kuka ta tuno da danta Faisal rungume juna sukayi Najib dariya yake harda rike cikin Dr Sardauna ko tunda sukazo ya gaidasu dama shi ba sabgar mutane yafi shiga ba to wannan abunda zee baby tamasa yau yasa yaji yanason kara nesa da kowa shigewarsa, part d'insu yayi itako zee baby dariya takeyi tana buga bayan Daddah har tayi shiru ta saketa ta nufi gun Daddy ta rumgumeshi ta saki kuka tun karfi agigice yace momy waya tabaki cikin shashekar kuka tace" Ammin wlh ku kirasa ku tambayesa kuji azabar da yamun yau kasheni ne baiba wai ni annoba ce cikin dangi baya ko jin nauyin sunan da nake dashi gaba daya jama'ar suka dauki salalami " aikuwa Dr bai kyautaba bakonka Annabinka ne gaskiya amasa magana ran Daddy amutikar bace ya rika waigawa inda zaiga Dr Sardauna babu alamarsa parlon suka nufa baki dayansu kafa yaran suka gudu gudun kar aturasu kiransa ya sabke akansu Mahabeer ya nufi part d'insu gun Sardauna ransa amutikar abace.....



🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀🤸🏻‍♀kuci GABA dabin yar mutan Niger domin kuji yada labarin zai tafi cikin wani yanayoyi da dama na rayuwar duniya Wanda Azahirima na faru

*ZEE BABY*



*DAN ALLAH KARKU FITARMUN DA BOOK WAJE*


*👉🏻7*


....kofar d'akin Dr Sardauna ya murda ya shiga da sallama ya fito daga wanka kenan daure da towel yana goge jikinsa ya amsa sallamar Mahabeer ya iso kusansa" Faisal meyasa baka tausayin Zainab yarinya cefa saida lallaba ba dukaba wlh bata da lfy tunda muka baro Saudia zazzabi take da amai amma kamata duka ko yaya take fah yar uwarka ce jinin kace bakada maraba da ita gata marainiya tunda Mahabeer ya fara magana Dr Sardauna bai kallesa ba murdaddan jikinsa ya shiga gogewa ya bude wardrobe ya ciro jallabiya fara sai kamshi take zubawa tamkar yanzu ya fesa mata turare ya saka jikinsa yaje gaban dressing mirror ya taje gashinsa Wanda yake kwance luf tamkar ka kitsa Dan Tara gashi yake tamkar yada indaiwa sukeyi ya dauki turaransa mai masifar kamshi da tsada ya fesa wlh zakace balarabene sak bai shafa mai ba" Faisal dakai fah nake magana? duk da yaji zafin abin da Mahabeer yamasa ga Wanda zee ta masa, ya juyo fuskarta dauke da murmushi " sorry my brother bazan karaba

ni nafita ma harakarta sai kayi kokarin hanata karta kuskura tashiga sabgata,nima ok? " insha Allah bata shiga ba amma ai kiné take tsoro ya zakace bazaka tsawatar mataba? baice komaiba ya dauki dadduma ya shimfida ya tayar da sallah la'asar har ya gama Mahabeer Na tsaye dan ya fahimci Sardauna yaji haushin abunda yamasa yana gamawa ya Mike wayarsa ta dauki ringing suna Daddy ya gani ya dauka yai picking ya kara akunnesa yana kallon Mahabeer ya daga masa gira " hello Daddy" dan uwaka zo yanzu ina parlo kitt ya kashe wayar " my brother karana takai muku ko? Hannusa Mahabeer ya kama suka fito suka nufi part d'insu Daddy da sallama suka shigo parlon zee baby na jikin Daddy tana matsar kwalla kusan Daddy ya zauna " Daddy gani? " meyasa da nace karka tabamun momy ka doketa momy wani irin duka ya miki? " Ammin wlh bankaremun hannuwa yayi ya daureni a karfan gadon hospital ya rika harbani wai sai yaga bayana wai ni annoba ce ya makoremun wuya saida na suma baci ba sha haka ya barni har likintan abonkinsa saida yamun kuka saboda tausayi tunda ta fara magana Dr Sardauna bai dagoba ya kalleta har takai karshen maganar tana kuka kowa ya tausaya mata Daddy ya dagata " ke Hafeeza maza kuje tayi wanka ta canza kaya tayi sallah tazo tafadi abun da takeson ci ko wani irine yanzu za'a nemoshi momy kuje kiyi wanka nine zan rama miki karki damu dariya tayi cikin farin ciki tabi Hafeeza suka nufi bedroom d'insu cikin fada Daddy ya fara magana" Faisal nine zaka rainawa hankali ka daureta kana bugo saboda zalumci yarinyar da uwarta tabaka Amana k'asakantar da kansa yai "Daddy ayi hakuri bazan sakeba nafita harakarta insha Allah idan tayi ba daidaiba ga Mahabeer

zai tsawatar mata jikin Daddy yayi sanyi marin da yayi niyar masa ya fasa dan yasan Sardauna yanada ladabi " to naji ka kiyaye ba ruwanka da ita Mahabeer yace "Daddy tafi tsoransa ai Dole sai ana dan tsawatar mata mai ran karfe yace wannan haka yake Daddah tace" ko zata zauna part dinmu? Hauwa tace" da dai ta zauna gun yan matan ghaisha tace" hakan zaifi Aunty amarya tace" gaskiya abarmana kuma fah inaga Dole Faisal ne zai tsawatar mata Mahabeer naga bayason laifinta Daddah dariya sukayi Dr Sardauna tafiyarsa yayi dan maganarsu ko ajikinsa dan yayi Alkawalin baya shiga harakarta mutikar bata shiga tashiba Abu daya zaigani ya horata shaye shaye, suna shiga bedroom khalisat ce ta hada mata ruwan wanka taje tayi wanka tajima sosai kafin ta fito dauré da towel ta goge jikinta tas Hafeeza ta dauko mata Riga da siket na atamfa har taso tayi musu ganin karamin dinkine kuma tanada son kayan atamfa ta amsa, ta saka tayi masifar kyau atamfar ja ce anmata adon fari dinkin Riga da siket mai karmin hannu yayi mata kyau cuf ya mata da yake Hafeeza batada jiki itama amma saide kowa da irin dirinsa hafeeza ta kalleta" sister kinyi kyau sosai? " shukran bani dadduma nayi sallah shimfida mata tayi tasaka hijab ta tayar da sallah, suna zaune har ta gama ta kalli khalisat " meye sunanki? " khalisat yar uwata Hafeeza" ita na sani kece ban saniba ai ke babbace kin grimemu sosai mekike jira bakiyi aureba? kunya ta kama khalisat har hafeeza ma

mik'ewa hafeeza tayi " sister muje parlo fuska ta yamutsa " ni kwanciya zanyi ina shantocina ne ko suna gun Ahukhuya? " gasunan ajere waiwayawa tayi murna ta kamata taje ta bubude komai da ta dauko sunan har kwayoyinta da sirot dinta na kwalba gudun kar su gani yasa bata fidoba duk da tana matse karamar jakarta ce bata ganiba wayarta na ciki " my khalisat muje parlo muyi hira ko ta fadi tana kallon hafeeza tare suka fito parlon ba kowa duk sun kama gabansu sai ghaisha kade tana waya khalisat taje jikinta ta kwanta zee baby ta tureta" gani yarinya ke katuwa dake ai nima ummi tace dariya hafeeza tayi khalisat tayi murmushi " my zee zo ki kwanta to ta Mike ta matsa mata tako zauna ta dora kanta cinyar ghaisha tana waya gashin zee ta shiga shafawa zee tana murmushi ummina dawa kukeyin waya nima inaso akiramun ummina dariya su khalisat sukayi yada zee take shagwaba saida ta gama wayar ta kira lumber ummi Raiyan bugo daya ta daga da sallama suka gaisa da ghaisha taba zee baby " hello ummina wallahi nayi kewarki sosai? " Zainaba nima nayi kewarki dan Allah ki zauna lafiya da kowa kinji yarinyata? tafada tana goge kwalla" ummina insha Allah ai satine kadai zanyi na dawo gareki murmushi Raiyan tayi " ina Mahabeer dazu ya kirani mun gaisa har Dr ma baki na tabe " suna lafiya ummi sun jima sosai suna hira kafin suyi sallama taba gaisha wayar" ummi ina Ahukhuya? ya fita zai dawo kinji kai ta daga sukaci gaba da hirasu

Dr Sardauna bayan ya fita part d'insu ya koma ya canza shiri cikin kananun kaya wanda sukayi masifar kyau ya fito ya nufi gidansu Ahmed dan ya isheshi da kira yazo yamasa Allura zazzabi ke damunsa yana zuwa yayi parking akofar gida ya tura get ya shiga gidan har parlon su Ami ya shiga da sallama tana zaune" Dr ne ince mutumin ya takuraka ko? " ami babu komai dama da kullum sai nazo indai ba aiki yana ciki ko" yana part dinsa mik'ewa yayi ya mata sallama ya nufi bangaran Ahmed yana parlo sai nishi yakeyi " dallah can ragon namiji kawai tashi mutafi asibiti zama yayi kusansa ya dafa jikinsa zafi radau " Dr Wlh inajin jiki fah " tashi muje dai mik'ewa yai dama jallabiya ce jikinsa suka fito rikeshi yayi suka fita har kofar gida suka shiga mota sa hospital din Dr Sardauna suna zuwa yashiga masa gwaje gwaje ya saka masa drip da ya sha magani ganin magarib ta gabato ya shiga toilet ya dauro Alwalla ya fito " namijin duniya na tafi masallaci kai ya daga masa yana mamakin tsokanar da Sardauna yake masa yau ba shegen miskilancin sa, tunda ya tafi bai dawoba saida akayi sallahr isha'i ya dawo har lokacin drip din bata kareba ya zauna ya kira mashakurah suna hira su ta soyayya sai shagwaba take zuba masa yana lallabata" sweet baby wlh inaso na ganki amma agajiye nake yanzu ina komawa gida sai bacci " karka damu Dr nima inason ganinka amma nafi bukatar ka huta na ajiye shagwabar " ok thanks sweet bye ya tsinke Kiran Ahmed ya zuba masa idanu" ni fah Dr naga kamar son da kukewa juna yayi yawa ku ragema yan baya mana banza yamasa ya Mike ya karawa, drip d'in gudu minti biyar ta gama yacire masa, " malam ina magana fah? " banda lokacin ka " to naji wai naga da araga mana maguguna ya hada masa" Oya mutafi

tunda kaji sauki Dole ka rainamun wayo fitowa sukayi Dr Sardauna sai gaishesa ake yana amsawa sama sama Dan bacci yakeji ga baisha sigari ba tunda ya dawo daga kano, ko amota iskacin Ahmed yayi tama Sardauna amma bai ko kallesaba bare yasamu arzikin magana har suka iso kofar gidansu Ahmed ya fito " Dr namu sai gobe idan na gama wartsakewa zanzo nama kanwarmu sanu da zuwa baimasa maganaba yaja motarsa ya tafi Dan lokaci yaja karfe kusan tara gudu yayi sosai yana zuwa yayi honr aka bude masa get ya shige parking space ya shiga ya faka yana fitowa part d'insu ghaisha ya shiga da sallama ya shigo parlon duk su hallara Ana hira zee baby na kusan Mahabeer zaune sai sangarta take zuba masa dannkwayoyin da taje yanzu taciyo aboe sun fara mata aiki shiko sa lallabata yakeyi su Daddy namusu dariya kusan Daddy ya zauna ya gaishesu " Dr Ashe baka gidan" wlh Daddy Ahmed ne ba lafiya muna hospital amma yanzu da sauki tunda taji shine danma karta kallesa ta boye kanta jikin Mahabeer dhiko baisan Allah yayi ruwantaba ghaisha tace" ayya Allah bashi lafiya Ashe shiyasa yau bai lekoba tashi kaci abunci tunda ya shigo khalisat ta zuba masa

idanu tana kallonsa amma ba Wanda ya lora da hakan dagowar da zaiyi karaf ya kamata tana kallonsa wata uwar harara ya zabga mata " ke ni sa'ankine ko salon raini ku tsare babba da idanu ya fada yana wucewa hafeeza dariyarta ta boye Nawwara ta bishi gun cin abuncin khalisat taji kunya duk da ba Wanda ya kawo aka da itace sai aunty amarya wani mugun kallo ta watsa mata tashi tayi sum sum tabar gun Daddy basu luraba don hira suke da ghaisha akan zee baby itako zee saboda daukar magana dan ta kuntatawa Dr yaki cin abuncin ya kwana da yunwa ta kalli Mahabeer " Ahukhuya yunwa nakeji muje kabani abunci mik'ewa yayi ya kama hannuta suka nufo kan dining din Daddy yaji dadin yada Mahabeer ke kula da zee wani tunani ya darsu azuciyarsa tunda dama sunyi sunyi dashi ya fito da mata kullum sai yace abashi lokaci Dr yana cikin hadawa kansa abunci suka iso yaja mata kujera ta zauna shima ya zauna " Dr ya jikin Ahmed? " Alhmdllh bro bai sake magana ba sanin ba lalle ya sake kulashiba yasa yaja bakinsa gum ya hadawa zee baby abuncin ashagwab'e tace" Ahukhuya bani abaki Dole ya bata abaki haushi ya cikata ganin Dr yaki ko kallonsa yanacin abuncinsa anutse shida Nawwara tana masa surutu kai kadai yake daga mata zee bakin cikin abuncin da yakeci take so take ya kwana da yunwa tarasa me zata masa gashidai atsorace take da yanayinsa tunda taga Mahabeer dinma shayinsa yakeyi burinta ya kwana da yunwa mik'ewa tayi dan ta fara jin juwa Mahabeer ya kalleta " ina kuma zaki kinacin abunci? " wayyo Akhuya cikina ciwo wayyo zan mutu tayi luuu zata fadi da sauri Mahabeer ya tarota su Daddy sukayo kansu Dr Sardauna ko gezau baiba kallonsu ma baiba Daddy yace" Faisal maza bari cin abuncin zo dubata ciwon ciki ai Dole sauyin ruwane ransa adagule ya Mike amma bai nuna azahiriba " Daddy ai saidai muje hospital sai agwada ta ko? " eh maza kamata ku tafi " bro kaimun ita mota bari na dauko abu adaki Mahabeer hankalinsa

atashe yake ganin idanuwanta sun rufe numfashi daket ya dauketa yai waje da ita ghaisha kamar tayi kuka tace" yarinya tunda ta diro

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login