Showing 3001 words to 6000 words out of 44142 words
Chapter 2 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt
bakin kofa.
Babu ko shayi ta nufi kofar tana taunar cingam
din ta kas-kas, malam Kabiru discipling master
ya dubeta da takaici sanda take shirin shigewa
ko kallonsa ma bata yi ba yace "Ke zo nan."
Babu ko shayi ta nufeshi tana taunar cingam. Ya
dubeta a kufule yace "Ni sa'an Ubanki ne da
zaki tsaya mini?" Ta murguda baki tana kunkuni
taki durkusawa, ya zanbada mata bulala yace
"Kade doron sha-sha-sha."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta murguda baki gami da cigaba da yin
kunkuninta ta durkusa "Me kike cewa?" "Uwarka
nace" Ta fada a hankali, da motsin bakin ta yaso
ya fahimci abinda tace yace "me kika ce?," Tace
"Ni fa bance komai ba malam." Yayi ajiyar
zuciya kana yace "Mai yasa ke kullum sai kinyi
latti ne eye? Idan baki son makarantar ki daina
zuwa mana sai kace an miki dole, shegiya tun
baki tafasa ba zaki kone, kina aji daya tal amma
kin gallabi kowa, to wallahi idan bakiyi hankali
ba sai an kore ki daga makarantar nan,tunda ta
uwarkace ba?" Ta fadi a hankali, yaso ya juyo
amman bai fahimci abunda tace din ba, don
haka yace "me kike cewa?" Ta dubeshi da
shagwaba "Haba malam ni fa ban ce komai ba."
Yace shikenan tashi kibi 'yan uwanki kuyi tsintar
shara. Ta ce "To shege." Ta fada a hankali,Ta
mike ta nufi inda ta hango dalibai sunbi, sai a
sannan ya hango hijabinta daure a kugunta "Ke!
ke!! ke!!! Zo nan." Ya kuma kwala mata kira
amman tayi banza "Ke! Zainab ba kiranki nake
yi ba?" Ta juya tace "Au ai naji kana cewa ke ne
bansan dani kake ba, gani malam." "Ki cire
hijabin nan ki saka a jikinki." Ta yamutsa fuska
tace "Gaskiya malam zafi nake ji, bazan iya
yafawa ba" Da haushi yace "Idan baki yafa ba
ko zan zaneki a gurin nan." Lallai Malam Kabirun
nan bai san Abu bane, ta murguda baki gami da
dafe kugu da hannu daya tace "Allah ko kasheni
zakayi ba zan yafa ba don zafi nake ji, haka
kawai ba za'a sanya kurajen gumi su futo mini
ba, dan babu mai sai mini magani." Ya hasala
sosai ya nufeta da fushi ya daga bulalar dake
hannunsa zai maka mata, amman ta rike ta
gam tace "Allah malam ba zan yafa ba." Can
wata firifet ta hasala tace "Malam ka barmu da
shegiyar yarinyar nan taurin kai ne da ita bata
da mutunci, kusan kullum haka muke da ita taki
ta daina yin latti," Bata gama mai maganar ba,
ya fisge bulalar daga hannun Abu ya tsula mata,
Ai kuwa sai ta fasa wata uwar kara kana tayi
kansa ta cakumu wuyar babbar rigarsa ta shige
ciki, ya rasa yanda zai yi da ita sai hargowa yake
yi yana fadin "futo don ubanki, kina ina ne?"
Tana ihu ya rasa yanda zaiyi da ita dole ya cire
babbar rigar data makale a jiki ya kalleta da
takaici yace "To tashi kije ki wanke bandakin can
na seniors." Ta wurgar da malum-malun din "ni
gaskiya ba zan wanke kashin wasu garada ba,
haka kawai?" Ya rasa yanda zaiyi da ita, yau
Allah ya hadashi da shegiyar yarinya mara tsoro,
duk yanda ake jin tsoronsa a makarantar banda
ita,ya mike ya nufi Ofis din principal yana fadin
"Yau zaki ci Ubanki wallahi," babu ko shakka ta
bishi wata firifet tace, Zaki ci ubanki yau, za'ayi
maganinki. Ta dalla mata harara tace "banza kiji
da wadannan hakoran naki masu kama da kaca,
"Ke ni kike gayawa haka?" Tayi kanta da bulala,
ita ko ta tsaya kyam tana jiran ta karaso ta huce
a kanta, wata ce ta rike ta tace ke me yayi miki,
Malam Kabiru ya kwala mata kira da yayi nisa,
ta debi littafanta dake hannu ta bishi kamar ba
zata taka kasa ba. Ya shiga Ofis din principal
dake zaune a wata katuwar kujera taci
kwalliyarta ta sha glass dinta, daga ganinta kaga
tsohuwar 'yar boko. "Yaya dai Malam Kabiru
lafiya ne na ganka rai a bace?" Ya sami kujera
ya zauna yana huci yace "Hajiya yau wata
fitinanniyar yarinya ce ta bata mini rai bari ki
ganta." Abu ta shigo Ofis din babu ko sallama ta
dubi principal din tace "Sannu Ma." Bata amsa
ba illa kara gyara glass dinta da tayi tana duban
Abu dake tsaye kerere tace "Kika tsaya mana a
kanmu kamar wasu sa'anninki." A hankali Abu
tace "Da fa?" Sannan ta tsugunna. Malam Kabiru
yace "Kinji ko da kunnenki?, tun dazu wannan
kun-kunin take mini bana jin abunda take cewa,
sai dai ina zaton zagina take yi." Hajiya Kubra
tace "Malam Kabiru sanar dani me ya faru
kwantar da hankalinka." Babu bata lokaci ya
zayyane mata komai tun daga farko har karshe.
Hajiya Kubra ta dubi Abu da harshen nasara
tace mata "Haka ne abinda yace?" Da yake Abu
jaka ce bata iya turanci ba, domin ba zuwa
makarantar takeyi ba sai taga dama, idan tazo
kuma din bata yin komai sai hatsabibanci, don
haka bata iya komai ba, hakan ce ya sanya ta
yiwa shugabar makarantar shiru tana guna-guni.
Shugabar makarantar ta hasala ta doka mata
tsawa gami da kara maimaita mata abinda ta
tambayeta da fari.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Abu tace "Maa nifa bana jin abinda kike fada
gwara kiyi mini da yarena, don ni bana jin
abinda kike fada." Tana wani fisge-fisge take
wannan maganar. Ran Hajiya Kubra ya kuma
baci, don haka ta dinga zagin Abu da turanci,
tana fada mata "Banza jaka, baki san komai ba
sai shegen iskanci da rashin mutunci, a haka
za'a gama karatu ba'a san komai ba sai a kare a
auren dan dako ko dan acaba."Kalma daya Abu
ta fahimta a duk cikin maganar Hajiya Kubra
wacce tace mata "donkey" wato jaka, hakan ne
ya sanya ta fahimci irin cin mutuncin da ake
mata dan haka ta kama guna-guninta tana
fadin "gaki nan babbar jaka, ki dubeki fa tamkar
kayan wanki." "Me kike cewa?" Shugabar ta
tambaya da dacin rai jin Abu na magana kasa-
kasa. Ta murguda baki tace, "Ni fa bance komai
ba." Hajiya Kubra ta dubi Malam Kabiru tace,
"Malan zane mani ita kafin na bata horon da
zan bata tukunna." Duk da gabansa ya fadi dan
yana gudun makalewar da Abu take masa,
amman sai ya daure yayi ta maza ya nufeta da
zabgegiyar dorina. Ai kuwa yanda tayi masa
dazu haka tayi masa yanzu, ta cukwikwiye shi
tana ta zabga ihu, amman babu ko alamar
digon hawaye a idonta, da kyar ya samu yayi
mata guda Uku yana mai da numfashi.Hajiya
Kubra tace "To maza dauki tsintsiya ki share
harabar malamai duka yanzun nan." Ta mike
tana guna-gunin nata tace "Oho dai! Ko yanzu
na wahalar daku,"Me kike cewa?" Ta tambayi
Abun wacce tuni tayi fucewarta, ta kuma duban
Malam Kabiru tana fadin "Lallai yarinyar nan
bata da mutunci, shegiya irinsu ne idan suka
hadu da maza jahilai irinsu suke lakada musu
duka." Shi dai baice komai ba, yayi godiya ya
fuce domin dai Abu ta wuce iyakacin tunaninsa.
Abu tayi zaton abun na wasa ne, sai gashi
wankin hula yana neman ya kaita dare, dan
bata kammala ba har aka fita tara (break),
sannan ta nufi Ofis din shugabar makarantar
(principal) tace "Maa na gama." Ta dubeta a
wulakance tace "Ki yafa hijab dinki, sannan kada
ki kuma yadda a kawo mini kararki Ofis dina,
idan ba haka ba sai na koreki ko kuma kizo da
Baban ki." Abu ta cire hijab din nata ta sanya
wanda daman dan mitsitsine tace "To!" Sannan
ta fice daga Ofis din. Hajiya Kubra tayi kwafa
gami da yin tsaki tana fadin "Dakikiyar banza,
bata san komai ba sai iskanci." Ita kuwa Abu
tana yin nisa daga Ofis din ta cire hijab din
daga kanta ta kuma yin damara dashi sannan ta
nufi ajinsu. Kawayenta ne suka tarota ana ta
ihu suka rungumeta suna mata kirarinta, domin
wadanda abun ya faru a gabansu sun basu
labari, da haka suka karasa aji suna shewa har
aka koma break. Sai dai da zamanta da rashinsa
kusan duk daya ne a ajin, domin dai bata
tambayi abinda akayi ba da bata nan ba,
sannan yanzu ma da malami ya shigo bata tsaya
ta saurareshi ba hirarsu kawai sukeyi da wata
kawarta, kusan sau uku malamin yana
gargadinta akan tayi shiriu amman batayi
shurun ba, har ya gaji dai ya tambayeta kamar
haka "Abu, tell me how many are types of
letter?" Yana nufin ta gaya masa kashe-kashen
wasika. Tayi tsuru-tsuru don bata fahimci
tambayar bama balle tasan amsar da zata
bashi, sai wani murguda baki kawai takeyi tana
guna-guninta. ganin bata da niyyar bada amsar
ne ya sanya ya kuma gargadin ta akan tayi shiru
ta saurareshi, dan darasin turanci yana da
amfani ga dalibai don ta haka ne zasu koyi
yanda zasuyi magana dashi, amman har ya fita
daga ajin nan Abu bata daina surutunta ba sai
dai ta rage murya ba kamar da farko ba.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Da aka tashi ma sai da sukayi fada da
kwandasta domin dai idan da sabo ta saba,
domin dai maimakon ta bashi naira biyar sai ta
bashi naira uku ba kuma don bata dasu ba, a'a
dan dai neman jidali kawai irin nata.
Kwandastan ya dubeta ransa a bace yace "Ke!
Malama cika mana kudin mu saura naira biyu."
Tayi tafi gami da doka cinya tana fadin ba zata
cika ko kwandala ba don haka kudin motar
yake. Nan fa rikici ya rincabe amman Abu ta
kekashe akan ba zata cika ko kwabo ba. Daga
karshe yace wallahi idan bata cika masa ba zai
warci dankwalinta, maimakon ta saduda ina sai
ma ta cigaba da tsiwarta tana tafa hannu,
kawayenta na ta zugata. Abin ya hasala direban
yace masa ya cire dankwalinta tunda bata da
mutunci, dan haka ya cire dan kwalin nata. Sai
dai abu da kwandastan bai sani ba shine tuni
Abu ta gama dana masa tarko, don haka da ta
sauka kafin ya hau motar tace masa "Malam ka
bani dan kwalina." Yace "Na karfi ne, idan kina
son dankwalinki ki cika mini naira
biyu.......Warce gudar Naira ashirin da fellewarta
da gudu ne ya katse masa zancensa, ya saki
baki galala yana kallonta tamkar zata tashi sama
dan gudu, don Allah ya yi mata baiwar gudu.
Direban ya hau masifa sanda ya ankara da
abinda ya faru yana fadin "Banza sakarai, kana
me wannan 'yar mitsitsiyar yarinyar ta warce
kudi a hannunka? ai sai ka shigo mu tafi." 'Yan
cikin motar banda dariya babu abinda suke yi,
shi kuwa cike da jin haushi yake fadin "Haba
Oga baka ga shammata ta tayi ba? An bani
murtala ina shirin bada canji ta fisga ba?"
"Kawai kazo mu tafi, shegiyar ta bamu a can"
Direban ya katse masa magana. Ya dubi inda
Abu tabi ko alamunta baya gani dan akwaita da
gudu tamkar filfilwa, hayaniyar fasinjoji ce ta
sanya shi shiga motar yana fadin "Ai na gane
wallahi duk ranar da Allah ya kuma hadamu sai
taci ubanta." Ya shiga mota har lokacin wasu
fasinjoji suna dariya abinda ya kara kular dashi.
Ita kam Abu tunda ta falla da gudu bata tsaya a
ko'ina ba sai a tsakar gidan su, ta zube a kasa
tana mai da numfashi. Sala dake kwashe wake
da shinkafa ta dago tana dubanta a rude tace
"Yaya dai Maitsada, lafiya kike wannan hakin
kamar wacce tayi tseren gudu?" Sai data
numfasa sannan ta kwashe da dariya harda rike
ciki, duk da Sala bata san ko dariyar me take yi
ba sai ta hau tayata tana fadin "Hatsabibiya,
yanzu haka tsiyar taki kika shuka tunda naga
kina wannan dariyar." Tayi kokarin tsagaita
dariyar sannan ta fara magana "Bari ke dai Sala,
yau wani shege na hadu dashi zai nuna mini
zara bai san na fishi ba....." Ta kwashe duk
abinda ya faru ta sanarwa da Sala din, gami da
karasa zancen da cewar "Shegen kinga ashirin
din dana warto, gobe ma ya kuma."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Sala ta kuma fashewa da dariya tana fadin
"Lallai kinyi maganin dan iska shege, banda
iskanci akan naira biyu sai ya warce miki
dankwali? Da ba'a cin arziki ai da bai sami
kwandastan ba tunda nasan ba motarsa bace,
amman maganinsa kenan kinga ai gobe ya
kuma. Maza tashi ki shiga wanka kada lokaci ya
kure Abulata mai kan alheri, ba irinsu O'o ba
mai kan kwantai Wato tana nufin Karima kanwar
Abun, domin dai ita bata da hali irin na Abun
dan tana jin irin nasihar da Yayansu yake mata,
dan haka ma basa shiri da Sala sam. Ta mike
har lokacin tana haki da dariya ta shiga
bandakin, kwandan wankanta daban ne, dan ita
sabulunta dankwali ne kamar yanda take cewa
giv da dai sauransu, ba irin nasu Karimaba dan
yanka. Bayan ta fito daga wanka aka kuma
zauna zaman kwalliya, Jagira kam da aka jata
har saida ta tabo kunne, ga kuma dige-dige da
aka yi a fuskar ko ina, leben nan kuwa yasha
baki sama da kasa, sannan aka cokala daurin
dan kwali ture kaga tsiya aka fito. Sala nayi
mata kirari ta nada gammo ta dora a kai, akayi
digir-gire da fanteka wacce ke dauke da wake
da shinkafa da robobi a gefe da mai da yaji duk
a kai, sai hannunta data dauki wani bokiti
wanda dashi take wanke kwanukan da sukayi
datti, aka fice babu addu'a sai da kirarinta data
bita dashi, sai da ta fice daga soron sannan Sala
ta bita da sauri ta leka duk rabin jikinta a waje
ta kwala mata kira ta juyo tana guna-guni. Sala
tace "Yi hakuri Abule na dawo dake, na manta
ban tina miki maganar makarantar allo ba kada
jarababben yayanki yaga ba kije ba ya hadani
da malam, wanda yake jin kamar ya jefani a
wuta dan dai nafi karfinsa ne kawai. Don ba dan
jarabar su ba daga bokon har allon daina zuwa
zaki yi tunda dai kin sami na sallah." Ita dai Abu
batace komai ba ta juya ta tafi tana kun-kuni
tana fadin "Kawai daman akan wannan maganar
kika dawo dani, wallahi da na san a kanta ne da
ba zan dawo ba." Sala din kuwa tace "Mai kan
arziki a kukkunga kada a dawo da ko kwalli
daya, na san ki, ai ba kya kwantai." To kawai
tace sannan ta wuce. Kai tsaye tasha ta wuce
tashar kofar Wambai, tana isa kwastomominta
suka yi mata caaa, domin akwaita da araha ga
sakin fuska da tsafta, idan kana so takai maka
har shagonka zata kai maka
Tun karfe hudu saura minti goma abincin nata
ya kare amman sai ta tsaya hira da samari da
wasan jakai da kawayenta 'yan talla. Can ta
hango Rodimasta, wani da take bi kudi tuntini,
ai sai ta cire gyalanta tace dammara dashi tana
fadin "Yau Allah ya kama tsinannan can, wallahi
idan bai bani kudina ba sai nayi masa rashin
mutunci wallahi, dan yau sai anyi bala'i a cikin
tashar nan wallahi." Laraba kawarta ta riketa
tana fadin "Haba Abu yawa ne, ki kyale shi
kawai kin san halinsa dan akuya ne..." Ta fincike
tana fadin "Dalla malama sakeni ai ya san
wadanda yake yiwa akuyancin nasa, ni idan ya
kawo raini ai sai inci (ta kunduma zagi)." Ta isa
gabansa yana shan tabar wiwi sai wani lumshe
ido yake yana rere wakoki kala-kala na gambara
zuwa wakokin 'yan dambe da na barayi, kai
gasu nan dai barkatai. Abu ta rike kugu tana
wani karkada kafa tace "Kai barawo bani kudina,
rannan na zuba maka abinci ka gudu baka bani
kudina ba, to yau Allah ya kama ka, ko ka bani
kudina ko nayi maka rashin mutunci wallahi. Ya
dubeta yana murmushin mugunta yace "Banza
ke wallahi karamar arniya ce, har kin isa kiyi
mini wata barazana, to na cinye na karfi ne ki
kwata." Ta tafa hannu tana fadin "Kan Ubancan,
lallai yau ka tabo ma kanka, yau zan nuna maka
kai karamin dan iska ne, dan ko sama da kasa
zata hade sai ka bani kudina." Ta kama kwalar
rigarsa ta cukwikwiye tana cigaba da bala'i. Shi
kuwa sai dariya yake yana fadin "Yarinya kece
mai aikin yi, in dai nine wallahi mu kwana a
haka." Ya cigaba da zukar wiwinsa yana lumshe
idanu. Jama'a sukayo gurin suna bada hakuri,
Abu tace wallahi ba zata cikashi ba sai ya bata
kudinta idan kuwa ba haka ba zata dauko masa
folis ita kam Laraba da yake matsoraciya ce sai
hakuri take baiwa Abun. Maimakon ta hakura
sai ta doka mata tsawa tana fadin "Dalla can
malama gafara daga nan, Uwarsa ta kauye ce
take bani jari ko ubansa na karkar....." "Ke Abu
don kazanki ni kike zagi?" Rodimasta ya katseta
a hasale dan ya fara kufula da rashin mutuncin
da take masa. Babu tsoro balle fargaba tace "An
zageka din, kai wanene da ba za'a zageka ba
eye?" Ya kuma hasala da zafin rai yake fadin "Ke
wallahi idan baki sakeni ba zan tattakaki a gurin
nan na farfasa miki jiki." Tayi shewa "Ahayye!
wallahi Bismillah dan halak ka fasa, don ka sani
duk mari daya a folissitashan naira dari yake,
don wata kila sai an hada da gonar kauye
sannan za'a biya kudin marin....." "Ke Abu dan
Allah kiyi hakuri ki sake shi, wannan ai ba
mutuncin ki bane kina mace kina fada da
maza."
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Ta kalli mai maganar tana fadin "Kaga Baba mai
taba ina ginin mutuncinka dan kana biyana
kudina ba irin wannan dan bashin ba, dan haka
kawai ka bar gurin nan sai ya biyani kudina zan
sakeshi." "Kinga ya isa sakeshi nawa ne kudin
naki na biya, tunda shima ya rantse ba zai biya
ba dan idan rigimar tayi zafi har mu zaku jawo
wa tunda dai haka 'yan sandan can ke so a fara
fada suzo kame." Ta murguda baki tana fadin
"Ai wallahi nima ba zan sakeshi ba sai dai idan
ka biyani, naira biyar ne dan haka sai ka biya."
Ya dauko naira biyar a aljihun gaba rigarsa yace
"Gata shike nan rigimar ta kare ko?" Ta saki
rigar Rodimasta tana fadin "Banza matsolo
matsiyaci, yau Allah ya rufa maka asiri da yau
kaga karshen rashin mutunci." "Ke! Ya isheki
tunda dai an biyaki kudinki 'yar matsiyata, dan
wallahi kika zageni sai na tattakaki." Ya fadi
yana nunata da yatsansa. Ta tsaya ta rike kugu
tana wani girgiza tana fadin "Wanda bai fasa ba
baya kaunar uwale da ubale..." Laraba ta
janyeta tana fisfisgewa da kyar aka samu ta
kama hada kayanta tana cigaba da bala'i ta bar
tashar. Tana isa gida ta dire fantekat kayan ta
mikawa Sala kudin wacce ke washe baki, ta fada
daki ta kwanta. Sala taji shiru ta leka dakin ta
ganta a kwance ta bude baki da mamaki tace
"Au Abula kwantawa kika yi? Ke da zaki je
makarantar allo? kada jarababban yayanki yazo
ya ishemu da mita." Ta mike gami da daukar
allo ta fice tana kun-kuni. Miskili kafi mahaukaci
ban haushi, Sala ta fada tana dariya. ta dora da
cewar "Abula diyar Salamatu wani lokaci idan
kina shan kunu ko miskilancin naki ya motsa sai
na ganki kamar wata diyar wani sarki, sai da
lallashi Abula ta." Bata dai ce komai ba ta
ficewarta.
Makarantar dake kusa da gidansu, dan
tsakaninsu gida uku ne, koda taje dinma hira ta
kamayi da kawayenta sai da malam din ya doka
musu tsawa sannan suka rude da hayaniya wai
su nan dole karatu sukeyi. Da ya kirawo ta ta
biya allonta kuwa inda-inda ta kama yi, nan fa
ya hauta da fada, tayi kum da baki kamar ba
Abula diyar Sala ba, dan idan akwai wanda take
tsoro da shayi a duniya bai wuce malam da
yayanta ba, dan malam din bai mata ta dadiba
tun tana 'yar mitsitsiyarta kuwa, gashi babu
yanda zasuyi dashi dan shine kamar matsayin
kakanta na gurin Uba, ya kuma maimaita mata
ta karanta kuwa tsaf. Domin dai duk iskancin da
takeyi tana sane don da ace tana maida hankali
akan karatu da mai kokarice ita dan
kwakwalwarta akwaita da saurin rike abu, sai
dai