Showing 33001 words to 36000 words out of 44142 words

Chapter 12 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt

28 Dec 2024

1937

yi miki alkawarin ba zan kuma
barinki ba har abada, ni din naki ne ke kadai, ba
zan iya kuma barinki ba Zainbau, ni kaina na sha
wuya, na yi miki alkawari." Ta yi luf ta gaza cewa
komai dan yayi mata yanda ba zata iya kuma
musa masa ba, anan suka baje suna shashancin
su. Sai karfe goma na safe suka sami sukunin
tashi suka fada wanka sannan suka yi sallah,
sannan Zainabu ta fada kicin da sauri don ta
samar musu abin da zasu karya dan yunwa suke
ji matuka. Ya bita kicin din tana sanye da wani
dan guntun siket, tare suka yi aikin suna ta
dariyarsu. San da suke karyawa yayi mata kuri da
ido yana kallo don Zainabu ta bashi mamaki, ta
wuce duk yanda ya santa, gaba daya ta gama
haukata shi a daran jiya, yanzu abu daya ya rage
masa ya auri Zainabunsa ya huta, kullum yana
manne a jikin ta shi kadai, sai ya ji wani kishi ya
kama shi mai tsanani dan bai san iyakacin adadin
mazan da ta yi mu'amala ba, sai yake da na
sanin tafiya da yayi ya bar ta, da shi kadai ya san
abarsa. Ita ma wani irin farin ciki take ji a cikin
zuciyarta, dan ta sha karo da maza kala-kala a
yawon iskancinta, amma bata ji wanda ya taba yi
mata dai-dai da Mustafa ba, don haka tana yin
bariki ne bawai dan dadi ba sai don neman abun
duniya(Allah ya kyauta), Zainabu hatsabibiya ce
ta kin karawa, dan haka maza da dama ke shan
wahala a kanta, yanzu ma mikewa tayi tsam ta
isa inda yake ta zauna cinyarsa, ta sakala
hannuwanta a wuyansa ta mika masa bakinta wai
ya sammata abin da yake taunawa (wainar kwai),
bai yi mata gardama ba dan shima gwani ne, dan
haka ya hada bakinsa da nata yana ciyar da ita
abinda ke bakinsa, da haka ta dinga kara susuta
shi tamkar wani karamin yaro ta mai da shi.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Bayan sun kammala cin abincin suka yi masauki a
doguwar kujera mai cin mutum uku. Ta kwanta
lamo a kirjin sa tana shafar sa tamkar mage,
cikin kunnensa ta ce, "Musty wai me ya sanya ka
tafi ka bar ni sanda nake tsaka da bukatarka?"
Yace, "Sai kin sanar da ni irin wahalar da kika ce
kin sha sannan zan sanar dake nima." Ta yi kwafa
tana fadin, "Labarina mai cike da abun tausayi ne
da takaici, domin daga ranar da na nemeka na
rasa na shiga tashin hankali, naje har gidanku
aka ce mini daman hutu kazo wai a kasar waje
kake karatu, na shiga tashin hankali da ciwo mara
misali, abu fa kamar wasa sai ciwo ya dinga yin
gaba, da farko na zaci ciwon soyayya ne, sai da
abu yaci tura aka gano ashe ciki ne dani....." "Ciki
da gaske Zainabu ko na wasa?" Ya tambaya da
sauri. Ta yi dariya tana fadin, "Da gaske Musty
wallahi ciki ne na gaske, kai ai munga tashin
hankali ni da Sala a wannan lokacin." "To yanzu
ina abun da kika haifa din?" Ya kuma tambaya.
Ta tabe baki tana fadin, "Cabdijam, ai tuni muka
zubar da shi." Ya dafe kai yana fadin, "Ya salam,
ai sam ban san kina da ciki ba, har na ji ina son
abuna wallahi Zainabu." Ta warware masa duk
abin da ya faru sannan ta dora da cewar, "Bayan
mun gama da wannan muna murna mun dawo
gida da kwanaki kuma sai ciwon ciki ya balle mini
ga zubar jini kamar jinina zai kare, amman da
muka je gurin shegen likitan da ya zubar mini da
cikin ya caje mu kudi masu yawa gashi a lokacin
bamu da komai duk mun saida 'yan
kadarorinmu, don haka yace ba zai taba ni ba,
sai nurse din da tayi mana hanya ce tace muje
asibitin kuroda tun da dai yanzu ba zubar da ciki
bane zasu karbeni, gahi an kwana biyu da zubar
da cikin sai nace ina da aure bari na yi, sai ta
shige mana gaba da sunan ni 'yar uwarta ce daga
kauye aka kawo ni. Amman duk da na Gwabnatin
ne ma sai da aka rubuta mana magunguna masu
tsada ga karin jini, sai yaya na ne ya bada jininsa
aka diba, sannan Sala ta je ta ciwo bashi aka sayi
magunguna, lokacin adadin kudin kusan dari
shida ne. Bayan na warke muka fara tunanin
inda zamu samu kudin da zamu biya dan daman
irin kayan nan na bashin watan nan ta amsa ta
karyar da su ta saida sannan aka sami kudin, don
ma matar tana shakkar Sala ba tayi magana ba,
da na samu sauki sosai Sister din nan ta bani
shawarar na dinga fita good evening (karuwanci),
cikin kankanin lokaci komai ya sauya domin dai
kasan ni ta daban ce." Suka yi dariya gaba
dayansu sannan ta cigaba da maganar, "Yaya
Sadiku kamar zai shake ni ya kashe ni don tsabar
tsana da yayi mini, don har cewa yayi da ya san
ci gaba zanyi da iskanci da bai yadda an kara
mini jininsa ba, gwara na mutu kowa ma ya huta,
sai da Sala ta tsawatar masa harda barazanar
zata tsine masa idan bai fita harka ta ba sannan
ya saurara mini. Sister ce tace na koma karatu
domin rayuwa babu ilmi tana tawaya don haka
Sadiku na komawa ya maidani makaranta wacce
na yi kusan wata shida banje ba, da farko yace
ba zai maida ni ba sai da nayi masa alkawarin ba
zan kuma yawo ba sannan ya yadda ya kwashi
katina da zai tabbatar da bani da lafiya ne
sannan muka wuce makarantar. Sanda muka isa
Principal dinmu ta ce ba za ta amshe ni ba
domin dai nayi wajen wata shida ban zo ba 'yan
ajinmu har sun zana jarabawar sake aji . Sadiku
ya marairaice yana bata hakuri, ji nake kamar na
harbe shi don haushi, daga karshe ya dauko kati
ya bata don ta tabbatar bani da lafiya ne. Ta
ware idanuwa domin dai duk da bata fahimci
abinda likitan ya rubuta ba ta fahimci kalmar
(bleeding after abortion), wato zubar jini bayan
bari, ta daga katin cike da tsana da takaici take
kallona sannan ta fara magana.
"Lallai yarinyar nan kin cika tantiriyar 'yar iska,
bayan iskancin da rashin kunya har karuwanci
kike tabawa, kamar ki ace an zubar miki da ciki?
Kai tir da halinki, Allah ya wadaran halinki." Sai
ta jefeni da katin akan fuska ta. Sadiku ya mike
jikinsa yana rawa domin bai san likitocin da
suka yi mini karin jini sun rubuta bari nayi ba
don bai san karyar da muka shirya ba, sannan
bai tsaya ya duba katin ba duk da ba komai zai
gane ba ma, ya fara magana da rawar jiki, "Don
Allah Hajiya kiyi hakuri kaddara ce da
tsautsayi....." "Da kuma sakaci da rashin
tarbiyya." Ta karbe daga bakinsa, sannan ta
dora da cewa, "Wallahi ka ji na rantse yarinyar
nan ta gama zama a makarantar nan, alfarma
daya zan iya yi maka na rubuta maka takardar
(transfer) canji zuwa wata makarantar, don ban
ga amfanin zama da daliba irin ta ba, ita ba
kokari ba sannan ga shegen iskanci ta addabi
dalibai da malamai tun yanzu tana matsayin
kwaila, ina ga ta zama babbar mace? (No i
can't) ina ba zan iya ba." ta karasa maganar a
hasale. Ni kuwa ina gefe na cika nayi fam,
domin Sadiku ya gaza rama mini cin mutuncin
da matar nan take mini, don haka na mike daga
tsugun nan da nake yi na dole, domin tun a
gida ya gargade ni na durkusa da munje kuma
na gaida ta don ta san na yi hankali. Ke! Ma ya
ishe ki haka, haka kawai zaki sanya ni a gaba
kina zagina kamar wata uwata? Ko abun da yafi
ciki nayi ina ruwanki, idan ba zaki karbe ni a
makarantar ki ba kawai kice ba zaki karbeni ba
amman kin saka ni a gaba kina zagina, ke
wayasan iskancin da 'ya'yanki suke..... Marin da
Sadiku ya dauke ni dashi ne ya sanya ni yin
shirun dole, na dinga dubansa da jin haushi
kamar nayi masa Allah ya isa, amman tunda
lallabashi nake yi ya sanya na hakura ina ta
kunkune dai. Kana ji a gabanka tana zagina ma
ko? To maza ku bar mini Ofis dina tun ban hada
ku da (security) ba, ta fadi a hasale. Ya dauki
katin da yake a kasa yace, Malama nagode, kiyi
hakuri hali ne kowa da irin nasa, sannan ya
dubeni yace idan kin ga dama sai ki taho mu
tafi. Bai jira abinda zan ce ba ya fice daga Ofis
din. Na dalla mata harara ina fadin, "Allah ya
sanya ba kece kika kawo ilimin boko duniya ba,
sannan Mangwafak ba dan gidanku ba ne, don
haka zanyi karatu a wata makarantar ko kina so
ko baki so....." "Ki fitar mini daga Ofis dan
ubanki ko na sanya a zane mini ke ko na hada
ki da 'yan sanda su kulle mini ke wallahi
shegiyar yarinya mara kunya kawai karuwa.....
Na ce, "Kin ga karuwa dai a gidanki ba niba."
Ina gama fadin haka na ficewata ina hangota
sanda ta zauna a kujera cike da bacin rai da
bakin ciki mara misaltuwa, na dai ji dadi don na
rama wulakacin da tayi mini. Bayan mun dawo
gida Sadiku ya yi kamar ya cinye ni don bala'i,
yace kuma babu ruwansa da ni, don haka na
rasa yanda zan yi na koma karatun, don na
gane idan mutum yana zuwa makaranta yakan
rage 'yan sa ido. Daga karshe dai Sister Asibi ce
ta yi mini hanya na koma Sheka da karatuna,
acan dai na kammala Secondary dina, bayan
sakamako ya fito babu lafi na samu admission a
FCE, domin a wancan lokacin ba'a tsaurarawa
gurin makin jarabawa, don haka da 2 credits 2
passes na sami admission. A wannan lokacin ne
na kuma wayewa na san lallai da kai na a duhu
yake, duk da dai ba wani karatun ne a gabana
ba, na hadu da malamai 'yan ban gishiri na
baka manda da taimakonsu na kammala. Dai-
dai lokacin da na kammala karatuna na hadu da
wani dattijo ma'abocin son holewa DPM ne a
wata karamar hukuma. don haka tunda ya
kyalla idon sa a kaina ya makale mini, shine dai
ya kawo min takardar fara aiki (upper) har gida
tun sakamako na bai fito ba, don haka na fara
aiki na, amman fa a kanyi wata banje Ofis ba
domin dai ina da manya a sama, sun ajiye ni a
cikin Sakateriya bangaren (Accountant), mai raba
kudi, don haka Salary bana wasa nake samu ba,
duk da ba abinda na karanta kenan ba kasan
Nigeria jaga-jaga inji wani mawaki, don wallahi
wadanda muka yi karatu dasu da dama basu
sami aiki ba har yau, kuma yawancinsu sune
masu kokarin sun fito da first class amman da
yake basu da wani a sama suna zaune, kai
Nigeria sai a slow wallahi." Ya yi dariya yana
fadin, "Wallahi ke din nan 'yar buyagi ce, ni
kaina wani lokacin tsoro kike bani, barin ma
yanzu, don haka ne ma na dinga jin tsoron
dawowa don kada kiyi mini buyagin naki." Ta yi
dariya gami da kai masa bugu na wasa, suka
kama dariya gaba dayan su, sannan ya gyara
zama yana kuma shinshinarta kamar wata diyar
mage sannan ya fara bata labari kamar
haka.Kamar yanda kika sani daran da yayanki
Sadiku ya yi mini wannan wulakancin na tafine
raina a tsananin bace, domin tun da nake ba'a
taba mini wulakanci kwatankwacin wannan ba,
don haka na kudirta a raina na hakura dake
tunda daman yace duk randa ya kuma ganina a
kofar gidan ku sai ya sanya an jefe ni, ni kuwa
bana son iyayena su san halin da nake ciki sam.
Sai da na koma gida ne ma sannan na tuna da
abinda ya kaini gurin ki, don muyi sallama ne ni
zan koma makaranta duk da na san ban taba
gaya miki hutu nazo ba. Sai da tafiyar ta kama
gadan-gadan sannan na ji wani irin masifaffan
son ki yana bijiro mini da kewar ki, amman na
dake don ina ganin da zarar na bar garin duk
zan daina ji, don haka na bar Kano da zummar
na bar Zainabu Abu na nufi birnin Califonia. Sai
dai tunda na isa garin na jini kamar wani mara
lafiya, surarki da kamar ki ta dinga bijiro mini
don haka na yi zaton ko kewar ki ce, don haka
na fara mu'amala da mata kala-kala masu kyau
masu ilimi har ma da masu dukiya, amman sun
gaza gamsar dani kamar 'yar kwaila Zainabu,
amman na dinga yaudarar kai na da lallai sai na
manta Zainabu, duk macen da na kalla sai naji
na raina ta burin yana ga Zainabu, na ki na
dawo hutu don ina ganin idan na dage zan
manta dake din, sai dai iyayena suzo mini hutun
can, har na kammala karatuna kina nan a raina
na kuma baiwa kai na wani lokacin na mantawa
da ke, don haka na fara aiki a can duk da ba
haka iyayena suka so ba, sai dai shi Mahaifina
mutum ne mai saukin kai da baiwa mutum
damar sa inda yaga babu cutarwa a kanta. Dare
daya na ji duk iyakacin dauriyata ta kare,
musamman da nake ta fama da yawan ciwon
kai da aka auna ni akace na rage sanya damuwa
a raina, na yadda muddin na cigaba da zama a
can ciwon zuciya yana gan da kamani saboda
yawan tunani, na yanke shawarar zan dawo
Nigeria na neme ki amman a wannan karon
auranki zan yi, don na gane kece kadai nake so
a rayuwa ta, na kuma yi kokarin jifan tsuntsu
biyu da dutse daya don daman iyaye na sun
damu da lallai na dawo nayi aure.Sai dai idan
na tuno ki sai naga kamar na rasa ki ko kin yi
aure, da zarar na tuno hakan sai naji duk
hankalina ya tashi, na yawaita sallah da rokon
Allah ya sanya baki yi aure ba, da wannan
shawarar na dawo gidan Nigeria, da zummar ko
a yaya na sameki zan aure ki, don ban yi zaton
Abun da na sani zata koma mace mai girma da
daraja da aji kamar haka ba, don dai a yanzu so
ne tsagwaransa a raina ba wata sha'awa ba. Sai
dai na sha mamaki a yanda na ganki a yanzu,
nasan tun a can baya kina da kyau don yana
daya daga cikin abunda ya sanya nayi mu'amala
dake, ga tsabta koda yaushe zaki wuce ta gaba
na sai na ganki tsaf dake, takalminki kamar ba
kya sakawa.Don haka Zainabu ba da wasa na
dawo ba da zummar na aure ki na dawo, don
haka bana son a dauki wani lokaci mai tsaho,
sannan dole ki daina kula 'yan iskan samarin
nan naki don ina da kishi mai tsanani, shi ya
sanya a wancan lokacin ma nayi kokarin ganin
baki kula kowa ba, don haka Zainabu gani
gabanki da kokon barata ina fata zaki amince da
bukata ta." Tayi dariya cike da jin dadi ta ce,
"Lallai Mustafa ka debo ruwan dafa kanka, ta
yaya zaka ce kai kadai zan dinga kulawa bayan
ba mijina kake ba? Ai hakan ba mai yiwuwa
bane ba." Ya mike zaune yana mata wani duba
idonsa fal da masifa ya ce, "Wallahi kina so ne
na fara rotse a kofar gidanku, don duk dan
iskan da yayi mini rainin wayo a kanki zan yi
maganinsa, da can sun yi yanda suke so, yanzu
kuwa mai guri ya zo kowa sai ya matsa ya bashi
gurin sa, duk mai neman kansa da arziki.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta makalkale shi tana dariya ganin yanda yake
masifa kamar zai rufe ta da duka, suka kama
dariya don tana masa irin salon ta da take siye
masa zuciyarsa. Bugun kofar da akeyi ne ya
fargar da su, Zainabu ta mike da sauri tana
fadin, "Ina zaton shegiyar nan ce ta dawo." Ta
dubi agogo sha daya da minti uku, sannan ta
nufi kofar da sauri tana kokarin budewa. Asma
ta shigo da gudu tana ihu da dariya tana fadin,
"Shegiyar ashe akwai mai maganin iskancinki,
gaskiya Mustafa ka ci a baka na daya, ya ci a
sara maka wallahi, don kayi mana maganin mai
shegen taurin kan nan." Mustafa ya mike tsaye
yana dariya sannan ya ce, "Daman ke muke jira
mu wuce." Ya mika mata makullin sannan ya
dubi Zainabu ya ce, "Ke madam sai ki shirya na
sauke ki a gida ko, don na san idan na tafi
wannan dan iskan ne zai zo ya dauke ki." Suka
fashe da dariya ita da Asma har da tafawa, yayi
murmushi yana fadin, "Lallai kwa yi mini dariya
don kun san kun kama wuya na, ni kam na
wuce mota kya tadda ni a can." Har ya kusa
kaiwa kofa sannan ya tsaya yana fadin, "Ahaf!
Hajiya Asma na gode kuwa zan gan ki." Tayi
dariya tana fadin, "A'a don ni kada ka damu
babu damuwa ai duk yiwa kai ne, don bani da
kamar Zainabu duk Kano." Yayi murmushi ya
ce, "Na dai gode din sai mun sake haduwa."
Sannan ya fice. Asma ta kalle ta gami da
fashewa da dariya su dukan sannan suka tafa
Asma ta ce, "Wallahi kawata kin iya iskanci, ki
dubi yanda kika juyar da zuciyar dan talikin nan
a lokaci kankani don Allah, don Allah yaushe ne
zaki sanar da ni sirrin nan ne?" Zainabu ta tafi
tana fadin, "Sirri ne abin." Asma ta bita da gudu
tana fadin, "Haba kawar, ki taimaka mini don
Allah." Zainabun tayi dariya sannan ta ce, "Ki
bari sai mun hadu kinga yanzu lokaci ya kure,
don zumana yana jirana a mota." Suka kuma
fashewa da dariya, sannan Asma tace, "Lallai
Mustafa ya ciri tuta don ban taba jin kin ambaci
wani namiji da ko sunan da iyayansa suke gaya
masa ba, daga shashasha sai dan wahala ko dan
akuyan can, amman Mustafa yaci Zuma gaba
daya ma." Zainabu ta zame da sauri ta falla da
gudu tana fadin, "Malama ki kyale ni haka nan,
kina bata mini lokaci." Sanda suka isa gida duk
'yan biki sun gama watsewa sai dai sauran
kwadayayyu, sun jima a mota suna sallama
sannan ta fita tana takawa da tafiyarta ta
daukar hankalin 'yan maza, sai da yaga shigarta
gida sannan ya ja motar tasa cike da tsananin
sonta, da wani nishadi da farin ciki.
Tana shiga Sala ta kama yi mata sannu da
zuwa, ta sami kujera 'yar tsugunne ta zauna
don cike take da nishadi. Sala din ta kama
murmushu don ganin diyar tata a cikin farin ciki
sannan ta ce, "Hala yau diyar tawa ta hadu da
mai barin dala ne naga bakin naki ya ki
rufuwa." Ta yi 'yar dariya sannan ta ce, "Sala
kin san abun mamakin da ya faru kuwa tun
daran jiya?" Bata bari ta bata amsa ba ta dora
da cewar "Mustafa ya dawo." Da mamaki Sala
din tace, "Mustafa kuma? Waye me wannan
sunan, ba dan dan banzan yaron nan da ya
cuce mu shekarun baya ba can?." Zainabu ta
bata rai matuka kamar zata yi kuka, ganin haka
ya sanya Sala din ta tsuke bakin ta, don ta yi
zaton zata yiwa Zainabun gwaninta ne, don ta
san irin alwashin da taci akan Mustafa. Ita kam
mikewa tayi tana fadin "Ashe daukar hakkinsa
muka yi daman, don ba laifin sa ba ne." Ta sha
ruwa a randa sannan ta dawo ta gaya mata duk
yanda suka yi da Mustafan. Sala din tayi dan
murmushi tana fadin, "A'a lallai bashi da laifi to
mun yafe masa." Zainabu ta ji dadin abunda
Sala din ta fadi, don haka ta mike tana dariya
sannan ta ajiye mata damin 'yan dari dari na
dubu ashirin tace, "Sala gashi nan kya kashe."
Sala din ta dauka tana dariya sannan ta ce, "Ke
Zainabu ba kya gajiya? Na ga fa kin sha
kacaniyar biki kwanan nan." Zainabu tayi dariya
tace, "Ai Mustafan ne ya bada

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login