Showing 36001 words to 39000 words out of 44142 words

Chapter 13 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt

28 Dec 2024

1942

ya ce a baki kya
sha ruwa kafin yazo bada hakuri da kansa." Sala
ta fashe da wata wawiyar dariya sannan ta ce,
"Kayya ki gaya masa ya kwantar da hankalin sa
komai ai ya wuce gashi kin ce daman ba laifinsa
ba ne." Ita dai Zainabu daki ta shige domin tayi
baccin gajiyar kwanakin da bata yi ba can baya,
kafin yamma tayi su hadu da zuman nata
************
Cikin kwanaki kalilan soyayya da shakuwa ta
kuma shiga tsakanin su, duk da suna rikici duk
lokacin da Mustafa ya ga Zainabu da wasu
Musamman Alhaji.... Dan haka duk inda tasan
zata gamu da samarin ta kan guje masa don
bata son ace kullum suna samun sabani da
Mustafa dan yana da matukar kishi, su kuma
sun gaza hakuri dan duk kusan namijin da ya
fara mu'amala da Zainabu bai iya daina wa dan
ta fiye fitina da yawa, sai dai idan Allah ne ya
kwato shi daga hannunta. Shi kam Mustafa
kullum hankalin sa a tashe yake dan bai kaunar
ya ga Zainabu da wani, dan haka nema suka
yanke shawarar yin aure a wannan lokacin. Shi
kam yana shakkar tinkarar Momin sa da
maganar auren nasa don ya san ta bata san
wargi sam ita, ga shi daman kullum tana masa
maganar ya zabo mace cikin 'yan matan gidan
ko kuma ya duba cikin 'yan uwa masu tarbiyya
dan bata son yayi zaben tumin dare, sai dai shi
a iyakacin ganinsa daga 'yan matan dake cikin
danginsu har na waje bai ga wacce tayi masa
kamar Zainabunsa ba. Yau ya tadda Momin
nasa a karamin falo, 'yan matan ta suna
karamin falo suna kallo sai musu a keyi tsakanin
'yan matan, don gidan nasu bai rabo da 'yan
mata na 'yan uwa dan su basu da yawa su biyu
ne kacal, gashi Momin su tana da son jama'a
dan haka koda yaushe gidan a cike yake banda
masu zama dindindin, banda kuma wadanda
aka aurar, dan haka tunda ya ga take-taken
Momin na su na son ta hadashi da wata a
cikinsu shi ya sanya ba ko da yaushe yake sakar
musu fuska ba. Ya shiga falon da sallama, ita
kadai ce don ya baro Alhajinsu a falo da baki, ya
isa gaban ta ya gaishe ta, sannan ya koma
babbar kujera ya zauna, ya dubi tibin inda yaga
hankalinta ya karkata. Yakin Falastinawa ne dai
da Isra'ilawa wadanda kanwa uwar gami
America ke daurewa gindi, ana nunowa a tashar
C.N.N. "Kai wadannan mutanen wallahi
azzalumai ne, ka dubi yanda suke kashe farar
hula da basu ji ba basu gani ba, sannan su yi
farofagandar basa taba farar hula, Allah dai ya
bi musu hakkinsu kuma ya nuna musu karshen
su, Amin." Hajiya Kubra ke fada da bacin rai.
Mustafa ya ce, "Haka ne Momi, sai dai idan kika
duba daman can zaki ga abun nasu bawai suna
yi bane don wani abu sai don su yaki addinin
musulunci kawai, yanzu fa idan kika shiga
kasashen turawa da gemu sai kaga an mai da
kai wani abin tsoro saboda sunyi farofagandar
batawa musulmi suna a idon duniya, dan ma
yanzu Allah yana nuna musu ishara mutanan su
turawa sai musulunta suke, musamman
matansu kamar su Kristian Barkeu da 'yar uwar
tsohon shugaban kasar Birtaniya Tony Blair,
Laurent Bothh wacce ma'aikaciyar jarida ce, da
sauransu, shine fa muke dan samun sassauci a
gurinsu, abun nasu dai sai addu'a." Ta amsa da
"Amin, ina wai ka shiga ne?, tun da safe nake
saka rai da shigowarka amman shiru." Gabansa
ya fadi, don yanzu sam bai zama a gida kullum
suna makale da Zainabunsa, amman sai ya
dake ya ce, "Momi kin san ina fafutukar fara
aikin tun da sun bani (offer), takardar daukar
aiki, shi ya sanya yanzu bana zama." Ta ce,
"Lallai kam haka ne, Allah dai ya taimaka ya
sanya a fara a sa'a." Ya ce, "Amin." Sannan ya
kama inda-inda don ya rasa ta yanda zai gaya
mata. Hajiya Kubra ta dube shi tana dariya tace,
"Babana duk yanda aka yi da magana a bakin
nan naka." Da yake sunan Baban ta ne da shi.
Ya yi murmushi yana sosa keya ya ce, "Momi
sirika na yi miki shine nake kunyar sanar da
ke."tayi dan murmushi dan ba hakan taso ba
taso ace anyi 'yar gida, amman sai ta danne
dan tana son yayi auren, dan haka tace, "Lallai
kam kace yau zanyi kwanan farin ciki, a ina ka
samo matar taka ko a can American ne?" Yayi
dariya ya ce, "A'a Momi a can dai unguwar da
muka taso take, can kasan layinmu na da,
sunan ta Zainabu." Ta ce, "Lallai kam, Allah ya
tabbatar mana. Waye kuma Babanta, a wane
gida take ne ma?" Da sauri ya ce, "Sunansa
Malam Abubakar." Tace, ai shike nan bari Alhaji
ya shigo sai a sanar da shi, amman dani na so
ace cikin 'yan uwanka da suke gidan nan ka
zaba, amman tunda Allah ya kaddara matar
taka a waje take ba zamu ja da ikon Allah ba,
sai dai muyi addu'a Allah ya tabbatar mana da
alkhairi kawai. Ya ji dadin abunda ta ce, yayi
mamakin kuma saurin shawo kanta da ya yi,
duk da saurin daukar zafin ta. Daga nan suka
cigaba da hirar su a cikin hirar nema take cewa
tana fatan zainabun tasa mai hankali ce da
nutsuwa. Ya ce, "Momi ko ke kika ga Zainabu sai
kinyi sha'awarta, ta kammala diplomarta yanzu
haka tana aiki ne." Tace, "To ai shike nan, na
san dai sai Baban ku ya sanya anyi masa bincike
don kada ayi zaban tumun dare." Kirjinsa ya
bada ras-ras, amman dai ya dake yace, "Na san
ma babu wani aibu da zai tadda ga Zainabu in
dai ya sanya mutanan kirki a binciken ba
munafukai ba." Tun daga sannan ya ji hirar ta
fita daga ransa gaba daya, don bai san irin
abinda za'a ce akan Zainabunsa ba, shi kam yaji
ya gani dan haka koma me zai faru sai dai ya
faru amman shi dai da ikon Allah sai ya aure ta.
Da haka yabar dakin mahaifiyar tasa ya nufi na
shi, amman yana cike da tunanin abunda zai
biyo baya idan suka san wacece Zainabu.
Kwanaki biyu shiru babu wanda yace masa ko
kala akan maganar, shi kam ya damu kwarai ya
ji anyi masa zancan, dan Baban sa ma da suka
yi maganar da Hajiya Kubran abinda ta fadi ya
maimaita, cewar zai sanya ayi masa bincike
sosai. Ya sami wani tsohon abokinsa acan
unguwar da suka taso ya ce don Allah ya bashi
amana ya binciko masa labarin wata yarinya
Zainabu diyar Malam Abubakar kamar yanda
aka ce masa, sai dai abokin nasa ya dan sami
matsala da farko dan duk wanda yace wa sun
san Zainabu diyar Malam Abubakar sai suce
gaskiya basu san taba, mutum hudu ya tambaya
amman duk ba'a dace ba. Sai da ya isa
majalisar da yake zama ya fara kawo maganar
neman Zainabu da yake yi, sai wani cikin
abokan hirar tashi yace, "Ko dai Zainabu diyar
Baba Abbakar mutumin Sudan din nan ake nufi,
in dai itace kuwa bai yi mata ba, domin dai
kowa yasan karuwar gida ce, duk da babu kyau
suka akan maganar aure amman tunda dai
amana ya baka sai ka sanar da shi gaskiya in
dai ita ce din, da dai kanwarta da aka yiwa aure
kwanaki ce ma da sauki dan ba halinsu daya
ba." Nan suka hau sanar dashi irin halinta dan
gaskiya shi ma'aikacine bai fiye zama ba sai
karshen sati kuma yawanci hirar siyasa suke yi
da matsalar da kasar ke ciki. Ba shi da wani ja
Zainabu diyar Baba Abbakar ce dai dan abokinsa
yake nema, dan haka ya je ya sanar dashi
yanda suka yi, daga karshe har kofar gidan su
Zainabun suka zo tare ya nuna masa. Haka nan
Alhaji Abdullahi ya koma gida jikin sa sanyi
kalau, domin dai ya tabbatar da lallai itace
wacce dansa ke so, shi kuwa duniya sam bai san
ya takurawa dan sa, yaso ace Zainabu da dan
sa yake so ta kasance kamila ce ba lalatacciya
ba, kafin ya shiga sallar Magariba ya kirawo
wayar Mustafa yace lallai idan an idar da sallah
yana son ganinsa,babu bata lokaci Mustafa ya
iso gidan dan kusan tare ma suka yi sallar Isha'i
da Baban nasa, ya dade a raka'ar karshe yana
addu'ar Allah ya sanya Zainabu ta zama
rabonsa, don yaji muryar Mahaifinsa kamar da
zafi shi ya sanya duk ya kidime. Ya riga Baban
nasa shiga gida, Momin nasa ta zuba masa
abinci amman ya gaza ci duk da uwar yunwar
dake addabarsa, dan kada ma Momi ta zargi
wani abu ya sanya ya dinga tsakurar kadan
yana ci har ma taso ta gane. Ta dubeshi da
kulawa ta ce, "Baba anya wani abu baya damun
ka? Na ga kwana biyu duk ka wani shiririce,
balle yanzu ka gaza cin abinci sai tunani." Ya
kakalo murmushi yana fadin, "Laaa! Momi me
kika gani? Babu komai gajiya ce dai kawai."
Ganin tana son ta gano shine ya sanya ya saki
jikinsa yaci abincin sosai, har Baban nasa ya
shigo, ya shige sashinsa ya kira Hajiya Kubra ta
wayar gida (land line) ya ce, "Baba ya shigo ne?
Idan ya shigo kuzo tare ke da shi." Ta amsa da
"Ya shigo, ga munan zuwa." Bayan ta ajiye
wayar ta dube shi duk ya sha jinin jikinsa ta ce,
"Alhaji yana kiranka." Sannan ta mike ta nufi
sashin Maigidan nata yana biye da ita a baya
har suka isa. Mustafa bai zauna akan kujera ba
a kasa ya zauna ya sunkuyar da kansa yana
gaida Baban nasa, fuskar sa babu annuri yake
amsawa, ba kamar yanda ya saba amsa masa
da sakin fuska ba, hakan ne ma ya sanya gaban
Mustafa ya cigaba da faduwa dan yana ganin
lallai wani abu yana shirin faruwa. Sun jima a
haka yana cigaba da duba jaridar leadership da
suka taddashi yana dubawa, labarin ya dauke
masa hankali wanda aka ce wai waye ya haifi
Obasanjo, sai da ya karasa shafin da yake
sannan ya daga kai yana duban Mustafa kur da
idonsa, abinda ya kuma fadar da gaban
Mustafa. Can ya daure ya ce, "Baba ka ce
yarinyar da kake nema acan kasan layin da
muka taso take har ma ta kammala karatunra a
F.C.E ko?" Bakinsa yana rawa yace, "Haka ne
Baba." Alhaji Abdullahi ya kuma gyara zama ya
ce, "To nayi bincike kamar yadda addini ya
umurci muyi a duk sanda aka tashi neman aure,
sai dai abun takaici duk mutanen da aka
tambaya wadanda ba zasu yi karya ba sun
sanar dani ko wacece Zainabu, dan haka sam
ban yarda da tarbiyyar ta ba da ta gidansu ba
ma gaba daya, don haka kaje ka nemo wata, ba
zan maka auren dole ba amman ya dace ace ka
samo mace mai mutunci da daraja a idon
duniya." Hankalin Mustafa ya yi mugun tashi
ransa ya baci, makwallaton sa sai kaiwa da
komowa yake yi, duk da sanyin A.C da fankar
dake dakin basu hana shi yin gumi ba, da kyar
ya iya bude bakin sa yace, "Baba kayi hakuri
bawai zan maka musu bane, ni na san Zainabu
diyar kirki ce, ka san halin mutanan yanzu ba
duka ne ke fadar gaskiya ba, dan haka ma
yanzu idan za'a yi aure ba'a cika zuwa a
tambayi mutanen unguwa ba, dan basu kaunar
wani ya cigaba, dan haka nasan zasu iya yiwa
Zainabu sharri dan haka ina neman yardarka
akan na auri Zainabu, watakilama ba wacce
nake so aka gaya maka ba." Alhaji Abdullahi yayi
dariya dan shi yana da hakuri da bin komai a
sannu ba kamar Hajiya Kubra ba mai saurin
daukar zafi ba da saurin fushi, sannan ya ce,
"Baba bana shakkar ba Zainabun da kake nema
aka sanar dani ba, amman bari nayi maka wasu
tambayoyi idan har ba ita bace shike nan." Ya
goge zufar dake tsats-tsafo masa ba tare da ya
iya cewa komai ba Baban nasa ya fara jeho
masa tambaya"Asali Abu ake ce mata sanda
tana yarinya, yanzu ne ake ce mata Zainabu
ko?" Ya ce, "Haka ne." "Kuma da can tana tallar
abinci da gyada da dai sauransu ko?" Ya hadiyi
wani yawu dan dai ya san lallai Baban nasa ita
ya gano, da kyar ya iya cewa, "Haka ne." "Tana
da wani Yaya mai suna Sadiku wanda shi ba irin
halinta gare shi ba, da kuma wata kanwarta da
aka yi mata aure kwanaki ba ko?" Yayi shiru bai
bada wannan amsar ba dan dai ya san Babansa
yayi bincike matuka akan Zainabu. Alhaji
Abdullahi ya cigaba da bayanin sa duk da bai
bashi amsa ba, "Babanta mutumin Sudan ne,
sunan shi Baba Abbakar, kuma ana kiran
Babarta da Sala....." "La'ilaha Illallahu! Yanzu
wannan karuwar yarinyar kake so Baba?" Hajiya
Kubra ta amshe zancen tun bai kai ga bada
amsa ba. Jikin sa ya kama rawa da rawar murya
ya ce, "Momi ba karuwa bace, don dai tana
aikine a (Local Govt.) ne shi ya sanya ake mata
kallon 'yar iska, wallahi ina sonta Baba kayi
hakuri don Allah, sharri kawai aka yi mata."
Hajiya Kubra ta amshe, "Sharrin gidan Uwar wa?
Ai ni sai yanzu ma na gane da ka fadi sunan
Mahaifinta Abbakar da sunan Babarta, yarinyar
da tun tana 'yar labubuwarta take iskanci, har
ciki aka zubar mata tana da shekara sha hudu a
duniya." Mustafa ya ce, "Kin ji ba Momi, sharri
ne aka yi mata dan ana....." "Sharrin Uwarka? to
tsaya ka ji na sanar da kai, na san Zainabu
shekarun da suka wuce, yarinya ce mara
mutunci kuma mara kunya dakikiya, ta addabi
kowa, duk wannan lami ne ma akan iskancin da
take yi." Ta dubi mijin nata tana magana, "Alhaji
idan baka manta ba na taba baka labarin wata
'yar iskar yarinya shekarun baya da tayi mini
rashin kunya har cikin Ofis dina, lokacin ina
makarantar 'yan mata ta Dala (G.G.C DALA), dan
ranar da tayi mini rashin mutuncin nan kasa
bacci nayi, don har sai da jinina ya hau, har yau
ina addu'ar Allah ya hadani da yarinyar nan
nayi mata rashin mutunci amman har yau Allah
bai hada mu ba, sai daga baya ma na ji 'yar
unguwar da muka baro ce a bakin wata 'yar
ajinsu, sai yanzu zaka ce kana son ta wai kuma
da aure ma? Ai ko da ku biyu kuka rage a
duniyar nan ba zaka aure ta ba muddin ina
raye." Ya dafe kansa idonsa ya kada yayi jajir
yana fadin, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un."
Dan ya riga ya gano Momi ta san komai, ta san
Zainabu farin sani, ashe ita ce wacce take bashi
labari din nan, sai dai ya rasa ta yaya zai sanar
da su wannan cikin da take tsanar Zainabu
saboda shi dan ta ne yayi shi, ta yaya zai ganar
da su shine ya fara lalata Zainabu tun a wancan
lokacin da take zarginta, duk da ya tadda
Zainabu da wasu muggan halaye amman shine
ya koyar da ita kashi saba'in cikin dari. Ya yi
tsamo-tsamo da shi kamar wanda kaza ta
fashewa a cikin sa, bashi da damar da zai kuma
musa musu abinda suka fadi, don idan yace na
Babansa sharri ne to na Momin sa fa wanda
Zainabu da bakin ta ma ta bashi labari, a sanda
take bashi labarin bai yi zaton Mahaifiyarsa bace
dan shi ko tambayar ta makarantar da take bai
taba yi ba balle har ya gano hakan ba. Alhaji
Abdllahi ya katse masa tunaninsa ta hanyar
fadin, "Baba ka sani ba wai muna kin Zainabi
akan kanta bane, A'a muna kin Zainabu saboda
halinta, don babu wanda zai so ace yau ya hada
zuri'a da lalatacce, da ace irin halin kanwarta
gareta babu abinda zai hana mu kyaleka ka
aure ta, dan haka ina baka shawara da lallai ka
koma ka sake nemo matar aure dan wannan
bata yi ba."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347


Zaharaddeen Shomar
Whatsapp 08168575100






Idan Zuciya Tagyaru1-05
Posted by ANaM Dorayi on 08:00 PM, 03-Feb-16
Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU
_____________ Na
________Fauziyya D Sulaiman_____
"Yo to banda abunsa ma a gidan nan wacce irin
mace ce babu kuma masu tarbiyya da kyau idan
ma shine ya rufe masa ido, don haka ka kwantar
da hankalinka ka zabi wacce ta dace da kai duk
'yan uwanka ne." Alhaji Abdullahi ya amshe, "Ki
na ji Kubra, ba wai dole sai anan gidan zai zabi
mata ba don zai iya yiwuwa bai ga wacce ta dace
da ra'ayinsa ba, ya je ko ina ya samo mata in dai
diyar musulunci ce kuma mai tarbiyya." Shi kam
duk bai fahimtar duk abinda suke fada don sam
hankalinsa baya jikin sa, ji yake kamar ya dora
hannu a kansa yayi ta zunduma ihu kawai ko ya
ji sanyi a ransa. Alhajin na sa ya ce, "Ka tashi ka
tafi Allah ya zaba maka abinda yafi zama
alkhairi." Ya mike da kyar yake iya daga kafarsa
yana hada hanya tamkar wanda ya sha giya ko
kwayar sanya maye, idanuwansa sun kada sun yi
jajir da su kamar gauta, har ya fice basu ce
komai ba illa binsa kawai da suka yi da kallo.
Hajiya Kubra ta ja tsaki tana fadin, "'Ya'yan yau
ba'a iya musu, banda haka daga ganin yarinya
baka san halin ta ba ka dage sai ka aure ta, ni
abun ma mamaki yake ba ni, yaushe har ya
dawo garin nan suka kulla soyayya da
hatsabibiyar yarinyar nan har ta dauke masa
hankali haka? Duka baiyi ko cikakkaken wata
guda a garin nan ba, ni ko bayan raina ba zan so
ya auri diyar nan ba, Wallahi Alhaji dan baka san
ta bane sam bata da kunya da ladabi ko miskala
zarratin, tuntuni na tsaneta wallahi." Alhaji
Abdullahi ya kuma gyara zama cike da tashin
hankali dan dai yana tausayin dan sa, don ya
gane ba karamin so yake yiwa Zainabu ba ya ce,
"Ai haka Allah yake ikonsa, shi kadai yasan a inda
suka hadu, sai dai muyi masa addu'ar samun
mace ta gari, da addu'ar ita kuma Allah ya shirya
ta." Hajiya Kubra ta ce, "Amin dai." Shi kam
Mustafa da kyar ya iya kai kansa sashinsa saboda
tsananin tashin hankalin da yake ciki, dan Allah
ya sani duk duniya baya ga iyayansa babu
abinda yake so sama da Zainabu, ya sani
Zainabu wata tsoka ce a cikin jikinsa mai yawo da
jininsa, a da can baya yana daukar son Zainabu
shirme kuma shiririta a zuciyarsa, sai dai a yanzu
ya sani muddin bai auri Zainabu ba lallai kam
rayuwarsa tana tare da hatsari. Ya kwanta
rigingine a gadonsa ya rintse idonsa, ina ma zai
iya kuka da lallai yayi ko ya sami sassauci a cikin
zuciyarsa. "Zainabu! Zainabu!" Ya fadi a hankali
ko ya ji sanyi a zuciyarsa, ya sani hakkin Zainabu
da sauran matan da ya cuta ne Allah ya saka
musu ya jarabce shi da son macen da ya raina a
da can, lallai da iyayansa sun san irin yanda yake
son Zainabu da sun barshi ya aure ta ko yaya
take. Haka nan ya dinga juyi a gadonsa bai san
sanda bacci barawo ya silalo ya dauke shi ba,
don yana cikin tsananin tashin hankali. Da asuba
da kyar ya iya tashi dan jikinsa duk ya masa
nauyi, a masallaci ya jima yana addu'ar Allah ya
karyo da zuciyar iyayansa su amince ya auri
Zainabu, har gari ya waye yana ta lazimi, sam ya
manta da zuwa Ofis dan haka sai da ya makara.
Ko da ya isa dinma kasa tsinana komai ya yi,
banda kallon hoton Zainabu dake bisa tebur
dinsa babu abinda yake yi, ya sani muddin
iyayansa suka hana shi ya auri Zainabu to kuwa
lallai zai jima bai yi aure ba, kai babu ma rana.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ya nufi kujerar da ke Ofis din doguwa ya kwanta
yana neman layin wayarta, bugu daya ta dauka.
Ita ce ta fara magana, "Hello My honey, Zuma
ta."Ta fadi da wata irin murya mai tsananin fisgar
hankalinsa, wacce ta ke siye zuciyar 'yan maza da
ita. Ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce, "Zainabu ina
tare da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login