Showing 99001 words to 102000 words out of 114936 words
Chapter 34 - Cuta Ta Dau Cuta Complete Hausa Novel By Billyn Abdull .txt
miƙa mata wayar tasa ta cigaba da ɗauke-ɗaukenta. Sai yamma lis suka dawo gida a gajiye. Washe gari kuma yace ta shirya zai fara koya mata mota. Jitai kamar ta suma a zaune dan sai da ya taɓata tai firgigit. Muryarta har rawa take ta ce, “Hamma mota fa?”.
Murmushi ya sakar mata mai sanyi, sai kuma a hankali ya kwanto da kansa saman cinyarta. Hannunta ya kamo yasa a ƙirjinsa ya rungume. “Ko jirgi kike son koya zan kai ki a koya miki na sayo miki shi Khadijah. Kin san waye mijinki kuwa. K dai kawai kiyita bani farin ciki wlhy zan zame miki fiye da bawa. Ba koyan mota kawai ba, nan da sati uku zaki fara zana waec ɗinki in sha ALLAHU. Dan ina son ki samu kwalin Sakandire sai mu tattara inamu-inamu mu koma abroad ki cigaba da karatunki har sai kin kammala zamu dawo. In sha ALLAHU sai kin gogema iyayenki hawayen da kika sakasu zubarwa a shekarun baya. Sai kin zama abar kwatance. Yanda mutane da dangi suka dinga jifanki da ALLAH wadai a shekarun baya sai sun koma sanya miki albarka. Yaron nan daya zaluntar min ke sai kin koma kece mai taimakonsa a rayuwa. Fatana ni dai ki zama mai gaskiya, mai amana, mai kuma jajircewa......”
A hankali hawayen da suke kwaranyo mata suka shiga ɗiga a kan fuskarsa. Murmushi ya saki tare da kai hannu ya share mata su. Sai kwai ta rungume kansa ta saki kukan mai ƙarfi. Tashi yay camak ya ɗauketa yay bedroom da kayarsa. Daga haka labarin ya canja salo...
Kamar yanda yay alƙawari ya fara koya mata mota da kansa. Sai dai a wajen koyar motar nan ma babu abinda ake sai shan soyayya ziryan. Komai suna yinsa cike da farin ciki da nishaɗi ne. Cikin sati guda ya fara sakar mata steering. Khadijah mai ƙwazo ce tun acan baya. Kawai taso zubar da damarta ne a dalilin busar shaiɗan data Dafeeq. Sai dai yanzu kam alhmdllh. Lokacin da ta cika sati biyu ai sai dai ace Alhamdullah. Bata motar ake ta fita ita kaɗai ma. Sai dai abinda bata sani ba Abaan na biye da ita a ɓoye. Dan shi dai a tsorace yake. Sai da ya tabbatar komai Alhmdllh sannan ya iya dinga daina binta. A haka ta fara exam. Abinka da makarantar masu kuɗi komai ya riga ya mata da kansa, sai abinda ba'a rasaba ne ya kaita ta ƙaƙƙarasa yi kafin farawar, ya kuma dage da koya mata abubuwa shi da Noor. Kai har Mamy ba'a bari a baya ba ta bada tata gudunmawar. A haka dai ta fara jarabawar, cikin amincin ALLAH kuma suka kammala lafiya. Tana cigaba da zuwa ganin doctor duk sati, dan gaskiya zubar mata da ciki da Dafeeq ya dingayi da abinda suka saka mata a jiki yaso mata illa. Amma Alhmdllh da yake akwai kuɗi yanzu kam Abaan ya dage sosai. Sai dai bai taɓa sanar mata abinda Doctor ɗin ya faɗa mata game da matsalar da taso samu ba a mahaifarta. Dan har ɗan ƙaramin aiki sukai mata batare da an warware mata al'amarin kai tsaye ba. Ya kuma gargaɗi likitan akan kada ya taɓa sanar mata komai ya riga ya wuce kawai.
Watansu uku da aure ya ɗauketa suka nufi Kano. Inda ta samu iyayenta cikin ƙoshin lafiya da wadatar zuci. Ga gidansu yasha gyara sosai kamar bashi ba. Babanta na sake samun kulawa ta musamman ashe har Egypt Abaan ya kaisa amma yace kar a faɗa mata. Sai da suka zo ɗin nan ta sani a bakin Jamila. An buɗema Baba ƙaton store na shinkafa a bakin titi. Aiko bawan ALLAH yay fes da shi kamar bashi ba, duk da dai har yanzu yana ɗan tafiya da sanda haka dan ƙafarsa na shagiɗawa. Jitai kima da darajar Abaan da mahaifiyarsa ya sake girma a idonta. Kai ita kam bata san mizata sakakankama mutanen nan da shi ba a rayuwa.
Tururuwa matan anguwa da yara da ƴammata suka dingayi ganinta. Dan tuni anguwa ta ɗauka Khadijah tazo a wata mahaukaciyar mota. Dan tsiyar da Abaan yay musu ita kaɗai ya bari ta shiga anguwar tasu a wata zazzafar mota yace mata zuwa dare zai ƙaraso dan yana da meeting a gidan gwamnati. Aifa ta janyo magana, dan har gidan su Dafeeq aka kai ma mamarsa labari. Sai ta dinga koro mutane da zagin cin mutunci da tsinuwa. Mutane kam nata mata dariya sun maidata mahaikaciya. Alokacin Dafeeq da Ƙainaat na asibiti sun je ganin doctor dan sam bata jin daɗi, cikin na matuƙar wahalar da rayuwarta, gashi a bayan mahaifa, ta kumbura matuƙa babu ƙyan gani. Koda suka dawo kuma dare yayi, Mama ta katsatstsare dan kar Dafeeq yaji labarin Khadijah tazo. Washe gari da asuban fari ta sashi gaba suka tafi wani ƙauye wai amsar magani, sai da tai yanda tai suka kwana acan. Sai washe gari suka dawo a randa su Khadijah suka wuce.........✍️
*_NACE KIN MALLAKI NAKI👋??._*
*_NAKI NAKE NUFI KIN MALLAKA KUWA👋🏻👋??_*
*_TIKITIN SHIGA JIRGIN TAWAGAR ZAFAFAN LITTATAFAN NAN NA ZAFAFA BIYAR NAKE MAGANA SISTER KIN MALLAKA👋👋👋🤔??_*
*_KIN SAN KUWA A WANNAN SHEKARAR TA 2024 TA DABBANCE. IDAN NACE DABAN INA NUFIN DABAN A CIKIN DABAN_*
*_A 2024 ZAFAFA BIYAR ƊIN NAN NAKU SUN SAKE ZUWA MUKU DA WASU SABON SALO NA MUSAMMAN DA ƘAYATARWA AKAN FARASHI KAI SAUƘI DA RAHUSA. DAN HAKA INA GAYA MIKI ƳAR UWA KADA KI BARI AYI TAFIYAR NAN BABU KE_*
_Littatafan sune kamar haka 👇🏻_.
*_KWANKWASON JIMINA....._*
_(NA MSS XOXO)_
*_GUDUN ƘADDARA_*
_( NA SAFIYYA HUGUMA)_
*_TSUSTAR NAMA....._*
_(NA BILYN ABDULL)_
*_AMEENATU_*
_(NA MAMU GEE)_
_Masoya ina ƙara gaya muku kada ku bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR ta 2024 babu ku. Dan wannan karon komai fa na musamman ne. Sabuwar Shekara, sabon zubi da babu irinsa._
_GUDA DAYA:400_
_BIYU:700_
_UKU:900_
_HUDU: 1200_
_BANK NAME:KEYSTONE_
_BANK ACC NO:6019473875_
_ACC NAME:MUSAA ABDULLAH SAFIYAH_
_ATURA SHEDA ZUWA;09166221261_
__
_IDAN KATI NE KUMA MTN/VTU A BIYA DA TURA SHEDA ZUWA GA:09134848107_
_*Al'ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din*_
*09033181070*
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
_MARABA DA LALE GA MASOYAN ZAFAFA BIYAR💖💯💖ALLAH YA KARA ARZIKI... ZAFAFA BIYAR NAKU NE💃_
🔥🔥🔥🔥🔥🔥💥💥💥💥
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_Shafi na talatin da tara_
Follow this link to join my WhatsApp community: https://chat.whatsapp.com/F7aIYP99bGn9mIqLhjUWKR MUNA SAYAR D KAYAN KITCHEN D FURNITURES N TURKEY D ABAYA AKAN FARASHIN SARI DA CAPSULES MASU KYAU D INGANCI.
___________
........Rayuwa taima ango Abaan daɗi fiye da yanda yay hasashe. Hakama amarya Khadijah dake samun kulawa a garesa da ahalinsa. Idan kaje gidan dolene rayuwar cikinsa ta burgeka musamman yanda kowa ke girmama ɗan uwansa. Tsakanin ango da amarya kam ai ba'a cewa komai. Dan soyayya ce mai tsafta da tarin birgewa, tuni Abaan ya kaɓar da ƴar sauran kunyar Khadijah musamman idan an shiga daga ciki. Yanda soyayyarta tai tasiri garesa haka itama tashi tuni ta mata shigar sauri saboda nagartattun halayensa. Bayan sun dawo Kano ya bar ƙasar. Ya barta da damuwar rashinsa kusa da kaɗaici, sauƙinta ma ta koma zuwa wata babbar islamiyya anan kusa da su. Sashenta kawai masu aiki ke gyarawa, nasa kuwa ita da kanta take wannan aikin batare da jin gajiyawa ko ƙosawa ba kullum duk da baya nan. Takan shiga sashen Mamy susha hirarsu, dan Noor ma tana zuwa aiki. Satinsa biyu ya dawo aka cigaba daga inda aka tsaya. Ita ke tsaye kan hidimar mijinta da safe. Hakama idan lokacin ɗora abincin rana yayi tayi musu da kanta dan in har Abaan na Abuja zuwa ake a amsar masa abincin rana daga gida akai masa office. Dan haka nan ma ta riƙe ragamar girkin rana. Bana safe da rana kawai ba, na daren ma ita ke shirya musu abincin mara nauyi, sannan ta koma sashensu tarbar mijinta duk da in har ya shigo gidan ƙa'idarsa ce sai yazo ya fara gaishe da mahaifiyarsa sannan, hakama idan zai fita sai yazo ya mata bankwana. Idan sun kamala ƴan hidimominsu kamar taimaka masa yay wanka da sauransu zai wuce massalaci har sai anyi isha'i ya dawo. Sukan nufi sashen Mamy ita da shi suyi dinner acan. Daga haka ai zaman hira. Goma nayi Mamy ke korosu, wani lokacin ma tara da rabi tace suje sashensu su ƙarasa hirar acan tagode. Noor kan dinga musu dariya dan su sunfi son ayi hirar anan. Saboda Mamy mace ce data san kanta. Dolene ma idan ka zauna da ita komanta ya dinga birgeka. A koda yaushe cikin gyara Khadijah take batare da Khadijahn ta farga ba. Dan ita dai sai dai kawai a bata abu ace ta shanye ko ta ci. Ita kuma saboda biyayya bazata taɓa tambayar Mamyn minene wannan ba balle ta musa sha kota zargi wani abu. Halayen Khadijahn na sake saka ƙaunarta a zuciyar mijinta da mahaifiyarsa harma da ƙanwarsa ɗaya tilo data zame mata ƙawa a yanzu duk da ta girmeta.
A wannan hali kwanci tashi Khadijah da Abaan suka cika wata goma da aure. Akan samu sassaucin yawan faɗa ko rigima ta ma'auratan zamani, ba komai yasa hakan ba sai kasancewar su su duka biyun masu haƙuri ne. Sannan Abaan ya girmi Khadijah nesa ba kusa ba, takanyi abu da yawa yay masa kallon ƙuruciyace kawai ya share. Wanda kuma ya zama dole yay magana a kansa sai ya zaunar da ita cikin nasiha ya ankarar da ita kaza ba dai-dai bane kazane dai-dai. Hakan da yake na ƙara saka girmansa da kimarsa a wajen Khadijahn, dan takanyi ƙoƙarin ganin ta kiyaye duk abinda zai ɓata masa rai. Takanyi waya da iyayenta a wayarsa, dan ita har yanzu bata da waya, bai siya mataba ba kuma ta taɓa masa magana ko nuna ta damu da son a sai mata ba duk da tana buƙatar hakan. Ko magana yake son yi da ita idan yana office sai dai ya kira wayar Mamy yace ta bata dan yasan da rana suna a tare idan bataje islamiyya ba. Idan kuma zatai waya da ko su Zuhrah ne tashin take amsa kota Mamy ko Noor. Bata taɓa nuna damuwar hakan ba garesa ko waninsa ko taji a ranta ana raina mata wayo. Sai dai ma takan ɗan ji kunyar cewa su ara mata tai wayarne wasu lokutan, koda tana da buƙata sai kawai ta haƙura.
Abinda Khadijah bata sani ba Abaan na gwadata ne kawai, dan Mamy tasha masa faɗan ya saya mata waya sai yace tayi haƙuri zai saya akwai abinda yake yi ne. Mamy tasan halinsa, dan haka ta saka masa ido kawai akan hakan. Dan daga baya itama sai ta fahimci dalilinsa akan ƙin sayen wayar. Ana cikin haka yay tafiya waje ya barta bata jin daɗin jikinta, takuma ƙi yarda suje asibiti, to anan ne fa shima abin ya fara cin ransa. Dan da rana dai yakan kira su Mamy su bata. Da dare kam yana son waya da matar tasa ko zaiji raguwar kewarta da lafiyarta babu dama. Da farko ya fara saka Noor ta bata tata, sai kuma nata saurayin yayta kira, wani lokacin kuma sanda shi zai kira saurayin Noor ya riga ya kira sai hakan ya ƙona masa rai. Ai fa babu arziƙi kwanansa goma sha biyu sai gashi ya dawo. Sam babu wanda yama san da dawowar tasa, dan ita Khadijah ma ranar jikinta ya takura mata ko sashen Mamy bataje hira ba, tadai je ta gaisheta ta dawo sashenta ta kwanta.
Cikin barci sama-sama take jin ƙamshin turarensa na hawar mata kai. Idanunta da sukai matuƙar nauyin barci ta buɗe a hankali. Lumshewa ta sake yi, sai kuma ta sake buɗewa domin tabbatar da shi ɗinne ko mafarkin data saba take yi. Shi ɗinne dai ba mafarkin take ba. Tashi tai da sauri, sai dai mi, ƙamshin turarensa na bugarta a guje ta nufi toilet sai amai. Hankalinsa ya tashi, ya taimaka mata ta gyara jikinta suka fito yana mata faɗan ya akai take barin ƙofa buɗe sauro na shigowa, dan shi zatonsa malleria ce, tunda yaga sanda aka kawota haka taita amai tana zazzaɓi. Ita dai batace da shi komai ba, sai faman toshe hanci ma takeyi.
Karon farko Mamy tazo sashensu tunda Khadijah tazo gidan, itace ta fahimci halin da Khadijahn ke ciki, tai mata tambayar ƙamshin miye bata so. Da ƙyar ta sanar musu turaren jikin Hamma. Idanu sosai ya waro waje, mi Noor zatayi inba dariya ba. Har sai da ya harareta sannan ya miƙe fuuu ya fita shi yaji haushi. Ita kanta Mamy sai da tai murmushi. Koda ya fitan ma Khadijah ta kasa sukuni, dan tace har lokacin tana jin ƙamshin. Dole aka haɗa turaren wuta da yawa Noor ta saka ako ina. Sai da aka ɗauki lokaci ga ac sannan tace ta daina ji, lokacin kuma Mamy ta kira Abaan da tunda ya tafi sashensa bai dawo ba tace yay kiran doctor.
Duk wanda ke a cikin wannan ahali yau kasan yana cike da ɗunbin farin ciki mara misali, dan hatta doctor daya tabbatar da ciki a jikin Khadijah yasha ƙyaututtuka. Tuni Abaan ya rungume Khadijah a gaban Mamy babu ko kunya, turaren ko da tace bata son ƙamshinsa duk da tsadarsa haka ya ɗauka ya bama Awwal shi, yace an bar sakawa. Sai ya koma idan ma zai saka turare sai ta zaɓi wanda ƙamshin yay mata koda shi baya so kuwa. A haka ta cigaba da rainon cikinta da kulawa, dan kowa tattalinta yake kamar ƙwai a cokali a gidan. Batun tafiya karatunta kuwa dole ya tsaya dan boss yace sai ta haihu kuma. Bata damu ba, dan abinda mijinta ke so shi take so itama.
Cikinta na wata shida Ni'ima ta haihu. Da farko dai Abaan yaso ya hana zuwan, amma ta saka masa rigima dan tunda sukai aure zuwanta ɗaya Kano bata sake ba. Sai dai Auta da Jamila sun zo mata hutu sau biyu, yanzu haka ma so take jamilar ta dawo kusa da ita saboda yanayin cikinta. Sai da Mamy tasa baki ya yarda taje jin cewa har Mamy zata je. Haka suka ɗunguma sai Kano ta dabo.
Sun sami tarba ta mutunci da girmamawa. Dan Mama tata roƙon Mamy akan su sauka anan, hakan kuwa akayi. Kasancewar ana gobe suna suka je washe gari tunda safe suka nufi gidan Ni'ima mai jego, inda suka sami itama Zuhrah na fama da nata cikin, dan tsakaninsu da Khadijah kaɗan ne. Babu zato sai ga Abaan, ta dinga harararsa dan bata san zai zo ba. Shiko yana mata dariya ƙasa-ƙasa dan yana tare da su Adams ne da wasu abokansu. Yaro kuma an masa takwara da Abaan ɗin ne. Zokaga murna wajen Khadijah da Abaan. Aiko yaron nan yasha ƙyautuka. Suna ya ƙayatar sosai, Abaan yasa rigimar ranar zai koma da matarsa har sai da Mamy ta tsawatar masa. Aiko yace in dai bazata koma Abuja ranar ba shima bazai koma ba yana nan Kano har sai sanda zasu tafi. Mamy tace yaje ya ƙarata.
Kwanakinsu uku a Kano sukai shirin dawowa Abuja. Kusan sha ɗaya na safe Khadijah ta shirya dan zuwa ta gaida wani kawunsu dake can ƙasan su. Hakan yasa Abaan da yazo yace tazo ya kaita. Dama tare suke da Noor. Tafe suke a mota cike da nishaɗi suna hirarsu. Da wani kalar sauri Abaan ya taka birki dan kaɗan ya rage ya buge wata yamutsatstsiyar mata goye da yarinya a baya ta fito a wani gida a guje da icce a hannu tana ɗura ashar manya-manyan. A harzuƙe ya taka birki, sai dai kafin yay magana sai ga wani mutum shima ya fito da nasa iccen a hannu yana zagin shima na rashin mutunci. Matar ya wulwuloma iccen, saura kaɗan akan Khadijah da ke ta saitinsu tayi zuru tana kallonsu kamar mai son tuna ina ta sonsu.
Tofa, an taɓo abinda Abaan bazai iya haƙuri ba, tuni ya ɓalle murfin mota Noor na take masa baya. Amma mi yana fitowar ya iso gabansu da nufi masifa yaja yay turuss kamar yanda matar nan mai goyo tai tsaiwar sojan badakkare ta zuba masa ido kamar zata suma. Dan namijin har ya ƙaraso gareta zai wanka mata mari sai kuma shima ya tsaya cak jin cikin wata irin murya mai rawa da karkarwa ta ambaci “ABAAN!!”.
Kasa amsa mata Abaan yayi, dan shi ƙoƙarin tuno ina yasan fuskar tata ma yake amma ya kasa. Sai da Khadijah data kasa haƙuri ta fito da sassarfa. Kainaat ta nuna sai kuma ta kalli Dafeeq da ya wani mugun rama yay rakwaf a tsaye kamar wani ɗan shekara arba'in da ɗoriya saboda wahala. Cikin son tabbatarwa ta ce, “Wai da gaske Kainaat da Dafeeq ne?”.
Da sauri Abaan ya kalleta ya ce, “Kainaat kuma Baɗɗo am?! Dama kin santa ne?”.
“Yess Hamma nasanta, ai itace ta auri Dafeeq gashi nan.”
Juyawa yay ya kalli Dafeeq ɗin da jikinsa ke rawa. Dan wani kalar kallon Khadijah yake kamar idanunsa zasu zazzago ƙasa dan tashin hankali da ruɗanin Ganin Khadijahn tamkar wata baƙar balarabiya, ga cikinta ya fito ɗas yay mata ƙyau. Wani shegen kishi ne ya ziyarci zuciyar Abaan. Hannun Khadijah ya kamo ya riƙota jikinsa. Batare da yace komai ba ya nufi mota da ita. Sakata yay, shima ya shiga ya zauna. Hakan yasa itama Noor dakema Kainaat wani kallon ƙyama