Showing 30001 words to 33000 words out of 44142 words
Chapter 11 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt
ta sha karya, ka dube ni da
kyau, sama da kasa zaka ga ba Abun da ka sani
da can bace, wannan Zainabu ce, dan haka ka ja
tsummar rayuwarka ka bar nan gurin idan ba
haka ba zan rotsa maka kanka da kwabar nan."
Ta nuna masa wata kwalba da ke kan tebur din
da suke zaune ta lemo.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ya yi murmushi gami da gyara zama har lokacin
yana zukar tabar sa yana kallonta babu ko
kyaftawa. Ta san halinsa mutum ne mara tsoro
sannan duk abin da ya sanya kansa babu mai
hana shi, dan haka tasan babu wata barazanar
ta da zata bashi tsoro, idan har ta yadda suka
cigaba da zama guri daya komai zai iya faruwa,
dan haka ta ga barin gurin kawai shine mafita a
gare ta, dan haka ta dauki Jakarta ta bar gurin
tana huci. Ya bita da kallo har ta bace wa
ganinsa, yayi murmushi sannan ya dawo da
dubansa ga Asma wacce ta zuba masa ido kawai
tana kallonsa, ta san lallai kawarta ta debo mai
zafi dan barazanar da takewa maza suna tsorata
shi tayi masa amman ko gezau bai yi ba. Ya yi
dariya ya ce, "Kawarmu yaya gida?" Ta yi wata
wawiyar ajiyar zuciya dan maganar ta zo mata a
bazata, sannan ta ce, "Lafiya kalau." "Kinga
yanda muka yi da kawarki ko? Na san halin
Zainabu muguwar 'yar buyagi ce zata iya yin
abinda ya fi haka ma, sai dai ban damu ba ko
dar ma banji ba, don na gano tsagwaron sona a
cikin idon Abu" Ya nuna kirjinsa da yatsansa yana
cigaba da fadin, "Ni ne mutum na farko da ya
san wacece Zainabu, duk wani iskanci da Zainabu
ke takama da shi nine na koyar da ita, ba wai ina
alfahari da haka bane, a'a zuwa yanzu ma duk
sanda na tina ni ne silar lalacewarta na kan ji
takaici kuma na ji haushin kaina, don haka nayi
alkawari yanda na zama sanadiyyar lalacewar
rayuwar Zainabu zan kuma zama jagora gurin
ganin na shiryar da ita." Ya manta Allah shi ne ke
shiryar da wanda ya so, ga shi ya yi hasashe ba
tare da ya nemi yardar Allah ba. "Amman ki bar
ni da Zainabu ni da ita kar ta san kar ne, na san
na yi mata laifi amman zata yafe mini komai
dadewa tunda nine mutum na farko da ta fara so
a rayuwarta." Gaba daya ya gama burge Asma
har ma take ganin inama ace itace ke da wannan
hadaddan gayen, amman ta san tunda Zainabu
ce a gabansa ba zai kalli kowa da daraja ba
musamman da yace shine masoyin ta na farko,
dan haka da wuya ya kalli wata mace da daraja.
Don haka ta share wannan tunanin ma a ranta
dan ta san ba mai yuwuwa bane, yanda kuma
suke da Zainabu ma ba zata iya yi mata zagon
kasa ba, dan haka ta fara jan sa da hira ta
Zainabu kawai, ya ma manta da Zainabu 'yar
buyagi ya zauna suna ta hirarsu har aka tashi
daga fatin, sannan ya nufi gurin Zainabu wacce
ke ta hada kayan su na fatin da ta san nasu ne,
ya isa gabanta yana dariya ya ce, "Yaya dai uwar
dakina ko za'a taya ni kwana ne yau dan ina tare
da gajiya wallahi na yo doguwar tafiya mai nisa."
Ba ta kalli inda yake bama balle ya sanya ran
zata kula shi, ya cigaba da surutunsa don a
ganinsa dole zata bi shi don yanda dare yayi
kuma kowa ya watse a gurin har amarya da ango
dole ta bishi dan babu wanda zai dauke ta, don
haka nema ya share guri ya zauna yana ta cigaba
da surutunsa. Can wata dankareriyar mota ta
kutso kai harabar da suke zaune, Zainabu ta
mike tsaye gami da kallonsa sama da kasa ta ja
tsaki sannan ta ce, "Malam ina gargadinka karo
na biyu da ka fita daga rayuwar Zainabu, ka
kuma gane yanzu Zainabu nake ba Abu ba."
Tana gama fadin haka ta nufi motar da salon
tafiyarta na yanga da jan hankalin maza. Ransa
ya yi masifar baci har yana ganin ba zai dauki
wannan raini wayon ba, don yana da masifar
kishin tsiya. Don haka ya nufi motar da sauri cike
da bacin rai, amman ina tuni ta riga ta shiga,
bayan ta zauna ta kalle shi yana wani huci kamar
tsohon zaki, ta yi wata mayaudariyar dariya mai
kularwa sannan ta rufe murfin motar, yana kallo
suka fice a guje, ya ji kamar ya rufa musu baya a
guje amman ina sun yi masa nisa. Ya doki iska
yana huci gami da fadin, "Ba zan taba daukar
wannan rainin hankalin ba wallahi, zamu gauraya
ne." Ku ji fa karfin hali namiji da suna Hajara
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
. Suna daukar hanya DPM ya kalle ta yana wani
lasar lebe yace, "Yaya dai gimbiya za'a taya ni
kwanan ne mu wuce gidan shakatawa ta?" Ta
galla masa harara ta ce, "Au abinda kake yiwa
kenan shiya sanya ka nace daman zaka dawo ka
dauke ni? Tsaya ka saukeni dan ka san kuna da
yawa 'yan iskan garin zan sami mai kai ni gida,
dan ni na gaji babu wani abinda zan iya yi." Ya
ce, "Kai Zainabu ke fa 'yar buyagi ce wallahi,
daga dan tayi sai jidali, shi kenan na hakura muje
kawai." Bata kuma cewa komai ba ta jingina da
kujera ta lumshe idonta tana tuno abinda ya
faru, wani ciwo mai zafi da ya dade yana damun
zuciyarta ya fara taso mata, tsigar jikinta ta fara
tashi yar-yar kamar mai jin sanyi "Mustafa!
Mustafa!" Ta fadi a cikin ranta gami da girgiza
kai. Lallai ta sani abu ne gingimeme a gabanta,
dan Mustafa da ban ne a cikin maza a gurinta,
kuma tayi wa kanta alkawarin a can baya duk
sanda Allah ya hada su ko a hanya ne sai tayi
masa rashin mutunci, amman sai ga shi a
gabanta amman ta kasa aiwatar da komai a
kansa, sai ma wani abu da yake neman ya dawo
mata da shi. Har suka isa kofar gidan su bata san
sun iso ba don tayi nisa a tunani, sai da ya kai
hannunsa yana shafarta tamkar wani maye
sannan ta farga, ta yunkura da masifa ta
hambare hannunsa gami da dalla masa harara.
Ya kama sosa keya yana dariya ya ce, "Tuba nake
yi, ai na zaci ko kinyi bacci ne, Allah Zainabu sam
ba na gajiya da ke, ke din ta daban ce, kamshin
ki kawai kan tayar mini da hanlaki, yanzu ji yanda
kamshin ki ya cika motar nan tamkar ni ban
sanya turare ba, wai ni da wane turare ki ke
amfani ne ma?" Ta yamutsa fuska ta ce, "Su
kuma wadanda ka ajiye a gidan fa meye amfanin
su? Dan haka wallahi nake tsoron aure, sai ku
baro matan ku a gida kuzo kuna hurewa
kadangarun bariki kunne da naira, yanzu haka
matan ka suna can suna jiranka kana nan kana
gantali da wannan daran." "Ke rabu da
wadannan matan, babu wani abu da suka iya sai
jarababban kishi da shegen bin Malaman Banza,
burin su kawai su tara kudi, da kun hau gado su
yi maka wani sumbukaka kamar jakai, babu wani
salo da suka iya wai su kunya, sau da dama idan
nayi niyyar daina bin matan titi na zauna da su
idan suka gaza gamsar da ni sai kiga na dawo
ruwa, balle ke Zainbau daban ce wallahi kin san
kan da namiji matuka, ko makarantar kika yi ne
na kawo matan nawa ki koyar da su?" Ta yi
dariya sannan ta ce, "Matsalarka ce wannan,
wata kila kai ma da laifinka, kana shigar musu
gida ne tamkar mala'ikan tsaron wuta babu
fara'a shi ya sanya suke kasa sakin jikinsu, ni dai
yau duk jarabar ka nan gani nan bari, ka ga fitata
ma.
Ta bude kofar ta fice tana fadin, "Asuba ta gari."
Ya bita da kallo har ta shige cikin gidan na su,
yayi tsaki da damuwa gamida kifa kansa bisa
sitiyarin motar tasa, Zainabu ta zame masa
masifa a rayuwarsa, muguwar hatsabibiya ce,
muddin ka yarda ta lasa maka zumar ta a baki to
lallai ka shiga uku, idan ba kana da kwararriyar
mace mai iya salo-salo ba sai ka ji ka rainawa
matan ka.Ya figi motar tasa ya bar kofar gidan
tamkar mai tsere da iska, ita kuwa tana isa gida
ta tadda gidan shiru kowa ya gaji da kacaniya ya
yi bacci, ta shiga ban daki ta dauro alwala ta
sanya kayan ta na sallah, ta shimfida sallayar ta
wacce ke ta kamshin turare ta haye ta fara
gabatar da Sallah. Idan ka ga yanda take
nutsuwa idan tana Sallah zaka rantse idan aka
sanya mata hannu a baki ba zata iya cizawa ba,
dan duk iskancin ta bata wasa da Sallah, tunda ta
taba jin wa'azi akan Sallah da irin azabar da
mara yinta ke sha ta nutsu da yin sallah, wannan
shine kadai abinda zaka daga a rayuwar Zainabu
ta yi tutiya da shi. Mu dai bi ta a sannu don
duniya ai takaitacciya ce.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Mustafa kam da kyar ya iya komawa gida, ya
dade a dakin sa yana sintiri hannuwansa sakale a
bayansa, wani masifaffan kishi da zafin Zainabu
ke addabarsa, lallai yau da yana da hali da sai
yayi wa Zainabu da wanda ya dauketa dan
banzan duka, gaskiya ba zai iya lamuntar wannan
halin nata ba na kula kowa, lallai dole ta daina
harka da kowa indai tana son kanta da zaman
lafiya, ya dade yana sintiri da kyar ya iya
daurewa ya dan kishingida har bacci ya dauke
shi. Da safe ya so yaje amman ya san da kyar zai
sami ganin ta don hidimar bikin da sukeyi dan ya
ji suna cewa yau din ne yinin biki, dan haka ya
yanke shawarar sai dare sannan zai shiga. Karfe
tara na dare ya isa gidan nasu ya rasa ta yanda
zai yi ya ganta, sai can ya sami wata budurwa
yace ta kira masa ita. Ta dube shi ta ce, "Ai Anti
Abu tun da aka yi Sallar Magariba suka fice da
kawarta Asma." Ya yi mata godiya ya koma motar
sa ya zauna, Allah ya sanya jiya ya amshi lambar
wayar Asma din, dan haka bayan ya shiga motar
ya zauna ya fara neman layin Asma din. Da
yanga ta dauka a yauki take maganar sanda taji
kira, "Hello wa ke magana?" Ya yi ajiyar zuciya
sannan ya ce, "Mustafa ne, don Allah ina son ki
bani kwatancen inda kuke, amman kada ki sanar
da kawarki yanzu zan zo." Ta dubi Zainabu da ke
zaune tana zukar tabar shaidan ta dora kafa
daya kan daya, tunda suka iso gidan abun da
take yi kenan dan cewa ta yi ba zata je kai
amarya ba don ranta a bace yake su wuce gidan
ta ta sami hutu, amman tun da suka karaso din
ta gaza tabuka komai baya ga busa taba, dan
haka ta riga ta gano kawar tata tunanin Mustafa
ne kawai don bata taba dora hankalin ta ga
namiji kamar haka ba. Sai ta ce, "Shike nan zan
yo maka text." Daga haka suka yi sallama. Minti
talatin da biyar kacal ya kwashe ya iso gidan ya
danna kararrawar kofa, Asma ta mike da sauri
don ta san Mustafa ne. Zainabu ta bita da kallo
ta ja tsaki tana fadin, "Banza, kin gayyato mana
wani kwarton ko? Ni da nazo dan na huta zaku
dame ni, daman tunda naji kina magana kasa-
kasa a waya na san jarabarki ta motsa." Bata ce
mata komai ba sai dariya kawai da tayi ta nufi
kofar, yana tsaye sanye da kananan kaya, wando
ne na jeans bulu da shet fara tas mai taswirar
birnin London, da silifas na fata a kafarsa dan
gasken, sai agogo na azurfa da wani kwalelen
zobe shima na azurfar, ya yi kyau matuka. Suna
hada ido da Asma ta yi ajiyar zuciya sai taga yau
yafi kyau ma fiye da jiya, dan ta kuma yadda irin
gogaggun mazan nan ne ma, ta kwantar da
murya tana fadin, "Yallabai barka da isowa." Ya yi
murmushi gami da fadin, "Yauwa kawarmu ya
gida?" Tana amsawa ta bashi hanya ya wuce ciki,
sannan ta kulle. 'Yar buyagin tashi tana zaune
tana ta busa hayakinta bata ko kalli inda suke ba
balle ma ta gane waye ba. Ita ma Asma tana
shigowa kiran wayar Alhaji Buba ya shigo wayar
ta, yace ga direba nan ya turo su taho, dan shi
baya zuwa da kansa dan kada masu ganin sa da
daraja su ganshi girma ya fadi, dan haka sai dai
duk sanda ya bukace ta ya turo direbansa a kaita
can gidan sa ta kwana, dan haka dakin ta ta
wuce ta hado 'yan kayanta. Har ya isa kusa da
ita ya zauna bata san ya zo ba, dan tabar
shaidan din ta fara gaya mata karya, ta jingina
da kujera ta lumshe idanuwanta tabar tana
tsakanin hannunta.A hankali ya zare tabar dake
tsakanin hannunta, kamar wacce ya tsikarawa
allura ta bude idonta firgigit ta ware manyan
idanuwanta a kansa suka yi ido hudu, sai ta yi
zaton ko gizo yake mata kamar yanda yake mata
tun dazu. dan haka ta mai da idanuwanta ta
lumshe wai ta daina ganin gizon sa, sannan ta kai
tabar ta bakin ta da zummar ta kuma zuka,
amman sai taji wayam babu komai, ta bude
idonta da sauri a kansa, shine din dai da gaske
yana taya ta shan tabar tata. Haushi da takaici
ya cika ta tama rasa yaya za tayi masa, amman
ta san ba kowa ne yayi mata wannan iskancin ba
illah Asma, dan haka ta mike da bala'inta ta nufi
dakin kwanan Asma din, sai gata sun ci karo a
hanya, ta ci uwar kwalliya sai kamshi take zubawa
rataye da jaka a jikin ta. Ta rike kugu tana
harararta, ita dai Asma dariya ta sanya sannan ta
nufi Mustafa ta cilla masa makullin tana fadi cikin
harshen turanci "Take care, good night." "Wai
Asma wannan wane irin iskanci ne?" Zainabu ta
tambaya a kule. Asma ta daga kafada alamar Oho
sannan ta fice da saurinta tana dariya. Ta kulu
matuka, ta mai da kallonta ga Mustafa dake
kallonta yana murmushi ta ce, "Wai kai kana gani
kayi mini dabara ne, to ka sani a yanzu na girmi
wayo da dabararka, sanda ka yi kaci nasara dai
ka yi amman ban da yanzu, don haka sai ka
zauna ka jire mata gida." Ta dauki dan yalolon
gyalenta da jakarta ta nufi kofa. Sai dai ina ya
rigata dan mikewa yayi da azamarsa ya sanyawa
kofar makulli ya cilla makullin cikin aljihun
wandonsa. Ta yi tsaye tana kallonsa cike da
takaici da masifa, ya isa gaban ta ya tsaya cak ya
zira hannuwa cikin aljuhunsa ya ce, "Ga ni
gabanki kiyi mini hukunci daidai da laifina zan iya
dauka, amman ki yi mini alfarma ki daina gudu
na sannan ki dai na mini kallon kiyayyar nan dan
yana bakanta mini raina, domin Allah ya
jarabceni da son ki Zainabu, na gaza kallon
kowace mace da daraja a rayuwata, ki taimaka ki
yafe mini laifin da nayi miki nasan mai girma ne,
amman na yi ne ba da son raina ba." Ta rike
kugu tana kallonsa idanuwanta sun sauya launi
zuwa jawur, duk wannan farin da kyallin babu
saboda tsabar dacin ran da take ciki, tayi wani
yake wanda yafi kuka ciwo sannan tace, "Mustafa
na sanka tuntuni gwani ne kai gurin iya yaudara,
da irin wadannan kalaman ka sami nasara a
kaina a wancan lokacin hadi da kuruciya da
talauci da son kudi irin na Mahaifiya ta, sai dai ka
sani a yanzu Zainabu Abu ta wuce duk iyakacin
tunanun ka, baka da sauran kalmar da zaka iya
yaudararta da ita, baka da kudin da zaka iya
yaudararta dasu, domin ina mu'amala da
wadanda suka fika kama daga Gwabnoni sai
Sanatoci da Ministoci zuwa manyan 'yan kasuwa
dake rike da akalar Nigeria, dan haka yanzu ina
da kudi da farin jikin da nafi karfinka, a yanzu
idan na buga waya kadai duk abinda nake nema
zan samu, dan haka kaga baka da makamin da
zaka yaudari zuciyata a yanzu, duk da kana
takamar kaine silar fadawa ta a wannan muguwar
harkar da kullum nake tsinewa mara albarka."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ya kuma kwantar da murya ya ce, "Zainabu
tunda na diro garin nan na ganki nasan lallai ba
Abun da na sani da can bace, kuma ban dawo
rayuwarki dan na nuna miki kudi ko kyau ko
mukami ba, na zo ne da sunana Mustafa
masoyin ki nida zuciya ta kadai ina fata zaki yafe
mini abinda nayi miki can baya, sannan na mai
da matsayina da martaba ta a zuciyarki kamar
da, koma yafi haka don a yanzu Mustafa bai zo
da zummar fasikanci ba sai dai da zummar auran
Zainabu, domin a yanzu Ubangiji ya jarabi zuciyar
Mustafa da tsananin son Zainabu." Ta kalleshi a
lalace tamkar ta ga mahaukaci sabon kamu tace,
"So! So! Lallai ka hadu da mugun ciwo idan har
da gaske kake, balle na san karya kake yi, domin
kai mutum ne mai yaudara da karya, don haka
ka bude mini kofa na fice kawai, dan bana son ko
kallon fuskar ka domin kai ne mutumin da ya
sanya rayuwata a cikin fargaba da tashin hankali,
nasha azabar da har abada ba zan manta da ita
ba dan haka bude mini kofa na fita ko na daina
ganin azzalumar fuskarka!" Ta karasa maganar
tana hargowa. Ya hadiyi wani miyau mai daci,
maganganunta suna yi masa zafi da suya a cikin
zuciyarsa, dan haka da kyar ya iya buda baki
yace, "Zainabu ba zan bude miki kofar nan ba
har sai kin amince dani kin yarda yanzu ni ba
mayaudari ba ne..." "Ba zan taba yadda da kai
ba, ka bude mini kofa kawai na fita tun ban
maka rashin mutunci ba wallahi." Yana tsaye
kyam babu alamun zai ko motsa, ranta ya kuma
baci matuka, ta ga lallai da gaske yake dan haka
ta nufe shi da azama ta kama kokarin kwatar
makullin, nan fa suka fara kokawa amman ina
namijin duniya ne maji karfi dan haka ta gaza kai
hannunta balle ta iya dauka har karfinta ya kare,
tayi kokarin janye jikinta amman ya hana ta
hakan dan ta tuno masa da wani lokaci da wasu
al'amura da ke masa dadi da sanya shi nishadi a
duk sanda ya tuno. Tayi kokarin ta kwace amman
ta gaza sai ma wani abu da yake shirin jawo
mata dan shin din daban ne a zuciyarta ya san
kanta da yanda yake samun ta a sama, daman
haka yake so ta shiga jikinsa dole sai ta sakko
don dai shine ya santa ya san wacece ita, tayi luf
a faffadan kirjinsa mai kirar zaki ta gaza kasa
aiwatar da komai. Ya sami yanda yake so dan
haka yake da salon yaudarar da sace zuciya,
yanzu kam ya soma nasara a kanta dan tana jin
zafinsa a ranta amman tana matukar son sa, dan
haka komai ya kwance mata, Mustafa ne namiji
daya tal da idan tana tare da shi take manta
kowa, amman duk sanda take tare da wani sai ta
tuno shi da soyayyarsa, don haka bata da karfin
halin da zata kwaci kanta duk da haushinsa da
take ji, dan haka sai ta fashe da kuka kawai.
Jikinsa ya dauki rawa don yasan ba karamin abu
ke san ya Zainabu kuka ba, don tana da taurin
zuciya, dan haka cikin tausasa murya da rada ya
ce, "Zainabu don Allah ki yi hakuri ki yafe mini na
tuba....."."Me ya sanya ka tafi ka bar ni sanda
nake tsananin bukatar ka a rayuwa ta eye?" Ta
tambaye shi tana kuka. "Ki yi hakuri na san nayi
miki lafi, sai dai na