Showing 21001 words to 24000 words out of 44142 words

Chapter 8 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt

28 Dec 2024

1934

su
dakin gwajin jini. Ma'aikaciyar jinyar ta fara
magana, "Ina ta addu'ar Allah ya sanya daman
baku tafi ba, na dan tsaye bata lokaci ne dan
kada likitan ya gane ku na biyo. Ai shi na gaya
muku dan ka'ida ne ba ya zubar da ciki, yana
wani fama da gemu kamar gaske. Don ma bai
kama yi muku wa'azi ba, shi ya sanya sam
bama shiri da shi, amman daman ka'ida ce duk
asibitocin gwamnati ba'a zubar da ciki idan na
da matsala ba, sai dai zan taimake ku yanzu dan
kun bani tausayi, bai dace yarinya karama
kamar wannan rayuwarta ta lalace tun yanzu
ba." Fuskarsu ta fadada da fara'a Sala ta ce,
"Kai amman likita mun gode miki kuwa, Allah ya
sanya ki gama da duniya lafiya." Ma'aikaciyar
jinyar tace, "Amin." Sannan ta fara yi musu
kwatancen wani asibiti mai zaman kansa inda
za'a cire musu cikin. Sala ta dinga godiya kamar
ta kwanta don durkuso tana godiya.
Ma'aikaciyar jinyar ta ce, "Babu komai idan baku
gane ba dai ku fada mini, sai dai yanzu rana ta
yi gobe da sassafe za kuyi sammako kuje." Sala
tace, "Mun gane ma." Haka nan sukayi Sallama
suka tafi suna ta godiya. Daren ranar dai cikin
farin ciki suka kwana, sai zumudi suke yi gari ya
waye su tafi, dan abun da ya so tauye musu
farin cikin su ma da farko bai wuce rashin kudi
ba, sai dai da yake ance mai kadara ba
matsiyace bane, sai suka daga wasu kayansu na
sawa har da wani saitin dankunnen gwal wanda
Mustafa ya saiwa Abu suka kai kasuwar Rimi da
kasuwar 'yan tsaye suka saida, Cas suka amso
kudinsu, dan haka suka daina fargaba suka
kwana da farin ciki wanda rabon su dashi tun
ranar da suka ji Abu tana da cikin. Sai dai idan
za suyi magana kasa-kasa sukeyi dan sun lura
da Sadiku ya sanya musu ido, ko ma su kulle
kofar.
Da sassafe suka yi sammakon shiryawa suka
nufi kwatancen asibibin da Ma'aikaciyar jinyar
nan ta musu, basu wani sha wahala ba suka
gano a nan cikin Sabon gari yake. Sanda suka isa
suka cika da mamaki dan ganin wannan
Ma'aikaciyar ta jiya, ta tare su tana dariya tace,
"Kun gan ni anan ko? ai ina aiki anan ma sanda
bani da aiki a can. Dan haka ne ma ya sanya
nayi muku kwatancan nan din, kuzo muje gurin
likitan." Wani katon Inyamuri ne kansa da sanko
ya sha kot, idanuwansa jajir suke da alamun
shan taba a lebensa, ta cikin gilashinsa ya dinga
leken Abu yana wani lasar lebe. Cikin harshen
turanci Ma'aikaciyar jinyar ta yi masa bayani
duk abinda ke damun Abu. Ya yi dariya cikin
gurbatacciyar hausarsa ya ce, "O.k na gane,
Yarinya ka zauna mana." Yana magana yana
dubanta kamar maye. Duk rashin tsoro irin na
Abu sai da ta tsorata da ganin mutumin, dan
haka ta tsaya ta kasa zama. Sala ta dubeta da
kulawa tace, "Abula zauna mana, shine zai raba
ki da wannan kajagar da ke tare da ke." Ta
zauna tana cigaba da kallon sa har lokacin
hankalinta bai kwanta dashi ba. "Hajiya ciki wata
nawa take?" Ya tambayi Sala. Tace, "Ban sani ba
likita, sai dai ka duba ka gani." Ya Umurci Abu
da ta kwanta a wani gado da aka zagaye da
labule sannan ya shiga yayi mata awo. Sai da ya
kammala sannan ya fito ya dubi Sala ya ce,
"Hajiya yarinyarka tana da shiki na wata uku ne,
amman kada ka damu idan da akwai kudi za'a
cire shi yanzu." "Nawa ne kudin? Mun zo da
shi." Sala ta fada da saurinta. "Ka je can waje ka
biya za su gaya maka kudin." Sannan ya dubi
Abu yana fadin, "Ka sauko za muje da ke dakin
aikin yanzu." Sala ta je ta biya duk kudin da aka
caje ta suka bata takardar shaidar ta biya, duk
yawan kudin bata ji kyashin biya ba. Bayan ta
karba ta kai masa ya amsa ya karanta ya
umurci Abu da ta shiga wani daki ita kuma Sala
ta jira a can wajen shakatawa. Sai da ya sanya
ta tube kayanta sannan yace dole sai ya fara
kusantarta sannan zai mata aikin. Hankalin Abu
ya tashi matuka ta mike ta daura zaninta tana
masa wani duba na tsana da tsiwa ta ce,
"Sannu tsohon dan iska Bunsuru, bayan an biya
ka kudinka, to na fasa ai ba kai kadai bane mai
aikin ba, ka biya mu kudinmu mu tafi wani
gurin." Hankalin likitan ya tashi don ya kwadaita
da Abu dan ya jima bai yiwa yarinya karama
mai kyau da kyan sura irin tata aiki ba, dan
haka ya kwantar da kai da gurbatacciyar
hausarsa ya dinga lallashinta, amman fir Abu
taki yadda. Da dai ya ga ba zai shawo kanta ta
haka ba sai ya ce, shikenan ya fasa ta hau
gadon yayi mata aikin, bata yi musu ba ta
kwanta, tana ji ya zurkuda mata wata allura
wacce ko minti uku bata yi ba taji duk jikinta ya
mutu ko hannu ba zata iya dagawa ba, bakinta
ma ya kasa buduwa balle tayi magana, za mu
iya cewa tayi karamar suma ne,
Amman tana jin duk abinda yake faruwa sai dai
ba zata iya yin ko motsi ba dan allurar bacci
yayi mata da yake tana da karfin jini ya sanya
ba tayi baccin ba. Tana ji tana gani katon
Iyamirin likitan nan ya biya bukatarsa amman
bata da halin hanawa, sai da ya kammala dan
kansa sannan ya dauko kayan aiki ya fara yi
mata. Sanda ya tura karafunan da zai dagargaza
abinda ke cikin nata ji tayi kamar ana zare mata
rai dan azaba, amman ko motsi ba zata iya yi
ba, sai dai hawaye dake zubowa ta gefen
idonta. Shi kuwa katon kedarin ko a jikinsa, ya
sanya karfan ya burge abun da ke cikin kamar
yanda ake markada kayan miya, bayan ya gama
watso abinda ke cikin ya kuma sanya wani ruwa
mai magani ya fara wanke cikin, sai da ya
wanke shi tas sannan ya maida mata kafafunta
yanda suke. Azaba dai ta sha ta, hawaye sai da
ya jika gefen da take kwance, ajiyar zuciya kawai
take yi amman ba zata taba mantawa da
wannan azabar a rayuwarta ba har abada. Yayi
mata wasu allurai na rage radadi sannan ya tura
ta can dakin hutu, cikin dan kankanin lokaci duk
kamanninta sun sauya saboda tsabar azaba.
Sala ta isa kanta da sauri tana mata sannu
sanda aka sanar da ita an gama, sai a lokacin ta
sami bakin magana ta fashe da kuka mai ciwo.
Wannan Ma'aikaciyar jinyar ce ta shigo dakin
hannunta rike da magani ta yiwa Abu sannu
sannan ta ce, "Likita ya gama da ita babu komai
a cikinta dan haka nan da awa uku idan ta huta
zaku iya tafiyarku, sai dai Hajiya daga yau sai ku
daina sakaci ciki yana shigar 'ya'yanku, don ke
Zainabu yanzu kin ji azabar da kika sha, dan
haka gwara ku dinga rigakafi kafin ciki ya shiga."
Sala ta dube ta da mamaki tana fadin, "Dakta
yanzu akwai wani abu dake hana daukar ciki
dama?" Ma'aikaciyar jinyar ta ce, "Eh akwai
mana, allura ce da magani har da kulle mahaifa
ana yi, in mace tayi daya daga cikinsu ba zata
sami ciki ba." Sala ta amshe cike da mamaki a
fuskarta, "Oh! Ni Salamatu ki ji wata fasaha,
rashin sani yafi dare duhu, da mun sani da
yaushe za mu sha wannan wahalar? Kin ji fa
Abula." (Sala ba ta ji tsoron Allah ko yin nadama
da abin da ya sami Abu ba, ba ta hankalta da
isharar da Allah ya nuna musu ba har take
neman hanyar da diyar ta ba za ta kuma yin ciki
ba, hakan ke nuna daman tashin hankalin da
suka shiga na samun ciki ne ba na gyaruwar
zuciya ba. Menene amfanin irin wadannan
iyaye? Kai, tir! Da su, domin su ne tushen
gurbacewar al'umma a ganina).
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ma'aikaciyar jinyar ta yi ta musu bayani, Sala
tana ta girgiza kai cike da mamaki, ita kam Abu
ita kadai ta san abunda take ji, sai dai tana jin
dadin bayanin likitar, ta kuma yi alkawarin ba
zata kuma samun ciki ba, yanzu ma rashin sani
ne. "To, yanzu likita a ina ake samun maganin
tsarin iyalin?" Sala ta tambaya. Sister din tace,
"Ai ana samu a duk asibitocin da kika je, sai dai
su asibitin gwamnati suna da ka'ida, basu
bayarwa sai matan aure, ko kuma idan kinje da
mijinki, har wasu masu zaman kan nasu ma
akwai wadanda ba sa zubar da ciki saboda
rakiyar asara, amman kin ga mu nan babu
ruwanmu za ki iya zuwa ki siya ko a chemist
dina." Sala ta ce, "Kai likita mun gode da
wannan kirkin naki." Ta yi murmushu ta ce,
"Suna na Sister Asibi, ko da wata rana kunzo
neman wani taimako,ta yi musu kwatancen
gidanta ta tafi ta barsu cike da murna, dan
itama tana da nata kason, don ka'idar asibitin
nasu idan mara lafiya ya zo ta sanadiyyar ka
kana da kaso mai tsoka musamman ma zubar
da ciki. Karfe biyar suka koma gida, shatar mota
ma suka dauka, da kyar Abu take iya taka
kafarta, san da suka isa jama'a na ta kallonsu,
masu zargi na yi masu addu'a kuma na yi, da
haka suka shige gida. Da suka isa daki suka baje
Sala ta dauko naman da suka yo tsaraba da shi
suna ci suna mayar da yanda aka yi suna ta
dariya ta abunda suka dinga yi jiya har da
kukansu. Ita kuma Abu sai baiwa Sala labarin
irin azabar da tasha take yi. Sala ta ce, "Ai an
gama, da kin samu kwarin jikinki zamu koma su
yi miki allurar da suka ce din, tunda dai duniyar
ta sauya gwara mu fizgi rabonmu muma, dan
na san idan kika murje kika goge, Alhazan birni
ne zasu yo miki caaa, tun da dai kina da kyau
da sura mai daukar hankali." Suka kwashe da
dariya har da shewa. Sadiku da duk maganar da
suke yi a cikin kunnansa ya daga labulan ransa
a bace hankalinsa a tsananin tashe, nan fa suka
yi tsamo-tsamo kamar wadanda aka watsawa
ruwa, cikinsu aka rasa ko mai tari balle su yi
magana, dan daga ganin fuskarsa sun san ya ji
duk abin da suka ce. Shaf! sun manta basu rufe
kofa ba, ko su yi a hankali ba. Da kyar ya iya
bude bakinsa cike da takaici ya ce, "Sala yanzu
tsakaninki da Mahaliccinki Ubangijin da ya
halicce ki kun kyauta abinda kuka yi? ko tsoron
Abu ta rasa ranta a gurin zubar da cikin nan
baki yi ba, daman tun ranar da na ga kin gigice
na yi zargin wani abu na shirin faruwa koma ya
faru, na yi iyakacin iyawata a kan tarbiyyar
yarinyar nan har kina jin haushina. Sannan
wannan abu da ya faru bai zame muku ishara
ba sai ma kara kangarewa da Abu ta yi? Shin
Sala kun san sanda zaku mutu? Ba kwa tsoron
Allah? Ba kwa tunanin Ubangiji ya dauki
rayuwarku kuna cikin wannan mummunan
sabon? Da nayi niyyar fita daga harkarku sai dai
ya zama dole na tunatar da ku gaskiya koda
kuwa zaku tsireni ne nauyi ne a kaina, tunda shi
Babanmu ya gaza. Sannan ke Abu azabar da
kika sha ba zata zame miki ishara ba? dan bata
kai kashi daya cikin dubu ta azabar lahira ba,
dan haka ki hankalta ki san..." "Kai! Ya isa haka
malam." Sala ta katse shi. Ta dora da cewar,
"Ka wani saka mu a gaba kana mana surutu
mara ma'ana sai kace wasu 'ya'yanka, idan
aljannar ta ubanka ce ka hana mu shiga, sannan
idan kace za'a yiwa Abu azaba dan tayi ciki shi
kuma mai saka ido sana'ar da babu uwa babu
riba yaya za'a yi dashi? Ka saka mana ido
kamar wani Ubanmu, wallahi ba dan a tsakar
dakin nan na haife ka ba da asibiti ne sai nace
musanya miki kai aka yi, dan baka kaunarmu ka
tsane mu, to ta Allah ba taka ba dan saka ido."
Yayi wani murmushi mai cike da takaici yace,
"Sala ina kaunarku a matsayin wadanda bani da
kamarsu a duniya, wannan ya sanya ni nake
gaya muku gaskiya, dan wanda baya kaunarka
bai gaya maka gaskiya.......Malam ka ishe mu
haka, ba'a san gaskiyar taka soko shashasha,
har ni zaka ce zaka gayawa gaskiya? Tun kafin a
haife ka na san gaskiya. Bace min da gani tun
ban daga maka nono kabi duniya ba." Ya saki
labulen jikinsa sanyi kalau zuciyarsa tana suya.
Abu tace, "Sala kiyi masa kashedi kada yaje yayi
ta fadi a duniya yace nayi cikin shege mun
zubar." "Hakane fa." Sala ta fadi da sauri ta
daga labulan tana fadin, "To, saura naji wannan
maganar a bakin wani, ranka zaiyi mummunan
baci Sa'idini, sarkin sa-ido." Shi dai baice komai
ba don ko juyawa ma baiyi ba ya cigaba da
tafiyarsa ransa yana cigaba da suya. Sala kuwa
cigaba tayi da balbalin bala'inta tana fadin,
"Haka kawai an saka wa yarinya ido dan anga
Allah ya bata kirar da zataji dadin rayuwarta,
dan haka babu ruwan uban kowa koda sadaka
take bada kanta balle ma da makudan kudi
ne." (Ubangiji ya shirya mu har wadanda suka
bata, mu gane gaskiya kuma ya bamu ikon
binta, Amin).Ku ziyarci blog dinmu domin
karanta Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
KANO: 15/5/2003
Kyakykyawar budurwa fara tas, sai dai bata cika
tsawo ba dan haka koda yaushe zaka ganta da
dogon takalmi,ba ta da gashi mai tsaho amman
akwai yawan gyara shi, tana da dogon hanci
wanda ya fito da ainihin kyawunta, bakinta
kuwa irin dan karamin nan ne kamar na yara,
sai idanuwanta wadanda ke ruda 'yan maza duk
sanda ta kalle su da shi saboda girmansu da
kuma kyansu, har wata digon zaiba ce a ciki, ga
ta da dan karan yanga da iya kwalliya,
wadannan abubuwan suka hadu suka maida ta
irin matan da zamani ke yayi. Tana sanye da
riga da siket na atamfa wanda ya matse ta
tsam-tsam daga kugunta, 'yar kibarta ta yi cas-
cas cikin kayan, fatar jikinta na da laushi tamkar
'yar jaririya, tana sanye da katon takalmi mai
kama da tsani don tsaho, fuskar nan tasha ado
irin na wayayyu, sai ta shafa jambaki kalar
kayan jikinta, bata sanya kwalli ba, sai dai ta
zizara jagira cikin idon nata, gashin girarta ya
kwanta luf-luf gwanin sha'awa, daga yanayin
shigarta da tafiyarta kadai ya isa ya yaudaro
'yan maza dan duk inda Zainabu ta bi sai an
kalle ta. Kayanta kalar katuwar jakarta ce, ga
wani kamshi da ke tashi a jikinta kamar kana
kantin sai da turare, tana da matukar fizgar
hankalin duk wanda ya dora idonsa a kanta,
sannan hatsabibiya ce ta fannin mu'amala,
domin ta kware ainun a iyar tafiyar da namiji
don haka duk mutumin da ya kusance ta ko sau
guda ne sai ya kidima a kanta. Ta fito daga
dakin nata bakinta sanye da wata alawa mai
tsananin kamshi tana tsotsa, Sala dake shan
kayan marmari wanda Zainabun ta kawo musu
tsaraba jiya da ta dawo daga Abuja, zaune ta
bararraje a tsakar gida tana kallon Zainabu, duk
da ranta a bace yake sai da ta yi murmushi dan
ganin yanda Zainabu taci uwar kwalliya, tana
dubanta da fara'a tana fadin, "A'a 'yar albarka
kin fito? Sannu da fitowa." Zainabu ta yamutsa
fuska gami da amsawa. Salan tace, "Jiya na so
muyi maganar yarinyar nan sai naga kin dawo a
gajiye, ga shi kun yo dare....." "Wani Abu ne
kuma ya faruwa?" Zainabu ta katse Sala din
(don yanzu ta tashi daga Abu ta koma
Zainabunta). "A'a a kan dai maganar nan ce ta
kwanaki ta matsiyacin yaron nan da ta nacewa,
shi kuma wannan yaron dan saka ido yana ziga
ta kamar shine uwarta, to yanzu wai iyayansu za
su aiko, ni kam sam ba na son tayi auren nan,
me take da shi? Ita ko sha'awarki bata yi, koda
yake ko ba tayi auran ba ma bata da wani
amfani tunda ta ki yarda ta ciwo arziki, dan
haka sai kiga shegiyar tayi sati biyu bata da ko
kwandala, sai dai idan an yi musu albashi ya
sanmata, wanda duka albashin nasa bai wuce
kudin takalmi da jakarki ba."Zainabu ta yamutsa
fuska tana fadin, "Sala ki barta ta yi auran nan
taji, in dai Maza ne ai zata gane kurenta, banza
ana neman a samo mata mai maiko tun da ta
nace sai tayi auren tana ki tana wani rawar kai,
ki rabu da ita kawai, dan rannan baki ga wani
abokin Alhaji T.J ba yanda ya mato a kanta, har
na nuna masa ya rabu da ita kanwata ce, sai ya
rantse mini da cewar shi da aure yake sonta,
amman babu yanda banyi ba yarinyar nan ba
taki ko kula shi, haka ya hakura ya kyale ta don
ya yi-ya yi ya gaji, shi da mata ke sonsa kamar
me? Shine fa kwanaki ya bani kujerar Makka
guda ukun nan da na kai ku ke da Baba."
"La'ilaha Illallahu, kai amman yarinyar nan bata
da rabo, arziki yana kiranta tsiya tana janye ta,
ina ga fa matsa mata zamuyi ta aure shi kawai
ko ta tsiya ko ta dadi." "A'a Sala ina ruwanmu?
Ita ce fa zata zauna da mijinta, sannan yanzu
idan muka hada su haushinmu zata dinga ji,
gwara mu kyale ta ta yi hankali, ni bari na wuce
kada na yi latti, kin san nace miki muna da bikin
cikar Asma shekara ashirin da biyar, zan je mu
fara shiri saboda shi na dawo jiya." "To-to, Allah
ya kiyaye, zaki dauki shatar mota ne?" Zainabu
tace, "A'a Alhaji Danlami sabon kudi yana waje
yana jirana." "To Allah ya tsare, ya bada sa'a."
Tace, "Amin." Gami da ficewa. Yana cikin mota
zaune ya sha manyan kaya kamar wani
mutumin arziki, tunda ta fito ya zuba mata ido
tamkar maye, ita kuma tana tafiya tana rangaji
tamkar ganyen bishiyar da iska ke kadawa,
tafiyar dake dauke hankalin 'yan maza. Tana
isowa ya bude mata kofa yana murmushi gami
da fadin, "Barka da warhaka Hajiya, irin wannan
shanyar haka har na bushe?" Tayi wata
mayaudariyar dariya ta jan hankali, tace, "Lallai
kam, to waye ya gayyace ka? Ina ga kaine fa ka
sakani fitar nan, da ka gaji ba sai ka tafi abinka
ba na huta." Ya kanne ido yana mata wani kallo
yace, "Ni na isa? ai kina da tsayawa mutum a rai
Zainabu, kusan duk aikin da nake fa idan kika
fado mini bani samun sauran sukuni muddin
ban iso gareki na ji duminki ba, ko matana na
kasa zama da su kamar ke, anya Zainabu kina
tausaya mini kuwa? Dan Allah ki daure ki aure
ni mana ko na sami nutsuwa." Tayi masa wani
malalacin kallo ba tare da tace komai ba ta
kauda kai gefe, ya kuma rudewa ya matsa kusa
da ita jikinsa har rawa yake yi. Ta kuma
matsawa gefe tana harararsa gami da fadin,
"Haba Malam, ko dai dan bunsuru ne ka
saurara mu bar kofar gidan ubana da kuma
tsakiyar ranar nan, duk iskancina ban taba yi a
kofar gidan ubana dan ina mutunta gidan." Ya
ja baya yana shafa haba yace, "Kai Zainabu kina
juya ni wallahi kamar waina, amman babu
komai zan matsa lamba har ki zama mallakina."
Ya tada motar yana ta sumbatunsa, ita kuma
murmushi kawai take yi, ta gama kashe shi da
kissarta da kallonta gami da tsananin kamshinta.
Sai da ya kaita wani babban gidansa na
shakatawa suka gama watsewarsu sannan ya
cika mata jaka da kudi dan ya san Zainabu mai
tsada ce, sannan suka dauki hanyar gidan
Asma, har lokacin yana ta sumbatu a kanta da
yaba kyanta da iya mu'amalarta. Sanda suka isa
gidan Asma ya kwantar da murya kamar wani
abun tausayi ya ce, "Yaya dai Hajiya, karfe nawa
zan dawo na dauke ki?"
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta galla masa harara tana fadin, "Kai fa tsiyata
da kai kenan ba ka iya cin kwan makauniya ba,
to ai ni din ba matarka bace da zaka hana ni
sakewa." Ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login