Showing 1 words to 3000 words out of 44142 words

Chapter 1 - Idan Zuciya Ta Gyaru Book 1 Complete by Fauziyya D Suleiman .txt

28 Dec 2024

1931

Idan zuciya ta gyaru 1-01
Posted by ANaM Dorayi on 07:28 AM, 27-Jan-16
Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU
______________Na
______Fauziyya D Sulaima
19/81992.
"Chalo! Chalo! Chalo!" Zazzakar muryar
hatsabibiyar yarinyar ta fadi, ko ba'ayi bayani
ba kasan abinda kalmar chalo take nufi, wato
tsokanar fada ne da 'yan wani layi ke yiwa wani
layin, ko 'yan wata unguwa zuwa wata unguwar.
Jama'ar dake gefen hanya masu saida rake zuwa
goba, da yalo da doya suka fara hada kayansu,
daya daga cikin su ke fadin, "Kowa ya hada
kayansa don shegiyar yarinyar nan tun da ta
ambaci wannan kalmar ta chalo, to kuwa wanda
yayi sakaci zai yi a..." maganarsa ta tsaya tsak
dai-dai lokacin da ya hango zugarsu sun nufo su
da gudu, sun biyo wasu, ya suri farantinsa
wanda aci bal-bal ke tsakiya na kifi, suma 'yan
uwansa suka rufa masa baya kowa na neman
inda zai adana kayansa. "Chalo! Chalo! Chalo!!!"
Muryar zugar yaran dake biye da Abu suka
cigaba da fadi suna biye da 'yan uwansu
wadanda suka biyo, sukuwa yaran da aka biyo
sai kuma kara gudu suke yi, domin kada a
badesu da barkonon tsohuwar da su Abu ke
wulwulawa. Toka ce ake hadata da citta da
barkono a dake sai a kulle ta a leda a sanya
dutse a tsakiya a sanya zare a dinga wulwula ta,
idan aka cillata daga nesa sai ta fashe kamar an
cillah tiyagas (barkonon tsohuwa), duk mutumin
da ke harabar gurin sai yayi tari ko ya shide,
idan kuwa akaci karo da mai cutar (ASMA) kuwa
sai ta tashi. "A cilla- A cilla." Muryar Abu ta
kuma futowa tana baiwa abokan ta umurni
kenan, dan ganin yaran da suka biyo sunyi
musu nisa, ai kuwa babu bata lokaci suka hau
cillah kullinan tokar dake hannun nasu ji kake
tush! tush! tush! Tana fashewa a tsakiyar yaran
dake neman tsira daga farmakin su Abu,
wadanda Allah ya taimaka sun tsere wadanda
kuma keda rabon shan wuya tokar ta fashe a
tsakiyar su don haka suka fara tari da atishawa,
hatta mutanen dake makota dasu suma sun hau
atishawa, balle maza dake zaune a kofar gidaje
ana hira duk suma sun hau atishawa. Su kuwa
su Abu dariya suka sanya gami da ihu suna
fadin "Eye! Eye! Eye! Munci gari ba namu ba,
munci gari ba namu ba- munci gari ba namu
ba, munzo gidansu mun cisu" Wani mai kanti
dake kokarin zuba kananzir dai-dai lokacin da
abun ya fashe, ya shide kalanzir din ya zube a
kasa ya hasala don haka ya shiga shagonshi da
sauri yana atishawa ya dauko dorina yayi kansu
yana fadin "Shegun yara masu kama da iblisai
ba a sati guda baku bada mana wannan jarabar
ba, wallahi yau duk wanda na kama sai na fasa
masa jikinsa da dorinar nan" Yayi kansu da
gudu, Abu ta fara hangoshi don haka ta kuma
fasa ihu tana fadin "Kowa yayi ta kansa! Nima
nayi ta kaina, kowa ya guje dai, nima na guje
dai, kowa yayi ta kansa." Ko batayi bayani ba
sun san abunda take nufi, wato wani ya taho zai
doke su don haka kowa ya gudu, wai ai kuwa sai
suka kama gudu mai kantin nan ya bisu da
wasu samari biyu, da suma ke cin abinci aka
bude su su da abincin da kura, basuyi nasarar
kama ko daya ba domin yaran sun fisu gudu
tamkar barewu don daman sun san za'a biyo
su. Don sun saba duk randa aka yi biki ko suna
a gidan wasu aka kai musu cingam din fati
akube-kube sai anyi fada, don haka iyaye da
yawa ke hana 'ya'yansu zuwa akube-kube (fati),
yauma haka dince ta faru domin 'yan layinsu
Abu (Hatsabibiya ce) ta gayyaci akube-kube (fati)
tofa shine wani dan bayan layin nasu ya
warcewa 'yar layin..
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
yauma haka dince ta faru domin 'yar layinsu
Abu (hatsabibiya ce) ta gayyaci akube-kube (fati)
tofa shine wani dan bayan layin nasu ya
warcewa 'yar layin su kwanonta na akube-kube
lokacin da suke tsaka da rera wakar akube-kube
sai walo, munje mun dawo sai walo, sannunku
da zuwa sai walo, ga kwanan fati sai walo. Tofa
shine Abu tace a futo da kwanon suka kiya
shine fa fada ya harke ana ta karawa sannan
aka bada oda a dauko bom, shine fa aka biyo
'yan bayan layi. A bakin wata makarantar boko
suka dinga zubewa suna haki don sun san sun
tserewa wadanda suka biyo su. Sai tillikar dariya
sukeyi suna mai da yanda akayi. Abu ta fito da
kifi a hannunta soyayye tace, banzaye nifa mai
kifin nan da yake gudu sai dana suri kifi daya
wanda ya fado, nan fa kowa yayi karaf yace
raba dai-dai (wato wata sarace ake kullawa idan
kuka kulla raba dai-dai to da kaga mutum yana
cin abu idan ka riga shi fadin raba dai-dai to sai
ya raba biyu ya baka idan shima yaga kana ci
yace maka haka to sai ka bashi kaima, idan
kuma mai cin abin ne ya riga fadin bazai bada
ba). Abu ta sha kunu tace "Dallacan wa zan
baiwa wa zan hana" Ta bare ta cire kayar ta
lunkuma a bakinta tana muzurai, kowa ya tsaya
yana kallonta don dai ita masifaffiyace tsoronta
ake ji, wani yaro ne a cikinsu yayi karfin hali
yace "Gaskiya mu kwance ke Abun nan." Ya
mika mata hannu "Idan kece kika ga mutum
yana ci kika ce raba dai-dai idan bai baki ba
warta kike yi, amma idan kece sai kiki badawa."
Ta cire dankwalinta taci dammara dashi tace
"Anyi din, duk wanda ya isa ya kwata wallahi"
Habu yace "Banza ai ba tsoronki ake ji ba, daga
yau mun kwance nima." "La-la-la, ni kake zagi
wallahi ba zan yadda ba." Ta danki kasa a
hannu biyu ta matsa gabansa tace "Gata tsiya
gata arziki." Ya tankwabe ta tsiyar ai kuwa sai ta
rarumeshi, nan fa dambe ya kaure sauran yaran
suka rude da ihu eyeh-eyeh-eyeh, sannu suna
musu wata waka, "Ku chasu arna ku chasu, ku
chasu ba mai raba ku, wanda ya raba su shi
yayi barna, kai ku chasu arna ku chasu, ku
chasu ba mai rabaku." Su kuma tamkar ana
kara zugasu sai dambe suke yi, da yake Abu
'yar dama-dama ce mai kiba gata da karfi da
karfin zuciya ta daga Habu ta naka shi da kasa,
aka kuma rudewa da ihu da kyar aka janye ta
daga kanshi tana fadin "Wallahi da kun barni
yau da sai na chas-chas karashi." Shi kuwa ihun
da ake masa ya sanya ya fashe da kuka yayi
hanyar gida, suma saura suka bishi ana masa
ihu, ita kuma Abu sai kuma masifa takeyi tana
tafa hannuwa tana fadin "wallahi mutum yaje
ya fada a gidansu wanshi yazo ya tabani gobe
nima na zane shi." Sauran 'yan fadan ta suna ta
zugata tana dariya, a haka suka isa kowa ya nufi
gidansu, Abu tace "Bari naje na dauko gyada ta
na kasa wallahi kuma naji yaro ya zageni ya
sani." Ta shiga gidansu har lokacin da
damararta, Babarta dake zaune wacce asalin
sunanta Salamatu ne suke ce mata Sala tace
"Yauwa 'yar albarka yanzu nake tunaninki tun
da kuka tafi akube-kube baku dawo ba." Ta
fashe da dariya tace yau na gaya miki Sala
wallahi na chas kara yaron nan Habu, daman ya
raina ni har kuka na saka shi wallahi ya tafi
gidansu yana ta kuka. Sala ta fashe da dariya
tace "Yata giwar mata, wanda ya tabaki ya tabo
ramin zuma, bana son sanya ki cigaba da chasa
duk wanda ya kawo miki wargi ni na saka ki."
Tayi dariya tana gyara kashin gyadar tata tace
"Ta nawa ce Sala?" Tayi dariya tace "Haba
maitsada (Sunan da take kiranta dashi kenan) ai
ke ba sai an kirga miki ba, ke ai me kan arziki
ce yanzu zaki dawo nasan kudina ba zasu bata
ba sai dai ma su karu, dauki kawai kije da dai
Karimatu ce mai kan kwantai (kanwar Abu ce)"
Abu tayi dariya gami da daukar farantin wanda
aci bal-bal ke tsakiyarsa tayi waje da kujerar
zamanta.
Can hanyar 'yar kasuwa ta nufa inda masu lemo
da agwaluma da rake ke saidawa, tun da ta fito
aka karbi kujerar wata kawarta Laraba, suka tafi
suna tafe suna hirarsu akan fadan da suka yi da
Habu, da kuma chalon su. Sanda ta isa bakin
'yar kasuwa ta ajiye farantin ta, samari suka
fara zagayeta kowa ya dauki gwangwani guda
yana ci ana hira, rabin hirar duk batsa ce,
amma da yake Abu ta saba jin irin wannan hirar
sam bata damu ba, sai dai ta sheke da dariya
tace shege wane, can wani Rosi yace "Ke ai
wallahi Abu har yanzu baki waye ba, ki duba ko
kwana bakiyi a waje kullum kina gida." Ta mike
tsaye tace "Kan Uban can, har zaka ce ban waye
ba, don Allah dubeka Rosi din nan kaifa wallahi
tsami ne, don dai yayana jarababbe ne wallahi
da nima kwana zan dinga yi kamar Laraba ko
yaya kikace kawas?" Ta bawa Laraba hannu suka
tafa
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
. Mudi Niga yace "A'a ba wani Laraba taso muje
muyi zancen mu bayan makaranta kada 'yan sa
ido su ganmu." Abu ta tabe baki tace "Wallahi
nima don jarababben yayana ya saka min ido
ne, yanzu da an ganni za'a gaya masa yaci
ubana, wallahi da nima acan zan dinga zancen,
amma zan yi maganinsa." Su Laraba dai suka
mike suka tafi ita kuma suka cigaba da hira da
su Rosi. Karfe goma da rabi sannan ta dauko
kayan tallarta tana ta mita a fili "Banza su Rosi
din nan shiyasa bana sakar musu fuska, da
Kwage ne ko Damisa ai da tuni sunyi mini juye
mtss!" Taja tsaki, yanzu da kwantai zan koma
gida? bari dai na biya gurin dan Oga dan nasan
shi dole ne kila ya siye yanzu. Ta nufi chemist
din nasa da fitilar kwai a bisa tebur, yana zaune
a bisa kujera mai kama da tsohon soja, babu ko
sallama ta bankade dan yalolon farin yadin dake
kofar da sunan labule ta shiga tana fadin dan
oga kana nan baka tashi ba? Ya mike cike da
murna yace Wow! Habu yanzu kana rena wallahi
ina son ka da gani (cikin gurbatacciyar muryarsa
yake mata magana) ita kuwa ta ajiye gyadar
bisa wannan tsohon tebur din ta hure aci bal-
bal din tace "Daman zan biyo yanzu ga gyadar
zaka siya duka ko?" Ya matsa jikinta yana cewa
"Habu Habu, wallahi kana da cho, ina ta sonka
da yawa, amman zaka kwana anan ko?" Ta zaro
ido waje tace "Kaifa baka da hankali wani
lokacin, idan na kwana a gurin ka nace me a
gida....." Ya jawo ta jikinsa yana mata abinda ya
saba duk da ba gamsuwa yake yi ba, domin dai
lalubeta yakeyi, don taki amince masa dari bisa
dari sai dai yayi abinda ya samu (Allah ya
shirya, jama'a ku duba diya mace ta futa har
zuwa wannan lokacin uwarta bata neme ta ba,
tur da irin wannan Uwa). .
…Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
Can tace "Malam na gaji zan tafi kada
jarababban can ya biyo sahuna don ma nasan
Sala zata kareni sallameni na tafi." Ya mike yana
gyara riga yace "Habu-Habu, wallahi yarinyar
nan baka da cho kina yawo da akalina, amman
zan rama ne." Tayi dariya tana fadin "Dan oga
kenan." Ya miko mata Nairori har na Naira
ashirin tace "La-la nagode." Ta sunkuci farantin
gyadar ta fuce da sauri tana fadin "Duka gyadar
ma ta naira ashirin ce amman ya bani Naira
ashirin" Shi kuwa sai kiran sunanta yake yana
dariya har ta kulewa ganinsa.(Wallahi sai mun
zamo masu taka tsantsan da irin kabilun nan da
suke mu;amala da yaranmu)….Sanda ta isa gida
an turo kofar da tirmi ba'a kulle ba, don haka ta
tura a hankali ta shiga da kullin namanta na
naira daya da ta siyo don kudin dake hannunta
naira ashirin da shida ne ga kuma sauran
gyada. Ta shiga dakin Sala ta taddata abisa leda
tana ta sharara bacci kamar matacciya (Ku duba
irin wannan Rashin tunani, ki tura diyarki talla
tayi dare amma ko damuwa bakiyi ba, bacci ma
kikeyi hankalinki kwance!!) A hankali ta dinga
taba ta tana fadin "Sala! Sala! Sala! Na dawo."
Sala ta mike tana magagin har ta wartsake tace
"Diyar arziki kin saida ko?" Abu tayi hamma
babu ko rufe baki balle salati, sai wani nishi da
tayi hmmmammman har bakin ya rufe da
kanshi, sannan tace na dawo ga kudin nan da
sauran gyadar dai, Sala ta sha kunu tace "Haba
Abu, kince fa a kunga-kunga har ta kare...." Tayi
shiru da zancen da taga ruwan Nairori a
gabanta, ta debo su da sauri tana kirgawa sai
ga naira ashirin har da Uku. Ta washe baki tana
fadin "Diyar albarka lallai kice samuwa kika yi
daga sama, wannan fa shine riba biyu ga kudi
ga sauran gyada, na baiwa Shehu da safe ya
karasata idan kin tafi makaranta, kin siyo
naman? Domin mai nema idan baya ci wata
rana shi za'a tafi nemowa." Abu ta nuna mata
ledar naman ba tare da tace komai ba ta mike,
Sala tace "Gwara dai aje a huta don ai kin gaji
na sani, sai da safe mai tsada." Tace to Allah ya
kaimu. Ta fuce a tsakar gida taci karo da Sadiku
yayanta ya shigo yana huci, ke don Ubanki ina
kika biya naje bakin 'yar kasuwa ban ganki ba
kuma ban dade da barin gidan nan ba? Ta
murguda baki gami da harararsa tace "To ina
ruwanka dani eyeh malam...." "Ke don ubanki
rashin kunya zakiyi mini? To yau idan baki gaya
mini inda kikaje ba wallahi sai na faffasa miki
jikinki." Yayi kanta ai kuwa suka kwasa da gudu
tayi dakin Sala wacce sukayi karo a bakin kofa.
Cikin hargowa da bala'i Sala tace "Malam meye
haka zaka biyo mini diya da gudu salon taje ta
karye ka cuceni? Wallahi yaron nan ka futa daga
idona na rufe kaji ko? Kai waye ne da zaka
matsa mata eye? Ko kai ne uwarta daka haifar
mani ko kuma kai ne Ubanta eye?" Cikin
hargowa take bala'in, ita kuma Abu tana gefe ta
rike kugu tana murguda baki da gatsina fuska.
Ransa ya kuma baci yace "Haba Sala, yaushe
zaki rufe idonki kina ji kuma kina gani Zainabu
ta dinga kaiwa dare a waje kuma idan ance
za'ayi mata fada kice baki yarda ba, yanzu ki
duba agogo karfe sha biyu har da rabi na dare
ace sai yanzu yarinya mace zata dawo gida." "To
Ubana ai sai kazo ka rufeni da duka, nace kazo
ka rufeni da duka!" Ta fadi da hargowa, kana ta
cigaba da cewa "Ina ruwana da wani lokaci ko
karfe dubu na dare zata dawo bai shafeka ba, ai
ba kai ne ka haifar mini ita ba, kuma da kake
cewar neman kudi hauka ne inace kaima nan
kake shigowa kana rara gefe a sammaka abinci,
kato dakai ba don tana nemowa ba zakaci ne?
shi solobiyon Uban naku idan muka daka ta
tashi zamu rayune? tun yaushe ya bar gidan
nan tun asuba ya tsallakemu ya gudu har yanzu
bai shigo ba sai mun kuma wani bacci, to zamu
zauna ne mu mutu idan bamu nema ba?
Wallahi ka fita daga idona ka samawa yarinyar
nan lafiya idan ba haka ba ranka zai baci." Ta
kuma cigaba da masifa.
Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai
masu nishadantarwa
Anamdorayi.mywapblog.com
Kokuma ku kasance taredamu a facebook
https://mbasic.facebook.com/HAUSA-
Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_
ID10%2C737012347
A gidan nan dame zata ji, da tsanar ta da 'yan
unguwa sukayi ko ko da jarabarka, yanzu daga
safiya suwa yanzu kasan nawa ta samu tun safe
kake,zan bata maka rai wallahi." Ya kwantar da
murya duk da ransa a bace yake yace "Sala ki
fahimce ni, ba wai ina yiwa Zainab fada don
bana sonta ba, sai dai a matsayina na
dan'uwanta ba zanso ace ta lalace ba, ki dubi
yanda kowa ya budi baki a unguwar nan
maganarta zaiyi, idan tsokanace itace gaba, Sala
yaushe... Kai rufe mini baki sai kwarara zance
kake babu kwama babu fulsu tof, ratatata
kamar zubar ruwan sama. To tayi din uban wani
ya hana, wato kafi so a dinga koro mini ita da
duka ko? To ban haifi sallamammiya ba, kai
tunda sallamamme ne sai kaje kayi tayi, ta dubi
Abu mai tsada shige daki kici namanki kiyi
kwanciyarki kamar tsumma a randa, naga
shegen da zai kuma takura miki." Abu ta kuma
murguda baki gami da yin gatsine ta shiga cikin
dakin su ita da kannenta duka uku duk matane
ta haye bisa katifarta ta bude namanta tana ci
gami da kunna rediyonta da wani saurayinta ya
bata, wakar lagireto ta fara futowa a hankali.
Itama Sala daki ta shige tabar Sadiku a can
tsaye kamar ya hadiyi zuciya ya mutu yake ji
don takaici, me ake da irin wannan rayuwa ace
kiri-kiri an san gaskiya ake takewa saboda son
duniya? Yaja tsaki yana fadin "Allah ya ganar
daku gaskiya." Ya nufi dakin sa dake soro yayi
fakare cike da tunani, jin kidan dake tasowa a
rediyon Abu yake yi har cikin ransa, don dai
yana shakkar bala'in Sala ne da wallahi sai ya
maka rediyon da kasa uban kowa ma ya huta,
yana nan kwance ya jiyo ta kashe da alamu
bacci zatayi kenan. Ba'afi minti talatin da hakan
ba yaji alamun shigowa, ko ba'a fada masa ba
ya san Babansu ne, ya dubi agogo karfe daya
da minti goma sha tara, yaja tsaki cike da
takaici, yana jinsa ya rufe kofar gidan ya leko ta
tsakanin labule yana kallonsa takalminsa a
hannunsa suke sai sanda yake sadaf-sadaf! Da
haka ya nufi daki, daga inda yake yana jiyo
munsharin Sala da alama bacci yayi awon gaba
da ita, ya saki labulen ya koma ya kwanta yana
tunanin wannan mummunar rayuwa da suke yi
da iyayensu, a haka har bacci barawo yazo ya
sace shi.
Da sassafe ta tashi ta shiga bandaki tayo alwala
tayi sallah, sannan aka jawo kayan kwalliya aka
maka mai, hoda da jan baki wato dai tayi tsaka
tsami kenan. Jagirar nan da aka ja har ta kusa
taba kunne ga jambaki an saka shi an kawo baki
an zagaye saman leben dashi, anyi wani digo a
tsakiyar goshin akayi wani bisa hanci, ga gefen
haba,sannan aka bude adaka aka dauko wata
atamfa 'yar kaduna Nichem, aka sanya aka yafa
gyale a kafada bayan ta daura dan kwali disko,
ta kalli madubi tayi kyau matuka, tayi murmushi
ta futo tsakar gida. Sala dake can kicin tana
suyar funkaso da miya tace "A'a kin shiryo, to
maza a dauka mai kan albarka kada lokacin
makaranta ya kure gashi nan na zuba miki
naki," tace To, kana ta nufi gurin da aka ajiye
mata nata din cikin watan fanteka, da miya a
cikin bokitin fenti, ta dora a kanta su kuma
kannenta suna ta mikawa na kofar gida dake
zaune suna siya. To maza mai kan albarka kada
a dawo da ko guda daya kinji ko? Bata ce komai
ba ta fice da digirgire don gwana ce gurin
daukar kaya a kanta. A hanya suka hadu da
Laraba, itama tana dauke da waina bandashe
mai kuli da mai da albasa) suka tafa kana suka
rankaya bakin tashar 'yan kifi, suna tafe suna
shan hirarsu suna dariya. Karfe takwas da minti
arba'in ta dawo, Sala ta tareta tana cewa
"Yauwa diyar arziki maza sauke ki shirya kada ki
makara, na zuba miki kici ne?" Tace "A'a naci
acan bakin tasha." ta mikawa Sala kudin ta
shige cikin dakin ta sanyo kayan makarantar ta
bulu din uniform da farin hijab, amman bata
sanya hijab din ba sai cin damara dashi tayi ta
rumgume littafai a hannu ta fice. Sala tace "Ga
kudin mota." Tace, "Ina da kudi ki barshi kawai."
"To a dawo lafiya a dawo dai da wuri." Tace to.
Ta fuce da sauri, tana fita ta sami hayis ta haye
aka sauketa a kofar makarantar 'yan mata ta
G.G.S.S Dala. Sanda ta isa ana taron 'yan latti
ko ma nace an gama, don wadanda aka tare din
an tura su cikin makaranta tsintar bola, sai
Discipline master da prefect ne a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login