Showing 27001 words to 30000 words out of 114936 words
Chapter 10 - Cuta Ta Dau Cuta Complete Hausa Novel By Billyn Abdull .txt
kenan to ita”. Tsaff ya kwashe komai ya sanarma Gwaggo. Murmushi Gwaggo keyi tana kallon JJ. Sai kuma ta kamo hannunsa ta zaunar kusa da ita. “Kaga kwantar da hankalinka Jazool. In dai Anoosh ce da yardar ALLAH ka samu kuwa. Na kuma tayaka murna dan yarinya ce mai tarbiyya da hankali. Sai dai bebiya ce dan bata magana amma tana ji. Tana kuma iya baka amsar da zaka iya fahimta ta motsin laɓɓanta. Zanfi kowa farin ciki da wannan al'amarin kuwa”.
Ba JJ ba hatta su MB kallon Gwaggo suke jin wai Anoosh bebiya ce. Sai dai a cikinsu babu wanda yace komai. Gwaggo da bata lura da yanayin nasu ba ta ɗaga baki ta kira Anoosh dake cikin falo. Kusan mintinan biyu sai gata ta fito tana rabe-raɓe. Fuskar Gwaggo da murmushi ta nuna mata su JJ. “Anoosh waɗan nan ƴaƴana ne, sun zo min gaisuwar salla ne”.
Jin jina kai Anoosh da idanunta ke ƙasa cikin gilashi tayi, sai kuma ta motsa ƙyawawan lips ɗinta a hankali alamar gaisuwa a garesu. Gwaggo ce ta sanar dasu tana gaishesu, cikin rawar lips suka amsa su duka, JJ kam yama kasa sai kallonta da yake kamar idanunsa zasu zubo ƙasa......
____________★
Wani irin shurinta yay da ƙafa tare da cilla mata mayafi yace, “Tashi dan ...” ya mulmula mata ashariya. Ganin bata da niyyar tashi yay wani irin fisgarta tana tirjewa yana janta kamar wata dabba har waje. Kasancewar anguwar babu wuta gashi wata yay nisa ya buɗe motarsa ya cillata baya ya rufe. Gidan ya kulle shima ya zagaya mazaunin driver yaja motar a fisge. Har suka iso katafaren gidan Khadijah na kuka. Maigadi ya wangale musu gate ya shige. Koda ya fito nan ɗin ma janta yay zuwa ciki kamar abar banza, a wani haɗaɗɗen falo ya shigo da ita, ɗaki na farkon shigowa ya buɗe ya cillata ciki ya maida ƙofar ya kulle ya wucewarsa sama abinsa...
Gaba ɗaya kukan da take ya tsaya cak saboda azabar wahalar buguwar da kanta yayi da gado a dalilin wullota da Dafeeq yayi. Tuni goshinta ya fara ɗigar da jini saboda fashewar da yayi. Kwanciya kawai tai yaraf tana sauke wasu irin ajiyar zuciya kamar wadda numfashinta ke barin gangar jikinta. Kafin dogon lokaci jikinta ya ɗime da zazzaɓi mai zafin tsiya. Gab-gab ta fara rawar ɗari saboda ac dake aiki a ɗakin. Tana kwance a cikin wannan wahalar take jin shigowar motoci da guɗe-guɗe alamar yanzu ne ma ake kawo amaryar. Zuwa can taji sun shigo falon. Yanda suke shewa da arerewa yasata fahimtar bama su da yawa ƴan rakkiyar amaryar. Zuwa can taji kiɗa ya fara tashi, sai kuma ta jiyosu suna ihu da shewar ango-ango. Hakan ya tabbatar mata da Dafeeq ne yaje inda suke kenan, da alama ma rawa yake shi da amarya kamar yanda take ji a kalamansu. Kusan awa biyu da wasu mintinan suka ɗauka a gidan, dan sai sha ɗaya taji gidan ya ɗauki shiru. Daga haka bata sake jin motsin kowa ba har dare ya raba tana dai kwance a wajen jinin dake ɗiga a goshinta ya fara rinjayar idanunta alamar jiri...
A ɓangaren amarya Kainaat da ango Dafeeq kam bayan wucewar ƙawayenta su Nadwa cak ya ɗagata daga tsakkiyar falon cikin kuɗin da suka musu liƙi yay sama da ita. Dan Kainaat dai bata da jiki sosai can, amma fa a murjenta take suɓul-duɓul kamar alalar gwangwani. Kai tsaye ɗakinsa ya wuce da ita suna faman sakarma juna murmushi, ya direta a tsakkiyar gadon yana hakki, dan duk da bata da ƙiba tanada nauyi, ƙarfin haline kawai da son ya birgeta ya sashi jurewa har ya kawota nan. Haƙuri ya bata akan bari yaje ya ɗakko wayoyinsu. Ta jinjina masa kai tana murmushi. Gudu-gudu sauri-sauri ya dawo falon, sai da ya waiga bayansa ya tabbatar Hajiya bata biyosa ba sannan ya durƙusa ya tattare dollars ɗin da ƙawayenta suka musu liƙin da ƴan dubu-dubu sabbi ƙal. Taf ya cika hularsa harda dannawa da ƙyar, bakinsa a washe dan yasan waɗan nan kuɗin ba ƙaramin kuɗi bane ba. Wayarsa da tata dake a Centre table ya ɗauka ya koma saman bayan ya kashe fitulin falon da kwasar ledojin kayan sayen baki. Da dabara ya zira hannu daga waje ya kashe wutar ɗakin sannan ya shiga, kai tsaye gaban gadon yaje ya tura hularsa mai ɗauke da kudin nan ƙarƙashin gadon sannan ya ajiye sauran kayan yana ƴar dariya da faɗin wasu maganganu wa hajiyar tashi irin shi ya kashe fitilar ne duk a cikin soyayya. Kainaat bata damu ba, dan itama dai zuciyarta ta tafi wajen tunanin ta yanda zata zille masa ne. Sai da ya gama ɓoye kudinsa da ƙyau ya kunna fitilar...
Anci ansha tsakanin amarya da ango. Sannan ya buƙaci suyi salla. Kai tsaye tace masa tana period. Ƙarara taga damuwa a fuskarsa, a ranta tace shege ai maganinka zanyi, dan daga gani mayen yaro za'ai anan. Suna haɗa ido ta sakar masa murmushi, shima dai mayar mata yayi cikin yaƙe. Jiki babu laka ya tashi ya canja kayansa zuwa na barci, itama yaje ɗakinta ya ɗakko mata. Amsa tai ta shiga bayi ta canja, bata fito ba sai da ta turama Abaan saƙo kamar yanda ta saba a kullum naban haƙuri da good night. Koda ta fito bata kula Dafeeq ba ta kwanta, dan zuciyarta ta tafi wajen Abaan ne kamar yanda ta saba a kowane dare bata iya barci sai da tunaninsa, mafarkinsa shine abin yinta a kullum kuma. Babu zato babu tsammani taji Dafeeq a jikinta, hankalinta ne ya tashi, ta shiga son turesa, amma ya tabbatar mata shifa ko rage zafine sai yayi gaskiya. Bataƙi ba anan, dan koba komai tana kewar abokin rayuwarta, musamman daya kasance ita bata iskanci ko'a yanzun.
Dafeeq shegen yaro ne, dan sai da yay yanda yay ya shagaltar da Kainaat har ya binciketa yaji babu wani period da takeyi batare data fargaba sai jinsa tai yana ƙoƙarin kai hari. Hankalinta ya tashi matuƙa, ta shiga turesa amma ya nuna mata shi sabon jinine, sannan ƙarfi ba'a shekaru yake ba, namiji kuma duk ƙankantarsa dai sunansa namiji...
★ Busowar iskar asuba mai sanyi da ni'ima ta farfaɗo da Khadijah. A hankali ta shiga buɗe idanunta tana karanto addu'a. Ganinta ba'a ɗakinta take ba ya sata maida idanunta ta rumtse komai na dawo mata dalla-dalla. Hawayene suka shiga sakko mata, itafa har yanzu kallon komai take kamar almara. Sannan wani gefe na zuciyarta na tabbatar mata Dafeeq ɗinta baya cikin hayyacinsa. Dole ne matar nan asiri ta masa. Ɗari bisa ɗari ta yarda da wannan tunanin, dan haka ta yinƙura ta tashi da ƙyar. Goshinta ta shafa, jinin ya tsaya, sai dai wajen ya mata nauyi kuma yana mata raɗaɗi. Mikewa tai gaba ɗayanta cikin ƙarfin hali ta nufi bayi. Bata damu da kallon ko'ina ba dan komai baya birgeta a gidan duk da ita kanta tasan ya haɗu. Ta jima tana kallon kanta a madubi kafin ta wanke busashen jinin goshinta zuwa fuska. Ashema raunin da taji ba wani babba bane can sosai. Alwala tayo tazo tai sallar asuba. Daga haka ta jingina da gado ta fara rera kuka, sai da taji kanta na barazanar tarwatsewa sannan ta haƙura. Har rana ta hasko windown ɗakin bataji motsin kowa na gidan ba, ga shi ya kulleta ta baya, dole ta haƙura ta zubama sarautar UBANGIJI ido kawai.......✍️
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_CUTA TA ƊAU CUTA_*
_(Ɓarawo ya saci akwatin maciji)_
_𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻_
_Shafi na goma sha uku_
_ADVERT👇_
_YERWA INCENSE AND MORE : (MASARAUTAR KAYAYYAKIN KAMSHI)_
_INA MA'ABOTA TURARE? KADA KU MANTA SHI FA KAMSHI RAHAMA NE, KUMA TSAFTA CE_
_TSAFTA KUMA TANA CIKIN IMANI… TOH KU MAR-MATSO KUSA_
_MUN KUMA ZUWA DA HAJAR KAYAYYAKIN_
_*YERWA INCENSE AND MORE*_
_DOMIN SAMUN ZAFAFAN TURARUKAN WUTA NA GIDA, KAYA, JIKI, TSUGUNNO, GASHI... AKWAI KHUMRAHS MASU DADI YAN BORNU, CHADI, SUDAN DAMA SENEGAL, AKWAI OIL PERFUMES, DA TURARUWAN MOPPING DANA WANKA DANA WANKI DANA GADO DA KUJERU DA BANDAKI DA DRAWER DA MOTOCI.._
_AKWAI MAN GASHI NA FESAWA ME SA KAMSHI DANA KITSO. AKWAI KAYAYYAKIN KAMSHI DANA GYARAN JIKI SOSAI AKAN FARASHIN SARI KO SAYI DAYA DAYA. •_
_ADIRESHI: KANO.. AMMA SUNA TURA KAYAN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE..._
_INGANCI KYAU RAHUSA DA DADEWA A GIDAH DA KAMSHI SAI KAYAYYAKIN TURAREN YERWA INCENSE AND MORE_
_NAMBAR WAYAR SU: 08095215215, INSTAGRAM/THREADS/TWITTER:yerwaincense_and more_
_YOUR NUMBER ONE STOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS... THEY 'VE GOT YOU AND YOUR HOME COVERED
_____________
.........A ɓangaren amarya da ango kuwa kowa ya tashi da mabanbancin yanayi. Ango na cikin farin ciki da nishaɗi, duk da kuwa ya shaida ya kuma tabbatar da amarya fa batako kama ƙafar Khadijahn sa ba. Dan a daren jiya ya tabbatar da zancen nan na mata sun bambanta. Tunda yake da Khadijah bai taɓa ganin tasha wani magani domin gyara jikinta ba yanda yake jin mata nayi, har bincike yasha mata amma bai taɓa cin karo da komai ba. Amma yarinyar nan ALLAH yay mata baiwa ta musamman da shi kaɗaine yasan wannan sirrin. Amarya kam da fushi ta tashi, duk da ango yayi wasan kura da ita tamkar ba ƙaramin yaron data raina ba taji a ranta Abaan ɗinta daban ne. A lokacin data samu kanta a hannun Dafeeq hawaye taitayi, dan gani take taci amanar Abaan ne. Ta jima tana hawayen kafin barci ya saceta. Basu farka ba sai yanzu da hasken rana ya hasko windown ɗakin. Itace ta fara tashi, ta zubama Dafeeq dake barcinsa hankali kwance ido ƙurr tamkar mai son tantance wani abu a jikinsa. Zuwa can kuma taja siririn tsaki tana ƙoƙarin sauka a gadon caraf taji an riƙe mata hannu. Da sauri ta jiyo, sai ko suka haɗa idanu da Dafeeq. Murmushi ya sakar mata ita kuma ta ɗan kauda kanta. Lips ɗinta dake motsi alamar tana son yin magana ya zubama ido, kamar wanda ya gama karantar abinda take son faɗa ya wani fisgota ta dawo baya. Idanunta ta rumtse da ƙarfi, cikin son sassauta fushinta ta ce, “Ranafa tayi, gashi bamuyi sallan asuba ba”.
Bai tanka mata ba, sai ma shigewa jikinta yay da jan bargo ya rufesu yana magana cikin kunnenta a hankali. Idanu ta waro waje tana turesa a jikinta. Amma ko gezau, sai ma abinda yay niyya ya fara aiwatarwa. Tana ji tana gani sai da yay yanda yake so da ita kafin ya kalleta yana dariya cike da shaƙiyanci. “Hajjaju karfa ki manta sadaki na biya”.
Harara ta zabga masa, a zuciyata tana faɗin (kaji ɗan iskan yaro. Ka biya kona biya maka) kamar yasan mi take faɗa, ya wani lakace mata hanci da faɗin, “Duk da fa ke kika bani na biya ni ne dai na biya a idon kowa”.
“Hummm”.
Tace kawai tana mai yunƙurawa ta tashi, da kallo ya bita harta shige toilet. Jin ta rufo ƙofar harda murza key yay wani kalar kwashewa da dariya. Sauka yay a gadon ya jawo handbag ɗinta mai ƙyau sosai. Tsaff ya bincike jakar, babu komai a ciki sai gold nata da ƴan kunne da sarƙa da su awarwaro data sanyo jiya da dare, ya jima yana kallonsu kafin ya wani taune lips ya maida ya ajiye. Da kansa ya gyara gadon, gamawarsa dai-dai tana fitowa. Baiyi magana ba ya shige bayin. Shima dai wankan yay ya fito, bata ɗakin, ta kuma ɗauke handbag ɗinta. Salla ya gabatar, sannan ya jawo hularsa dake ƙarƙashin gado ya shirya ƙuɗaɗen jiya tsaff ya nufi wadrobe ya ajiyesu a ƙasan kayansa. Cikin ƙananun kaya ya shirya. Kai tsaye ƙasa ya sauka yanata bulala ƙamshi, ɗakin da ya jefa Khadijah jiya ya nufa, yasa key ya buɗe...
Tana zaune a inda tai salla har yanzu, gyangyaɗi take ga hawaye sun bushe mata a fuska. Idanu ya zuba mata na tsawon minti ɗaya. Haka kawai yake jin wani iri a ransa mai kama da tausayi. Da kyar ya ture tunanin gefe dan kuwa duk abinda ya shirya bazai fasa ba. Khadijah tana cikin plans ɗinsa akan mallakar Hajiya da komanta, sannan ita kanta Khadijah yay alƙawarin sai yay punishing nata akan baƙin ciki da hassada da kuma maganganun data gaya masa jiya dan nan gaba ta kiyaye. Saboda shi dai yasan wannan yaƙin da zaiyi sai tafi kowa mora ai.
Saukar mari ya saka Khadijah farkawa a gigice. Yanda take shuri yasa Dafeeq daka mata tsawa. Babu shiri ta nutsu, dan harga ALLAH tana tsoron Dafeeq. Saboda tafi kowa sanin baida mutuncin. Gaidashi ta shiga yi jikinta na mazarin rawa. Bai amsa ba, sai harara daya zuba mata ya juya zai bar ɗakin yana bata umarnin ta biyoshi. Sai da ta share hawayenta sannan ta miƙe ta biyoshi, dan tayi alƙawarin matar nan tasa bazata taɓa ganin kukanta ba, yanda ta ƙwace mata Dafeeq da asiri itama zata ƙwato abinta da addu'a. Babu kowa a katafaren falon, sai ƙamshi mai daɗi da sanyin safiya. Wani banzan kallo yama Khadijah da nuna mata wata hanya. “Ga kitchen, ki haɗama amaryata break fast mai ƙyau da daɗi, awa ɗaya na baki. Bake kina da bakin yimin rashin kunya ba, zaki gane kuranki ne”.
Komai batace masa ba ta raɓa ta gefensa ta wuce. Da kallo ya bita ƙasa-ƙasa harta shige, sai kuma ya kalli inda Hajiya take tsaye tamkar sai yanzu ne ya ganta. Kainaat da tun fitowarsu da ga ɗaki itama take sakkowa ƙasa da mamaki take kallon Dafeeq da shima tun fitowar tasu ya ganta amma ya basar. Kamar bazatace komai ba, sai kuma fuska a yamutse ta ce, “Dafeeq wannan fa?”.
Tasowa yay ya kama hannunta, kamar wata ƴar yarinya ya kawota ya zaunar a cikin kujera. Zama yay shima kusa da ita yana wani kwanta mata a jiki. Idanunsa a lumshe yana shinshinar ƙamshinta ya ce, “Uwargida”.
Idanu ta waro sosai, dan duk da tasan matarsa ance mata yarinya ce batai zaton haka sharaf ba sosai. Dan Khadijah nada ƙaramin jiki, sannan bata cika tsayi ba can. Idan ma baka sani ba bazakace takai 19years ba yanzu. Tana kallon fuskarsa sosai ta ce, “Haba Dafeeq. Yaya zaka saka matarka mana girki. Ni fa ban aureka dan ka wulaƙanta matarka ba, fatana ma mu haɗe kai mu zauna lafiya”.
“Nima burina kenan hajjaju, sai dai ta nuna ita ba haka take buƙata ba. Jiya ban san munafukin daya kai mata hotonki ba na samu bata gida da yammar nan bayan gama ɗaurin aure. Sai bayan magriba ta dawo bata san zata saman a gida ba. Koda na tambayeta ina taje sai cewa tai gidan Baba Hakimi. Na ƙwace jakarta na duba sai ga ƙulle-ƙullen maganin asiri da hotonki da nawa, wai mu zata kai gidan boka ama asiri yarinyar nan”.
Ruɗewa matuƙa Kainaat tayi, dan duk da tasan itama ta taɓa yima Abaan asiri bada kanta taje wajen bokan ba, Mommyn Nadwa ce ta aiki mai aikinta. Kuma tun daga nan bata sake amsar wani maganin tsubbu ba, wancan ma tayi ne dan bata da mafita akan Abaan. A tsorace sosai ta ce, “Na shiga ukuna ni Kainaat wajen boka kuma? Baby dan ALLAH idan da matsala ka sakan kawai nan da sati guda. ALLAH ina masifar tsoron harka da masu asirin nan”.
Wata dariyar ƙeta Dafeeq yay a ransa, dan Kainaat bata san yasan duk manufarta na auren kisan wuta bane ba. A zahiri kam sai ya gimtse fuska kamar zai yi kuka. “Haba-haba Hajjaju daina wannan batu dan ALLAH. Ai ni da ke mutu ka raba takalmin kaza. Sai dai wata ƙaddara kuma amma bata wannan shashashar ba mara aji. Ki barni da ita zan horata a gidan har sai ta zama baiwarki, kema kuma na baki damar sakata duk aikin da kike so dan ki sallami masu aikin gidan nan suje su huta ita zata cigaba dayin komai”.
“Kana ganin babu wani damuwa baby”. Kansa ya jinjina mata da sauri. Ajiyar zuciya ta sauke a zahiri. A baɗini kam zuciyarta ce ke tafarfasa. Bata auresa dan shiga sabgar matarsa ba, balle ma wannan cilikowar da ko autan gidansu ya girmeta, ko shi Dafeeq ɗin sai dai suyi sa'anni da autansu balle ita. Amma kuma dolene kafin ta rabu da Dafeeq ta barma yarinyar nan tarihin ruwa ba sa'an kwando bane ba. Har ita zata kai gidan boka. An faɗa mata zama tazoyi ne. Fitowar Khadijah da tray bayan kamar awa ɗaya yasa Kainaat zuba mata ido, a cikin sakanni ta gama tsara gwada Khadijah taga shin da gaske yarinyar kishi take da ita ɗin....
________★
Gwaggo ita ta shigema JJ gaba wajen mahaifiyar Anoosh, dan kuwa mahaifinta ya rasu. Akwai mutunci da girmama juna tsakanin Hajiya Lailah da Gwaggo. Dan Hajiya Lailah na ɗaukar Gwaggo tamkar uwa a anguwa. Bata huɗɗa da kowa sai ita. Jin JJ nada alaƙa da Gwaggo ta bashi damar neman soyayyar Anoosh. Tare da roƙonsa kar yaci amarta. Ya mata alƙawarin da tabbatar mata sai dai ya zamewa Anoosh garkuwa bawai shi ya kutsama mutuncinta ba. Kalamansa sun tasirantu a zuciyar Hajiya Lailah, dan haka taji ta sake yarda da JJ. Dan kuwa dai da fuskar musulinci yaje gabanta.
Anoosh dai ita kaɗai iyayenta suka haifa. Mahaifinta ya rasu tun tana ƴar shekara bakwai a duniya. Mahaifiyarta Hajiya Lailah ta cigaba da kula da ita da bata tarbiyya duk da ta sake aure. Mahaifin Anoosh ya bar dukiya mai