Showing 39001 words to 42000 words out of 44142 words

Chapter 14 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt

28 Dec 2024

1938

matsala mai girma, na rasa yanda zanyi
da rayuwata ba ni cikin hayyacina da walwala ta."
Ta ji gabanta ya fadi amman sai ta dake ta ce,
"Ayya Zumana ka kwantar da hankalinka komai
zai zamo da sauki Insha Allah, ka na ina ne
yanzu?" Ya lumshe idon sa kana ya bude ya ce,
"Ina Ofis yanzu amman na gaza komai, ji nake
kamar bani da lafiya ma." Ta kuma kwantar da
murya ta ce, "Kana jina ko zumana, ka kwantar
da hankalinka gani nan zan zo yanzu Ofis din
naka don bani son bacin ranka....." "A me zaki zo
ne?" Ya tambaye ta da sauri. Ta yi murmushi don
ta san Mustafan ta da shegen kishii ta ce, "Ka
kwantar da hankalinka zan zo a shatar tasi ne,
don nima ina Ofis yau." Ya ce, "Yayi kyau, ina
jiranki kada ki jima." Ta dubi abokin aikin nata da
yake kallonta tamkar maye sai dai duk iyakacin
jarabarsa da gulmarsa ya gaza jin abinda take
cewa, ta galla masa harara kana tace, "Wallahi
Oga kai mugun dan saka ido ne, wannan kallon
da kake mini fa kamar maye?" Yayi dariya yana
sosa keya ya ce, "Ke din Zainabu da tsokano
mutum kike, banda ni waye zai daure zama da
zukekiyar mace irinki yana kallonta..... yanzu dai
ina zaki naga kina shirin fita bayan yanzu D.P.M
yayo waya zai zo." Ta yamutsa fuksa tana fadin,
"Idan yazo kace masa na fita idan da dama zan
dawo." "Zainabu ki yiwa Allah ki tsaya idan
ba....." Ko kuma bi ta kansa bata yi ba ta fice
abunta ya bita da kallo yana girgiza kai sannan
ya ce, "'Yar jidali, yarinyar nan kina gara zama
wallahi, ko da yake kin isa ne." Ta isa Ofis din
nasu cikin wani ubansu leshi, zanin ya zauna
dam a kugunta rafa ne,rigar bata fiye girma ba
don da kadan ta iya wuce cibiyarta, sai dai
hannunta dogo ne, yanayin kirarta ta kalangu ya
fito sosai duk wanda ya kalleta sai ya kara sai dai
mai karfin zuciya, kamshinta ka dai zai iya sanya
ka kalle ta balle kyau da tsarin tafiyarta.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta murda kofar Ofis din ta yi sa'a kuwa a bude
take don yasan zata zo, ta san Ofis din dan kusan
tare suka tare ma, ta shiga da sallama, yana bisa
kujera yayi tagumi, har ta isa inda yake bai motsa
ba sai dai idonsa yana kanta har lokacin. Matuka
kwalliyar ta burge shi, ta isa ta zauna bisa
cinyarsa ta janye hannunsa daga tagumin da ya
yi, ta shafi gurin tana magana kasa-kasa,
"Zumana waye ya taba mini kai?, hankalina a
tashe na iso Ofis din nan." Ya daga idonsa yana
dubanta, abinda ya kuma bata tsoro don ganin
idon yayi jajir da alamar tashin hankali, ta kuma
shafar fuskar sa abinda ke sanya shi jin sanyi a
ran nasa ta ce, "Zumana ka sanar da ni abinda
ke faruwa wallahi hankalina a tashe yake." Ya
lumshe idonsa sannan ya fara magana har
lokacin tana shafar fuskarsa yace, "Hajiya Kubra
tsohuwar Shugabar makarantar ku ta G.G.C Dala
wacce kika yiwa rashin kunya itace Mahaifiya
ta....." Ta mike a zabure gami da dafe kirji tana
fadin, "Innalillahi wa inna ilahihi raji'un, na shiga
uku, Mustafa yanzu Hajiya Kubra Mominka ce?
Wayyo Allah na yanzu ya ya zan yi? Ina fatan
baka sanar da ita ko ni wacece ba?"Ya ware
idanuwansa wadanda suke jawur yana fadin,
"Zainabu babu hanyar fita, Momi ta sanki farin
sani kuma tasan kece Zainabun da nake so yanzu
a raina, Baba na ya sanya anyi masa bincike a
kanki matuka, ina sonki Zainabu amman iyayena
sun hanani auranki, abunda basu sani na yanda
Zainabu take haka ma dan su yake, amman na
rasa ta yanda zan sanar dasu abinda suke gudun
Zainabu saboda shi na dansu ne." Jikinta ya
dauki rawa dan ta shiga tsahin hankali matuka,
ya kamo ta ya tallafe ta a jikinsa yana shafar ta,
ta yi lamo a jikinsa tana ajiyar zuciya tamkar
diyar mage, ta ayyana a ranta wannan wace irin
masifa ce ta doso su, yanda suke son juna ace an
haramta musu auran juna, don dai duniya bata
da abin so kamar Mustafa, ta gama sallamawa
kanta a yanzu shine bango majinginarta, don ta
gaji da walagigin yawon iskanci da shan bakar
azaba ta saida mutunci a gurin maza, domin dai
ta lura yanzu ta sani babu abinda ke tattare da
bin maza sai bata da sai da mutuncin kai,
amman gashi wani katon abu na neman ruguza
mata wannan burin nata. Ta san halin Hajiya
Kubra mace ce mai kafiya da dagewa bisa duk
abinda ta sanya a gaba, wuya da dadi basa
sanyawa ta sauya daga kan ra'ayinta, bata manta
kirarin da malamansu ke mata lokacin tana
makaranta, "Mace mai kamar maza kwari ne da
babu." Sun yi shiru na tsahon lokaci kowa da
abinda yake sakawa a zuciyarsa, sun gaza sanya
kansu farin ciki kamar yanda suka saba a duk
lokacin da suka hadu don basu gundurar
junansu. Ita ce tayi karfin hali tace, "Musty
zumana yanzu yaya zamu yi, ko shike nan mun
rabu babu mafita?" Ya kuma rungumar ta tamkar
zai maida ta cikin sa kada wani ya kuma ganinta
sannan ya ce, "Zainabu abinda nake tunani
kenan tun daga daran jiya har zuwa yanzu
amman na gaza samun mafita, sai dai na sani
ruwa ko iska da duk wata azaba basu raba ni da
sonki, ko da an rabani dake a fili ba za'a iya cire
sonki a raina ba, son ki shine so na gaskiya mai
wahalar da ruhin Mustafa da zuciyarsa." Tayi
sanyayyar ajiyar zuciya mai cike da jin dadin
kalamansa, sannan tace, "Shike nan zumana kada
ka damu ka kwantar da hankalinka mu cigaba da
addu'a, sannan mu tsaya kan ra'ayinmu na son
juna duk wuya da dadi ina ganin zamu yi nasara
komai dadewa." Yace, "Hakane Zainabu kin kawo
shawara mai kyau, har naji raina yayi fari." Ta
kuma kwantar da murya tana fadin, "Kada ka
damu ka kwantar da hankalinka ni din taka ce
har abada." Ta fara masa salon nata na jan
hankali a cikin kunnensa take fadin, "Musty
zumana (I love you so much) Ina sonka da yawa."
Bai iya hakuri da Zainabunsa musamman idan
tana masa salonta na kauna dan haka sai ya
shiga maida mata martaninta, ya ma manta inda
suke.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
**************
Abubuwa sun hadu sun jagulewa Mustafa har ma
da Zainabun kanta, don dai yanzu ba ta iya
kallon kowanne da namiji da gashin arziki idan ba
Mustafa ba, wadanda take watsewarta dasu a da
can ma ta kisu yanzu, kawarta Asma tayi mata
lallashin duniya akan ta cigaba da harkarta ko da
a boye ne amman ta gaza, dan sai dai tayi mata
wani kallon ta ce, "Asma baki san Mustafa ba ne,
shine namijin da idan ya baki zumarsa baki iya jin
dadin ta kowa, shine namijin da ya iya soyayya
mai kwantar da zuciya, shine mai kula da duk
wasu bukatu na macen da yake matukar so,
shine ya sadaukar da kansa ga Zainabu, shin kina
tunanin yana gabana da ransa zan iya kula wani
da namiji? Ki barni kawai baki san Mustafa ba
kina kallonsa ne kawai." Don haka Asma sai dai
ta zuba mata ido kawai don ita da kanta ta san
Mustafa daban ne a cikin maza kamar yanda
kawarta ke fadi. Samarin ta da dama sun damu
da wannan sabon halin da ta bullo musu da shi
musamman Alhaji Jamilu da kuma D.P.M, don
haka ma ta kashe duk wayoyinta, idan kaga ta
kunnasu lallai Mustafa zata kirawo. Hankalin Sala
idan yayi dubu ya tashi, domin dai tana ganin
kamar ana son kashe mata jin dadin diyar tane
da walwalarta, dan da farko ma fada ta kama yi
mata tana fadin, "Haba maitsada yaushe zaki
zauna namiji kwaya daya yayi ta gare-gare da
rayuwarki a banza, ki dubi irin wahalar da kika
sha a baya, amman yanzu duk kin daga
hankalinki don uwarsa tace ba zai aure ki ba, ga
maza nan kala-kala suna binki wadanda suka
fishi komai kamar su cinye ki amman kin makale
masa, dan haka ki rabu dashi kawai tunda dai
yanzu ba da bace." Ita dai shiru kawai tayi tana
ayyanawa a ranta, "Sala baki san so bane shiya
sanya kike fadin haka, da kin san irin abunda
nake ji akan son Mustafa da kin tausaya mini, zan
iya jure rashin komai amman banda Mustafa,
wannan wata jarabta ce da Allah ya doro mini."
Da dai Sala taga fada da mita ba zasu yi magani
ba sai ta koma lallashi, amman duk a banza wai
talaka ya girmi Sarki, su kuwa abokan watsewar
ta sai kyauta ta bajinta suke mata wai ko zasu
shawo kanta, amman idan an aiko ma sai dai
Sala ta karbe tana godiya tace bata jin dadi ne
shiya sanya bata fito ba. Idan mutum ya fiye
matsa mata da aike kuwa fita take yi tayi masa
rashin mutunci, don dai muguwar 'yar buyagi
ce.Haka zaka tadda ta tayi dif da tabar shaidan
ko shandy din ta a gidan Asma dan can Mustafa
ke tadda ta suyi watsewarsu acan da lallashin
juna, don ma dai shi yanzu Mustafa bai son
shaye-shayen da take yi don shi kam baya ga
taba yanzu bai shan komai sai dai idan wani yana
shan tabar shaidan a kusa dashi ya amsa yayi ja
uku ko hudu, amman giya kam tuntini ya daina
sha, don haka take rage shan su don su kan yi
fada idan ya tadda ta tana sha. Al'amura sun
kuma tsauri a gare su, don Momi ta kama shi da
hoton Zainabu wacce tayi tunanin ya rabu da ita
tuntuni ya fara neman wata ma, ta yi matukar
girgiza musamman da taji kalaman da yake
furtawa akan Zainabu din. Ta yi neman wayar sa
ne ta sanar dashi sallahun da Babansa ya bari ya
kaiwa kanin sa Kawu Sale, amman duk wayoyin
nasa a kulle suke, gashi kuma ta ga motar sa a
kofar gida abun da ya tabbatar mata yana ciki
kuma dai lokacin babu yara a gidan don haka ta
nufi sashin nasa da kanta don ta sanar dashi
sakon Baban nasa. Ta tadda shi zaune bisa
kujera ya dora (laptop) akan cinyar sa ya kura
mata idanu wadanda suke rine saboda tsabar
tashin hankali, a fili yake fadin, "Zainabu yaya
zanyi da son ki a zuciyata, ni kadai na san irin
azabar da nake sha saboda raba mu da ake
shirin yi, na gaza ganin ko wace mace da kima da
daraja don kece kadai kika san Mustafa, ba zan
iya auran wata mace ba muddin kina raye a
duniyar nan ba, san yani a kafadarki ko naji sanyi
a raina, na zama mutum-mutumi sai yanda kika
yi dani Zainabu." Hankalin Hajiya Kubra yayi
mugun tashi da jin kalaman da Mustafa ke
furtawa, ta kuma jin tsanar Zainabu ta lunku a
ranta don sai taga kamar yanzu yafi son Zainabu
sama da ita ma daga yanda take jin kalamansa,
kai ita tana ganin wannan son da yake wa
Zainabu ma bana Allah bane asiri kawai tayi
masa, banda haka meye hadin shi da ita, don ya
fita komai a ganinta, ta nufe shi da sauri dan ta
bayansa take baiga shigowarta ba, sai ta tsaya
turus tana kallon abinda ya dauke masa hankali
har bai ji shigowar ta ba. Wani katon hoton
Zainabu ne ta dauka da wani yadin material (light
purple), mai yarfin fulawowi jajaye da ruwan
zaiba, tana sanye da wani dankunne na fashion
mai kyau, ta tallafe habarta da tafin hannunta
tana dariya, (dimple) dinta ya fito sosai, fuskar ta
yi fayau, gashin idonta ya tashi gazar-gazar,
girarta ta kwanta luf-luf, labbanta sun sha
jambaki kalar kayanta sai walkiya suke yi tamkar
ba a hoto ba, hoton ya dauko matuka don an
futo da ainihin kyan Zainabu. Lallai ba Zainabun
da ta sani da ba ci, don ta goge matuka tana
kuma da kyan da lallai zata iya yaudarar Mustafa
ya sota, sai dai ita kyanta baya gabanta tunda
bata da kyan hali. Zuciya ta dauke ta don ganin
wai har lokacin bai san ta shigo ba hankalinsa
yana ga Zainabu ne kawai, ta fisge laptop din ta
kwadata da kasa, ai kuwa sai gashi ta bare gida
biyu, da alama da kyar zata kuma moruwa gashi
mai kyau ce dan daga kasar waje ya taho da
ita.ya daga kansa a gigice dan yaga wanda yayi
masa wannan yankan kaunar sai yaga Momin sa
a tsaye tana ta huci ta cika fam, nan da nan gumi
ya fara karyo masa don yasan Momi babu wargi
ba iri Babansa bane mai sanyi ba. "Mustafa! (ta
kirawo sunan sa yau babu sayawa saboda bacin
rai), wato dama baka rabu da wannan karuwar
ba ko? to tsaya kaji na gaya maka ko mutuwa
zaka yi akan sonta ba zaka auro mana jaraba ka
kawo mana gida ba, da mun sakankance ka rabu
da ita, ashe 'yar jarabar tana tare da kai. Shin
wai ni me ka gani a jikinta da har tafi sauran
mata da ka kasa kalla da daraja ne eye? Kai
yanzu ba zaka ji kunya ba ace matarka tsohuwar
'yar tallan goro bace mara tarbiyya ba? Bata gaji
tarbiyya daga uwa ko uba ba sam?, to tsaya kaji
na gaya maka ta mahaukaci, ko bayan raina ka
auri Zainabu ban yafe maka ba, sannan daga yau
idan ka kuma zuwa gidansu ko inda zaku hadu
ban yafe maka ba." Ya runtse idonsa gami da
dafe kai hankalinsa yayi mugun tashi, babu
abinda yake fadi sai, "Innalillahi....." Ta kuma
kufula tana fadin, "Kai ko mutuwa zaka yi babu
kai babu Zainabu na gaya maka in dai nice na
haifeka dan halak." Tana gama fadin haka ta juya
ta fice sam ta manta da abinda ya kawo tama
sashin nasa. Ya zauna jabar a kujera har lokacin
bai cikin hayyacinsa, ya kuma fadin, "Ya Salam!
Ya Salam!" Har lokacin zufa tana karyo masa duk
da sanyin A.C da fankar dake dakin. Maganar
Momin ta dunga masa amsa kuwwa a kunnensa
sai yake ji kamar har lokacin tana tsaye a kansa
tana ta maimaitawa ne, don haka ya sanya
hannuwansa ya toshe kunnuwansa wai ko ya
daina ji, amman da yake abin daga zuciyarsa
yake fita sai ya cigaba da ji kamar ma karuwa ya
yi. Lallai ko yaki ko ya so yasan rabuwar sa da
Zainabu ta zo kenan, idan har ya kasance da mai
albarka, don dai ya san duniya bai hada
Mahaifiyar shi da kowa ba, ko da kuwa zai mutu
din kamar yanda Momin nasa ta fada din ya rabu
da Zainabu har abada.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
WAI WACECE ZAINABU-ABU MAI TAGWAYEN SUNA
NE?
Asalin Salamatu mahaifiyar Zainabu 'yar cikin
birnin Kano ce, ta tashi babu arabi balle boko,
bata da aiki sai dai ta dauki tallan soye (dan tayi
da ake cirowa daga dabbar da aka yanka na kasa
mata a kokuna sannan a jera a cikin faranti). Don
haka kullum da sassafe zata yi sammako ta tafi
Mayanka ta siyo dan tayin wanda zama suke
kusa da dabbar da ake yankawa da zarar an
hango da dantayi sai a kwasa da gudu, wacce ta
fara kamawa nata ne sai ta saka a kwanonta ayi
ciniki sannan su kuma matsawa gaba da haka har
ka tara na iyakacin kudinka, sannan sai ta tafi
gida a yayyanka shi a soya, a zuzzuba a kokuna
sannan a tafi tallanshi kasuwanni. Idan ta dauki
tallan tun safe sai yamma likis take komawa gida,
don haka bata da lokacin karatu, sai dai ran da
taso sai ta tafi makarantar dare ita ma bata
fahimtar komai dan banda gyan-gydi babu
abinda take yi, don an sha yawo an gaji, idan
kuma ranar alhamis da Juma'a ce a tafi gidan
amare a yita wasan 'yar carafke ko lido da
sauransu. Mahaifinta yana so tayi karatu sai dai
bai isa ba dan matar sa tafi karfinsa, don haka
yana ji yana gani 'yarsa ke wannan rayuwar babu
kwaba balle harara, sannan idan dare yayi wani
lokacin zaka ga samari sun cika kofar gidan anata
zance da shewa da kawayenta kuma bana aure
bane illah ayi shashanci da zancen batsa a watse,
amman babu na aure a cikinsu. A gurin da take
sai da soye wani mutumin Sudan sunansa
Abbakar, shayi yake saidawa irin na babbar butar
nan wanda ake dauka a hannu da biredi da
kofuna a faranti, Abbakar mutum ne mai kirki da
hakuri dan kullum Salamatu sai ta tsokane shi
dan hausar sa bata fita sosai, gashi kuma da
shegen surutu da son tsegumi. Duk danginsa
suna can Sudan, yaki ne ya sanya suka watsu
suka yo Nigeria da 'yan uwansa, sai dai tun da
suka zo kowa ya nemi masauki, shi kam yayi sa'a
ya fada hannun wani Malami Malam Nadabo
mutumin kirkine ya bashi gida inda yake saukar
baki ya zauna cikin almajiransa, yana fita neman
abincinsa don shine ma ya bashi jarin da ya fara
sana'a tun yana zagaye cikin unguwar har ya
koma yana shiga kasuwanni.Da yake ya iya
shayin sai ya samu kwastomomi dan irin na
larabawan nan yake yi, a haka suka hadu da
Salamatu ma, don Allah yayi shi mutum ne mai
shegen surutu da son gulma dan haka duk
abinda ya gani sai ya nuna mata ko ya tambaye
ta da haka har soyayya ta shiga tsakaninsu. Abu
kamar wasa sai gashi sun saba matuka, sai dai
tun a wancan lokacin tayi mugun raina shi tayi ta
masa masifa bai damuwa, domin yana da
matukar hakuri sai dai zancan gulama amman
sam baida abokin fada, sai dai mutane da dama
suna ganin abun nasu kamar ba zai yiuw ba don
shi fari ne tasa kamar balarabe gashinsa ma a
nannade yake sai dai wahala ta sanya shi ya dan
dafe, yayin da Salamatu take baka, amman bata
da muni, sai dai bata da tsawo gajera ce sosai
mai jiki. Malam Nadabo dai shine kamar matsayin
mahaifinsa don haka shine ya tsaya masa har aka
yi wannan auren, suka tare a nan gidan Malam
din da yake zaune da almajirai, wasu suka koma
shagon gidan wasu kuma suka koma daya gidan.
Ta addabi kowa a gidan don gidan kusan a hade
yake da na Malam kasancewarta masifaffiya ce,
su dai matan malam bata yi da su don sun ja
girman su haka malam, sai dai duk 'ya'yan gidan
'yan dakinta ne musamman matan, amman duk
kusan almajiran malam tayi fada da su don ma
malam yakan yi mata fada, don haka babu
wanda take shakka kamar malam don babu
wargi, a nan gidan ta haifi dan ta na fari Sadiku
wanda aka haifa rana daya da dan Malam Zaidu,
don haka rana daya aka yi suna Malam ne ma ya
rada musu sunansu duka. Sun tashe tare da
Zaidu da yake Sala bata wani damu dashi ba don
ita ta fi son ta haifi mace wai itace abokiyar
neman kudi, don haka kullum a cikin watangariri
yake a cikin gidan musamman da ta yaye shi sai
ta bar musu a can, don haka kusan a gidan nasu
ya taso.Tare Malam ya sanya su a makaranta Ma,
sannan ta kuma samun wani cikin tayi ta tanadin
kayan mata har su dankunne da awarwaro
amman sai gashi ta kuma haifar namijin, shima
din haka ya taso a gidan malam din, sai dai daga
kansa bata kuma samun haihuwa ba har ya
shekara biyar, sai wata annoba ta zo ta kyanda
shima yana ciki, ai kuwa dai wannan kyanda itace
ta yi ajalin Sabitu. Rashin samun cikin nata ya
sanyata fara tunanin wai matan Malam ne sukayi
mata asiri don ta fara haihuwar da namiji, su a
kan Zaidu suka fara haihuwar namiji duk mata
suke haifa, ita fadi take banzaye ni da ana
musanye da munyi don nafi son matan, sai dai
bai ya wata goma ba da rasuwa Sala ta kuma
samun wani cikin. Ai kuwa dai wannan karon tayi
sa'a a wannan karon ta samu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login