Showing 27001 words to 30000 words out of 80494 words

Chapter 10 - INSAF BOOK COMPLETE BY Amnah El Yaqoub.doc

12 Sep 2025

45

zai fara jero ma tambaya mezakai da kudi, taqarqari yabaka dubu hamsin kaje ka qarata,kokuma yahau fada shi bayason almubazzaran Ci da kudi saboda bakasan zafin nema ba (>?#?)
yanzu ta wacce hanya ya kamata tayi masa magana Akan suna so Yabasu kudi suje shopping? Minal batada komai, kamata yayi Yabasu ko dubu dari ne, asiyo mata komai da komai tafuto gari ta dinga shiga mai kyau, wata zuciyar tace mata to kode mamy zata fadawa? To ai kuma mamy ma idan taji cewa zatayi Asim din baqonsu ne da bazasu fada masa ba? (>??)
To'ita yanzu Wai ya yazasu yine? Amjad har code din Atm dinsa tasani saboda tsabar yanda yake Bata kudi komai Baja Baja, amma Yaya Asim, hmm inajin ma saudaya tataba ganin nasa Atm card din, Shima ganine daga nesa (=??)
Shi Ala dole Yana tattalin dukiyar insaaf, kuma dacan Bahaka yakeba, tunda aka dauki wannan kudi na insaaf aka bashi, Tofa daganan komai ya canja


Sake Kallan Amina tayi, tayi gyaran murya tace "Am...Minal, ko zaki fadawa Yaya Asim yabamu kudi mutafi shopping ? Tunda Kinga babu abinda mukeyi yanzu, ni wallahi Kinga har fargabar magana nake masa"

Cikin mamaki ta kalli Amrah "to Anty Amrah kema kina fargabar yimasa magana ni kuma dayake bani tsoro mezan iya fada masa?"

Amrah tazaro ido waje tace "tsoro kuma? Tsoron sa kikeyi dama?"

"ni wallahi tsoro yake bani Anty Amrah, tayaya zan'iya tambayar sa kudi? Idan naganshi agabana tsoro yake bani"

Amrah ba tasan lokacin data kwashe da dariya ba, ta kalleta "to ai danaga ke har fira kukeyi Keda shi, shiyasa nafadi haka, amma Bari yafuto Sai na gwada, amma tare zamuje dake"

Ahankali tace "to"



Basu Dade da Gama magana ba yafuto daga dakinsa cikin shirin tafiya wajan aiki,yau shigar manyan Kaya yayi, harda babbar riga,yadine me mutuqar tsada launin Light blue, hular daya Dora akansa tayi masa mutuqar kyau, sajen daya zagaye masa bakinsa yaqara futowa, Hankalinsa Yana kan waya yayi hanyar fita daga falon

Cikin sauri Amrah tace "Yaya ina kwana"

Kallo daya yayi musu yadauke kansa "lafiya"

abinda yafada kenan, daga nan bai qara sauraron suba yafita daga falon

Amrah ta kalli Amina tace "Kinga mutumin damuke jira yayi gaba yabarmu" =?A?

Tace "Tomu hakura kawai Anty Amrah idan yadawo kokuma wata Rana...."

"wacce irin wata Rana?, Toni in banda wajan cin abinci ma bakoda yaushe nake ganinsa ba, kullum Yana aiki kamar computer, tashi mu bishi"

Cikin sanyin jiki tace "to"

Suna fita compound din gidan suka hangeshi yana danna waya kusa motarsa, ga driver nan Yana qarasa goge motar, Sai sheqi take tana daukan ido

Dago kansa yayi ya hangesu suna qarasowa wajansa, shigar jikin Amina ya kalla yaga wannan de atamfar tatace datasa ranar aurenta,daurin dankwalin kanta ya kalla anan ya hango tulun gashin kanta daga gefe, duk yayi wani iri saboda babu gyara, tsaki yasaki cikin ransa, yarinyar nan batason gyara gashin ta, kuma gashin nata yanada tsawo sosai, may be ma tsawon nasa ne yasa yayi mata yawa wajan gyara, yarinya qanqanuwa da wannan uban gashi dama tayaya zata iya gyarawa? dududu batafi a zaunar da'ita ayi mata kwalliya ba =??

Qarasowa wajan sukayi itade ta sunkuyar da kanta qasa taqi dagowa su hada ido
Driver ya dubeshi yace "Yallabai zamu iya tafiya, nagama"

Amrah tayi sauri tace "Yaya..., Dan Allah Yaya ko zaka bamu kudi munaso muje shopping nida Minal"

Qura mata ido yayi Yana kallonta, Yana jira tagama magana

Amrah kuwa tana ganin haka cikin ranta tace shikkenan, dama nasani, yanzu haka dubu hamsin din daya saba zai wullo mana mutafi, danya qara musu wani abun saita cigaba da cewa "kuma Yaya kaga Bata da abubuwa dayawa, duk muna so musiyo, dasu takalma da jaka"

Asim ya sake kallanta yaga Sai abubuwa take jerowa, itama dataga haka saita sake cewa "dasu mayafai, da riga da Wando"

Dauke kansa yayi daga kallonta, yaga alama bazata Dena yimasa lissafi ba, ya maida kallonsa ga Minal yaga kanta Yana qasa tana Jan yatsun hannunta, itada ake maganar saboda ita amma takasa cewa komai, yanzu haka Yana sata yin magana zata fashe masa da wannan shegen kukan nata

Hannunsa yasa ka cikin aljihun wandonsa, Amrah tayi tunanin kudin zai basu harta fara Addu'ah Allah yasa yadebo dayawa (=??)
Saitaga ya miqo mata ATM card dinsa yace

"gashinan,7788 ne cord din, kuciri yanda zai isheku"

Amrah ta hangame baki hannunta riqe da atm card, lokaci daya ta Lula duniyar tunani, eh lalle Sai yau taqara tabbatar wa Yaya Asim Yana ciki (=??)

Shikuma Yana Bata card din yashige Mota, driver Yaja suka tafi, sun danyi tafiya kadan yasa driver ya tsaya, sannan ya sauke glass din motar qasa ya qwala mata Kira "Amrah!!"

Sai alokacin tayi firgigit tadawo daga duniyar tunanin data tafi, cikin sauri ta kalleshi "Na'am Yaya"

"please kubiya ta saloon awanke mata kanta"

Cikin sauri Amrah tace "to Yaya, zamuje ko'ina" =??

Tajuyo ta kalli Amina "muje mu shirya mutafi Minal, ba zamuje da motar gidaba, taxi zamu hau tunda ba waje daya zamuje ba, idan mukaje da Mota itama kaya zata zame mana"

Tace "to Anty Amrah"


Ko awaya daya basu qara agida ba, suka tafi, Kai tsaye Barack sukaje, suka shiga ERENA, Amrah kawai kwasar kaya take tana miqa ATM >?#?
ta lodo mata riga da Wando masu masifar kyau, banda dogayen riguna masu mutuqar kyau da tsada, takalma, jaka, Dan kunne, sarqa, kayan kwalliya, dakuma less daban daban Kala Kala masu kyau da shadda, atamfa ce batada yawa, itade Amina kallonta kawai take, kayan sunyi yawa kamar wanda za'a hada wa wata lefe, ita tsoro ma kasuwar tabata da farko, yanda taga jirgin sama Yana yawo a saman kasuwar

Daga nan sukaje wajan saloon, tsananin mamaki ya kama Amrah dataga yawan gashin da Minal take dashi, tana ganin gashin babu wanda yafado a ranta Sai Anty Ishraqa, har so take wataran tazo gidansu idan zatayi sallah tabude kanta taita kallon gashin

Harta Bude baki zatace amma Minal kede ba bahaushiya bace kawai kuma Sai tayi Shiru, saita ga idan tayi mata maganar kamar cin fuska nema agareta tunda kowa yasan cewa ita din batasan asalinta ba

Harda wankin qafa saida akayi mata, lokaci daya kuwa tafuto fess, Wai ahakan ma Bata fara amfani da mayukan dasuka siya ba

Saida suka kai kayan daya kamata adinka wajan dinqi, sannan suka bashi kudinsa, suka dauki taxi suka tafi gida

Amrah Sai daria take a ranta, kawai hango Yaya Asim take a office yanajin alert, Suda daukan kudi shida karbar alert =??





*** ****** ***




"kamar de yanda bincikenmu ya nuna Alhaji, kaida Hajiya bakuda wata matsala dangane da rashin haihuwa, lafiyarku kalau, kawai Allah ne bai kawo samun Rabon ba, may be Sai zuwa nan gaba, saide kuci gaba da Addu'ah Allah yakawo masu albarka"

El Hameed yamiqawa doctor din hannu tare da yimasa godia, yakai kallonsa ga Ishraqa yaga har idanuwanta sun kawo ruwa

Yace "Habibty tashi muje"

Bata'iya ce masa komai ba ta tashi tafuto daga office din, motar yabude mata ta shige, tana zama kuwa takifa kanta acinyarta tafashe da kuka
Shima zagayawa yayi ya shiga Yaja motar suka dau hanyar gida, kallanta yayi ya maida dubansa kan titi "yanzu Habibty ashe bazaki godewa Allah Akan kyautar da yayi mana abaya ba?, lokacin daya bamu Insaaf roqarsa mukayi? Karki manta wasu mutanan dayawa neman guda d'ayan ma suke amma basu samu ba"

Cikin kuka tace "tomu damuka samu d'in ina take? Ina 'yata take?" tasake rushewa da kuka

Kansa ya Girgiza yace "Ishraqa bake kadai fa kike son Insaaf ba, Nima Ina qaunarta, inaso kisani banida kowa a duniyar nan saiku, bayan ke banida kamarta, muyi Addu'ah idan tana Raye, Allah ya baiyana mana ita, idan kuma Bata Raye Allah yabamu hakurin rashin ta"

"nide 'yata Bata mutu ba, karka sake cemin 'yata ta mutu, zata dawo wajena" (=??)

Shiru yayi bece da'ita komai ba ganin sun qaraso gida, Hon yayi Yana jira megadi yabude musu get amma Shiru da alama baya kusa ne

Adede wannan lokacin aka kawo mutanan kasuwa, d'an taxi ya saukesu da kayansu niqi niqi a hannu

Ishraqa acikin Mota tana kuka taga maigadi bashida niyyar budewa kawai saita Bude murfin motar tafuto, idanunta sunyi jajir kasancewar ta farar balarabiya

Amina tana ganinta tasaki ledar hannunta qasa, faduwar abun da Ishraqa taji ne yasa tajuya ta kalli wajan, idanunta yahadu dana Amina, lokaci daya faduwar gaba ta ziyarcesu


Junansu suka zubawa ido suna Kallan kallo amma babu wanda yayiwa wani magana acikinsu, jikin Ishraqa yayi sanyi, kallon yarinyar take sosai tanaso tasan meyasa gabanta yake faduwa kawai daga haduwar su?

Amina hamdala kawai take a ranta, batasan meyasa ba haka nan taji Allah ya d'ora mata son matar, komai nata birgeta yake, musanman yanda take kwalliya,Anya bazata koyi irin kwalliyar matar nan ba? Ahankali tafara takawa zuwa gare ta, Ishraqa tazuba mata ido, haka itama Amina idonta cikin na Ishqara, ganin da gaske kamar wajan ta zatazo kawai saita Girgiza kanta tawuce cikin gida

Cikin sauri Amina ta miqa hannunta tanaso takira sunan ta amma kuma saide tuni tashige cikin gida, jitayi wani irin baqin ciki ya kamata, ta d'ade tana son ganin matar gashi yau Allah ya had'asu amma kuma batayi mata magana ba, dama hakane, Saikaga Allah yadora ma kaunar mutum aranka, amma shi awajan sa ba Bahaka bane, wata zuciyar tace da'ita, meyasa zakiyi mata magana?inake ina wannan matar? Gwalgwalan da suke hannunta kad'ai ya'isa kasan cewa ba qaramar mace bace, girgiza kanta tayi, afili ta furta "bazai iyu ba"

Daganan tanufi get din gidan, Sai alokacin maigadi yabudewa El Hameed get, kafin yarufe tuni Amina ta fad'a cikin gidan (=??)

Amrah tayi sauri ta kwashi ledojin kayansu tabawa maigadinsu itama tabiyo bayan Amina cikin sauri

Tun kafin El Hameed yafuto daga Mota Amina ta qwalawa Ishraqa Kira

"ANTY ISHRAQA"

Cak ta tsaya awajan datake batare data juyo ba, me kuma wannan yarinyar take nema awajan ta? Kawai daga haduwa saita shigo mata gida? da waye ma yafada mata sunan ta?
Shareta tayi, taci gaba da tafiyar ta batare data juyo ba bare Amina tayi tunanin samun kyakkyawan kallo


Ganin zata shige ta qyaleta ne yasa ta daga muryarta tace "MAMAN INSAAF !!"

Cikin sauri Ishraqa ta juyo, saboda an kirata da sunan datake mutuqar so, d'an sauran kukan data riqe ya qwace mata, Ahankali hawaye ya silalo daga idonta

Amina tana ganin tajuyo ta qarasa wajan ta da sauri, duk da gabanta Yana faduwa bataji tsoron taba, kawai saita bar faduwar gaban nata a matsayin kwarjini da matar tayi mata, dakuma rashin sabo

Kallon idonta tayi cikin in-ina tafara magana "dama.. Nace... Dan Allah... Ko zaki iya rungume ni?"

Amrah tashigo gidan, tana ganin Amina awajan Ishraqa tace "yau Naga takaina"

Tadaga murya takirata "Minal !!"

Amina tana jinta ta qyaleta
El Hameed yana daga gefe Yana kallon ikon Allah, yasan Ishraqa ba zatayi abinda yarinyar tafada ba, musanman yanzu datake cikin bacin rai tsaf zata huce akan yarinyar, amma abinda yaqara bashi mamaki harya Kasa boyewa shine ganin Ishraqa ta meqawa yarinyar hannu

Amina na ganin haka tafada jikinta ta rungume ta sosai, itama Ishraqa jin yarinyar a jikinta saitaji wata irin nutsuwa tana shigar ta, hawaye ya sakko daga idonta, Ahankali tasaka hannu ta rungume Amina, lokaci daya Amina ta lumshe idonta, tana sauke wata irin Ajiyar zuciya









Pls kuyi hakuri da wannan ba yawa



Sharhi please











Amnah El~Yaqoub
' [2/11, 10:41 PM] El~Yaqoub: INSAAF

writing by:Amnah El~


19&20


Like my page on Facebook =?G?
https://m.facebook.com/Amnah-El-Yaqoub-Novel-105487771101493


Tsawon minti uku suka dauka a haka, El Hameed dai yayi Shiru Yana kallansu, ita kanta Ishraqa bazata ce ga dalilin dayasa ta rungume yarinyar ba, Amrah ta qaraso ta janyeta daga jikin Ishraqa, tace "Anty Ishraqa Dan Allah kiyi hakuri"

Ko sake kallon fuskar Amina batayi ba, cikin sanyin jiki ta dagawa Amrah kai, hannun Amina cikin na Amrah suka futo daga gidan, Amma Sai waigowa take tana Kallan Ishraqa, wani dadi yana qaruwa acikin zuciyar ta


El Hameed ya qaraso wajanta Yana mamakin yanda fuskarta tasaki kamar ba'ita ce take kuka ba,yayi Ajiyar zuciya Yana kallon get din nasu bayan fitarsu Amrah "yanzu fa inda ace Insaaf tana nan zata iya kaiwa kamar wannan yarinyar"

Hararar wasa tayi masa "Habibiy yaushe zan iya haifar kamar wannan?, kaduba kaga yarinya budurwa kace zan haifi kamarta?"

"Habibty koda yaushe maida Insaaf baya kike, karfa ki manta last month mukayi mata birthday party na 18 years, saboda haka yarinya de ta girma, ke kuma kin zama tsohuwa" ya qarasa maganar cikin sigar tsokana

Ahankali tad'an daki qirjinsa sannan tad'ora kanta akai, murmushi yayi yasa hannu Yana shafa gadon bayan ta




*** ****** ***



Da daddare gaba dayansu zaune suke afalo, Widad tana cinyar Mamy, Asim yana daga can gefe azaune Yana kallonsu, waya ce a hannunsa Yana dannawa, amma hankalinsa yanakan su, Amrah da Amina suna zaune aqasa kowa Hankalinsa Yana kan kallo, Amrah tana Bawa mamy labarin inda sukaje d'azu dasuka fita kasuwa, saida tayi maganar kasuwa sannan ya tuna da maganar gyaran gashin dayace ayi mata, kallon gashin nata yayi yaga Sai sheqi yake, yakai dubansa zuwaga rigar jikinta, idanunsa sukai arba da nashanunta wanda rigar tabasu haqqinsu na futowa sosai, fuskarta de babu kwalliya, amma tayi kyau sosai, kayan ya karbi jikinta

Widad ta tashi daga cinyar mamy tadawo wajan Amina takama dogon gashinta, tace "laaa kema Ana saka miki gashi irin wanda ake Sawa momy na?"

Mamy tayi dariya tace "Widad Bari mana, kidena ja mata gashi, wannan ba irin na momynki bane"

Sake dago kansa yayi yaga yanda widad take wasa da gashin, Sai hakan yabashi sha'awa yakasa dauke Idonsa akansu, Yana qaunar gashi arayuwarsa, shiyasa ma da Lubna take saka attachment beta6a Hana ta ba

Amrah tace "Ai mamy awajan saloon dinma bakiga yanda ake kallonta ba, saikace gashin Anty Ishraqa"

Mamy tace "eh maman Insaaf ma irinsa ne da'ita, ko anyi mata kitson baya iyuwa, shiyasa kullum take hanyar wajan masu saloon"

Amina tana jinsu batace komai ba saide Dan qaramin murmushi da tayi kawai

Amjad ne ya shigo d'akin bakinsa dauke da sallama, yayi kyau sosai acikin qananun kaya,wasu takardu yabawa Asim sannan yayi wajan mamy yazauna akusa da'ita tare da d'ora kansa Akan kafadarta yace "Mamy nadawo"

Kansa tashafa tace "Sannu Autana, kunyi waya da Daddynku kuwa?"

"eh nakira shi dazu, mun gaisa, yacemin ma yakusa dawowa, mamy Wai kinyi masa maganar sa ranar ne?"

Amina da Amrah da Asim duk suna jinsu, kowa yasan Akan abinda suke magana, amma ita ko kadan ba tasan a kanta ake maganar saka ranar ba

Mamy tace "nayi masa magana, yace abari yadawo tukunna, amma nasan babu wata matsala zai amince, saboda haka kawai kufara shirye shirye kaida yayanku"

Lokaci daya yaji wani irin farin ciki ya lullu6eshi, Wai shine zai auri Minal, shide Allah yadora masa qaunar yarinyar acikin ransa, kallonsa yakai gareta yaga hankalinta Yana kan kallo, haka yadinga jifanta dawani irin kallon soyaiya mai tsayawa a zuciya

Asim ya kallesu shida mamy, ya sake kallon Amjad yaga yanata farin-ciki Sai wani kallo yake mata, girgiza kansa yayi cike da taqaici,maganar zuci yafara, Sai wani rawar jiki yake saboda zai auri bazawara, besan tayi aure harsau shida bane shiyasa yake wannan yarintar, uwa uba ma da yaji cewa duk mazan data aura mutuwa suke dabai fara wannan rawar kafar ba, >?#?
yasan cewa yarinta ce kawai take damun Amjad, shi kam yanason ransa, bazai iya auren mutuwarsa ba, to yarinyar datayi aure shida ma ai ba qaramin namiji ne zai Iya Mata ba, tunda tashiga hannun maza Kala-Kala

Tsintar maganar mamy yayi tana cewa Amjad "kunyi maganar kaida itane, babu wata matsala daga nata bangaren?"

Asim yaqurawa Amjad ido yanaso yaji amsar dazai bayar,Minal d'in ta amince kokuwa

Amjad ya shafa kansa cike da kunya yace "bamuyi magana ba mamy, amma nide a nawa 6angaren babu wata matsala, ko a Yaya take zan'iya auren ta"

Asim yanajin haka ya tashi yabar falon, ya nufi nasa falon, cikin ransa Yana cewa ai shikkenan tunda yaga zai Iya karbar mutuwar >?#?
Wannan ai babu amfanin ma afad'a masa mutuwa ake kokuma bazawara ce, idan sukai auren shida kansa saiya tabbatar waya aura >?7? B&?

Mamy tabishi da kallo cike da mamaki, me hakan yake nufi? >??

Amrah kuwa bayansa tabi da kallo tana dariya qasa-qasa

Mamy ta kalleta tace "Amrah kawowa Amjad abinci"

Saida tad'anyi jimm sannan ta nufi kitchen tana gunguni, saikace wani Babba mamy zata sata ta tashi, bayan itace ya kamata ace ta aikeshi, tana cikin tafiya taji muryarsa yace "AMRAH"

Cikin mamaki ta juyo ta kalleshi, Rabon dataji Amjad yakirata kai tsaye harta manta, zata iya cewa tun suna Yara, cikin masifa tajuyo tana kallonsa, shikuwa wani irin murmushi yasaki Yana shafa sumar kansa sannna yace "ki zuba min d'an kadan"

Abincin ta kawo masa ta dangwarar a gabansa ko zuba masa batayi ba, tawuce dakinsu

Yana zuwa dakinsa abokin sa Muhsin yakira shi, dauka yayi tare da lumshe Idonsa yace "ina jinka"

Daga d'aya bangaren Muhsin yace "Abokina munyi magana da principal din wannan makarantar , yace zata fara zuwa ranar Monday"

Dasauri yabude Idonsa yace "Monday... Jibi kenan fa"

Muhsin yace "akwai damuwa ne?"

"no, da'inaso nayi mata lesson ne kona one week ne kafin tafara zuwa, to bansamu lokaci ba"

"tokai da ina kaga lokaci? da Amjad Kasa ma Aida tuni sunyi Nisa"

"Amjad kuma?"

"to menene dan Amjad din yakoya mata?ko kana kishi ne?"

"A a.... Allah yasawaqe"

Muhsin yayi murmushi yace "Amin, Nima Ina hanya ganinan zuwa gidan naka, ya kamata kayi mata karatun de kafin Monday din ko Yaya ne, Saikaga qoqarinta, kaga daga nan Sai kasan abinda zaka yanke"

"da sonake kawai tazana jarabawan ssce, saina nema mata Admission tatafi University, madecine nakeso tayi, tunda yarinya ce qarama saitai tayin karatun, nasan karatun nata bazai wuce 6 years ba"

Muhsin yanajin wannan qarfin hali na Asim yayi daria, kaiba auren yarinya zakayi ba amma Kaine da tsara mata yanda kakeso, afili yace "kaga gashinan naqaraso gidan, Bari nashigo"

Katse wayar yayi, yakira Amrah, tana dauka yace "turomin yarinyar nan, tataho da littafi da biro"

"yarinya kuma Yaya...? Wacce yarinya?"

Dan qaramin tsaki yayi yace "Minal"

Amrah tadauki littafi da biro takaiwa Minal da suke falo itada mamy da widad, Amjad baya nan, tafada mata saqon Yaya Asim, sannan tajuya Takoma cikin daki

Gabanta ne yafara faduwa haka de ta nufi hanyar d'akin nasa duk jikinta yayi sanyi


Muhsin yadubi Asim bayan ya zauna acikin kujerun falon nasa launin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login