Showing 42001 words to 44142 words out of 44142 words

Chapter 15 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt

28 Dec 2024

1939

abinda take so din,
don haka murna ba'a magana, sai da dauki son
duniya ta dora akan Zainabu sunan Mahaifiyar
malam din ya sanya mata kenan, da farko tace
bata yarda ba sunan Sima take son a sanyawa
diyarta, shi kuwa malan sunan matarsa ta fari ne
da ta rasu yana son sunan, sai da Abbakar yayi
ta lallaba ta sannan ta amince, akan Zainabu sai
tayi fada da uban kowa a kuma sannan ne
Abbakar ya kammala ginin gidansa da taimakon
malam, don haka suka tattara ya nasu-ya nasa
suka koma, amman banda Sadiku wanda sai dai
yaje gidan nasu ya koma gidan malam don
kamar ba Sala dince ta haife shi ba musamman
idan Zainabu tana kin ji yana mata fada, dan
haka shima bai fiye zuwa gidan ba sai da ya
shiga sakandire ne ma yake zuwa sosai.Sala kam
sana'a ta kafa sosai a gidan ta, don daman tun
tana gidan malam jarabar neman kudi ne da ita,
don haka ba ta zama kullum cikin neman kudi
take. Tun daga wannan lokacin shike nan
haihuwa ta bude a gidan nasu, sai dai yaran
suna tashi babu tarbiyya, da farko malam ya fara
kiran Baba Abbakar akan halin da yaransa suka
tashi da shi, don haka yayi masa nasiha mai
shiga jiki, sai dai idan aka ce namiji bashi da
katabus a gidansa babu tarbiyya, don haka san
da Baba Abbakar yaje mata da abinda Malam din
ya ce, tsalle tayi ta dire tana fadin, "Wallahi baka
isa ba, wacce tsiyar kake tsinana mana da har
zaka yi mini wannan tsarin (don a lokacin babu
ciniki a sana'ar ta shi sai dai yayi ta yawo bai
samun ciniki sosai, daga karseh sai ya koma
kame-kame)." Malam Nadabo yana ji yana gani
gidan Baba Abbakar ya koma yanda yake don dai
yayi har ya gaji, sai dai shifa duk wani abu na
tsawatarwa yana musu dan haka shi kadai suke
shakka a rayuwarsu, don duk wanda ya doki
Zainabu sai inda karfin Sala ya kare, amman idan
Malam ne sai ta ce, "Sai kiyi hakuri na gaya miki
ki daina zuwa gidansa mana." Shi kam Sadiku ya
sami karatu mai kyau don ya sami makarantar
firamare mai kyau da sakandire, daga nan ya
wuce kwalegin share fagen shiga jami'a, shi kuma
Zaidu da yake bangaren Arabic ya dauka yana
Jami'atu Ummul Qura dake birnin Makkah yana
karantar harshen larabci, wannan shine mafarin
komawar Sadiku gidansu don dai babu abokinsa.
Da kyar da sidin goshi Sala ta bar 'ya'yanta suke
makarantar boko da ta allo don Malam yana fada
ne da kuma Sadiku, sai dai duk da haka Zainabu
ba kullum take zuwa ba sai jefi-jefi. Sai dai da
yake ba karatun ne a gabanta ba sam bata yi,
Zainabu ta taso da hali irin na Babarta don haka
bata da wargi duk wanda ya taba ta sai ta rama,
don dai Sala ta bata ta tun tana yarinyarta, ga
fadan ta baya mutuwa kamar fadan kurma, don
sai tayi wata tana fada sai dai idan iyayen yaran
sun gaji su zo gidan a baiwa Sala hakuri sannan
za ta hakura, idan mutum yafi karfinta ba ta raga
masa don da cizo da yakushi zata kwaci kanta, ko
kuma idan ka doke ta tayi ta jifanku ko duk inda
kuka hadu sai fadan ya tashi. Wannan halin nata
ya sanya duk unguwar kowa yake shakkarta,
abinda ke farantawa Sala rai kenan don takan ce,
Abulata da na kai kararki gwara a kawo mini
wallahi, don haka duk wanda ya taba ki koda
gemunsa yana jan kasa kada ki kyale shi ki rama,
daga nan har ofishin kwamishinan 'yan sanda zan
iya zuwa a kanki Abulata. Don haka har siyan
fada take yi, duk wanda bashi da karfi Zainabu
kan sayi fadan ta casa wanda ake fadan da shi
don akwai ta da karfi, idan kayi gulmarta za ta
sanya a kama ka a tura ka lungun ka-ci-uwaka a
tura maka kashi a baki ko bara-gurbin kwai, don
haka ta addabi kowa a unguwar tasu. Ko fakin
din mota aka yi bai gamshe ta ba sai tayiwa
mutum faci a motar tasa, don haka duk kofar
gidan masu hali na unguwar da an gan ta masu
gadi zasu bita da gudu tana dariya. Idan aka tura
ta makarantar firamare kuwa masu kosai da 'yar
tsala na sadaka take bi da waina wadanda ke
yawo da almajirai mutane na siya suce su raba
wa almajirai sai an fita tara take tafiya
makarantar. Yawo kuwa ko kare ya gan ta ya
kyale, don kullum za ta hada zugar yara suna
shiga karkashin manyan motoci da ke fakin a nan
kan tudu, dan haka duk wanda baiga dan sa ba
yana tare da Zainabu, yawo bola-bola sun iya
shi, gashi babu dama kayi magana sai Sala ta
hau bala'i tana fadin, "Kun ga kada ku sanya
mini diya a gaba, waye Abula ta daurawa igiya a
wuya kowa na ga da kafarsa ya bi ta, don haka
duk matar da ta kara cewa Abula ta ja mata
'ya'ya yawo wallahi sai na dirji bakinta, duk
wacce ba ta son 'ya'yanta su je yawo ta daure a
kofar gida, kurwar Abula kur! Na gaya muku."
Wannan shine kadan daga cikin labarin Zainabu
Abu mai tagwayen suna.
**********Ku ziyarci blog dinmu domin karanta
Littatafai masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ubangiji babu ruwansa yakan bar bawa ya sakata
ya wala ya yi sabo son ransa ba tare da ya matsa
maka ba a duniya, amman abu kalilan zai jarabce
ka dashi duk sai ka gigice ka ga ashe kai din ba
komai bane, ka koma abin tausayi. To, Lallai kam
hakan ce ta faru ga Mustafa, don bai taba zaton
zai shiga ko da kwatankwacin wannan matsalar a
rayuwarsa ba, Allah ya jarabce shi da son
Zainabu wacce ita kuma mahaifiyarsa ta tsana
kamar mutuwarta, Zainabun da ya raina a baya,
sai ga shi son ta yana neman raba shi da duk jin
dadin rayuwarsa, don wacce ta kawo shi duniya
ta yi musu katangar karfe a tsakaninsu. A da can
da suka hana shi auran ta bai damu kamar
yanzu ba, don yaka je gurinta ya kwanta a
kafadarta ta lallashe shi, amman yanzu babu
dama don haka abubuwa suka masa yawa, yanza
haka yana ofis ya hada tagumi da hannuwa biyu-
biyu kamar wani karamin yaro, wani inji aka ce ya
je ya duba amman ya gaza tashi, gashi yafi kowa
iya gyara a sashen nasu, yanda kasan maye haka
yake idan ya sanya gyara a gabansa sai ya ga ya
gyaru, don haka suke ji da shi.Yana nan zaune ya
ji kiran wayarta ya shigo, ya zabura da sauri ya
dauka ya kara a kunnensa. Da kashe murya da
shagwaba ta ce, "Zumana shiru kwana biyu babu
kai babu wayarka, ko Zainabu ta yi laifi ne bata
sani ba?" Ya lumshe idonsa gami da kwanciya
jikin kujera, ransa ya yi fari tas saboda jin muryar
Zainabu kawai da yayi, sai dai ya gaza bude
bakinsa ma balle yace wani abu. Hankalin ta ya
kuma tashi da jin shirun da ya yi mata, ta kuma
duban wayar ta ga lallai a kunne take, da tashin
hankali ta ce, "Mustafa ka ce wani abu mana, ko
dai ka manta da Zainabunka ne?" Hankalinsa ya
kara tashi don jin muryarta kamar za ta yi kuka,
ya daure ya bude bakinsa da kyar ya ce,
"Zainabu baki yi mini komai ba, illah dai
Mahaifiya ta ta kafa mini mummunan sharadi a
kan idan na kuma zuwa inda kike ko duk inda na
san zamu hadu, to lallai ba ta yafe mini ba....."
"Me ka ce Mustafa? Yanzu kana nufin shi kenan
mun rabu har abada? Yanzu yaya zan yi da
sonka a raina Mustafa na? Anya zan iya rayuwa
babu kai, Zumana?" Yayi kokarin jawo dauriya ya
sanyawa ransa ya kwantar da murya da lallashi
ya ce, "Kin ga Zainabu kwantar da hankalinki, ni
din naki ne har abada ba zan iya rabuwa da son
ki ba, sai dai dole zanyi biyayya ga maganar
Mahaifiyata don ina son na rabauta duniya da
lahira, na yi miki alkawari ni naki ne har abada,
sai mu cigaba da addu'a komai ya zo da sauki,
don ina ji a jikina ke matata ce da zan rayu da ita
cikin ni'ima da soyayya." Hankalinta ya dan
kwanta ta yi ajiyar zuciya tana fadin, "Zumana
yanzu yaya za muyi kenan? Don na san zan sha
walahar rashin ganinka matuka." Ya lumshe
idanuwansa wadanda yake jin suna masa nauyi
ya ce, "Ki bari zan ga Babana idan ya dawo zan
sanya shi ya lallasar mana Momi din, ina ganin
shi zai tausaya mini idan ya ga halin da nake ciki,
don yafi Momi saukin kai." Ta ce, "Shike nan
zumana, amman zan dinga jinka a waya ko?" Ya
ce, "Dole ne ai Zainabu na kiraki a waya, idan ba
haka ba zuciyata ai bugawa zata yi." Ta yi
murmushi gami da fadin, "Ina sonka matuka
zumana." Ya yi dariya ya ce, "Nima haka Zainabu,
sai dai ina son don Allah ki yi mini alkawarin kin
bar hulda da maza kamar kina ganina, don na
danka miki amanar kanki, ina jin kamar zuciya ta
zata babbake idan na ganki da wani, shin zaki iya
rike mini kanki da alkawari har komai ya lafa?."
Ta yi murmushi gami da fadin, "Mustafa ko da ba
kace ka ba ni amanar kaina ba ba zan iya hulda
da kowanne namiji ba, don kai din kayi mini
yanda ba zan iya kallon kowa da gashi ba, ka
kwantar da hankalinka a yanzu Zainabu taka ce
kai kadai." Da kyar suka iya rabuwa a wayar don
suna ta sanar da kawunansu irin son da suke
yiwa junansu ne kawai. Sai a sannan ya sami
karfin gwiwar da zai iya tunkarar aikin da ke
gabansa, don haka ya shiga dan wani daki ya
sauya kayansa daga na gida zuwa na aiki ya nufi
inda injin da zai gyara yake. Ita kuwa Sala ce a
kanta a tsaye tana rike da kugu jira kawai take ta
kammala amsa wayar, ai kuwa tana ganin ta
gama wayar din ta dirar mata da jaraba. "Yanzu
Abula shi kenan zaki zauna namiji daya tal yana
miki yawo da hankali? Ga wadanda ke son ki
kuma sai wahalar da su kike yi? Yanzu jiya Alhaji
Hayatu Tumbin kudi sai da ya kashe kunyarsa ya
zo ya sameni ya ce don Allah ki fito ko gaisawa
ne ku yi, shi da gaske yake auranki zai yi ma, ya
cake mini dubu hamsin a hannuna ke kuma ya ce
idan kin fita zai baki duk abinda kike so, amman
yarinyar nan kika bada mini kasa a idona, har
mutumin ya gaji da jiranki ya yi zuciya ya tafi, kin
kwallafa ranki a kan shegen mayaudarin yaron
nan, kin ki ki saki zuciyarki ki ci arziki ki bar arziki
a mazauninsa? Wallahi kin bani mamaki Abula
ban taba zaton zaki koma sokuwa a hannun
namiji ba, su da kike juya su kamar waina?."
Zainabu ta dinga duban Sala da mamaki da
takaici da kyar ta iya buda bakinta ta ce, "Sala
kin san So kuwa?" "Ban san shi ba sai ke diyar
zamani, ba kuma na fatan na san shi tunda shi
din masifa ne da jaraba, ki dubi yanda ya maida
mini ke, wallahi da zan gan shi shi So din dana
rade masa kai don Ubansa, tunda ya hana ki ki
zauna lafiya." Ta dafe kirji gami da jingina da
kujera tana fadin, "Sala ki kyale ni kawai tunda
dai kin ce baki san So ba, yanzu haka kirjina ciwo
yake mini, lallai idan na rasa Mustafa na san
mutuwa zan yi don Allah ya jarabce ni da
tsananin son sa, zan iya yin komai don na same
shi Sala, yanzu kam na gane so yana gaba da
kudi da komai, ki rabu dani kawai don na yiwa
Mustafa alkawarin ba zan kuma kula kowa ba zan
yi ta jiransa har ranar da Allah ya sanya iyayansa
suka amince ya aure ni din." Sala tayi Salati tana
tafa hannu tana fadin, "Shike nan an sammace
mini ke Zainabu, don in dai ba asiri ba babu
abinda zai sanya ki gaza hulda da kowa sai shi
kadai, kuma yanzu ba ya nan baya ganinki ba kya
ganinsa ma, amman kin ce ba zaki iya kula kowa
ba, to wallahi ya yi a banza, don ni ma ai ba'a
zaune nake ba, duk neman sa'ar da nake miki a
ce ya tashi a banza, bari na tafi gurin boka na
kan tudu zan sanya ya raba min ku, idan ya so
sai na ga karshen shegen So din, tunda dai shi
ciwon masifa ne." Zainabu ta riko hannun Sala
da ke shirin fita daga dakin nata tana fadin, "Sala
kada ki rabani da Mustafa idan dai ba so kike na
mutu ba, shin wai kin san abinda ya sanya iyayan
Mustafa ma suka hana ni aurensa? To ba wani
abu bane illa yawon da nake yi na bin maza
tamkar karya, kowa ya zo ya dauke ni a mota ya
je yayi abinda ya ga dama da ni kan kudi, sun ce
ni karuwar gida ce, yanzu me ye amfanin irin
rayuwar iskancin da na yi? Ni kam zuciyata ta
gyaru don haka na bar abinda kike so na yi." Sala
ta kuma shiga rudu ta ce, "Ahaf! Kinji ba? Ai na
sani asiri yayi miki, banda asiri ke da bakinki ki
dinga kiran kanki 'yar iska, yanzu kin yarda ke
din 'yar iska ce? Kalmar da da idan aka gaya miki
sai inda karfinki ya kare amman yanzu kike gaya
wa kanki, to ba karuwa ba ko ke mecece kinfi
karfin danta wallahi, idan tace kuma ke karuwa
ce shi dan nata ai karuwi ne tunda dai shine ya
watsa miki rayuwa, sai nayi maganinsu shi da
uwar tasa in dai sunana Sala." Ta warce
hannunta daga rikon da Zainabun tayi mata ta
nufi waje tana cigaba da bala'inta.... To, masu
karatu, mu hadu a littafi na biyu don jin yadda
Sala zata aiwatar da wannan mataki.
Take cewa kar ku damu na dayan tare suka fito
da na biyun,Mai kaunarku da yi muku fatan
alkhairi a kullum: FAUZANKU CE! Mrs Q for Q,
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.co
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login