Showing 15001 words to 18000 words out of 44142 words
Chapter 6 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt
suke yi
amman basa fahimtar maganar da suke yi sai
dai hayaniya kawai da suke ji, Sadiku yafi kowa
tashin hankali don tun yana yaro yake takaicin
abinda iyayan nasa keyi don ma abokinsa Zaid
na bashi baki. Sai dai addu'a al'amarin nasu,
lallai ba a sakewa tuwo suna, haka nan ba'a
sauya iyaye, shi kam da tuni ya sauya da ace
suyo su ake yi, domin kowanne da tabonsa. Sala
masifaffiya mai shegen son kudi da abun duniya
da son 'ya'ya, yayin da Baba Abbakar ya
kasance mai matacciyar zuciya da gulma da
munafurci, don sana'arsa kenan kullum yana
gindin dirimi shi da abokanan sana'ar ta shi
(magulmata) suna ta sana'ar tasu, bai saida
komai balle ya sanya ran zai samu ya kaiwa
iyalansa, 'yar sana'ar tasa ta saida shayi ya
watsar tuni zuciya ta mutu, sai dai gulma a
gindin dirimi. Don haka a cikinsu akan rasa na
zaba, shi dai yana godewa Allah da ya sanya bai
dauko halin ko daya ba a cikinsu, amman dai
yana takaicin irin rayuwar da 'yan uwansa da
iyayensa ke yi, don haka ranar da bakin ciki da
takaici ya kwana, amman yayi alkawarin zai yi
maganin abun da kansa, koda kuwa Sala zata
tsine masa ne Allah dai yaga niyyarsa.
*******************
Karfe takwas na dare Mustafa ya tsaida motarsa
a kofar gidansu Abu, ya tura yaro ya kira masa
ita, kusan tare suka futo da yaron taci uwar
kwalliya da atamfa mai barewa, tayi daurin
Hindu Rufa'i, ana wani tauna cingam wai ita
dole ga 'yar gayu, leben nan ya sha jambaki a
sama baki da kasa, an ja jagira mai cin birki a
gefen kunne. Ta hasken wutar lantarki ya hango
ta kamar ya yi dariya, don kwalliyar tata kamar
'yar kauye tayi mata, sai ya dake don kada ya
tsokanowa kansa don yasa halin tsiwar Abu. Ta
isa ta bude gaban motar aka zauna irin a
karkacen nan ana wani fari da ido wai ita a dole
ga 'yar gayu. Ya kamo hannunta yana dariya
kasa-kasa yace, "Kai gimbiya, kin ga yanda kika
yi wani kyau kuwa? Irin wannan kwalliya ai
sai....." Finciko ta da aka yi ne ya sanya shi yin
shiru cike da mamaki da razana. Sadiku ne ya
finciko ta ya watsar a tsakiyar titi, sannan ya
kalli Mustafa dake kallon sa sororo cike da
mamaki yace, "Kai dan iska mara mutunci
wallahi daga yau na kuma ganinka a kofar gidan
nan sai nayi maka rashin mutunci, don haka ka
ja tsummar rayuwarka ka bar kofar gidan nan
tun ba sanya yara sun maka atile ba." Ya juya
kan Abu wacce ta mike tana goge jikinta wai ita
nan ya bata mata kwalliya, sai murguda baki
take yi tana kun-kuni wanda ya san zaginsa
kawai take yi, ai kuwa yayi kanta ya zabga mata
mari sannan ya sanya kafa ya haure ta. Ta zube
a kasa gami da rike cikinta ta fasa ihu gami da
fadin, "Wayyo Sala na shiga uku!" Ya kuma kai
mata duka amman ta yunkura ta mike ta kwasa
da gudu ya rufa mata baya da bel din
wandonsa da ya zare. A soro suka ci karo da
Sala wacce ta futo a gigice saboda jiyo ihun 'yar
lelenta da tayi. Ai kuwa Abu na ganin Sala din ta
zube a soron tana fadin, "Wayyo Sala na shiga
uku zai kashe ni cikina Sala, zan mutu na shiga
uku (Kuji Makirci). Sala tace "Na shiga uku, wane
shegen ne ya taba mini ke Abula?...." Shigowar
Sadiku yana huci ne ya sanya ta gano abinda ya
faru. Sala ta zaro ido waje cike da bacin rai tana
fadin, "Lallai ka cika mara mutunci, yarinyar
tana zancen ta kawai za ka kama dukanta, to
me tayi maka, mugu?" "Haba Sala wane irin
zance? Iskanci dai kawai. Waye a unguwar nan
bai san abinda yarinyar nan takeyi ba? Haka
kawai ta sanya ana zaginmu da raina mana
hankali, wallahi na kuma ganinta da shegen
mutumin nan sai na karya ta." Sala ta kuma yi
masa kallon banza tana fadin, "Sannu Abbakar
Ubanta da yayi cikinta, to tsaya kaji na gaya
maka, kayi kadan kai uban da ya haife ka ma
yayi kadan balle kai karan kada miya, haka
kawai ka takurawa yarinya ka hana ta rawar
gaban hantsi? Kai ne ka haifar mini ita ko kaine
ka halicceta, eye? Bala'in naka ya wuce na baki
har ka fara kai hannu kana dukan ta? Za ka zo
kana gaya min ana gulmarku a unguwa, ina
ruwana da wasu 'yan unguwa 'yan saka ido
sana'ar banza ana ruwa suna kirgawa, su bari
su koma sata yafi. To bari inyi maka mai gaba
daya ta mahaukata tunda naga abun naka yana
neman ya wuce gona da iri,Wallahi daga yau
idan ka kuma taba mini yarinyar nan ko ka
kuma shiga rayuwarta da sunan fada ban yafe
maka nonona da ka sha ba!" Sadiku ya dafe kai
cike da tashin hankali yana fadin, "Innalillahi wa
inna ilaihi raji'un, Sala mai yasa haka? Yanzu
dan ina gaya muku gaskiya dan gudun kada ku
fada cikin halaka ya sanya zaki tsine
mini....."gaskiya ko kuma munafurci da sanya
ido? Kai waye ya shiga rayuwarka? Kullum kana
yawo da kodadden wando jins da rigar gwanjo
kamar tsohon matsiyacin bature." Ya girgiza kai
cike da takaici yace, "Shike nan Sala Insha Allahu
kome Abu zata yi a unguwar nan da gidan nan
na daina yi mata magana, taje in dai duniya ce
ta ishe ta riga da wando, za ta koya mata
hankali." "Ka ga malam kada kayi mata baki,
koda yake ai ba kai ka haife taba balle bakin ka
ya bita ba, wadanda ma suka fika sunyi sun
gama babu abunda ya same ta sai ma cigaba
balle kai, don kurwar Abu kur! Maye yaci kansa."
Sadiku bai kuma cewa komai ba ya juya ya fice
daga gidan, don sai yaji gaba daya gidan ma ya
ishe shi. Sala ta kama Abu dake zaune dirshan
tana kallonsu don taji yanda Sala ke afke masa
ta wanke mata zuciya, Sala din tana fadin "Tashi
muje gida ki kwanta kinji? Koda yake Alhaji
Mustafan yana can yana jiranki. Goge idonki kije
ku cigaba da zancenku, ki gaya masa ya kwantar
da hankalinsa kamar tsumma a randa, nayi
masa maganin dan saka idon can, ba ku da
sauran mai matsa muku yanzu, muje na raka ki
ko yana kofar gida a labe bai tafi ba." Ta daga
ta tana goge mata idon ta wanda babu ko
alamun kwalla ko guda daya, daman kukan nata
na sharri ne bawai na zafin duka ba. Suka nufi
kofar gidan tare, sai dai babu motar Mustafa
babu alamarta sai dai filin wajen kawai, dan
yana ganin sun yi cikin gida ya ja motarsa yayi
gaba don kada Sadiku yazo yayi masa tijara a
cikin jama'a har asirinsa ya tonu, don haka ya ja
motarsa ya gudu. Ai kuwa suna ganin baya nan
ran Sala ya kuma baci suka koma cikin gida tana
ta masifa da bala'i, wanda har makota suna
jiyota, ita kanta Abun ma taji takaicin tafiyar
Mustafa dan ta saka ran ya bata wasu kudi yau
na ankon bikin Larai, dan haka dai sun dauki
laifi gaba daya sun dora akan Sadiku wanda ya
bar musu unguwar ma gaba daya. A daran nan
Sala batayi baccin kirki ba sai bala'i da masifa
kawai take yi har Baba Abbakar ya dawo tana
yi, shi dai yayi mata banza bai kulata ba dan dai
yasan 'yan bala'in ne suka motsa, idan kuma
suka motsa babu wanda take saurarawa dan
haka shi dai ya lallaba ya haye gadonsa na
karfe yayi lamo kamar mai yin bacci amman a
zuciyarsa Allah wadarai yake yi da halin Sala,
har ya tuno wata mata data wuce ta gabansi
dazu suna majalisa wani yayi subutar baki a
cikinsu yace "Ka ga wannan matar idan ta fara
bala'i sai ta kwana tana yi." Ashe matar nan ta
jiyo shi don haka ta dawo ta tsaya a kansu gami
da rike kugu tana kallonsu shekeke tace, "Mai
kuka ce, eye?" Wanda ya fadi maganar ya yi
murmushi irin na matsorata yace, "A'a Hajiya ai
yabonki muka yi nace duk unguwar nan babu
irinki a mutunci, ba irin babata ba 'yar bala'i,
idan ta kama masifa sai ta kwana tana yi." Jin
abunda yace ne ya sanya tace, "Allah ya so ka
wallahi, da yau na lakada maka duka a unguwar
nan na ga mai kwatarka, da sai kaga karshen
masifa ta." Sai da tayi nisa sannan suka fashe
da dariya suna zolayarsa sai yace, "Ku ai gwara
da na yi haka, dan wallahi yanda na ga tana
wata girgiza bata ki mu casu a tsakiyar titin nan
ba, ni kuwa ina zan iya da ita kana ganin mace
kamar bishiyar kuka? Ai irin wadannan sai da
lallashi." Lallai kam haka ne sai yanzu ya gano
gaskiyar Malam Sabo, masifaffu ba'a iya musu
sai dai a bisu da lallashi ko kuma ayi musu
banza kawai. Shi dai har bacci ya dauke shi bai
san sanda Sala ta gama masifarta ba.
Da safe ma da bala'in Sala ta karya dan Sadiku
ko koko da kosan da ake bashi ranar ba'a bashi
ba sam, shima bai nema ba ya tafi makarantar
sa da yake yana karatun Low ne a B.U.K,
karatun da yake matukar shan wahala a kansa
dan babu wanda ke taimaka masa a iyayansa
sai Malam ne ma yake taimaka masa wani lokaci
da kuma rufin asirin Allah, dan ya iya zane idan
ya samu ya kan yi, ko kuma idan bashi da lakca
ya tsaya shagon wani abokinsa ya taya shi aski a
bashi wani abu, da kuma tallafi na karatu da
suke samu (Scholarship), haka nan yayi
ficewarsa da yunwarsa gashi banda kudin mota
bashi da ko kwandala. Ita kuwa Abu 'yar mulkin
ko shirin makaranta bata yi ba, don kwanciyar
ta ma tayi tace kanta ciwo yake yi, yinin ranar a
daddafe tayi shi dan takaici, ita kuwa Sala sai
kawo mata kayan dadi takeyi kala-kala wai dan
ta kwantar mata da hankali. Yamma na
karatowa aka yi wanka aka ci uwar kwalliya ta
jiran Mustafa aka kame akan kujera, duk yaron
da ya shigo gidan sai taji kamar ita zai ce ana
kira, gashi ita yanzu ta daina kula samari dan a
ganinta ita kalar manya ce kamar yanda
Mustafa ke gaya mata. Sai dai me? Har kusan
karfe goma na dare babu Mustafa babu alamar
sa, har gajiya tayi da lekawa amman babu shi
babu alamunsa. Daga karshe dai ta sanyawa
Sala kuka tana fadin "Sala ina ga fa Mustafa
fushi yayi da wulakancin da Sadiku ya yi masa
jiya, dan baki ji maganganun da ya dinga gaya
masa ba, shi ya sanya ya yi fushi ya ki zuwa."
Sala tace, "Bari ke dai Abula ai wannan yaron ya
goga mana bala'i, yanzu idan yaron nan ya
daina zuwa ina zamu sanya kanmu? Ki duba ki
ga irin kudin da yake bamu a sama ba tare da
mun sha wahala ba, yanzu idan ya daina zuwa
sai dai mu koma abincinmu kenan." "Abinci
Sala? Cabdijam!! Wallahi Sala na fi karfin tallar
abinci yanzu, dube ni fa ki gani? Ni samari ma
tsami na daina harka da su balle wani tallah,
idan mutum bashi da kudi ko kallo ma bai ishe
ni ba." Sala tayi dariya tana fadin, "Ho Abulata,
kinyi gaskiya wallahi kin fi karfin talla yanzu,
tunda Allah ya baki abun neman kudi ai shike
nan. Ki sha kuruminki na ma sani zai dawo,
watakila wani abin ne ya tsre shi, dan na san ba
kowa ne zai sami kamarki ya yasar ba... Ke
kamar na ji karar mota ma." Sukayi shiru, can
Sala tace, "Allah karar mota ce." Suka bazama
suka yi kofar gida har suna karo da juna, sai dai
me? Kurar mota kawai suka gani ta wuce tuni,
haka nan suka dawo suna zaman tsammanin
warabbuka, Malam ya ki noma yana jiran
sadaka. Sai dai har suka fara gyangyadi babu
Mustafa babu alamarsa, haka nan suka hakura
kowacce ta kama makwancinta cike da takaici.
Abu kamar wasa karamar magana ta zama
babba inji Garba Sufa, dan yau kwanaki shida
kenan amman babu Mustafa babu alamarsa,
uwa da 'ya sun shiga tashin hankali, tun suna
tunanin zai zo har sun hakura sun fidda ransu
da zuwan nasa, shi kuwa Sadiku da har yau bai
daina shan bala'in Sala ba murna yake yi don
ko babu komai ya kori Mustafa, lallai barazanar
da ya yi masa tayi tasiri a kansa. Daran daya
cika kwana bakwai suka yanke shawarar zuwa
gidansu dan su bashi hakuri, domin dai kudi
sun fara musu karanci don ma su Karimatu
suna daukar abinci da funkaso, don ita macece
mai jarababban neman kudi dan tun tana
budurwa bata iya zama babu sana'a ba.
Washegari da yamma Abu taci kwalliyar ta duk
da kanta da yake mata ciwo, ana taku dai-dai
kamar ba zata taka kasa ba, aka nufi gidan su
Mustafa wanda yake can gangaren layinsu.
Sanda ta isa ta tsaya tana kallon gurin da yake
zama bisa farar kujera karkashin bishiyar
Umbrella, lokuta da dama da jarida a hannunsa,
sai dai yanzu babu ko alamarsa ko kujerar tasa
ma babu a gurin. Katuwar koface wacce ke
garkame, bata mantawa da can suna zuwa
tsokanar kare, idan ya biyosu su zunduma da
gudu ko kuma suyi ta jifansa, wata rana sun
taba fasa masa kai mai gadin ya bi su da gudu
ya kama daya a cikinsu ya zane, shine fa suka
kulla masa, ai kuwa rannan maigidan ya futo da
motar zai tafi sai kuma yayi mantuwa ya koma
cikin gidan, su kuwa daman suna fakonsa dan
haka suka dauko wani abu mai tsini suka soka a
tayar gaba ta sace, ai kuwa sanda mai gidan ya
futo ya gani ya dinga yiwa maigadin fada daga
karshe dai sai wata ya hau ya bar wannan a
nan, bayan maigidan ya tafi suka dinga yiwa
maigadin ihu da tsokanarsa, ai kuwa ya bisu da
gudu sai dai kasa kama kowa yayi dan 'yar
zilliya suka dinga yi masa, haka nan ya gaji ya
koma yana nishi, don haka yanzu take fargaba
kada ya gane ta. Ta daure dai ta kwankwasa
kofar, ya bude ta 'yar karamar taga ya leko dan
yaga wanda ke magana, yana ganin ita ce ya
zaro ido waje yace, "Me kike nema a anan,
eye?" Yana maganar fuskar nan tasa a murtike.
Ta rike kugu da murguda baki a hankali tace,
"Banza dan gadi, kai ba don ta kama ba ka isa a
wani tsaya ana magana da kai, dalla ka bude da
wani bakinka duk gansa-kuka." Ya kuma hasala
dan dai bai ji abinda tace ba amman da alama
zaginsa take yi, dan haka ya bude ya futo da
wata zungureriyar bulalarsa yana muzurai. Ko a
jikinta bata ji ko dar ba don ba dabi'ar ta bace
tsoro, ta kuma ayyana a ranta wannan tsohon
ya tabata zai gane kurensa dan wallahi sai ta yi
masa sharri, ta kuma gyara tsayuwa. Ya hasala
matuka dan haka da zafin rai ya fara magana,
"Ke yarinya bana son rashin mutunci, don a
haife kin san na haife ki ko? Don haka ki bar
gurin nan tun ban zane ki ba." Ta yi masa kallon
baka isa ba sannan tace, "Ka ga Malam ni ba
wani abu ya kawo ni ba Mustafa nazo nema,
idan yana ciki kace masa Abu tana magana da
shi, ka daina mini surutu kana feshe ni da
yawu." Mamaki ya bayyana a kan fuskarsa, mai
ya hada Mustafa nutsatstsen yaro da wannan
hatsabibiyar yarinyar? Amman bai san alakarsu
ba, dan haka ya dan saki fuska ya ce, "Mustafa
fa kika ce?"
Ta motsa fuska tace, "Ko kana mamaki ne?" A
ransa yace, "Kai wannan yarinyar 'yar bala'i ce,
gwara ya lallaba ta su rabu lafiya. Don haka ya
kuma gyara tsayuwa ya fara kora mata bayani,
"Ai Alhaji Mustafa ya koma don daman hutu
yazo da kuma ciwon Babansa da ya tashi na
hanta, dan a can kasar waje yake karatunsa,
yau kwanansa shida da komawa, kuma ba shi
da ranar dawowa dan tun da ya tafi shekara
uku sai wannan karon ya dawo." Ta dafe kirji
cike da tashin hankali ta ce, "Yanzu ya tafi wata
kasar babu daman na ganshi dan Allah?" "Af! Ai
kuma sai kiyi, mutumin da aka ce miki bai kasar
gaba daya ma, kinga komawa ta ma." Ya koma
ya garkame kofar tasa. Kafarta ta yi mata nauyi
ta kasa dagawa, yanzu yaya zata yi da
rayuwarta? Don Mustafa ya koyar da ita darussa
masu wuyar mantawa, yanzu waye zai dinga
bata shandy tana sha? Waye zai dinga bata
tabar shaidan tana sha? Waye zai dinga kai ta
hotel taci kayan dadi ta hau gado mai laushi?,
waye zai dinga bata kudi mai yawa irin na
Mustafa? amsar ita ce babu, babu wanda zai
maye mata gurbin Mustafa ko ta ina. Da kyar
take iya gane hanyar da take sanya kafarta duk
hankalinta a tashe yake, don ma Allah ya
taimake ta ba wata tafiya bace mai nisa, da
kyar ta samu ta lallaba ta isa gidan dan zazzabi
da ciwon kai sun hadu sunyi mata taron dangi.
Bisa wata tabarma da ta tadda a tsakar gidan ta
zube, wacce Sala ta shimfida ta shiga kicin dora
sanwar dare, ta zauna idonta na zubar da
hawaye, azaba biyu take ji a jikinta gata rabuwa
da Mustafa ga kuma ta ciwon da ke addabarta,
ta zame ta kwanta ta kama juyi da malailaikuwa
a tsakar gidan tana kuka mai ciwo da taba rai.
Sala ta futo daga kicin dan ta dan huta, sai dai
mai zata gani? Abu ce 'yar lelenta tana birgima
a tsakar gida tana kuka dafe da kanta. Ta isa
gurin da sauri tana tambayar ta, "Abula diyar
kirki yaya aka yi? Bai hakura ba ne Mustafan?
Idan bai hakura ba ni sai naje da kaina na bashi
hakuri. Kwantar da hankalinki, banda abun dan
yau ma ai saurin fushi ba nasa bane ba, idan
yayi mana haka ai yayi mana tsiya, bari naje da
kaina na bashi hakuri ina ne gidan nasu?" Ta
mike tana neman gyalen da za ta yafa. Abu da
taga da gaske take yi ta ruko hannunta, ta juya
tana kallon ta amman ta gaza cewa komai, cikin
kuka Abun tace, "Kada ma kije Sala, ko kinje ba
zaki same shi ba don baya nan wai daman a
kasar waje yake karatu hutu ya zo, yanzu ya
koma yau kwanansa shida da komawa. Wayyo
Sala cikina zan mutu." Ta karasa maganar da
kuka tana rike ciki. Sala ta rude sosai ta ruko
hannun diyar tata tana mata sannu gami da
lallashinta tana fadin, "Kiyi hakuri Abula na san
zai dawo ya nemeki komai dadewa, domin ke
din mace ce da duk namijin da ya ganki sai ya
rude balle shi Mustafa da yake sonki, share
hawayenki ki daina kuka kinji Abula ta? Na san
zai dawo komai dadewa." "Ni fa cikina ne yake
mini ciwo. Wayyo Sala ciki....." Sai ga amai kyah!
kyah! kyah! Tana kwararawa. Sala ta kuma
rudewa ta mike da azama tana neman fo don
taimakawa diyar tata, tun tana yin amai na
abinci da ruwa har ta koma na majina take yi,
da kyar suka samu aman ya fada. Sala ta
taimaka mata ta raka ta bandaki dan ta wanke
jikinta, ita kuma ta dawo dan ta gyara gurin
zuciyar ta na cike da tsananin tausayin diyar
tata, dan ta gano ta fada kangin soyayyar
Mustafa.
Haka nan ta karasa yammacin a kwance ga juwa
da tashin zuciya dake damunta, daga karshe dai
Sala tace bari ta je gurin dan Oga ta karbo mata
magani ko aman ya tsaya. Tana isa dan oga ya
kama wage baki yana fadin, "A'a mana ne?
Sannu ka da zuwa. Ina Habu ne dan bana ganin
shi yanzu?." Sala tace, "Abu tana nan, yanzu ma
ita na zo na karbawa magani bata da lafiya." Ya
kuma wage baki yana fadin, "Habu babu lafiya?
Bari a bata magani mama, ka bari kudinka ma."
Ya kama hada magunguna bayan ya kammala
yayi mata bayanin yanda za'a sha kowanne, ta
amsa da azama ta nufi gida. Sanda ta sha
maganin kamar gaske dan aman