Showing 24001 words to 27000 words out of 44142 words
Chapter 9 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt
kammala maganar tana murguda
baki. Ya lankwasar da kai yana fadin, "Tuba
nake Hajiya, kece din sai a hankali, amman na
hakura sai gobe zan bullo." Ta daga kafadarta
gami da fadin, "Kai dai ka sani, sautun
mahaukaciya." Ta fice daga motar. Har tayi nisa
yana kallonta kamar ya kuma binta yake ji.
Zainabu macece hatsabibiya mai tsayawa
mutum a ransa, ta san yadda take iya tafiyar da
shi kamar wacce ta karanci abun, ya rasa
abinda ya sanya matansa ba sa masa irin yanda
Zainabu ke masa, da zai sami mai masa kamar
Zainabu cikin matansa ai da babu abinda zai
sanya shi yawo ana wulakanta shi, dan yana ga
idan ya sami Zainabu ta aure shi yana jin ko
kofar gida sai anyi da gaske zai fita, da kyar ya
samu ya iya jan motarsa ya bar kofar gidan. Ta
shiga gidan da ihu babu ko sallama, Asma dake
zaune daga ita sai gajeren wando da 'yar rigar
mama tana busa tabar wiwi tana wani lumshe
ido, ta mike tana ihu suka rungume juna. Asma
ta ce, "Shegiyar, wallahi na yi zaton ba zaki zo
ba, da kin kwafsa mini." Suka zauna suna mai
da numfashi, sannan tace, "Haba Hajiyata ai kin
san dole na zo, yaushe zan yarda chasun nan ya
wuce ni?" Asma ta fashe da dariya tana fadin,
"Dan akuyan naki ne na san shi da jaraba ko
bunsuru ya rufa masa asiri, na san da kyar zai
barki ki dawo, ko da yake Zainabun akwai iya
iskanci, har tsoro nake ji idan na ga saurayina
yana kallonki, don har ta kafa sigina kike yiwa
namiji,suka fashe da dariya gami da tafawa.
Zainabu tace, "Wai ni yaya shirye-shiryen fatin
ne? Ina fata kin tanadar mana komai?" Asma ta
tabe baki tace, "Kin san akwai maza 'ya'yan
wahala wadanda iyayensu da matansu suka
sallama mana, sun gama komai. Senator Tanko
ya kama mana hotel dama komai da za'a ci a
gurin, sai dai shegen wai ba zai zo ba dan kada
'yan adawa su sami abin da zasu soke shi a
kafafan watsa labarai. Oho, ni ko a jikina dan
daman bana son ganin wannan mummunar
fuskar tasa wacce zata hana samari 'yan bana
bakwai isowa jikina mu sha minti, dan kin san
sun kwana biyu sai a hankali, dan wallahi duk
sanda na kalli fuskarsa sai ta tuno mini da wani
tsohon goggon biri." Suka kuma fashewa da
dariya gami da tafawa. Zainabu ta zira hannu
cikin jakarta da dauko kwalbar Shandy ta kama
tsotsa, ta jingina da kujera tana lumshe idanuwa
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Asma ta kalle ta gami da fadin, "Ke 'yar duniya
babu ko dandano? Kin kafa kai kina tsotsar
abun ki?" Zainabu ta dube ta da ido daya dayan
kuma ta kanne shi, "Malama kada ki matsa mini
ki bar ni na yi dif! Ina ce tadda ke na yi kina
busa tabar mulki kin mini tayi ne?" Ta kuma
matsawa gabanta tana kwantar da kai tace,
"Haba tawan ki yiwa Allah ki ba ni na kurba ko
sau daya ne, na kwana biyu ban tsotsa shandy
ba" "Amshi 'yar jaraba ba zaki bar ni na sha ta
ishe ni ba." Ta mika mata kwalbar giyar, sannan
ta dauko nadaddiyar tabar shaidan a jakarta ta
bata wuta, hayaki ya fara gauraye dakin, Asma
ta sakar musu kidan Bob Marley nan fa suka
tashi suna cashewa suna wani gantsare-
gantsare, daman Zainabu gwana ce gurin rawa.
Misalin karfe goma na dare motoci suka fara
sauke mata a kofar hotel din da zasu yi fatin,
sun ci uwar kwalliya sai dai babu wacce zaka
kalla kace diyar Hausawa ce balle Musulmai, don
duk irin shigar turawa suka yi, daga masu
gajerun wanduna sai masu damammnun kaya
da 'yan kananan wanduna. Dakin taron kuwa
kida ne kawai ke tashi kamar zai tsaga daki,
kowacce da saurayinta take shigowa. Shigowar
Zainabu da Asma ne ya sanya kallo ya koma
kansu, dan komai iri daya suka sanya, wani
gajeren siket suka sanya wanda ya tsaya
iyakacin gwiwarsu ya matse su sosai yana ta
kyalli, sai wata 'yar yalolowar riga mai rawa ta
zauna das a jikinsu, takalmansu har gwiwarsu,
sai gyaran gashi da suka yi, duk da Zainabu
bata fiye sanya gashi ba yau ta sanya, fuskar
nan ta dauki kwalliya sai wani kamshi ke tashi
daga jikinsu. Mai jawabi sai kwarara musu kirari
yake, "'Yan mata adon gari, 'yan matan da
duniya ke yayi, Asma ta Zainabu manyan Bebis
da duniya ke yayi, kun girmi kwailayen Kano,
kuna ruda mazan kano." Aka fashe da ihu.
Zainabu sarkin rawa sai ta hau taka rawa dan
daman yanda ka san mazari haka take, gaba
daya sai ta dauke hankalin mazan dake gurin
dan Zainabu daban ce, irin matan nan ne masu
kamar fitila duk inda suka je sai sun haske shi,
nan fa maza suka yi caa a kanta, ana ta mata
liki amman miskilar ko a jikinta dan babu wanda
ta baiwa fuska.Zainabu daban ce ko a duniyar
barikin tasu, dan idan namiji bai yi mata ba duk
kudinsa bai isa ko kallo a gurinta ba, tana jan
zaranta yanda take so, dan ta san Allah yayi
mata kirar daukar hankalin maza, an sha dambe
da yanke-yanke a kanta, ko waye kai idan zaka
kwana dubu kana mata magana ba za ta tanka
maka ba, musamman idan tayi dif da Shandy
dinta. Sai karfe hudu na dare aka tashi daga
fatin nasu, an rakashe an cashe an sha kayan
maye kala-kala, Zainabu kam tangadi take yi
dan ta cake da yawa, ganin haka ya sanya Asma
ta sanya ta a motarta suka nufi gidanta don ta
san 'yan gidansu basu san tana shan giya da
wiwi ba sai dai tana fita yawon gantalinta. Sai da
gari ya waye sannan ta dawo hayyacinta, bayan
ta farka ta shiga ta yi wanka ta yi ramuwar
Sallar dake kanta sannan ta yi shirin tafiya gida.
Tana sanye da doguwar riga ta atamfa super da
aka ciwa mutunci, dinkin ya kama ta tsam daga
kirjinta yayin da yayi baza daga kasa, hannun
rigar tamkar shimi yake, ta yafa karamin gyale,
sai tsireren takalminta mai kama da tsani, ta
sanya zobba na gwal kirar dubai, da wani dogon
dan kunne a kunnenta, kamshin dake daga
jikinta tamkar kamfanin turare dan Zainabu
ma'abociyar son kamshi ce. A adaidaita Sahu ta
sauka dan bata nemi dan rakiya ba, duk yawan
mazan da ta dauki hankalinsu daran jiya dake
neman shiga, ta shiga gidan nasu da sallama
muryarta tamkar sarewa. Sala da ke zaune ta
mike tana hangame baki gami da fadin, "A'a
diyar albarka har kun dawo? Har an gama fatin
kenan." (Kuji wannan Uwa fa, diya budurwa ta
kwana ta hantse a titi amman wai mahaifiyarta
tace har ta dawo? Hmmm, su Sala ko sai yaushe
za’a dawo kan hanya).
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta zauna jabar bisa tabarmar da Sala din ke kai
tana fadin, "Mun dawo Sala, wallahi fatin yayi
kyau.Yaya na ji gidan shiru ne ko duk ba sa
nan?" Sala ta tabe baki gami da fadin, "Yaran
dai basa nan amman Karimatu na nan, dan jiya
nayi wa yaron nan tas mai hure mata kunne,
nace kada ya kuma zuwar mini gida shine take
ta kumbure-kumbure, motarsa fa daya ce tal
Abula, mai na sama ya ci balle ya baiwa na
kasa, mtsw!" Ta yi tsaki cike da takaici. Zainabu
ta yi kwafa kana tace, "Ke ma Sala da son bata
ranki kike a banza, ina ce tun jiya mun gama
maganar, tunda ta dage sai shi ai sai ki rabu da
ita ta aure shi, kowa rai yayi ma dadi baya ga
mai shi ne." Sala tace, "Ai shike nan, kina ji ke
Karimatu sai ki gaya masa ya turo iyayen nasa
ko ma huta da naci kamar maye." Sala dai
kamar tsoron Zainabu take ko dan tana kawo
mata kudi? Duk hukuncin da ta yanke a gidan
babu wanda ya isa ya ja da shi koda yayanta
kuwa. Karimatu dake daki tana karatun Kur'ani
dan ta sami sassauci a zuciyarta saboda kwana
tayi tana kuka saboda yanda Sala ta bada ita ga
saurayin, wanda ko da ya aure ta ba zai kuma
ganin darajar Mahaifiyarta ba, tayi hamdala ga
Allah gami da yin Sujjada tana kara gode masa,
don Allah ya sani tana son Abbas kamar ranta,
shima yana masifar son ta, soyayya suke mai
tsafta, sai dai tun da ta kawo shi gidan da
sunan wanda zata aura Sala take aibata shi,
daman yaya lafiyar kura balle ta yi hauka? Don
daman basa shiri sam da Sala, dan tun tana
yarinya taso ta yi hali irin na Abu amman ita
Allah ya tsare ta shine fa Sala ta tsangwame ta
kamar ba diyarta ba, ko da harkar karatunta
Sadiku ne ke tallafa mata da komai,Don zamu
iya cewa kusan su kadai ne shiryayyu a gida,
dan kannanta dake bin ta maza duk sun fara
shaye-shaye, Sadiku ya yi dasu har ya gaji don
yana tufka Sala na warwarewa ne, su kuma 'yan
kannansu mata kanana guda biyu suma tallan
suke yi, kusan hanyar da Zainabu tayi rayuwa
suke kai, sai dai karamarsu ce ta dauko halin
Karimatu da alama sai kuma autansu. Bayan
Karimatu ta gama godiya ga Allah ta dauko
wayarta da sauri duk da tana jin nauyin Abbas
din amman haka ta yi kiransa, bugu daya ya
dauka don tun jiya yake neman wayarta har ya
gaji ya hakura, ita kuma ta rufe ne saboda
nauyinsa da take ji don ma kada ya kira ta bata
san mai zata ce masa ba kuma.
Gaba dayansu suka yi shiru kowanne yana jin
nauyin dan uwansa ita kam har da kunya ma.
Shine ya daure ya ce, "Yaya dai Karimatu, tun
jiya nake neman wayarki a kulle, har hankalina
ya tashi na yi zaton ko kin daina daga waya ta
ma." Tayi wata doguwar ajiyar zuciya kana tace,
"Abbas kunyarka nake ji ban san da idon da zan
kalle ka ba, don na sani Sala jiya tayi maka cin
mutuncin da ina jin ba'a taba yi maka ba, sai
dai ba kai tayi wa ba illa ni, don Allah ka yi....."
Kuka ya kwace mata ya hana ta karasa maganar
tata. Ya kwantar da murya yana fadin, "Kin ga
Karimatu ki kwantar da hankalinki, na riga na
san halin Sala tuntuni na kuma ji na gani don
babu gudu babu ja da baya a son ki, na san tayi
haka ne dan na yi fushi na rabu da ke, ni kuwa
sai na ji ma yanzu na fara son ki, dan haka ki
kwantar da hankalinki mu yi batu a kan abinda
zai fishshe mu." Ta dan ji sanyi a ranta dan
haka ta sami kwarin gwiwar gaya masa abunda
ake ciki, na yanda Sala ta amince ya turo da
iyayensa, abin ya bashi mamaki sai ya ga kamar
mafarki yake yi don shekara nawa suna fama da
Sala, amman ace lokaci daya ta amince? Sai
Karimatu ta nuna masa kawai karfin addu'ar da
suke yi ne ya sanya hakan ta faru, ya amince
da lallai hakan ne dan haka ya dinga hamdala
ga Allah, daga karshe suka yi sallama cike da
farin ciki. Abbas kam jin sa yake kamar yafi
kowa farin cikin zai mallaki Karimatu, duk da
sanda ya fara nuna wa abokansa yana son
Karimatu sun kwabe shi dan suna cewar waye
bai san iskancin da yayarta Zainabu ke yi a
unguwar ba ‘karuwar gida’ haka suke kiranta a
bayan idonta, yace shi kam ya ji ya gani dan ko
Allah bai kama wani da laifin wani, Tunda kowa
ya san halin Zainabu da na Karima ba daya ne
ba, don babu wanda zai ce gida daya suka taso
ma, sai dai kamar su da tayi daya baya ga
Zainabu gajera ce amman ba can ba, sannan
tana da dan jiki yayin da Karimatun ta kasance
doguwa siririya, Allah ya kuma sanya iyayensa
masu ilmi ne kuma wayayyu dan haka suka
goya masa baya gami da yi masa addu'a ta gari,
wacce ita ce ke dawainiya da shi a duk inda ya
sanya gabansa.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
*************
Ba da wani dadewa aka sanya rana ba wata uku
ne kacal, sai dai tun da aka sanya ranar Sala ke
mitar bata da shi, dan bata ga abinda Karimatu
ta yi da zata mata kayan daki ba, dan ko sanda
suka yi talla banda kwantai babu abun da take
yi, balle yanzu da bata da ko na sayen kwalli.
Shi kuwa Baba Abbakar ba'a ta tasa, don kudin
da aka kawo na zance ma so ya yi ya cinye sai
da Sadiku ya yi masa jan ido, shine ya ji haushi
shima yake fadin, "Ya ga mai yin gadon." Shi dai
Sadiku kallon su kawai yake yi yana ta kokarin
ya rufawa 'yar uwarsa asiri. Biki ya rage saura
kwana uku Sadiku ya shigo da kayansa na
katako irin wanda ake yayi, da kujerunsa masa
kyau da tsada. Maimakon Sala ta yi murna da
sanya albarka sai ta hau tabe baki tana fadin,
"Eh! Da yake Karimatu ce kayi mata kaya masu
tsada, da Abula ce da ka tsana da ko tsinke ba
zaka yi mata ba." Sadiku yayi murmushi ya ce,
"Sala kenan, da Zainabu da Karimatu duk 'yan
uwana ne, ita ma ta daina iskancin ta fito da
miji kin ga idan ban mata wanda ya fi wannan
ba." Zainabu da ke zaune tana yankan kumba
tana zaune bisa darduma ta doka tsalle tana
tafa hannu ta ce, "Wallahi karya ne, na fi karfin
na tsaya ka yi mini kayan daki, dan yanda kake
aiki nima ina yi, da kake ce mini 'yar iska ai na
gode Allah tunda ba na neman mata, ka duba
ka ga yanda yanzu mata ke neman....." "Dalla
can, rufe mana baki marar kunya, ki yi abinda
duk kika ga dama ai rayuwarki ce, na san komai
dadewa zaki gane kurenki, Karima dai Allah ya
rufa mata asiri, ba ta yi irin halinki ba, dan haka
kuka tsane ta gidan nan....." "Ahaf! Ahaf!, Wato
dai ni kake gayawa magana ko?" Sala ta amshe
da saurinta, "To ka ga fita daga gidan nan tun
ban bata maka rai ba, duka yaushe ka fara
samun kudin? Kafin ka fara rike dubu daya
Abula ta rike dubu goma, kuma duka albashin
naka nawa ne? Abin da ko kudin takalmi da
jakarta ba su kai ba? Ka da ka kuma furta mini
ko kala, fice ka bani guri tun ranka bai kai ga
baci ba." Ya gallawa Zainabu harara wacce ta
rama sannan ya fice, yana yiwa Karimatu
magana, "Ki lura da yanda za'a shiga da kayan
kada fentin su ya goge." Tana daga can zaune
gefen kicin tana yanka Salad da zasu ci abincin
rana da shi tace masa "To." kawai. Ai sai bala'in
Sala ya koma kanta, ina wuta ta jefa ta, zagi ta
uwa ta uba da gori tana fadin, "Dadin abin dai
da abincin da Abula ke ciyar da ke kika rayu ke
da shi din." Ita kam ko kala bata ce ba, dan
idan da sabo ta saba, ita kam aikin ta ma ta
cigaba da yi ko a jikinta. Zainabu ta ce, "Haba
Sala, ki yi shiru haka mana ka da muyi bakin
kunya." Ai kuwa tamkar ta ji wahayi daga
mala'ika ta yi shiru. Ita dai Karimatu dariya ma
abin ya bata ta ce, "Idan ka ki sharar masallaci
kayi ta rumfar kasuwa ai."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
CALIFONIA: 30/9/2003
Yana tsaye jikin window hannuwansa nannade a
kirjinsa, dogo ne ba sosai ba yana da dan jiki
irin na maza majiya karfi, jikin nasa a murde
yake, yana da kyau irin na gogaggun maza da
suka san duniya, bai cika fari ba amman ba
zaka sanya shi a layin bakake ba, yana da irin
gashin nan da samari ke ajiyewa a fuskarsu, ya
iya daukar kwalliya irin ta namijin duniya. Bai
fiye hayaniya ba, miskili ne ga wanda bai san
shaidancinsa ba, ma'abocin farin jini ga shan
yabo ga jama'a saboda faran-faran din sa da
sakin hannu (kyauta), amman a badini mutum
ne mai tsananin son holewa, sai dai yana da
matukar taka tsantsan don yana gudun bacin
ran iyayensa. Ransa a cunkushe yake, lokuta da
dama idan abin ya motsa masa sai ya ji kamar
ya zama tsuntsu ya bar garin, ya dade yana
tausar zuciyarsa a kan abinda yake gani ba
komai ba ne, sai dai yanzu abin yana neman fin
karfinsa da shallake iyakacin dauriyarsa. Abin da
ya faru dashi tsahon wasu shekaru da yake
ganin a can baya mara amfani da muhimmanci,
har idan ya tuno abin yakan kira shi da tsuntsu
daga sama gasashshe, sai dai tunda ya yi nisa
abin ya fara damunsa, da farko yakan ga kamar
abin nan ne da Hausawa kan kira 'Sabo tirken
wawa' sai dai da yaga duk kwanan duniya abin
yana kuma tsiro a zuciyarsa har ya kai matsayin
da ya cika zuciyar tasa babu sauran wani gurbi
na tirjiya da dauriya. Ya yi kwafa a karo da
dama ya juyo yana kallon kayataccen falonsa
wanda ya sha kayan alatu kamar ba za'a mutu
ba, ya isa dan gurbin shan lemo, ya zuba lemo
a kofi ya hada da shandy ya cilla kankara ya
daga ya shanye wai ko zai ji sanyi a zuciyarsa,
sai dai har lokacin abin yana nan, sai yaga
kamar ma karuwa ya yi saboda mutuwa da
jikinsa ya yi sabon tunani ya shige shi. "Me ya
sa haka ne?" Yayi wa kansa tambaya, wadda
tsawon lokaci yake yiwa kansa, ya dauko taba ya
kunna ta ya bata wuta a hankali yana lumshe
idanuwansa amman har lokacin bai ji sanyi a
ransa ba. Ya jawo takardar da ya bayar da irinta
a Ofis dinsu jiya ta barin aiki yana kuma
dubawa, wayarsa ta fara kara ya dauka da kyar
yake magana, abinda aka gaya masa kamar kara
hasala shi aka yi don haka da zafin rai yake
magana cikin harshen nasara. "Eh! Ni ne na
rubuta dan na yanke shawarar barin aikin nan
don jama'ar kasata na bukatar gudummawa ta,
sannan iyaye na sun damu da su ganni,haba
Mustafa kada ka yi mana haka, idan albashinka
ne ya maka kadan zamu iya kara maka mu." A
ransa yace, "A wannan karon babu wanda zai
hana ni tafiya dan zan biyawa raina bukatarsa
ne, dan idan na cigaba da zama a haka zan iya
asarar farin ciki da kwanciyar hankalina."
Amman a fili sai yace, "Oga kuyi hakuri ba zan
iya janye kudirina ba a wannan karon na tafiya
ko da nawa zaku kara mini, nayi muku alkawarin
dai duk sanda na sami dama zan dawo muku
gaba daya, amman yanzu hankalina ya yi
kasata." Dan Baturen da suke maganar ya sare,
dan 'dan zaman da suka yi sun san Mustafa
mutum ne kaifi daya, idan ya sanya abu a
gabansa babu wanda ya isa ya hana shi
aiwatarwa, dan haka ma ya rike aikinsa da
gaskiya da amana, dan haka suke masifar ji
dashi, shine zai bare inji ba tare da ya tsaya ya
kalli 'yar takardar bayani ba ya maida ya hada
shi kuma ya tashi tsaf, ba kamar sauran
Turawan da sai sun duba ba a rubuce, ya dai
daure yace, "Shike nan Mustafa muna maka
fatan alkhairi, sai mun hadu a Ofis din. Ya yi
ajiyar zuciya ya ce, "Shike nan Oga sai mun
hadun." Ya kashe wayar tasa gami da lumshe
idanuwansa, wata rayuwa ta dinga bijiro masa
wacce ta wuce shekarun baya wacce a da can
yake daukarta shirme, sai dai yanzu ya tabbatar
ita ce rayuwarsa mai cike da ainihin farin ciki da
sanya shi nishadi da dariya, sai dai duk sanda
yake tunanin wani abin mai fadar da gaba kan
fado masa, sai dai yana addu'ar Allah kada ya
tabbatar da wancan abinda ke fadar masa da
gaban. Washegari jikinsa babu kwari ya fito daga
Ofis din nasu dan alhinin rabuwa da abokan
aiki, sai dai daman haka rayuwa ta gada dole
wata rana