Showing 12001 words to 15000 words out of 44142 words
Chapter 5 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt
mike da sauri ta isa
gurin, ta saki baki tana kallo da shafawa, can ta
kuma fashewa da dariya tana fadin "Wallahi
kifin da ransu kuma yawo suke kamar a teku."
Shi kam Mustafa yayi tsaye yana dubanta,
hannuwansa cikin aljihu yana dariya saboda
ganin irin kauyancin da take yi, lallai ya kuma
tabbatarwa Abu sokuwa ce mara wayo, sai dai
rashin kunyar, domin da ace tana da wayo ba
zata yi wannan kauyancin ba, ko kuma dan bata
da wasu shekaru da yawa ne? Can ya hango ta
tana kiciniyar bude wata kofa sai turawa take
iyakacin karfinta.
Ya karasa yana dariya yace "Dakin bacci ne, bari
kiga yanda ake budewa." Ya kama marikin kofar
ya murda a hankali sai gashi ta bude. Ta kuma
bude baki cike da mamakin ganin wani irin
katon gado kuma dan karami ba irin na Sala mai
rumfa ba, ta nufi gadon da gudu tayi tsalle ta
fada tana kyalkyala dariya har da rike ciki tana
kuma birgima. Can kamar wacce aka kuma
tsikara sai ta kuma mikewa da sauri saboda
hango wata kofa da tayi ta san lallai wani abin
kallon zata kuma gani, wannan karon bata sha
wahala ba ta bude domin taga yanda ya bude
waccan, ta rufe bakinta cike da tsananin
mamaki taca cewa "Na shiga Uku ni Abula,
menene wannan kuma?" A cikin kunnenta taji
yana mata rada, "Wannan bandaki ne gurin
wanka irin na 'yan gayu, idan kina son irinsa zan
gina mana." Ta juya tana dubansa da mamaki
dan bata yarda da abinda yace ba, yaya ma
za'a yi aga bandaki a cikin daki kuma ga wasu
irin abubuwa a ciki kamar daki ma? Ya daga
mata kai alamar haka ne da gaske, ta nufi gurin
kwamin wanka ta shiga sai ya sakar mata
shawa, ta firgita ta fito da gudu tana ihu,ta
kankame shi domin ta firgita, ya fashe da
dariya. Lallai Unguwarsu da manyan gidaje
amman bata taba shiga ciki taga yanda suke ba,
domin ita kam bata iya jure wulakanci ko kaka
yake, su kuwa 'ya'yan masu kudin unguwarsu
wulakanci ne dasu, sam basu kula su ko fita
zasu yi ma sai dai a mota, shi kansa Mustafa
sanda ya fara cewa yana sonta tayi mamaki
sosai, sai daya dinga yi mata kalamai masu dadi
da yaudara sannan ta yarda, har yana cewa
shifa so babu ruwansa da mai kudi da talaka
duk yana shigarsa, da haka ya samu kanta dan
wani lokacin har mamakin kanta take yi data
afka son wanda ta tsana a da can. Tasha yiwa
motocin jama'a faci domin ta tsani gudun da
sukeyi a layin suna kade kaji da akuyoyi wani
lokaci harda mutane, idan anyi magana sai su
biya dan suna da kudi, sai da takai duk kofar
gidan da aka ganta sai an koreta domin idan ta
kullawa mutum duk sanda taga mota a kofar
gidansa koda ta baki ce sai ta koma gida ta
dauka kibiya ta kitso ta sossoka a tayoyin, dan
masu gadin da sun ganta zasu bita da bulala. Ya
janye ta yana dariya saboda yanda ya ga ta
tsorata yace "Bari naje na samo mana abinci da
dan ruwan lemo." Bata ce masa komai ba illa
tafiya da tayi gurin wani abin tana tabawa. Ya
dawo dauke da wani katon faranti mai dauke da
abinci da manyan kwalabe na giya (wa iyazu
biLlahi) ya ajiye bisa tebur din dake falon kana
ya shiga ya kirawo ta, da kyar ya samu ta baro
bandakin tana cewa ya tsaya tana kallo, yace In
dai kina son kallon kullum zan dinga kawo ki."
Dadi ya cikata, da wannan dabarar ya samu ta
futo. Abinci ya mika mata mai dauke da naman
kaza zuku-zuku, ta amshe kuwa da azama ta
fara ci, shima yaja nasa farantin yana ci yana
kallon ta yana dariya ,Can ya dauko kwalbar
Shandy dinsa ya bulbula a kofi ya kafa kai ya
kyankyama ya dire kofin. Ta dubeshi da mamaki
a tsorace tace, "Kai Musty (haka take ce masa)
Giya ce fa? ba zata bugar da kai ba? Naga dan
tasha idan ya sha yayi ta maye har kwata yake
fadawa." Yayi murmushi gami da lumshe
idanuwansa kana ya bude a hankali, "Ai shi
karamar giya yake sha wato burkutu shi ya
sanya yake maye, amman wannan original ce
wato mai kyau din ce, bata sanya maye bari na
zuba miki ki sha kiji." Ta manne kafada da sauri
tana fadin "Kai bana sha tsoro nake ji ni dai."
Yace, "Haba dai tawan don Allah kisha wallahi
ba zaki bugu ba sai dai kiji karfi." Da kyar ya
samu ta sha kofi guda, can kuma sai ta wawuro
kwalbar ta kafa kai ta dinga kyankyama, ta dire
kwalbar bisa tebur din. Ya fashe da dariya gami
da tafa mata yana fadin Wonderful, wato
mamaki ta burge shi, ya zira hannu cikin
aljihunsa ya zaro tabar shedan wato wiwi) ya
kunna ta ya zuka kana ya mika mata, wannan
karon batayi gardama ba ta amshe da azama ta
zuka domin bata cikin hayyacinta, sai dai zuka
daya ta kware ta kama tari, ya tashi da sauri ya
nufe ta yana rike ta har tarin ya lafa.
Amman don ta saba maimakon ta hakura sai ta
kara zuka don abin ita sha'awa ma ya bata, don
ta dade tana sha'awar yanda ake shan taba
musamman idan taga wanda ya kware mai
fesar da hayaki ta baki ta hanci. Dadi ya kama
Musty sai ya kuma zaro wata cikin aljihunsa ya
kunna ta ya hau zuka. Ta fashe da dariya karan
tabar na tsakiyar yatsunta guda biyu shima ya
taya ta suka dinga dariyarsu da zukar tabar
shedan din har suka gama, sannan ne kuma
Abu ta soma tangadi tana zage-zage da yarfe
hannuwa. "Wallahi karya ne! Babu wani sauran
shege da zai raina mana hankali wallahi! Ha-ha-
ha." Ta fashe da dariya. Ya isa inda take da
azama yana fadin "Kwantar da hankalinki
yarinya." Ta fada jikinsa shabar tamkar kayan
wanki, ai kuwa ya sami yanda yake so don haka
ya shiga aiwatar da mugun nufin da zuciyarsa
ke kintsa masa, da fari bai samu matsala ba sai
da abu yayi nisa data fara jin zafi sannan ta
nemi kwace kanta, amman da yake a buge take
hakan bai samu ba har sai da ya cimma burinsa
a kanta (Wa'iyazu billahi). Duk irin iskancin Abu
da gantalinta namiji bai taba aike mata kai tsaye
ba don tana tsoro da gudun kar aji mata ciwo,
ko su Dan Oga da dan tasha da suke siyan
abincinta, basu taba samun hadin kanta haka
kai tsaye ba sai Musty, yau ya samu daga sama
don haka shine mutum na farko da ya fara
sanin Abu diya mace, abunda ba zata taba
mantawa ba a kundin tarihin rayuwarta. A nan
bacci ya dauke su don duk cikin su babu wanda
ke cikin hayyacinsa. Basu ankara ba sai da gari
ya waye tangararau, sannan suka farka a firgice
Abu ta saki kuka da ta tuno abinda ya faru a
daren jiya, shi kuwa Musty kwantar da kansa
yayi ya dinga bata hakuri harda guntun
hawayensa, karshe dai yayi mata alkawarin kaya
da zai sai mata kala-kala har ya samu ya shawo
kanta don ya lura muguwar kwadayayyiya ce, ya
samu ya lallaba ta ya hada mata ruwan dumi
cikin bahon da tayi kauyanci daran jiya ta shige
ciki. Shigar ta bandaki da kuma tuno irin
alkawarin kayan da yace zai siyo mata ne ya
faranta ranta har ma ta daina ganin aibun
abinda suka yi din, don haka da kwarin
gwiwarta ta fito shima ya shiga don ya shirya.
Sanda ta kammala shiryawa ne gabanta kuma
ya soma dafuwa tana tunanin me zata ce da
Sala yanzu don ta Babanta sam bata jinsa,
domin sam ba zai lura bata gidan ba, domin bai
shigowa gidan sai dare ya raba, haka nan daga
gurin Sallar Asuba yake wucewa majalisarsu,
idan ka ganshi a gida da rana to lallai Alhazan
da suke wa a dawo lafiya sun kawo musu zakka
zai zo yaci abincin rana a kudinsa, yakan ce sai
ya ci guminsa wai, sai kuma jarababban yayanta
da take tsoro kada ya gane bata kwana a gida
ba. Ya fito shima ya gama shiryawa, ya dubeta
sanda suke karya kumallo sai ya ga ranta har
lokacin a bace yake, gabansa ya shiga faduwa
domin shi yanzu ma yaji ya fara sonta, don
haka ya kwantar da murya ya kamo hannunta
yana fadi, "Wayyo masoyiya ta, mene ne? Har
yanzu fushin ne? Ko baki huce bane?" Yanda
yake maganar ya kashe mata jiki, ta dinga jin
soyayyarsa da kaunarsa suna ratsa jikinta, ga
wani shaukinsa, ta kwantar da kai tace, "Wallahi
na huce, ina dai tunanin yanda zan sanar da
Sala ne, don ka san ban taba kwana a waje ba."
Ras! Ras! Shima gaban sa ya fadi don sai yanzu
ya tuna ya fito da motar Mominsa gashi ya
kwana, me zai ce mata yanzu? Lallai yasan zai
sha fada a gida, amman sai ya dake domin dai
yanzu matsalar Abu ce a gabansa.
Ya kuma kwantar da murya yana wasa da
hannunta yace, "Kada ki damu za muje nayi
miki siyayya ta ban mamaki wacce zata faranta
ran Sala din, na san ba zata yi fada ba muddin
taga kayan, ga kuma kudi da zan baki, kada ki
damu kinji ko?" Tayi ajiyar zuciya gami da cewa,
"Shi kenan." Wani katon kantin sayar da kaya
suka je. Bayan sun shiga yace ta zabi duk
abinda take so. Lallai kam yaga hauka domin
dai haka ta dinga jidar kaya kala-kala tana
sanyawa cikin dan keken da suke turawa har sai
da taga babu gurin da zata sa ta hakura, dan
wani abun ma sam bata san amfaninsa ba take
dauka, in dai taga kwalin yayi mata kyau to an
gama, domin har abin aski na maza sai da ta
dauka, shi dai binta kawai yake yi da kallo cike
da mamaki, amman bai ce komai ba domin dai
lallaba ta yake yi kada yayi magana yayi laifi. Da
suka isa gurin biyan kudin aka lissafa aka gaya
musu, kudin tsababa ne amman shi ko a jikinshi
domin dai yasan ta cancanci ya sai mata abinda
yafi haka ma. Ita kuwa 'yar jidalin wani kallo
tayi wa mai karbar kudin tana fadin, "Kai malam
dan wannan kayan ne zaka tsugawa wannan
kudin wanda yafi na buhun shinkafa 'yar
gwamnati? Kawai kayi mana ragi idan ba haka
ba mu fasa saya wallahi." Ta karasa maganar
tana tafa hannu da doka cinya. Kunya ta kama
Mustafa dan dai ta nuna cikakkiyar 'yar kauye
ce ita wacce bata taba zuwa irin wannan wajen
ba. Ya dubi mai karbar kudin sanda yake ajiye
masa kudin yace, "Ka yi hakuri daga kauye aka
kawo ta." Cikin harshen turanci yayi maganar
dan haka sam bata ji abinda yace ba. Mai
karbar kudin yace "Babu damuwa." Tana kallo
ya biya kudin don ma kada tayi magana ya
kama hannunta suka fice yana fadin ma'aikatan
su biyo shi da kayan, kamar jira ake su fita sai
wadanda ke gurin suka kama dariya. Tana daga
can ta hango suna mata dariya dan haka ta
kutuntuma wani zagi tana fadin, "Lallai ma
wadancan mutanen 'yan rainin wayo ne, ni
sukewa dariya? Wallahi bari naje nayi
maganinsu." Ta nufi gurin nasu da sauri. Ya riko
hannunta yana fadin, "Haba Zainabu na kada ki
mai da kanki 'yar kauye mana, ki zama
wayayyiya." Tayi kwafa tana dubansa tana huci
tace, "Wallahi sunyi sa'a da yau sun gane
kurensu, ni kawai ka fasa siyan kayan ma ka
bani kudin kawai na rike abuna." Yayi murmushi
yace, "Don Allah kiyi hakuri in dai kudi ne zan
baki." Da haka ya lallaba ta suka saka kayan a
mota suka wuce gida. Bayan sun shiga motar ta
turo baki gaba tana fadin, "Gaskiya wadannan
mugaye ne, dan wannan kayan zasu ce kudinsu
kenan, wallahi zai sayi buhun shinkafa har da
na wake ma, kai zai iya kai mutun Makka da
Madina ma." Dariya ta kwace masa har yana
dukan sitiyari yace, "Kai Zainabu akwai ki da
wauta wallahi, koma dai nawa ne yawan kudin
ai kinfi karfinsu a gurina, fatana dai kawai ki
dinga bani hadin kai, zaki zama tauraruwar
mata gagara-gasa a cikin unguwarku, zaki zama
abin kwatance." Ranta yayi fari kal! Amma bata
ce komai ba har suka isa kofar gidansu ya
tsaida motar. Ta dubeshi bata ce komai ba
amman ya lura da fargaba take yi dan haka
yace, "Kin ga kada ki damu tsaya kiga dabarar
da zamu yi." Ya bude motar ya fito ya kirawo
wani yaro yace maza ya shiga da kayan cikin
gida zai bashi lada, nan da nan yaron ya fara
jidar kayan yana shiga dasu cikin gida, su kuwa
suka cigaba da hirarsu, har saida yaron ya gama
shiga da kayan ya sallame shi. Ya dube ta da
salon da yake kashe mata jiki yace, "Yaya dai
Zainabu ina fatan babu matsala." Bai jira ya ji
abinda zata ce ba ya zura hannu cikin aljihunsa
ya zaro wata sabuwar ambulan mai dauke da
sabbin murtala (N20) ya mika wa Abu yana
fadin, "Ga wannan kyautar faranta mini rai ce,
sai da daddare idan na dawo." Ta fizgi kudin da
sauri kamar wani ne zai kwace, ta bude murfin
motar babu ko sallama ta fada gidansu da
sauri. Ya girgiza kai cike da dariya sannan ya
tuka motarsa ya nufi gidansu amman gabansa
na faduwa dan bai ma san irin karyar da zai
shirya ba.
Abu ta fada gidan babu ko sallama kamar wacce
aka hankada, a tsakar gida ta tadda su Sala da
kannanta suna kallon kayan da aka shigo dasu,
fuskar Sala cike da annuri. Tana shigowa Sala ta
mike da azama ta rungume ta tana fadin "'Yar
albarka, jiya sam banyi bacci ba na dinga darura
da sake-sake ko 'yan yankan kai ne suka yi
gaba da ku, sai yanzu da naga ana shigowa da
kayan nan hankalina ya kwanta nace na san
dare ne yayi muku a inda kuka je kuka ki
dawowa saboda 'yan sa ido, ai gwara da kika
kwana a can din ma dan baki ga yadda
jarababban yayanki ya dinga sintiri ba, sai da
nace masa kina daki kina bacci sannan ya
hakura ya kwanta, shi ya sanya na dinga
fargaba kada ki dawo ki buga kofar yaji ya hau
surutu da wa'azin nashi tamkar dan sarkin
Limamin Makka." (Kuji fa irin wannan Uwa,
wacce ya dace a ce hankalinta ya tashi saboda
kwanan da diyarta tayi a waje amman ko a
jikinta saboda tsabar kwadayi da son duniya,
Allah dai ya shirya). Abu kam da taji abinda Sala
ta fadi sai taji hankalinta ya kwanta, don haka
ta share karya da ta shirya da zata fada, cewar
wai mota ce ta lalace musu a hanya da suka
dawo daga siyo wadannan kayan, sai da gari ya
waye sannan suka sami masu gyara. Sai kawai
ta dauko kudin da ya bata na ambulan tana
fadin "Sala har da kudi fa ya bani." Sala ta
amshe da sauri ta kama kiciniyar farke ambulan
din ta hau kirgawa, Naira dubu biyu cif! Nan fa
suka kama tsalle da murna Sala tana fadin, "Kai
wannan yaro dan arziki ne, dan haka Abu ki rike
shi da kyau, Ubangiji ya sanya ya gama da
duniya lafiya." Haka nan suka dinga murna,
ranar nan dai ko abincin sayarwa Sala bata dora
ba. ga Abu kuwa wannan daurin gindi da ta
samu daga gurin Sala shine ya kaita ga
fandarewar da duk wanda yake da hannu gurin
lalacewar tata sai yayi da-na-sani wata rana,
rana mara alkhairi a kansu gaba daya, da-na-
sani mara amfani. (ALLAH YA KIYASHE MU DA
SHARRIN SON ZUCIYA, WANDA BAHAUSHE YACE
“BACIN ZUCIYA” Ameen)
KANO: 22|12|1993
Rayuwar Abu gaba daya ta sauya daga fari zuwa
baki, idonta ya kuma budewa da harkar banza,
domin wannan dan lokacin ta iya shan tabar
shaidan ta hanci ta baki, sannan kowane dare
kai wata rana ma har da rana Mustafa sai ya zo
ya dauketa sun tafi hotel sun sheke ayarsu.
Amman fa a wannan dan tsakanin sun sami
kudi mai dama a jikinsa, wanda duk iyakacin
shekarun da Abu tayi tana talla basu samu ba,
karatunta na boko kam sai dai muce sam barka,
domin Mustafa mai son ilmi ne dan shi ma dan
boko ne, dan ya kan sanar da ita irin yanda
mutum kan zama idan yayi karatu, yana zama
wani a duniya. Karatun allo kuwa tuni ta watsar,
Malam yayi hargagin a banza dan ba sai ya
ganta ba ma sannan zai doka ba. Sai dai kullum
tayi wanka taci kwalliya tana taku daidai a
unguwa, su Larai duk ta raina su yanzu idan
tayi kwalliya takan zagaya su tana musu yanga
idan sun dawo daga tallah. Baba Abubakar ma
sanda ya isa da fuffukarsa da Malam ya sanar
dashi halin da Abu ke ciki, ya shiga gidan da
fuffukarsa yana yiwa Sala korafi. "Yanzu Sala ba
zaki dinga tsawatarwa da yarinyar nan ba tana
neman ta jawo mana magana a unguwar nan,
kina kallonta....." "Kai Malam rufe min baki!"
Sala ta katse shi, ta dora da cewar "Kai har wani
namijin arziki ne da zaka zo kana mini wata
maganar banza, to tsaya kaji na gaya maka,
wallahi babu shegen da zai takura wa Abula a
garin nan, tun da dai ba Uban wani ya haifar
mini ita ba, kuma Uban wa muka je muka ce ya
taimaka mana da abinda zamu ci? Ko uban
waye ke ciyar damu? don haka babu wanda ya
isa yace mata 'yar iska na kyale shi. Shi kansa
Malam din da yake wannan fuffukar 'ya'yan
nasa ba karatun boko suke suna sheke ayarsu a
can ba? Har makarantar kwana sukayi fa, don ni
Allah ya bani yarinya mai kashin arziki za'a saka
mu a gaba? To wallahi ba'a isa ba, kuma daga
yau idan ka kuma zuwar mini da irin wannan
maganar sai ranka yayi mummunan baci, soko
sobarodo da baka yin maganin sisi, sai yau zaka
hau ni da fada." Duk da tsananin hakuri irin na
Baba Abbakar sai da ransa ya baci da tijarar
Sala yau, ya dubeta a hasale sanda ta diga aya
yana fadin "Au dan na gaya miki gaskiya shine
kike mini wannan tijarar? Wato dan kinga bani
da shi ko? Don da ina da shi baki isa kiyi mini
irin wannan rainin hankalin ba, dan haka ki
shiga taitayinki, idan ba haka ba ranki zai yi
mummunan baci wallahi Salamatu." "Ahayye
ayyururuuuiii!" Ta rangada guda da tafa hannu
sannan tace, "Lallai yau mazantakar za'a nuna
mini kenan ko? To tsaya kaji Abbakar, wallahi
baka isa ba, ka yi kadan, idan kuma kayi wasa a
cikin daren nan sai mu baiwa hammata iska." Ta
kama cin damara da wani zani dake yashe a
gefenta tana wani girgije-girgije da buga kafa.
(Tambaya: wai shin akan samu masu irin halin
Sala a wannan Zamanin kuwa????)
Ya fi kowa sanin halin Sala, don a shekarun
baya gidansu kamar silima yake gurin kallon
dambensu, sai dai shi da jarabar ta ishe shi ya
sallama mata, don haka yanzu ma ba zai iya
biye mata ba, don haka yabi lafiyar gadonsa na
karfe yana fadin, "Kanki ake ji, wai mahaukaci
ya fada rijiya, da girmana da 'ya'yana aga muna
raba hali a titi, ki yi da wani ba dai dani ba." Ya
runtse idonsa duk da ba bacci yake ba. Ta ja
dogon tsaki gami da fadin, "Oho dai! Kai dai
kawai kace ka ji tsoro, wallahi da ka tsaya da ka
gane kurenka yau, munafuki kawai wanda ake
gulmar 'ya'yansa da shi maimakon ya hana sai
maya kara tunzira abin." Ta haye gadonta na
katako tana cigaba da mita, "Ba ku da aiki sai
zaman gindin bishiya kuna gulma, sam ba a iya
juya kwandala ta koma Naira, ba don Allah ya
bani mata masu daukar min tallah ba ai da
nasha haushi, ka dubi wannan yaron da ya
kwaso matacciyar zuciya irin taka, idan don taku
ne sai dai yunwa ta kashe mu." Haka nan take
ta bala'in ita kadai, shi dai bai kula ta ba har
bacci yayi awon gaba dashi don dare ya tsala,
domin bai shigowa gidan da wuri sai dare yayi
sosai. Duk yaran nasu suna jiyo abinda