Showing 9001 words to 12000 words out of 44142 words

Chapter 4 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt

28 Dec 2024

1936

da hanci, tunda kin iya
daurin dankwali ai magana ta kare, ladan ya isa
haka. Shi kuwa dan Baba zaizo ya sameni
wallahi sai nayi mummunan saba masa, sai ya
yabawa aya zakinta."
Haka nan ta wuni tana mita kamar zata ci babu.
Shi kuwa Sadiku yana sane yaki dawowa gidan
da wuri sai da ya bari dare yayi ya lallaba kicin
dan ya dauki abincinsa, ai kuwa tayo waje
daman lambo tayi tace dawa Allah ya hadamu,
donma dai ya wuce duka ne da ranar sai yasha
duka a gurin Sala, shi kam ko kala baice ba da
yaga ba'a ajiye masa abincin ba ya juya ya fice.
Ta bishi har zaure tana fadin "Babu zuciyar
nema sai ta ci, ita dai wacce ka tsana din ce ke
nemo abinda kake ci kuma wallahi ko ruwa ba
zaka sha a gidan nan ba, idan kayi zuciya ka
siya, wanda na san ko sisi baka da shi baya ga
tarin takardu da bakar zuciya." Shi dai dakinsa
ya shige ya kwanta ranar haka ya kwana da
yunwa, ita kuwa saida ta kusa kwana tana mita.
Wannan shine sanadiyyar daya sanya dole aka
daina tallar safe, domin dai Sadiku yace duk
sanda tayi laifi a daina turata gida tayi noma da
wankin bandaki, abinda ta tsana a rayuwarta,
ya kuma rantse idan ta daina zuwa makarantar
sai ya ballata yaga da kan da kafar da zata yi
tallan, dole kanwar naki aka hakura da tallan
safe dan ta dinga zuwa da wuri. Da farko Sala
tace bata yadda ba amman ganin da rana ma
ana samun ciniki mai yawa kuma ita Abu tana
tsoron bala'in Sadiku ya sanya dole suka
hakura, sai dai su Karima suyi tallan safen kafin
su tafi makarantar, amman ita da yake ba irin
halinsu daya da Abu ba takanyi hanzari ta saida
ta tafi makaranta, domin ita halinsu kusan irin
na Sadiku ne shiya sanya basa shiri da Sala
sosai kullum tana mata fada da cewar mai kan
kwantai.
Misalin karfe biyu na rana ta fito daga gidansu
dan dakonta yana dauke da fantekar abinci da
kwanuka da miya a kansa, ita kuma tana rike da
farin bokitin roba mai haske an yanka salak da
tumatir da albasa, daya hannun kuma kaji ne
soyayyu cikin irin farin bokitin, anyi wanka an ci
kwalliya, zanin nan an daurashi kwauri a waje
anja jagira lebe yasha jambaki da baki, sai dai
anyi kilin an daina dige-dige da kwalli, hatta
takalmi dan madina dake kafarta yasha wanki
sai sheki yake yi, ana tafe dagwas-dagwas
kamar mai jin tausayin kasa, domin tun can
daman Abu akwai tsafta da kwalliya balle yanzu
da aka fara zama 'yan mata, gwalli da feleke ya
karu, duk cikin kawayenta tafi kowa iya tsara
kwalliya, daman gata ba baya ba gurin kyau.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
zandakata a nan,insha Allahu Zuwa yamma
zamu dora,domindai aikin Littafin yayi bisa,Wata
tangarda ce ta hanani farayimuku a
ana,nagode..






Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100






Idan Zuciya Tagyaru 1-02
Posted by ANaM Dorayi on 05:26 AM, 28-Jan-16
Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU
_________________ Na
________Fauziyya D Sulaiman____
Mustafa dake zaune kofar gidansu bisa farar
kujera karkashin bishiyar Umbrella, yana
karatun jarida kamshin Abu ya bugi hancinsa ya
daga kansa da sauri yana dubanta, kusan sati
guda kenan yake ganinta tana wucewa irin
wannan lokacin, kwarai yarinyar ta kwanta masa
a ransa, da kuma dai alamun ba za'a sha
wahalar samun kanta ba, kullum yana son yi
mata magana amman ya rasa ta yanda zai fara,
yau dai dabara ta fado masa dan haka ya fara
kwala mata kira. "Ke! Ke mai abinci! Kawo." Ta
tsaya turus gami da waigowa tana dubansa,
domin bata saba saida abincinta cikin unguwa
ba sai ta dangana ga tashar kofar wambai,
amman sai taga yayi mata kwarjini ba zata iya
kin saida masa ba, domin dai abincinta sai
wanda taga dama take saidawa, don haka ta
hau kwalawa almajirin dake dauke da abincin
kira "Kai Mudi! Kawo abincin za'a siya. Babu
musu yayo ribas ya juyo, ya isa gaban Mustafa
wanda ke zaune akan farar kujera mai tambarin
kamfanin coca-cola ya tsaya kerere. Ta galla
masa harara tana fadin "Kai fa tamkar jaki kake
komai sai ance kayi zaka yi ko? To sauke kayan."
Sannan ta dubi Mustafa tace "Malam na nawa
za'a zuba maka?." Yayi wani mayaudarin
murmushi yana mata wani duba na yaudara da
kwarewa a harkar iya soyayyar 'yan zamani yace
"Haba 'yan mata babu ko gaisuwa?" Tabbas yayi
masifar yi mata kwarjini, hasalima tunda suka
hada ido taji wani abu ya bugi zuciyarta wanda
ya sanya ba zata iya yi masa musu ba ko rashin
kunya, shi kansa ya gano hakan a kwayar idonta
ya kuma san haka nan Allah yayi masa kwarjini
da farin jini ga kowa, domin dai da wani ne
cewa zatayi, ban iya ba ko kuma tace baka kai
matsayin da za'a gaidaka ba din ne, amman shi
sai ta tsinci kanta da ce masa "To ina wuni?"
Yayi dariya yace "Ko ke fa, lafiya kalau, yaya
sunanki ne, dan kallon farko naga kin mini dari
bisa dari."
Ta kosa da zancan nasa ta daure dai tace "Ka ga
sauri nake kada rana tayi mini, na nawa za'a
baka? Dan kada kaja nayi kwantai." Ya kuma
murmushinsa dake kashe mata jiki yace "Haba
dai, ai kyawawa basa kwantai, ko domin kyanki
ai a sayi abincinki." "Ka ga nifa zan wuce kana
bata mini lokaci, wallahi dan kaine kawai na
tsaya." Ta fada tana yamutsa fuska. Ya kanne
mata ido daya yace "Haba dai ke kya soma
tafiya ban san sunanki ba? domin dai zaman
nan naki ne, dan tun randa na fara ganinki
Allah ya dasa mini tsiron sonki a raina wanda
kullum yake kuma girma, dan haka nake zama
kawai naga wucewarki naji dadi. Ta dubeshi cikin
ido, yanayin kallon da yake mata ya kashe mata
jiki ta gaza masa komai, amman sai ta dubi
Mudi da ya baza kunnuwa kamar na zomo yana
sauraran abinda suke fada tace "Mudi dauki mu
tafi yana bata mana lokaci." Mudi ya yunkura zai
dauka amman sai Mustafa ya dakatar dashi
yana fadin "Kai ajiye, maza nemo 'yan uwanka
almajirai ka raba musu, kyaky-kyawa kamarki ai
kin wuce tallan shinkafa, ke fa gimbiya ce."
Yana maganar yana dubanta da wani kallo daya
bambanta da wanda samarinta kucaku ke mata.
Mamaki ya cikata amman sai ta gaza cewa
komai tayi shiru kawai tana dubansa. "Kaje
mana ka kira 'yan uwanka ka raba musu ka
baza kunnuwa ka saki baki sai kuda ke fadawa."
Yace da Mudi wanda ya saki kunne da hangame
baki yana dubansu. Mudi dai gani yake kamar
da wasa yakeyi, amman da yaji ya doka masa
tsawa ya kuma nanata masa ya sanya ya fara
kwalawa 'yan uwansa kira. "Alalan Alalan
almajiri, Alalan Alalan kazoo kaci, Alalan Alalan
Alalan kai ba tumatiri." Ai kuwa nan da nan
gurin ya cika da almajirai, yace "To maza abi
layi." Ya kalli Mustafa dake kallon su. Mustafa
yace "Ka rarraba musu mana." Ai kuwa nan da
nan ya fara zubawa almajirai kafin kace kwabo
sai fanteka da bokitin salad. Abu na tsaye rike
da kugu cike da mamaki tana kallonsa, lallai
wannan mutumin dan rikice ne, ko tambayarta
kudin abincin baiyi ba yasa aka raba, zata yi
maganinsa kuwa yau, don wallahi sai ta tsuga
masa kudi masu yawa. Ya dubi Mudi yace "To
maza a hada kayan a koma gida uwar dakin
naka zata taho yanzu." Sai da yaga Mudi yayi
nisa sannan ya dubeta na dan wani lokaci tana
tsaye rike da kugu da alamun mamaki da
shakka a fuskarta. "Adon gari tunanin me kike
yi? Har yanzu baki fadi mini sunanki ba." Ta
yamutsa fuska tace "Sunana Abu......" "A'a
babban suna Zainabu Abu mai tagwayen suna
kenan, gaskiya Zainab baki dace da kalar tallah
ba, dubeki fine baby ace kina daukar tallah? to
gaskiya ni dai daga yau na soke tallar nan." Ta
dubeshi a tsiwace tace "Ka ji mu da mutum sai
kace wani Ubana? ko kai ne zaka dinga biyana
kudin da nake samu eye?" Yace "Eh mana zan
dinga biya ko nawa ne, don gaskiya bana son
rana tana taba mini kyaky-kyawar fuskarki,
kyanki hutu Zainabu."
Ta tabe baki don zancen bai gamsar da ita ba,
don tasan bai san yawan kudin bane shiyasa
yake wani cika baki amman yanzu zata yi
maganin firiritarsa. Don haka tace "Ka ga ka cika
ni da surutu bayan baka biyani kudin abincina
ba." Yayi dariya yace "Haba Zainab, baki yarda
dani ba naga alama, ko don kin ganni da dan
wando jeans da shet? kin san mu 'yan boko
bamu san kaya masu nauyi, amman nawa ne
kudin? Kila idan na baki hankalinki yafi
kwanciya." Ta murguda baki wanda ya zame
mata kamar al'ada sannan tace "Dari uku da
ashirin da biyar ne, sai nama na naira talatin da
biyu...." "A'a Zainab, duka zaki hade mini?" Tayi
dan duru-duru don tasan zulake tayi duka
kayan nata basu wuce na dari biyu da tamanin
ba, don haka ta kasa hadewa ta fadi don bata
iya lissafi ba (bata da Maths tab akin yara), da
ya fahimci halin da ta shiga sai ya zura hannu a
aljihunsa ya debo 'yan murtala (Naira Ishirin)
har na dari hudu yace, "Ga dari hudu ma ni na
kara miki." Mamaki ya cikata matuka, hannunta
har rawa yake yi gurin karba don tana ganin
kamar zai maida yace ya fasa ne. Sai da taji
dumin kudin a hannunta sannan hankalinta ya
kwanta ta dube shi da mamaki tace "To nagode!
Zan tafi gida." Yace "A'a ai dole na yiwa gimbiya
rakiya ko don naga gidansu." A wannan karon
bata yi masa musu ba don yayi mata ba zata,
don haka suka nufi hanyar gidansu, a kofar gida
yayi mata sallama yace sai gobe tace Allah ya
kaimu. Ta shiga gida da gudunta Sala na zaune
tayi tsuru cike da shakkun labarin da Mudi ya
bata, gaskiya tafi zargin bari kawai suka yi yace
wani wai juye wani saurayi dan gaye yayi mata.
Abu na shigowa ta mike da zakuwa tace, "Ke
maza sanar dani menene ya faru?" Abu tayi
dariya gami da nuna mata kudin da saurayin ya
bata, ta fizge daga hannun Abu da azama ta
hau kirgawa, Abu kuwa sai dariya takeyi. Sala ta
kammala lissafawa ne ta dubi Abu cike da farin
ciki tace "Diyar arziki yau kuma wane mai arziki
kika hadu dashi? Kai wannan diya da kan arziki
kike, shi ya sanya aka tsangwameki a unguwar
nan, ki dubi yadda su Sarai da Sakina kawayenki
suke kwantai kullum sai sun dawo da ragowar
abinci, sai dai a cinye ko kuma akai dakalin 'yan
kwantai da daddare abincin naira biyu a karyar
dashi naira daya koma sis daya. Abu tace "Bari
ke dai Sala, ni tunda nake ma ban taba haduwa
da mutum mai ban mamaki irin wannan ba."
Sala tace, "Yaya ne sunansa?" Ta tabe baki tace
"Oho!!! Ni ko tambaya ma banyi ba." "Kiji
sokuwa, arziki yana kiranki kina masa kutufo, to
gobe ki tambayi sunansa kuma ki saki jikinki
dashi, kin san su irin wadannan basu son ki
dinga dari-dari da su, idan abin ma gaba
daya....." Abu tayi dariya gami da shigewa
dakinta. … Allah ya shirya.
Washegari ma haka ce ta faru, Mustafa yayi
mata juye ya rako ta gida, sai dai wannan karan
ya tsaya sun dan taba hira duk da ya lura
sokuwa ce sam bata waye ba, da kuma alama
girman jiki ne kawai da ita babu shekaru, sai dai
ko menene shi dai yaji ya gani yana kuma so a
haka.
Yau da gobe sabo da shakuwa ya shiga
tsakaninsu har ya zama an daina fita da abincin
ko ina sai dai a bawa almajirai a gida. Abu an
daina fitowa kamar yadda Mustafa yace bai son
kyaky-kyawar fuskarta ta baci da zafin rana don
haka tana gida kullum. Wani abu kuma da
Mustafa ya koya mata shine cin dadi, yanzu
abincin kala-kala take ci ba irin wanda take ci
ada can ba, ga kaya da yake kawo mata na
kwalliya da na sanyawa, sai ga Abu ta kuma
futowa fes da ita kuma yanzu da motar Babansa
ma yake zuwa zance gurinta ko ta Mamanshi
don haka cikin motar suke zancensu. Ta futo
daga wanka tana tsakar gida bisa tabarma da
kayan kwalliya a gabanta ana ta kwalliya da
hasken wutar nefa, dan Mustafa na gab da
zuwa, Sala ta zauna daga bayan ta tana kallonta
cike da murmushi tace, "Kai diyar nan wallahi
akwai ki da kwalliyar daukar ido, dubeki kamar
wata sarauniya. Ai ba don bamu gama cin kudin
ba da kin auri yaron nan don ya dace dake, ga
kyau ga kudi, sai dai na lura kamar dai iyayensa
ne masu kudin ba shi kansa ba ko?" Abu ta
tabe baki tace, "Oho! Ni ban sani ba, ke idan
banda abinki ma Sala yaushe na isa aure? Ni
yanzu ma sai nayi digiri, don Mustafa yace mace
idan tayi ilimi wai tafi kyau da tsada. Ni fa yanzu
Sala dan-na-sanin talla ma nake yi, ki dube ni ki
gani yanzu kamar wata diyar wani basarake."
Sala tayi shewa gami da rangada guda tace, "Kai
Allah nagode maka, ai abinda nake ta nusar
dake kenan tun da can, ki sami samarin da zasu
dinga kashe miki kudi mu huta da tallan, yanzu
ba gashi munyi kyau ba? Ga kudi suna shigowa,
wannan shegen yayan naki yana saka mana
ido." Ta ja tsaki, "Mtsw! Wallahi idan ya sake sai
nayi masa baki, wai har ni zai kalli idona yace
mini sai Allah ya tambaye ni duk abinda muke
aikatawa, wai don kina zance a mota, wai 'yan
unguwa sai zarginki sukeyi gashi kin daina talla
ma a ina kike samun kudi yanzu? Nace a gidan
ubansa. Sai fa da nayi masa wuta-wuta sannan
na samu ya fice daga gidan nan, kuma nayi
masa barazanar duk randa ya kuma shiga
shirginki sai na tsine masa, idan muka biye ta
tashi zamu rayu ne? Da yanzu mun mutu,
Mtsw!" Ta kuma jan tsaki. Abu ta hasala ta
murguda baki gami da tsiro shi gaba tace, "Ki
fita harkarsa kawai Sala, na lura talauci ne ke
damunsa, kuma wallahi yayi sa'a shi yayana ne
da wallahi 'yan sanda zan dauko masa." Sala
tace, "Ai bake ba ni kaina ba don gudun abin
kunya ba da saka ido irin na tsinannun mutanen
unguwar nan, da wallahi sai na hadashi da 'yan
sandan sun lallasa mini shi." Sallamar da wani
yaro yayi ce ta katse musu hirar tasu tamkar
wasu kawaye, su kuwa sauran kannan nata duk
sun bazama tallar gyada a can kofar gida. "Kai!!
Meye ka ishemu da sallama?" Sala ta katse shi
cike da haushin katse musu hirarsu da yayi ba
tare da ta kai aya ba don ko amsa sallamar ma
bata yi ba. "A'a daman wani ne a mota ke
sallama da Abu..."
"Au! Yi hakuri na hauka da fada, kace tana zuwa
dan albarka, ka ji?" (HMMM) Yaron ya fice yana
fadin to. Ta dubi Abu da ta mike ta nufi daki
don sanya kaya tana dariya tace, "Yau dai naga
kwalliyar nan ta daban ce, kiyi sauri kada ki
bata masa lokaci." Ita dai bata ce komai ba ta
shirya ta fito sai kamshi take yi, kai tsaye ta fice
ta nufi gurin da Mustafa yake, yana hango ta ya
bude mata gaban motarsa wato kusa dashi sai
wani malalacin murmushi yake mata na
tsananin yaudara irin na gogaggun samari, ita
kuwa sokuwar sai wani kara zobara baki takeyi
tana wani yauki har ta shiga ciki ta zauna tana
wani fari kamar 'yar tsana. Ya shaki kamshinta
gami da lumshe ido, cikin mayaudariyar
muryarsa yace, "Kai Zainabu, kin yi kyau kamar
wata sarauniya." Tayi dariya cike da jin dadi
tace, "Haka ma Sala tace wai nayi kyau sosai."
Yayi murmushin jin wautarta, Ya riga ya gama
karantar halin Abu da Sala, don haka ya san ba
zai sha wahala gurin samun hadin kan Abu ba,
don haka ya mika hannuwansa ya kamo hannun
Abu yana wasa dashi yace, "Kai yatsunki akwai
ban sha'awa, dube su zara-zara. Dadi ya kuma
cika ta na yabon da yake mata tace, "Haka kowa
ke cewa, wai yatsuna da na hannu da na kafa
suna da kyau kamar ba nawa ba." Yayi dariya
yace, "Gaskiya haka ne, amman kyanki ai yaci
suma suyi kyau." Cikin dabara ya jata jikinsa
yana fadin, "Ya dace dai yau na shaki kamshin
nan naki da kullum ke ruda ni." Ga mamakinsa
sai yaga Abu ta saki jikinta har ma tana kokarin
taya shi, abin ya bashi mamaki don yayi zaton
sai yasha wuya zai sami kanta, sai gashi ya
same ta a ruwan sanyi, amman sai ya danne ya
dinga aiwatar da mugun nufinsa da zuciyarsa ke
ingiza shi. (Allah ya kiyashe mu da aikin assha.
amin).
Da ya tabbatar ba zai sami wata matsala da Abu
ba, sai ya lankwashe murya yace, "Abu ko zaki
rakani wata 'yar unguwa?, daga can kin ga sai
mu wuce nayo miki siyayya ko?" Tace "Babu
damuwa muje kawai." Ya dubeta ta dan hasken
dake cikin motar na farin wata da ya shigo yace,
"Kina ganin babu matsala idan Sala ta aiko bata
ganki ba? dan kada tayi fada." Ta tabe baki tace,
"Kada ka damu ba zata ce komai ba tunda dai
ta san siyayya zaka yi mini, kuma ta san ai
muna tare." Yaji dadin abinda tace dan haka ya
tada motar gami da karo sautin wakar dake fita
a cikin rediyonsa, muryar Bob Marley ce a
wakarsa ta One Love, duk da Abu bata jin
turanci wakar tana mata dadi musamman da
yake koda yaushe za kaji kaset din Bob Marley
Mustafa ke sanyawa, har ma ta iya bin wakar
tana girgiza kai duk da ba daidai take fadin
wasu kalmomi ba. Suna tafe a hanya suna hira
har suka isa wani hotel, kasancewar kaurin
sunan da hotel din yayi baka ganin jama'ar kirki
a cikinsa domin kada sunansu ya baci, wannan
ya kara baiwa 'yan iska damar cin karensu babu
babbaka, gurin shiru babu alamun jama'a, sai
ka shiga daga ciki zaka ga kamar tsakiyar rana
ce dan haske da tashin kida. Ya dubi Abu yana
murmushi yace, "Zainabu ya dace mu dan tsaya
a nan musha lemo mu huta, kafin na wuce yi
miki siyayyar domin har dan kunne da sarka na
gwal zan sai miki, kema ki shiga sahun manyan
mata ko?" Yana mayaudarin kallonsa yake
maganar. Tayi dariya cike da jin dadi tace "Babu
damuwa." Ya sami guri ya faka motar tasa, ya
bude ya fito sannan ya bude mata ta fito suka
jera, Abu jin kanta take yi da girma saboda ta
fito daga mota, a ganinta ta gama cinyewa.
Sanda suka isa cikin reception din hotel din sai
ta kama zare idanu cike da kauyanci, domin
tunda take bata taba ganin guri mai kyawun
wannan ba, ta saki baki galala tana kallo ga
hasken wuta ga fankoki suna juyawa ga A.C da
Tibi, ga 'yan mata nan kala-kala kowacce da
shiga ta rashin mutunci, sai taji ta raina kanta,
lallai ta yadda da Mustafa da yace zai nuna
mata rayuwar 'yanci da wayewa, gashi kuwa ta
fara gani. Sai ta kama muzurai kamar ta koma
gida ta sanyo atamfarta Wagambari da tafi
kowacce kyau da tsada, amman sai taga ai ko ta
sako ba zata yi kyawun wadannan ba, ta
shagala da kallonsu tana fadin dama itace
wannan, can kuma idan taga wata sai taji tafi
waccan tace, kai waccan zan zama, shi kuwa
yana can yana biyan kudin dakin da zai kama
musu. Ya kammala ya amshi makulli ya nufe ta,
sai yaga sam hankalinta baya tare da ita har
hannu take sanyawa tana taba duk abinda ya
burgeta, ya kama hannunta suka nufi dakin da
ya kama musu. Sanda suka shiga dakin kuwa sai
labari ya sha bamban, sai taga ai can wajen ma
ba'a sanya komai na more rayuwa kamar nan
ba, ta fada kan tumemiyar kujerar dake falo da
karfi tana fadin, "Kai bari muga za ta loma
kuwa?" Ta saka wata dariya ganin ko motsi
sosan baiyi ba, can idon ta ya hango mata wani
gilas dake dauke da ruwa da kifaye da wasu
'yan kananan bishiyoyi, ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login